Garkuwa complete novel - Chapter 36
Garkuwa complete novel Chapter 36: Garkuwa complete novel Chapter 36. Cike da jin daɗi Ummi da Aunty Juwairiyya ke cewa. "Kai maraba lale lallai yau munada…
4,424 words
Cike da jin daɗi Ummi da Aunty Juwairiyya ke cewa. "Kai maraba lale lallai yau munada manyan baƙi , oh duniya Yusuf da Aryan kamar ba kuba". Dariya sukayi tare da zama a kujeru. Hibba kuwa tuni ta isa gaban Affan lakace hancinta yayi tare da cewa. "Sakaliyar Umaymah ashe kina nan bana zakiga shagalin sallan Masarautar Joɗa". Cikin sauri ya kalli Shatu dake ce musu. "Sannunku da zuwa". Da sauri ya juyo ya kalli Ummi kana ya kalli Aunty Juwairiyya tare da cewa. "Wannan ce Auntyn nawa amaryar Sheykh Ustaz Malam Dr Jabeer akarmakallu". Murmushi Ummi tai tare da cewa. "Eh itace". Cikin dariya ya kalli Yusuf da Aryan da suke gaisawa da ita yace. "Kan bala'i ashe dama Sheykh Hamma Jabeer yana kallon mata kalli yadda ya zaƙulo zankaɗediyar sarauniya". Yusuf ne ya daki kafaɗarshi tare da cewa. "Kaifa Affan ɗan iskane baka da mutunci, baiyi aureba kace mishi. Shugaban tuzuran Afirka. Yanzu yayi auren kuma zakace yana kallon to dama ce maka akayi shi makaho ne?". Dariya sukayi baki ɗayansu, Aryan ne yace. "Bar Affan da shegiyar surutu". Dariya suka kumayi kana duk suka zauna.
Suka gaisa cikin tsokana Affan ya kalli Shatu dake danna wayarta tana kallon hotunan da sukayi yanzu yace. "Aunty Amarya Hamman namu yana nan ne, ayi mana iso wurin shi mu kwashi gaisuwa". Shiru ta ɗanyi tare da kallon Ummi. Da sauri Hibba tace. "Eh yana nan yanzu ya shiga". Kai ya gyaɗa tare da cewa. "To Aunty Sayyada ayi mana sallama dashi ace ɗaliban shi ne, Affan, Yusuf, Arya,". Cikin tsoron kada Shatu ta kuma zuwa ɗakin abun da ya faru jiya ya sake faruwa Ummi tace. "Ai yana bacci ne yanzu ko". Da sauri Affan yace. "No ba matsala in ance masa Yusuf ne, tashi kice muna sallama dashi." Cikin murmushin jin Yusuf da Aryan sunce. "Eh gsky gwara mu gaidashi kada ya gammu a wurin sukuwa yace bamu nemi izininshi ba". A hankali tace. "To bari a gaya mishi". Ta yunƙura zata tashine Ummi ta riƙe hannunta tare da cewa. "Shatu kadafa". A hankali tacewa Ummi. "Ba komai fa Ummi". Ganin hakane yasa Ummi ta sake mata hannun tare da cewa. "To Allah yasa". Amin Amin Juwairiyya da Hibba sukace. Shi kuwa Affan cewa yayi. "Allah bazaiyi faɗaba in yaji mune". Kai Ummi ta gyaɗa sabida basu san me take tsoron ba.
Ita kuwa Shatu a hankali ta nufi Side ɗinsa.
Su kuwa hirarnsu sukaci gaba dayi a falon.
A hankali ta tura ƙofar falon nashi ta shiga. Shiru babu kowa babu komai sai sautin ac dake tashi fuuuhhh.
A hankali ta lumshe idonta kana cikin sanyi ta nufi ƙofar ɗakin nashi. Tare da cewa. "Salamu alaikum! Salamu alaikum!! Salamu alaikum!!!". Shiru babu motsin komai, hakane yasa a hankali tasa hannun hagun ta dafa ƙirjinta dake bugawa. Kana tasa hannun damanta ta tura ƙofar Bedroom ɗin. Sai kuma gashi ta buɗu ƙofar. Wani sassanyan ajiyan zuciya ta sauƙe jin wani irin masifeffen ƙamshi da sanyi daya ratsa mata jiki da zuciya. Sallama ta kumayi shiru ba amsa. A hankali ta cusa kanta cikin ɗakinta da yake duhu.
