Garkuwa complete novel - Chapter 50
Garkuwa complete novel Chapter 50: Garkuwa complete novel Chapter 50. Baki ta ɗan zumbura tare da cewa. "Nifa bansa maka tutarenka ba". Tana faɗin haka ta…
4,431 words
Baki ta ɗan zumbura tare da cewa. "Nifa bansa maka tutarenka ba". Tana faɗin haka ta juya ta nufi hanyar fita.
Da ido ya rakata, tana fita shi kuma ya buɗe ƙofar da zata sadashi da Garden ɗin da ke bayan sashin nasa.
Washe gari kuma ranar suyan jan nama, sosai Aysha ta tsaya kan aikin, dan cikinta yabar ciwon nanda nan sukayi aikinsu suka gama.
Haka dai akayi shagulgula bikin ƙaramar salla lafiya.
Yau kwana huɗu da yin salla a wuni na biyar ne.
Affan da Aunty Juwairiyya kusan a tare suka shigo.
Wani roba mai kyau Affan ya miƙa Aysha tare da cewa. "Aunty ƙarama gashi inji, Mami a kawo miki". Murmushi tayi tare da amsar robar. Soyayyan namane yayi kyau ya samu kekyawan aiki sai nason mai yakeyu. "Kai a lallai nako gode sosai". Murmushi yayi tare da cewa. "Wai tasan naku duk muke haɗuwa muna cinyewa, wai kowa ya bar na gidansa yazo ya cinye naku". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Tayi gsky ai haka kuke gaku bakwa gajiya da cin nama kamar ba Fulani ba. Gwara ma Jalal shi bai fiye damuwa da namaba amman Kai Affan Jamil Imran da Sulaiman ko kuraye sai haka". Murmushi sukayi. Kana Aunty Juwairiyya ma ta miƙo mata robar da tazo dashi tare da cewa. "Gashi wannan a bawa Sheykh". Fuska ta ɗan yamutsa tare da cewa. "A a barshi kawai".
Shiru Ummi tayi dan tasan za'ayi hakan. Ta rasa dalilin da yasa Aysha batason kyautar komin na wurin Juwairiyya da Hajia Mama. Su kuma basa gajiya da ba amsa takeyin ba sai sun bata. Cikin tsareta da ido Juwairiyya tace. "To aini ba ke na bawaba Sheykh nace a bawa". Fuska a daƙile tace. "Bazan bashi ba, bazai ciba. Kije kici abunki. Baya buƙatar nakin". Da mamaki Affan yace. "To Aunty ƙarama meyasa". Juyowa tayi ta ɗan kalli Affan tare da cewa. "Ita ai tasan dalili". Daga nan ta juya ta nufi ɗakinta. Sosai Affan yayi mamaki. Ita Juwairiyya kuwa, ciki takaici tace. "Uhumm lallai ma yarinyar nan, bansan me take nufi da niba, ban san me nayi mata ba, shiyasa yanzu ni bana ko son shigowa nan".
Ta ƙareshe mgnar tana miƙewa zata fita. A hankali Ummi tace. "Kiyi haƙuri JUWAIRIYYA KINSAN abubuwan sai a hankali kada ki damu, kin san mutun in yanada ƴar matsala wasu lokutan ma, ba yin kanta bane". Uhum kawai Juwairiyya tace ta fita.
Sukuwa sukaci gaba da hirarsu. Washe gari Hajia Mama ta aiko hadimanta su kawowa Sheykh dambun nama. Suna shiga tace, suje su rabashi an basu.
Dama Ummi kam tasan za'ayi hakan. Sheykh dake shigowa kuwa cewa yayi. "Ke aka bawa ne da zaki kyautar dashi". Fuska ta ɗan yamutsa tare da cewa. "Bazaka ci bane".
Amsar kwanon yayi a hannun Ummi tare da cewa. "Kuje kuce ngd".
Daga nan ya nufi ɗauki shi. Da sauri ta miƙe tabi bayanshi.
Yana shiga ya ajiye kwanon kan Bedside drower'n. Ɗauke kwanon tayi tare da cewa. "Dan Allah dan Annabi kada kaci, ka barshi, in dambun kakeso ai nayi maka". Taɓe baki yayi tare da cewa. "Nata yafi daɗi akan naki ai". Da sauri ta kalleshi idonta na cicciko da hawaye. Juyawa tayi ta fita da kwanon. "In kinje kin boye kizo". Yace mata, to tace. Ai kuwa taje ta zubar dashi ta bawa Saratu kwanon tace ta maida mata.