Wani irin bugawa ƙirjinta keyi kana. Kanta na sarawa da masifan ƙarfi. A hankali ta juya gefen mashigar ɗakin hannun tasa ta lalubi abin kuna wutan ɗakin danna ɗaya daga ciki tayi, hakan yasa ƙoyin wutan ɗaya mai kalar Sky blue ya kawo wuta. Sanadin hakane ɗakin ya kawo wani irin haske mai ƙayatarwa. Yanayin wutan ɗakin labulayen da kayan jikinta dana jikinshi sukazo iri ɗaya. Juye- juye tayi tare da cewa. "To ina yak". Shiru tayi bata ƙarisa rogowar mgnar ba hangoshi can ƙasa yana konce rigingine yayi pillow'n da tafukan hannunshin.
A hankali tayi taku uku zuwa biyar ta matso kusa dashi cikin sanyin da ya fara yimata yawa ga cikinta dake tsuma a hankali tace. "Salamu alaikum". Ko motsi baiyiba bare tayi zaton zai amsa. Sallama ta kumayi shiru ba amsa. Ganin hakane ta matso a hankali take takun saɗab-saɗab take taka sawunta a hankali har ta isa kusa dashi.
Da sauri ta zubawa ƙafar damanshi ido. Ajiyan zuciya tayi mai sanyi tare da mgnar zuciya. "Uhumm ashe dama yana komciya a ƙasa haka babu shimfiɗan komai ba pillow, da kuma ƙaramar riga da wondo iya guiwa." A hankali ta iso gab da kanshi, Cikin yin numfashi a hankali wai karya jita, ta rusuna ta zauna bisa sawunta irin zaman yin tahiyan salla. Cikin ƙurawa babbar yatsar ƙafar damanshi inda ta rinƙa biyo wannan zanen macijin dake kwance lib a ƙafarshi. Da ido tabi zanen har kan guiwarshi inda iya nan wondon 3 qtr ya rufe. A hankali ta ƙara sunkuyowa ta kurawa wurin ido, tare da mgnar zuciya. "To iya ina wannan zanen tafiyar macijin ya tsaya ne a jikinshi?". Jim kaɗan tayi kana a hankali. Ta miƙa hannunta, cikin sanɗa a hankali hankali tasa yatsunta biyu ta kamo bakin ƙafan wonɗon ta ɗan jawoshi a hankali tayi sama das...!
Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276 in Kuma special Group kikeso wanda a mako biyu ake gaba part 1 kuma abiyu za'a gama Part two da izinin Ubangiji yimin TRANSFER ɗin 1k ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. sai ki turo screenshot shaidar biyanki ta wannan number 09097853276. By *GARKUWAR FULANI*
Cikin sassarfa bisa tsarin addinin yaci gaba da ɗawafin. Yana mai bin bayan tawagar mutanen da yaga fuskar wannan mutumin a cikinsu. Idonshi yaketa karkasawa amman ina ya kasa sake ganinshi. Zuciyarshi nike da mamaki. Haka yaci gaba da ɗawafin. Saida sukayi. Kana suka fito. A hanyarsu ta komawa gidane ya haɗu dasu Jannart da Jazrah da Umaymah da Sitti da kuma Aunty Hafsat ƙanwar Umaymah dake ƙasar Masco. nan Aunty Hafsat tayi ta sayan kayan tsaraba tana bawa Sheykh wai a kaiwa surkarta. Dan dole ya amsa sai kuma Aunty Rahma ƴar autar Sitti itama a gaban Aunty Hafsat ta girma. Kuma sa'ar Sheykh Jabeer ce shiyasa akwai yar tsama a tsakaninsu. Cikin hausarsu data fara basu wuya tace. "Ba dai kayi auren sirri ba, in sha Allah zanzo zamuzo auren Haroon zamuga amaryar, inga surkar tawa ya take"
Taɓe baki yayi tare da cewa. "Ke tafi daga nan da Allah ki bar manya suyi mgna ba irinki ba". Murmushi Umaymah da Aunty Hafsat sukayi dan sun san tsamarsu. Kuma suna masifar shiri. Ammi suke kiranta ita Aunty Rahman.
Jazrah kuwa hakanan take jin daɗi in ta ganshi. Shiyasa taketa murmushi. Haroon kuwa girarshi ya ɗagawa Jannart tare da cewa. "Wai auren ya kusa ko?". Cikin jin kunyar Umaymah tace. "Ban saniba." Haka dai sukaci gaba da tafiya.