A zaune ta sameshi da wata leda a gabanshi. Nuna mata ledar yayi tare da cewa. "Gashi ni na mance tun zuwanmu Umrah Aunty Hafsat da Umaymah suka bada sukace in baki".
Sunkuyowa tayi ta ɗauki ledar tare da cewa. "Ngd matuƙa Allah ya biya musu buƙatunsu".
"Amin Amin". Yace. Juyawa tayi ta fita.
Shi kuwa wayarshi ya zaro yabi bayan kiranda Haroon yaketa mishi.
Ita kuwa Aysha tana shiga ɗakinta ta buɗe ledar. Turarukane masu kyau da ƙamshi. Harda setin na miski da manshi da samubulunshi da turaren. Taji daɗin su sosai. Dan dama yanzu take shirin tayi wonkan tsarki. zata ci gaba da salla daga la'asar.
Wonkanma ta shiga, ta fitowa tasa ɗaya daga cikin dogayen rigunan da suka turo mata.
Yau kwana goma da yin salla ya kama saura kwana sha biyar auren Haroon da Jannart ƙanwar Juwairiyya. Tako ina shirye-shiryen biki ya kankama. Washe gari kuwa su Aunty Hafsat da ahlinta duk suka zo.
Kai tsaye masarauta Leddi julɓe suka nufa. Daɗi a wurin Sitti babu bayani. Ga ƴaƴanta ga jikokinta, dan Umaymah ma ta kasa jira su iso wurinta randa sukazo da safe suka iso ita kuma da yamma ta iso. Farin cikin Sitti da Jadda basa faɗuwa. sai dai duk sanda sukayi irin wannan haɗuwar, yana tono musu tabo da damuwarsu da tashin hankali su.
Hibba ce ta kira, Aysha, take sanar mata. Su Aunty Hafsat sun iso. Yanzu an fidda ankon aure da tsara duk abubuwan da zasuyi. Kwanan Umaymah uku a can ta koma ita da Hibba da Isha yar Aunty Hafsat budurwa, kamar Hibban komai na biki Umaymah ta shiryawa Aysha shi.
Yau auren kwana bakwai bikin. Suna zaune shida Ummi suna tsara tafiyar tasu. Dan dole Juwairiyya zataje, amman zata tafi da Ya Jafar da yaransu da Jalal. Su kuwa zasu tafi da Jamil da Ummin.
Sai Hajia Mama da su Ramla da Batool da har yau bata komaba.
Kiran Haroon ne ya shigo wayarsa. Bayan sun gaisa ne yake cewa. "Wai kai Sheykh yaushe zaku zone? Dudufa yau saura kwana bakwai ne, kuma daga gobe za'a fara hidimomin". Da sauri yace. "Kai haba Haroon ka nitsu mana kaja numfashi kayi mgna a hankali. Ni dai bazan je duk sauran shagulgula kiɗe-kiɗe da raye-raye kuba bazan ce kada kayi bane, sanin Abun harda Aunty Rahma iyayen bidi'a." Cikin hatsala Haroon yace. "Za dai kazo kayi mana walima kam". Kanshi ya gyaɗa tare da cewa. "Eh walimar maza ba, shima dan Abba da kanshi ne yamin mgn da dan ta kaine ba yi zamba sabida, ba amfani da abinda ake faɗa a walimar akeyi ba". Dariya Haroon yayi tare da cewa. "To Ustazu Allah ya kawo ka lfy". "Amin". yace "To yaushe zaku zone?". Jibi ya bashi amsa a taƙaice."
Daga nan sukaci gaba da hira.
Yau saura kwana biyu bikin kuma yaune zasu tafi. Aunty Juwairiyya da Ya Jafar da Jalal kuwa tun jiya suka tafi.
Su kuma yau zasu tafi da dare.
Ƙarfe takwas dai-dai jirginsu ya tashi zuwa jihar Tsinako.
Tara dai-dai jirginsu ya sauƙa cikin birnin Tsinaku.
Bayan sauƙansu da wasu ƴan daƙiƙu, aka buɗe jirgin, kana aka fara fita, daki-daki. Kasan cewar Ummi da Jamil na ta bakin ƙofar sune suka fara fita. Sheykh Jabeer da Aysha kuwa suna can VIP Side. Hakan yasa kusan sune ƙarshen-ƙarshen fitowa.