Washe gari da safiya. Duk kan al'amur musulmai na duniya suna farin ciki da ranar salla. Manya da yara tsoffi maza da mata duk anata shirin zuwa idi. A dukkan ƙasashen duniya a ko wani saƙon da suke da musulmai.
Hakace ta kasance a ƙasashen Afrika ma. Wanda ciki ƙasar Nigeria yake. Tun daga idar da sallan asuba. Saratu da Larai sukazo. Nan suka samu Ummi da Shatu suna kitchen. Its Ummi fura take kirɓawa mai ɗan karen laushi da ƙamshi yaji sugar. Ita kuwa Shatu dakkeren Couscous tayi, dambu inji hausawa. Bayan sun gamane suka killace shi gefe.
Kana ita Shatu. Ta haɗa kajin nan tayi Pepper Checken mai ɗan karen kyau yaji jajjagen taruhu da al'basa mai yawa ga kayan ɗan-ɗano dana ƙamshi sunji komai yayi maɗau. Su Sara kuwa robobi ta miƙo musu, suka rinƙa mulmula gumbar nan manya manyan mulmulellen masu kyau sai sheƙi da ƙamshi gumbar keyi, dakkeren kuma a robobi Ummi ta rinƙa zubasu. Hibba ce data shigo tare da kuloli a hannunta tace. "Wow Aunty Shatu lallai yau masarautar Joɗa zata amsa sunanta masarautar Fulɓe zata kuma gane an auro mata cikekkiyar ba fulata, gsky tsarin yayi kyau". Cikin jin daɗi Ummi tace. "Gsky nima naji daɗin wannan abu. Dama ace ko wanne yare ranar salla tayi abincin da yarenta keyi ta rabawa maƙota. Hakan zaisa asan cimar juna, kuma yasa aci abincin salla da marmari, amman kayan haushi duk sai a tafi kan shinkafa taliya masa, da dai ire-iresu. Su kuma akeci kullum". Murmushi Shatu tayi tare da cewa. "Ha Ummi ai yanzuma sai nayiwa su Jalal koda dafadukan taliyace, nasan zasuce wannan ai sai mu". Da sauri Hibba tace. "Tab wlh Aunty Shatu karkiyi komai, kinga yanzuma an kawo abincin gidan Barrister Kamal. Ga kuma na gidan Aunty Juwairiyya. Sannan kuma Gimbiya Aminatu ma zata aiko". Cikin sauri tace. "Allah ko Ummi mu huta kawai kenan?". Da sauri tace sosaima. Dan duk yawanci sai an kawo abinci nan wai tunda ke baƙuwace, wannan karamawar masarautar Joɗa akan bago. Kuma koda kin dade ana aikawa juna abincin salla part 2 part". Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa. "Shike nan mu haɗa wannan a kai ko wanne sashin". Ta ƙarishe mgnar tana rufe ƙatuwar Foodflaks ɗin da ta juye Pepper Checken ɗin. Bayan ta ɗebawa sashin Ya Jafar da kuma Lamiɗo da Hajia Mama.
Ƙananan robobin da a ƙalla suma nonon dake cikinsu zai kai kwanon sha ɗaya da rabi ta fara firfitarwa. Kana ta fito da madaidatan ƙoren da zasuci kwanon sha biyu da kaɗan sai manyan da sukaci kwanon sha uku da rabi-rabi. A hankali ta jerasu kan table ɗin dake tsakiyar kitchen ɗin. A hankali ta buɗe ƙwaryar forko dake gabanta. Wani irin murmushi tayi tare da cewa. "Alhamdulillah kunɗirmo ya konta yayi bacci yayi kyau". Leƙowa Ummi tayi tare da buɗe na kusa da ita. Nonon yana konce yayi lib ya daskare yayi fari ƙal-ƙal sai alamun maiƙon man nonon da yayi ɗan yellow-yellow kaɗan. A hankali suka fara bubbuɗe fefeyayen tsakan zaren taburma da aka rufe ƙoren dashi. Gaba ɗaya duk sun konta sunyi kyai Yan madaidai robibin da akasa take ɗauka na fura ɗaya na dakkere ɗaya sai na sugar ɗaya kana da ludayin duma. Sai ta jerasu kan fefeyayen da robobin. Ganin haka yasa Saratu da Laraima suka matso suna taya. Har saida ta jerasu kab. Gwanin sha'awa. Manyan ƙore biyu ta maida cikin Fridge. Kana ta irga sauran tsakanin manya da ƙananan Ƙoren da robobin su Talatin da tara Juyowa tayi ta kalli Ummi tare da cewa. "To Ummi gashi mun gama ki gaya musu duk inda zasu kai. Zasu isar ko". Cikin jin daɗi Ummi tace sosaima kuwa harma da sashin bayi zai isa sabida part-part talatin garemu a cikin masarautar Joɗa. Sai sashin bayi part takwas. Cikin jin gamsuwa da tsarin Shatu tace. "Yanzu a kai ƙore biyu sashin Lamiɗo kana duk manyan iyayen Sheykh akai musu kwarya ɗaɗɗaya, sai sashin Ya Jafar kinga manyan ƙoren sun ƙare sai abin na tsakiyan a kai sauran sashin ƴaƴansu robobin kuma akai sashin bayi".