A hankali yake taku cikin nitsuwa da kamala ta nitsastsun malamai magada annabawa. A hankali ya saƙo ƙafarsa kan step ɗin forko na farfin jirgin. ido ya lumshe tare da buɗesu yana son jihar Tsinako so mai tarin yawa sabida, yanada jigo shaƙiƙai masu sonshi fiye da yadda suke son kansu. Su Umaymah, Haroon, ga ƙarinsu Aunty Hafsat, da Aunty Rahma, da ahlinsu.
Hannunshi yasa ya tattare bakin faffaɗan al'kyabbar jikinshi mai masifar kyau da taushi tare da sheƙi.
Yanayin garin da ɗan hadari, ko ina yayi lib, garin yayi duhu yayi baƙi mai kyau, gajumare masu duhu sunyisa sararin samaniya ƙawanya. Ga wasu kyawawan ciyawi kore shar da suka malale can baya kaɗan, iska mai sanyi ke busowa tana ratsa jiki da jinin mutanen dake wurin. A hankali take biye dashi a baya inda ya taka ƙafarsa ya cire nan take taka tata ƙafar.
Tayi shigar larabawa tayi masifar kyau, kasan cewar tasa Niƙabi baka iya ganin komai sai fararen idanunta da take ɗan jujjuyawa.
A hankali ya gama sauƙa kan, steps ɗin. Yayinda ita kuma take step ɗin ƙarshe. Kanta ta ɗan juyo jin dirin wani jirgi a bayansu yana tashi, yana keta gajumare. Hannunshi yasa a hankali ya kamo nata, da sauri ta ɗan juyo jin hannunshi cikin nata. Takowa tayi ta sauƙo kana ta fara bin takunshi sabida bai rigaya ya sake mata hannun ba.
Suna sauƙa gefen jirgin kaɗan baifi taku bakwai sukayi ba, suka isa gaban wata tsaleliyar mota fara ƙal mai sheƙin sabunta, ganin dogarai guda biyu a gefe da gefen motar sanye da jajayen kaya da surkin kore, sai tabka-tabkan rawuna, ne ya tabbatar mata su akazo ɗauka.
Shi kuwa tafin hannunshi ta haɗe da nata ya sarƙafe yatsunshi cikin nata. Wasu dattawane suma sanye da kaya da rawuna amman su ba shigar dogarai sukayi ba, bisa alama suma, sunada ƴar saurata.
Da sauri suka nufi gabasu. Suna isa dottawan suka ɗan saki murmushi tare da cewa. "Barka da isa lfy Malam Jabeer". Murmushi ya ɗanyi tare da cewa. "Barka dai Baba Wambai". Sai kuma ya juya wurin ɗayan tare da cewa. "Barka da yamma Malam Liman". Ya ƙarishe mgnar yana miƙa musu hannunshi na dama, dan dana hagu yake riƙe da hannunta. Cikin kulawa Malam Liman ya amshi hannunshi tare da cewa. "Allah yayi maka al'barka ya bada ladan raya zumunci". Amin Amin yace. Cikin nitsuwa Aysha ta gaidasu, cike da jin daɗi suka amsa, tare da juyawa suka nufi motar, da tuni dogaran nan biyu sun buɗe musu, bayan motar.
A hankali suka nufi can yayinda Wambai kuma da Malam Liman suka kama hanyar tafiya dan motarsu na can woje.
Shi kuwa Sheykh suna isa ya ɗan ja da baya tare da sakin hannunta, ya nuna mata hanyar shiga da hannunshi. A nitse ta rusuna kana ta shiga. Bayan ta shiga ne, ta gyara zamanta tare da lumshe idonta sabida wani irin masifeffen ƙamshi da sanyi da sukayi mata sannu da zuwa a lokaci ɗaya. Gyara zamanta tayi ganin yana shigowa, can gefe ta matsa, shi kuwa yana shiga ya zauna, da sauri dogarin dake gefenshi ya kamo bakin al'kyabbar jikinshi ya samishi ita, ta ciki. Sannan ya maida ƙofar ya rufe.
A hankali motar ta fara juyawa alamar direba na ciki.
Su kuwa dogaran suka fara bin motar a hankali, har ta gama juya kanta, ta dai-dai-ta.
Sannan suka fara sauri yadda tafiyarsu zaiyi dai-dai dana motar dake tafiya a hankali.
A haka suka fito asalin farfajiyar kowa da kowa. Nan Ummi da Jamil suke cikin motar da aka ware musu. Kana Baba Wambai Wanda yake Aminin Abban su Jabeer ne ƙut da ƙut, shida Malam Liman suka shiga motarsu. Suma dogaran suka shiga tasu motar, haka suka jera motoci biyar tasu Sheykh ce a tsakiya, ta fadawa a gaba sai tasu Jamil sannan tasu, sai ta malam Liman sai kuma ta dogarai can baya.
A haka suka nufi masarautar Tsinako. Cikin mota da Sheykh da Aysha suke kuwa, waya Aysha keyi bisa alama da wata ƴar uwarta ce. sabida yaga tarin farin ciki a fuskarta. A hankali ta ɗan juyo ta kalleshi lokacin da Junainah tace. "Adda Shatu ina mijin naki baki taɓa bashi waya mun gaisa ba, ko bakice mishi kinada ƙanwaba?". Da sauri ta ɗan janye idonta tare da cewa. "Gashi nan, na gaya mishi mana". Da sauri Junainah tace. "Ayyah Addana dan Allah bashi wayar." Juyowa ta kumayi ta kalleshi cikin raɗa dayin ƙasa da murya tace. "Junainah shi miskiline, yayi fuskar bosawa, baya dariya baya son mutane, kada ki damu dashi badai gani kina gaisawa da yar uwarki ba, mai ruwanki da wani can bare". Da sauri ta juyo ta kalleshi, jin yasa hannunshi ya zare wayar a kunnenta. Ido ta zuba mishi ganin ya manna wayar a kunnenshi. Ita kuwa Junainah baki ta tura tare da cewa. "A a Adda Shatu, shina ɗan uwanane, tunda yana tare dake yar uwata. Kuma ma Bappa yacemin da baki da lfy shi yake miki mgnin har kika samu lfy, Ni dai ko yayi fuskar bosawa bashi mu gaisa ina dai ba dukana zaiyiba". Wani irin bugawa da ƙarfi zuciyarshi tayi jin sautin amon Muryar yarinyar tamkar sautin amon da bazai taɓa mancewa a duniya ba. hakane yasa yayi shiru yana jin muryarta na dukan dodon kunnenshi da zuciyarshi, jin tayi shirune ya sashi yin sassauƙan numfashin tare da cewa. "Ƙarya takeyi miki Baby sherri take min. Ni Bana fuskar bosawa, kuma ina son mutane sabida Allah da kanshi yace. "Walaƙat karram'na bani Adam. Toni waye da zanƙi mutane, bazan dakekiba kinji ko". Ya ƙarishe mgnar yana kallonta tare da tsuke fuskarsa ya ƙanƙance idanunsa ya tsura mata su cikin nata, yana mai son ganin iya tsaurin idonta. Ita kuwa Aysha da sauri ta janye ƙwayar idanunta Allah ya sani batayi zato ko tsammanin zaiji abinda ta faɗa cikin raɗaba. Towai shi wanne irin kunnene dashi a rayuwarsa.
Junainah kuwa cikin jin daɗi tace. "Yauwa Ina kwana Hamma". Ido ya lumshe tare da cewa. "Lfy Baby me sunanki".
Da sauri tace. "Junainah, wani lokacin Adda Shatu na cemin Junnu ko tace min ƙanwaliya ko tace min Baby Ummey'nmu kuma tace min Mamana ko tace min auta". baisan sanda wani murmushi ya subce mushiba. Lokacin ɗaya yaji son yarinyar a ranshi. cikin nitsuwa yace. "Toni kuma da wanne sunan zan kiraki?". Da sauri ta kuma cewa. "Junainah dan Bappa na yace in dena bari ana ɓata min sunan. Hamma kai me sunanka, yaushe zaka kawo mana Addana". Juyowa yayi ya kalli gefenshi ganin sun isa cikin masarautarsu Haroon.
A nitse Suka nufi Side ɗin Umaymah. dasu a cikin motar.