Haka kuwa akayi su Sara suka fara rabawa. Ita kuwa Ummi ita da kanta da Hibba suka kai na sashin Gimbiya Aminatu. Kana suka dawo da kuloli har uku na abincin sallan da Gimbiya Aminatu ta basu. Kana ɗaya daga cikin tace na Sheykh ne a ajiye mishi. Koda suka dawo samu sukayi su Saratu sun gama rabawa kab. Kamar yadda Ummi ta tsara. Har sun tattare ko ina sun gyara sun share sun goge sun tafi. Zuwa lokacin kuwa gaba ɗaya kan dinning table ɗinsu cike yake da Foodflaks iri da kala abinci kala-kala. Wani irin kallo Shatu tayiwa kulolin kana tayi murmushin da ita kaɗai tasan ma'anarsa ta juya ta nufi tsakiyar falon.
A gaggauce sukayi wonka kowa yayi shirin idi. Ƙarfe tara saura kwata duk suka fito falo. Tuni lokacin kuma liman har ya fara huɗuba. Su Jalal, Jamil Ya Jafar suna tsaye cikin shiga ta al'farma. Karon forko dataga manyan kaya a jikin Jalal. Sai kamanninshi da Hamma Jabeer ɗin nasu ya fito sak-sak kamar an tsaga kara hatta rashin yawan dariyarsu iri ɗaya ne. Sai dai shi Sheykh ko yaushe zakaga lips ɗinshi na motsawa yana tasbihi saɓanin Jalal da zaka ganshi baki a tsuke.
Hibba ce ta fito cikin tarin farin ciki da son Jalal yayi murmushi tare da cewa. "Masha Allah ya Jalal kayi kyau kafisu duka". Ya Jafar dake karatu kamar ko yaushene ya kalli Shatu da Hibba da sukayi shigar atampa iri ɗaya da manyan hijabai har ƙasa ga sallaya da carbi a hannunsu sunyi matuƙar kyau, murmushi yayi musu kana ya juya yayi gaba. Jamil ne yace. "Aunty Shatu sai mun dawo, in munci abinci sai mu sharewa. Oga, Dr, Garkuwa, Malam, akarmakallahu, Sheykh, mijin Sayyada, ɗin ɗakinshi". Dariya sukayi dukansu yadda ya jero masa sunayen nashi. Ummi dake cikin shiga ta al'farma ta miƙa tare da cewa mu tafi.
Suna fita suka rufe ƙofar.
Suka tafi masallacin. Masarautar Joɗa ɗan yin sallan idi. Suna fita su mata sukayi gefen mata su kuwa maza sukayi gefen maza.
Bayan an idar da sallane kuma sai suka zagaya suka shigo ta asalin ƙofar sukayi yadda sunna ta koyar.
Suna dawowa kuwa a falo suka zube nan sukaci suka sha sukayi haniƙan.
A dai-dai lokacin kuma su Sheykh dama sauran al'ummar Annabi duk an sauƙo sallan idi. Suna ɗawafin ban kwana. Sosai Sheykh ke baza ido ko zai sake ganin wancan mutumin amman ina hakan bai samuba.