Shi kuwa Sheykh Jabeer gyara zamanshi yayi tare da cewa. "To Junainah, Sunana Muhammad Jabeer, yanzu munyi tafiya sai mun dawo zan roƙi Bappa a kawo mana ke mu zauna ko". Cikin jin daɗi tace. "To Hamma Jabeer Allah ya dawo daku lfy, bari in meyarwa Bappa na wayarshi kar ya dawo ya sameni." Kafinma yace wani abun ta katse kiran.
Dai-dai lokacin kuma motar su ta isa bakin farfajiyar shiga Big Part ɗin Umaymah, parking akayi. hakama motar Ummi da Jamil. bin wayar yayi da ido yanajin wani abu na musamman a zuciyarshi.
Ita kuwa Aysha da sauri tasa hannun ta, zata buɗe marfin motar ganin Umaymah, Hibba, Aunty Hafsat da wasu ƴan mata da samari ƴan saffan-saffa kyawawa masu suffar larabawa sun fito daga wata babbar ƙofar suna tako wani babban steps masu faɗi dake jikin barandar wurin.
Zura wayar yayi cikin al'jihunsa.
A hankali yasa hannunshin ya kamo nata, jawota yayi kusa dashi tare da ɗan juyawa ya fuskanceta da kyau fuskarshi ya haɗe tare da cewa. "Nine mai fuskar bosawa ko? Ina zaune a gabana kikemin sherri da ƙazafi. Nine bana son mutane ko wato bana dariya". Bakinta ta turo ta cinnnashi sama. Idonshi ya tsurawa tattausan red lips ɗinta masu masifar taushi sai sheƙi sukeyi. mui-mui tayi da bakin alamun zatayi tsiwar Tata. Cikin murza bakin tace. "To kanayin dariyar ne? Ban taɓa ganin k..!" wani irin zaro ido tayi da ƙarfi cike da bugawar zuciya. Lokacin data buɗa lips ɗin ta tare da rabasu biyu zata furta kalmar K.
Da sauri ya lumshe idonshi tare da kusanto da fuskarshi kan tata manne gishinsu wuri ɗaya, tattausan lip ɗinshi na na sama yasa cikin bakin ta, tare da kamo lip ɗinta na ƙasa, yasa cikin bakinshi ya zama nashi na sama yana cikin bakinta.
Da sauri yasa tafin hannunshi ya tallabo ƙeyarta da kyau. Wani irin gigitaccen rugguma yayi mata. cikin rawan jiki ya c...!
Littafina GARKUWA na kuɗine
By *GARKUWAR FULANI*
: Idonshi ya lumshe jin fatar idanun sun mishi nauyi. Wani irin abu yakeji yana yawo a dukka cikin jininshi yana zaga jikinshi, manne lips ɗinshi da nata yayi, suka haɗe tamkar mayen ƙarfe.
Hanunshi yasa ya ƙara tallabe kanta da kyau.
Ita kuwa Aysha wani irin tsuma jikinta keyi tare da miƙewar tsikar jikinta, a lokaci ɗaya taji wani irin masifeffen mamaki, tsoro, kaɗuwa, domin abun yazo mata a baka-ta-tam ba zato ba tsammanin hakan daga gareshi domin bai taɓa gwada yin hakanba koda a kamace ne.
Jin yadda yayiwa lip ɗin ta wani irin lasa da kuma tsotseshi tamkar ya samu tom-tom ne yasata. Yin yunƙuri da kiciniyar ƙwace kanta. Ronƙofawa yayi kanta da kyau jin zata kawo mishi wargi. Nauyin ƙirjinshi ya sakar mata ya danne nata ƙirjin da ƙirjinshi, kana ya buɗa al'kyabbar shi, ya rufesu ruf, wani irin numfarfashi yake fesarwa da sauƙewa a jere-a-jere. Cib tayi jin yadda ya mata ƙawanya da jikinshi kana ya sakar mata nauyinshi da yimata garkuwa da al'kyabbar jikinshi.