Koda suka fito daga ɗawafin ban kwana. Kai tsaye gidan Sheykh Abdulkareem suka wuce. Nan yayi musu addu'o'in komawa lfy. Kusan duk baƙin gidan a ranar suka bar gidan. Da su Aunty Hafsat ma ranar suka juya Masco hakama Ibrahim. Koda suka iso Airport kowa da inda ya nufa. A nan Ibrahim ya ruggume Sheykh tare da ɗan dukan bayanshi yace. "In Sha Allah Auren Haroon dani za'ayi". Shima Sheykh ruggumeshi yayi gam-gam tare da cewa. "Allah yasa, ina kewar rashinka a ƙasar mu". Aunty Rahma ne tace. "Kai jirgifa ba jiranku zaiba oga Sheykh". Sakin juna sukayi kana kowa ya nufi inda jirgin ƙasarsa yake.
Bayan duk matafiya sun shiga, jirgin ƙasar Nigeria wanda zai sauƙa jihar Ɓadamaya.
A hankali ya zauna. Ya Hashim na gefenshi. Kasan cewar yana kusa da window ne, ya ɗan juya yana kallon mutanen daketa hada-hadar nufar inda jiragan ƙasar su jihohinsu suke. Can cikin wasu ayarin mutane maza da mata ya hango wannan fuskar da ya gani. Sun nufi can ciki suna tafiya yankin da jiragen ƙasar Cameroon suke. Cikin tarin mamaki ya bishi da kallo tabbas badon jirginsu ya fara ƙugin tashiba da ya fita yaje ya tabbatar da fuskar dattijon da yake hangowa.
A haka dai suka ɓacewa ganinshi. Kana jirginsu ya ɗaga zuwa ƙasarmu ta haihuwa.
Ana gida Nigeria kuwa cikin Jihar Ɓadamaya a Masarautar Joɗa. Zaune suke a falon. Shatu na waya da Junaidu nan yake ce mata, Sun samu sauƙi dukansu. Ance za'a sallamesu bayan salla. Kuma harda ɗinkunan kayan salla akayi musu.
Bayan sun gama waya da shine ta kira Rafi'a. Nan suka gaisa har ta bawa Ummi su gaisa. Bayan ta bawa Ummi wayarne. Jamil ya ɗan kalli agogon hannunshi a hankali ya miƙe tare da kallon Shatu yace. "Muje mu gyara Side din boss kar ya dawo ya samu da datti". Kai ta gyaɗa mishi kana ta amshi wayarta da Ummi ke miƙa mata. tare da ce mata. "Eh dan Allah Shatu tashi maza-maza kuje share wurin da kyau". A hankali ta miƙe tare da cewa. "To." Hibba ce ta bisu a baya. Jamil na gaba ita Shatu'n tana tsakiya. Hibba na bayanta. A haka suka shigo falon. Da komai na ciki yake fes-fes babu wani daddi ko ƙura ko hargitsewa, sabida an share falon safiyar yau, sai ƙamshi da sanyi ke tashi.
A hankali Jamil ya ɗan sa hannunshi tsakanin ziri-zirin igiyoyine masu sarkafe da jeren duwatsu masu sheƙin Daimond dake matsayin labulen Dinning area ɗin shi. Ita dai Shatu ido ta zuba mushi, ganin ya zaro key ɗin a cikinsu. Ƙofar bedroom ɗin ya nufa tare da cewa. "Muje." To sukace kana suka biyo bayanshi. Tana nazarin wurin da suke ajiye key ɗin. Key ɗin ya saka cikin raminshi tare da murzawa.
Da sauri Shatu ta rumtse idanunta. A hankali take jin zuciyarta na harbawa da sauri-sauri. Shi kuwa Jamil tura ƙofar yayi bayan ya murɗa key ɗin ya buɗe. Wani irin masifeffen harbawa da azaban ƙarfi zuciyar Shatu tayi.
Kutsa kai cikin Jamil yayi. Tare dasa hannunshi jikin ginin a hankali ya kunna wutan ɗakin hasken ya gauraye ko ina, jikin window ya wuce ya yaye labulen tare da buɗeglass ɗin. Iskam cikin Garden ɗin dake bayan window wanda ɗawisu yake ciki. Ya buso ɗakin.
Juyowa yayi ya kalli Shatu da ke tsaye bakin ƙofar. "Ku shigo, in nuna miki yadda zakiyi mishi". A hankali Hibba ta ratsa gefenta tare da cewa. "Aunty Shatu mushiga". Ido ta buɗe a hankali tare da bin bayan Hibba da kallo. Kana ta ɗaga ƙafarta da kyar ta. Taka cikin ɗakin, wani irin azabebben sarawa kanta yayi tamkar ana buga mata guduma a tsakiyar kan. Cikin rawan ƙafa ta ɗaga ƙafafuwan ta, Tayi taku huɗu zuwa biyar. Ta kusa isa tsakiyar ɗakin. Kenan. Wani irin jujjuyawa taga kanta nayi. Wasu irin ababe masu ban tsoro ta fara gani suna gilmawa cikin ƙwayar idanunta, shiyasa taketa jujjuya kanta. Ta kalli gabas ta kalli yamma ta kalli kudu ta kalli arewa. Hibba ce ta juyo tana kallonta jin Jamil nata mgna bata bashi amsaba. Cikin sauri ta matso kusa da ita ganin yadda taketa jujjuya kai, ga idanunta da suka juye suka zama kamar harari garke, kana sai Rollin ball eyes ɗin ta take da sauri-sauri. Cikin Mamaki Hibba tace. "Aunty Shatu! Aunty Shatu!!". Shiru ba amsa hakane yasa. Jamil juyo kanshi ya kalli inda suke, da sauri ya juyo gaba ɗaya jikinshi ganin. Wani irin karkarwa da jikin Shatu keyi. Hibba kuwa da ƙarfi cikin tsoro tace. "Aunty Shatu lfy kuwa?". Ita kuwa Shatu, zuwa yanzu bata jinsu bata kuma fahimtar me suke faɗa hankalinta ya juye.
Cikin wani irin layi da rawan jiki tamkar mazari ta nufi tsakiyar ɗakin.
A nan ta tsaya gis gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi. Cikin tsananin tsoro da firgita. "Hibba ta juya a guje tana cewa. "Wayyo Ummi! Ummi!! Ummi!!! Kizo zakiga yadda Aunty Shatu keyi." Ummi dake falo ita da Aunty Juwairiyya, Kamar daga sama suke jiyo muryar Hibba tana rabka musu kira cikin firgici da razani. Haka yasa Ummi da Aunty Juwairiyya miƙewa da sauri suka nufi corridor'n da suke jiyo muryar Hibba na fitowa. Kiciɓis sukayi a bakin ƙofar falon. Cikin sauri Ummi ta ture Hibba ta wuce da gudu ta nufi cikin ɗakin. Sabida jiyo muryar Jamil na cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahuwani'imal wakil. Ummi! Ummi!! Kizoooo". Kusan a tare Ummi da Aunty Juwairiyya suka shigo. "Dai-dai lokacin kuma rawan da jikin Shatu keyi ya tsananta. Wani irin kuka tasa tare da tafiya ƙasa luuu zata faɗi
Kusan a tare Ummi da Aunty Juwairiyya suka tarota. Bisa jikin Ummi ta faɗi hakan yasa itama Ummi tayi ƙasa ta zauna.
Babu abinda suke maimaitawa sai innalillahi wa innailaihi rajiun. A kiɗime cikin tsananin gigita Jamil yace. "Subahanallahi Ummi ta sumafa". Jiki na rawa Aunty Juwairiyya ta juya da gudu babban falon ta fito tare da ɗauko goran ruwan sanyi. Kana ta juyo a da sassarfa ta nufi can.
Hibba kuwa a gigice take gayawa Jalal da Ya Jafar abinda ke faru. Da sauri ya Jafar ya tashi ya nufi can.
Jalal kuwa ya zauna dan ya lura Hibba tayi masifar tsorita.
A ɗakin nashi kuwa, Shiru ta lafe jikin Ummi kamar babu rai koda. Ummi ta yayyafa mata ruwan sanyi a fuskarta, a banza saida ta kuma watsa mata a karo na uku ne. Kafin taja wani dogon numfashi cikin sanyi da tsoro Ummi tace. "Alhamdulillah". Sai kuma ta sunkuyo kanta tana ɗan kiranta. "Shatu! Shatu!! Shatu!!!". Ba amsawa kuma bata buɗe ido ba,
A hankali ya Jafar ya zauna gefensu, karatun da yakeyi yaci gaba dayi.
Cikin sanyi ta buɗe idanunta.
Sai kuma ta yunƙura a hankali ta tashi zaune. Da sauri Ummi ta zaro ido ganin yadda idanunta suka juye a murɗe.