Buɗe idonta tayi ta zubasu kan kyakkyawan fuskarshi, da take yalwace da. Hasken addini, ta ƙawatu da kyawun sura da hali da nagartacen haiba da imani. Gashin girarsa ta zubawa ido, tana kallo tare da sajenshi. a hankali ta shaƙi ƙamshin turaren OudKareem dake tashi a jikinsa. meda idonta tayi ta lumshe da sauri ganin Umaymah ta iso har gaban motar kusa da ƙofarsu. Mutsu-mutsu ta farayi. Sam ta kasa zillewa. Hakane yasa ta ɗago hannayenta, tasa bisa fuskarshi ta tallabe gefen hagu da damanshi ya zama tafin hannunta na kan sajenshi duka biyu. A hankali ya buɗe kyawawan idanunshi ya zubasu cikin nata. Da sauri ta janye nata, kanshi ya fara janyewa still dai yana liƙe da lip ɗinta kan harshensa. da sauri ta turo kanta jin kamar zai tsinke mata shi. Ɗouhh haka ya saki mata wani sauti mai kashe jiki da zuciya cikin kunnenta lokacin daya saki laɓɓan nata. Da sauri tasa tafin hannunta tana fifita lips ɗin tare dayin rau-rau da ido tace. "Zafi! zafi!! Zafeeeh!!!." Hannunshi yasa ya kama tsinin hancinta da yatsu biyu kana ya ƙanƙance idanunsa, cikin wata iriyar fitinenneyar murya yace. "In kika sake murguɗa min bakin, haka zan miki. In kuma kika sake yimin sherri ko ƙazafi tsinke bakin zanyi". cikin kwaɓe fuska tana fifita laɓɓan tace. "Ka tsinke min baki kamar maye". Kafaɗunshi ya buɗa tare da ɗagasu sama ya taɓe baki kana yace. "Mayen ne ai ni. In na tsinkasu haɗiyesu zanyi sai kije in sa miki na Aku kinji daɗin yin surutu da kyau". Ya ƙareshe mgnar yana janye al'kyabbarshi daga jikinta yana gyara shi. Hannunshi yasa ya jawo niƙabinta daya ɗage ya rufe fuskarta tare da cewa. "Ki rufe fuskarki kar Hibba tayi miki dariya tace kin zama mai dogon baki dengin jaɓa". Yana faɗin haka yasa hannunshi ya buɗe marfin motar tare da saƙo ƙafarshi ta dama waje. Wani irin murmushi mai cike da tarin. So, ƙauna, shaƙuwa, tausayi, da kulawa. Umaymah tayi mishi. Hakama Aunty Hafsat.
Ita kuwa Aysha bakin ta ɗan tura tare da cewa. "Allah ko sai na gayawa Umaymah ka cinye min lips ɗin a".
Juyowa yayi yana kallonta, tare da murmushi a fuskarshi. Sai kuma ya juyo da sauri jin Umaymah da Aunty Hafsat su ruggumeshi ta baya. Hannunshi ya miƙo mata tare da cewa. "To fito ki faɗa kada in rigaki yin nawa sharhin". Ture hannunshi tayi ta fito. Shi kuwa tana fitowa yasa hannunshi ya kamo nata tare da jawota bayanshi. Da sauri Aunty Hafsat ta sakeshi tare da komawa bayanshi hannunta ta jawo tare da Ruggumeta tana cewa. "Masha Allah diyar kirki". Da sauri tasa hannunta ta yaye niƙabin.
Umaymah kuwa murmushi tayi cikin tsananin jin daɗin ganinsu take kallonsu cike da so da kulawa tare da cewa. "Jazlaan naji daɗin ganinku". Murmushi yayi tare da cewa. "Muma haka". Sai kuma ya juyo da sauri ya kalli Haroon da Ibrahim da suka fito can gaban motar bisa alamu duk Ibrahim ne yaja motar. Haroon kuwa yana gefen mai zaman banza. Cikin dariyar tsiya Haroon ya matsoshi tare da ruggumeshi ta gefe, dan su Umaymah duk sun sakeshi sun koma kan Aysha. Cikin tsiya yace. "Ur welcome Mr Jabeer Ustazu ƙalilan iya shege kasiran". wani irin tsare fuska da gira Sheykh yayi tare da watsa Haroon kallon. "Hegen munafurcin sa ido". Ya faɗa tare da Ruggume Haroon da ƙarfi yadda zaiji zafi. Da sauri Haroon yasa ƴar ƙara tare da cewa. "Wayyo Aunty Hafsat zai karyan baya in rasa na amarci". Dariya sukayi dukansu.
Shi kuwa Sheykh ture Haroon yayi yana mamakin subutar baki irin na Haroon, kwaffa yayi tare da Ruggume Ibrahim murmushi Ibrahim yayi tare da cewa. "Barka da zuwa Garkuwan Masarautar Joɗa". Shima murmushi yayi tare da cewa. "Barka da zuwa, magajin masarautar Leddi julɓe".