Ita kuwa Shatu miƙewa tsaye tayi, cikin rawan sanyi da karkarwa, ta fara zagaya ɗakin a hankali taje baki Bathroom nanma buɗe ƙofar tayi ta shiga. Jim kaɗan ta fito. Idanun suna yadda suke sai dai. Yanzu hawayene keta shatata babu ƙaƙƙautawa. A hankali tazo bakin gadon. Sai kuma kawai sukaga ta faɗa kan gadon a sune! Wannan shine tashin hankali da ba'a samishi rana. Da gudu suka kumayi kanta, cikin firgici da tsananin tsoro Ummi ta ƙara yayyafa mata ruwan. Amman shiru, haka suka tsaya cirko-cirko, shi kuwa Ya Jafar sai gashi yana karatu yana kuka kamar dai yadda yakeyi kafin a auro Shatu a masarautar Joɗa in Sheykh baya nan.
Gaba ɗaya sun birkice sunma rasa me zasuyi.
Aunty Juwairiyya kuwa itama kuka ta farayi. Jiyo kukanta da na Ya Jafar ne yasa, su Jalal da Hibba shigowa. Ganin tana can yashe kan gado a sumene yasa Hibba ma kuka. Cikin ƙarfin hali Jamil yace. "Aunty Juwairiyya Hibba kada kuyi kuka, kuja hankalin mutane nan. Gashi yau salla ba mamaki akwai mutane a cikin Garden." Cikin tashin hankali Ummi tace. "Bari inje in sanarwa Gimbiya Aminatu abinda ke faruwa, ta sanarwa Lamiɗo, sai in biya in sanarwa Hajia Mama." Da sauri Aunty Juwairiyya tace. "Eh yafi kam". Ta juya zata fita kenan sai sukaji tayi wani irin nakasheshen dogon numfashi mai sassanyan sauti. Da sauri Ummi ta juyo ta dawo jikin sanyi tace. "Shatu! Shatu!! Shatu!!!". Shiru babu amsa sai binsu da ido tayi ɗaya bayan ɗaya. Ganin hakane Jamil ya matso. Tofi ya farayi mata.
Ummi kuwa ci gaba da kiran sunanta tayi. Cikin tsoro Hibba tace. "Ummi kinga idonta ya koma dai-dai." A tare sukace Alhamdulillah. Sai kuma Ummi ta kuma kiranta. "Shatu!". A hankali tace. "Na'am Ummi". Sai kuma ta kalli inda take, kana ta juya ta kallesu baki ɗayansu, cikin mutuwar jiki ta yunƙura ta tashi. Murya a sanyaye tace. "Jamil sharan kenan ka tsaya kanata kallona. Gaya min ya za'ayi sharar". Cikin sauƙe tagwayen numfarfashi suka kalli juna, Cikin mamaki Jamil yace. "No ki huta kawai my Aunty zan share". Bata da ƙarfi a jikinta ko ta dage tace sai tayi sharar. Bazata iyaba jikinta duk a mace. Hakane yasa tace to. Hannu ta miƙa Ummi tare da cewa. "Ummi ɗan jamin hannuna mana". To tace tare da kamo hannun. Ta tsaida ita, cikin tafiyar sanɗa ta juya ta nufi hanyar fita. Binta sukayi a baya gaba ɗayansu.
Jamil kuwa dube-dube yayi a cikin ɗakin kana. Ya fara tattarewa da kimtsawa da sherawa, ya canza mishi beshit and blanket, da rigunan pillows. Kana ya goge ko ina fes Sannan ya shiga bathroom ya wonke ya goge mishi.
Su kuwa suna biye da ita har falonta. Ganin ta wuce bedroom ɗinta ne yasa Hibba da Juwairiyya suka tsaya.
Ita kuma Ummi tabi bayanta.
Ganin tana shiga ta hau gado ta kwanta ne a take sai bacci yasa Ummi ta juyo ta fito.
Can babban falon suka koma suka zauna. "Ikon Allah sai kallo wannan abu da ban tsoro da ban mamaki".
Ummi ta faɗa cikin al'hini.
Jiki a mace Aunty Juwairiyya tace. "Sosai kam wannan al'amari ya firgitani". Hibba dai sai zuru-zuru tayi da ido.
Nan sukayi ta mamakin wannan abin.
Jamil na fito shida Jalal suka tafi.
Shi kuwa Ya Jafar bayan matarsa yabi suka tafi.
Hibba kuwa da Ummi nan suka zauna. Ummi ce ta kalli Hibba tare da cewa. "Sai anjima zan kira Umaymah na sanar mata abinda ya faru".
Kai kawai Hibba ta kaɗan mata.
Ita kuwa Shatu baccin tayi mai nauyi sai kiran sallan azahar ne ya tasheta.
Su Sheykh Jabeer kuwa suna can sunata keta hazo. Tafiya awa huɗu ne zai kawosu ƙasar mun.
A hankali ta buɗe idonta, miƙa tayi tare da yin salati. Kana ta tashi zaune. Bathroom ta shiga, wonka tayi da ruwan ɗumi. Kana tayi al'wa tana fitowa. Ta zura Hijabi tayi salla. Bayan ta idarne, ta zauna gaban dreesing mirror. Simple makeup tayiwa fuskarta. Sannan ta sauya shiga, wani tattausan lace mai ɗan karen kyau da tsada tasaka duguwar rigace tayi cib-cib da jikinta. Kasan cewarta kalar pink guava da ɗigo-ɗigin mint green ne yasa tayi masifar dacewa da kalar jikinta. Gyara gashin kanta tayi ta tubƙeshi tare da kitsen jelar. Ta saketa bisa kafaɗunta. Ɗaurin asseta tayi ya zauna ɗas a kanta, tattausan gyale minti green color ta yafa a kafaɗunta. Kana ta fesa turarukan ta masu daddaɗan ƙamshi.
Sosai jan lallen gargajiya dake kan ƴan fararen yatsun hannunta yayi masifar kyau. Ga kuma zanen da akayi a saman hannun hakama ƙafafun ta, suma sun sha zanen jan lalle tayi kyau sosai, Ta fito ras da ita.
Baki ɗauke da sallama ta foto falon. Cikin murmushi Ummi ta amsa sallamar tana mai kallonta, Hakama Hibba da Ummi ta kokkontar mata da hankali taji tsoron ya ragu. Gefen Ummi ta zauna, tana kallon Hibba na ɗaukarta hoto tana cewa. "My Happiness Aunty kinyi kyau". Murmushi tayi tare da cewa. "Na kaiki ne?". Da sauri Hibba tace. "Kin fini ma". Murmushi ta kumayi tare da cewa. "Ngd matuƙa". Sai kuma ta kalli Ummi tare da cewa. "Ummi me zamuyi abincin dare". Cikin jin tausayinta Ummi tace. "A a akwai abinci harda na gobe da safe ma, yanzu kam ki huta, sai dai in akwai abinda kikeso ki gaya min in yi miki". Kai ta jujjuya alamar a a kana tace. "To Ummi a kaiwa Hadimai wani abincin kada ya lalace a banza ko". Cikin gamsuwa Ummi tace to.
A can Airport kuwa ƙarfe uku dai-dai jirgin Ahlin masarautar Joɗa ta sauƙa. Nan motoci suka kwatsosu. Suna isa masarautar ana kiran sallan la'asar hakane yasa matan cikine kawai suka shiga cikin gida su mazan. Masallaci suka wuce. Ana idar da salla kuwa fada suka wuce baki ɗayansu.
A sashin Gimbiya Saudatu kuwa wani irin dariya mai cike da masifar jin daɗi tayi tare da cewa. "Dai-dai kenan yaro zai dawo ya taradda da mummunan lbrin matarsa ta zama zautacciyar mata...!
By *GARKUWAR FULANI*
Tare da cewa. "Lahh Ummi kalli Hamma Jabeer kusa da Uncle Jabir Ali ɗin can". Cikin Murmushin Ummi tace. "La ai kuwa, Allah sarki masha Allah, tabarakallah. Allah ka ƙarawa Annabi daraja, Allah ka ƙara bamu hasken addini da imani a zuƙatanmu." Amin Amin Hibba tace. Tare da juyowa ta kalli Shatu da tayi kamar bata jisu ba, Sai tea ɗinta take zuƙa a hankali. A zahiri zakace idonta kan cup ɗin yake, amman a baɗini kan allon TV'n idonta yake, ta zubawa fuskarshi ido. Duk da bawai kai tsaye shi kaɗai ake ɗaukaba, limamin dake jansu ake ɗauka hakan yasa suma suka fito da yake yana cikin mamun limaman sahun forko.