Hibba kuwa baki ta tura tare da cewa. "Aunty Aysha wato kinga su Umaymah ni Ko ki kulani ko?". Da sauri ta juyo ta ruggume Hibba tare da cewa. "Oh sorry my Hibba ai ke ta dabance".
Da sauri ta juyo ganin wata kekyawar budurwa kamar Hibba ta gane Azeema ce yar Aunty Hafsat. cikin bagwariyar Hausa Azeema tace. "Wato mu bana musamman bane ko Aunty". Da sauri ta jawo hannun Azeema ta haɗa su ta ruggume.
Da sauri Umaymah ta juyo ganin Ummi ta fito. Ruggume juna sukayi cikin jin daɗin ganin junasu sun kasa mgn sai murmushi. Jamil kuwa da sauri yaje ya Ruggume Abudul-azeez da Sadiq ta baya. Juyowa sukayi suma suka ruggumeshi suna farin cikin ganin juna.
Sheykh kuwa sake Ibrahim yayi ya kalli Sadiq da Abdul-azeez ya shafa kan ƴan matasan.
Umaymah ce ta juya ta nufi cikin gidan tare da cewa. "Ku shigo, maza ku taho ko". To sukace kana duk sukabi bayanta.
Wani babban falo mai zaman kanshi wanda yake ɗauke da lumtsuma-luntsuman kujeru set biyu da Dinning table a can babban Dinning area da ƙaton fili a tsakiyar falon. Suka zauna. Su Hibba da Azeema sun sa Aysha a gaba.
Haroon da Ibrahim dasu Sadiq kuwa suna ɗaya sashin.
Umaymah da Aunty Hafsat da kansu suka rinƙa kawo musu abubuwan ci da sha.
Bayan sun gaggaisa ne.
Suka ɗan zauna suna hirar Yaushe gamo.
Ummi ce ta ɗan kalli Umaymah tare da cewa. "Ina Rahma ne ban ganta ba ita". Aunty Hafsat ce ta amshi zancen da cewa. "Tab uhum Rahma taji biki ta zauna. Ɗazu da safe jirginsu ya wuce. Leddi julɓe, kinsan gobene za'ayi kamu, to taje ita da su Isha dasu Farida, sun haɗu dasu Juwairiyya sunacan suna shiryawa hidindimun da za'ayi". Ɗan juyowa sukayi suka kalli Azeema da ke cewa Sheykh. "Hamma Jabeer zamuje da Aunty Ayshan can ko gobe in Allah ya kaimu". Ba tare da ya ɗago kanshi bare ya kalletaba ya ɗan jujjuya kanshi alamun. A a, da sauri Azeema tace. "Ayyah dai". Umaymah ce ta ɗaga mata hannu alamun tayi shiru. Ummi da Aunty Hafsat kuwa murmushi kawai sukayi. Hibba kuwa ƙasa tayi da muryarta tare da cewa Aysha. "Zamuje ai". Kai Aysha ta gyaɗa mata alamun eh.
Haroon kuwa juyowa yayi ya kalli Sheykh tare da cewa. "Yaushe kace zamu tsaida lokacin walimar?".
Kanshi na sunkuye yana kallon wayarshi yace. "Na gama mgn da Abba, babu wani Dinner'n da za'ayi. Madadin dinan shi zamuyi waliman". Da sauri Haroon yace. "Wannan ai tatsuniya ce". Ibrahim ne ya ɗan kalleshi tare da cewa. "Wlh sun gama mgn da Abba, yace tunima ya gaiyaci manyan mutane duk akan walima za'ayi. An gama shirya komai ma, kuma babban wurine aka kama gefen, maza da matane, za'ayi walima mai kyau da ma'ana. Yafi akan yin wannan bidi'ar nan da zamuje mu gwamutsu maza da mata a wuri ɗaya a rinƙa kiɗe-kiɗen da bushe-bushen da raye-rayen banza da wofi". Murmushi Umaymah tayi ganin yadda Haroon ya haɗe fuska kamar zaiyi kuka cikin takaici yace. "To Ni yau ma zan tafi dan inje mu shiryawa kamun da kyau, duk sauran abokanmu zasu je". Ya faɗa yana kallon Sheykh, kafaɗarshi ya ɗaga tare da buɗawa kana yace. "Ya rage naka, Ni nan Muhammad babu inda zanje walimace da ɗaurin aure ya kawoni. Dan dole in jamaka kunne kasan tsarin zaman aure a musulunci ba a yahudance ba". Dariya sukayi sosai. Aunty Hafsat ce ta ɗan gyara zamanta tare da cewa. "In anyi bikin a can, kana in mun dawo nan anyi walima, washe gari ayi fansan ido da daren ranar Lahadi da dare zamuyi mother's day, dan ranar tamuce kuma biki biyune, tunda bamu samu zuwa na Jazlaan ba. Anyishi babu bikin komai to in sha Allah mu dai iyaye zamuyi namu shagalin wannan umarnine ba shawara ba, bakuma neman iziniba". Ido Sheykh ya zuba mata cikin sanyi yace. "Mom". Hannu ta ɗaga mishi, alamar yayi shiru. Sai ta kuma juyo ta kalli Ummi tare da cewa. "Ummin Jabeer kunzo da shiri ko?". Cikin murmushin Ummi tace. "Sosai ma kuwa". Nan dai sukayi hirarsu da tsara yadda abin zai kasance.
Hibba ce taja hannun Aysha, ɗakin Umaymah Suka shiga. Suna shiga tayi wani irin tsayuwa tana kallon tsarin ɗakin yayi masifar kyau. Wasu ƴan mata da manyan mata suka samu a zaune. Cikin murmushin Hibba tace. "Aunty Rabi'atu ga matar Hamma Jabeer Aunty Aysha da nake faɗa miki". Da sauri duk suka juyo. Masha Allah shine abinda suka faɗa kusan a tare. Ɗan rusunar da kai tayi ta gaidasu. Murmushi tayi ganin Aunty. Kubra ƙawar Umaymah dake Ɓadamaya. Motsowa tayi kusa da ita ganin tana miƙo mata hannu cikin kunya tace. "Aunty Kubra Ina wuni. yaushe kika zo". Murmushi tayi tare da cewa. "Alhamdulillah Aysha. Ni tun jiya nazo, ina ɗan nawa yana lfy ko?". Murmushi tayi a kunyace tace. "Alhamdulillah yana falo". Nuna mata sauran matan tayi tare da cewa. "Kinga nan duk ƙawayen Umaymah ne yawanci daga wasu garuruwan sukazo. Kin san Umaymah taku ta jama'ace". Sannu ta sake yi musu.
Ita kuwa Aunty Kubra miƙewa tayi tare da kamo, hannun Aysha. "Zo nan". Tace tare suka fita Hibba na biye dasu a baya. Juyowa tayi ta kalli Hibba tare da cewa. "Jeki kira min Hafsat kice ina ɗakin can". Da sauri Hibba tace to, kana ta juya taje falo. Ta kira Aunty Hafsat kamar yadda Aunty Kubra ta umarceta.
Tare suka juya suka tafi.
Haroon da Ibrahim da Sheykh kuwa miƙewa sukayi suka nufi wanni babban part dake bayan na Umaymah wanda yake da yalwan ɗakuna babban falo sai 3 bedroom sai ƙaramin falo. Nan suka nufa, wanda akwai wani a gefenshi kuma nanne Haroon zai tare da Amaryarshi Jannart.
Suna shiga suka samu abokansu.
Hunnu sukayi ta bawa juna suna gaisawa cike da fara'a sukeyiwa Sheykh tsiyar yayi auren sirri wato dan baya son suje susha rawa ko. Murmushi yayi tare da cewa. "Mazarai sarakunan rawa yanzu ai kun samu wurin rawan ko?". Dariya sukayi.
Aunty Kubra kuwa suna shiga ɗakin. Ta jawo wani matsakaicin akwati. wasu zafafan ɗinkuna ta fara fitarwa. Ko wanne da mayafinshi da takalminshi da jaka ko fosa. Shigowar Aunty Hafsat ce yasa tace. "Yauwa Hafsat Ni ina anko ɗin su na ƙawaye da a abokai wanda za'asa a kamun. Zama tayi gefenta tare da cewa. "Gashi nan gefenki ɗazu aka dawo dasu daga ɗinki. Harda na Farida shine fa tun ɗazu ta buwayeni da kira kadafa a manceta". Jawo ledar tayi ta firfito dasu, kowa da sunanshi a jikin nashi, shiyasa babu wuyan ganewa.