Garkuwa complete novel - Chapter 84
Garkuwa complete novel Chapter 84: Garkuwa complete novel Chapter 84. “In ma ni bakya sona! baki da lokaci na! Bakya buƙatar ganina! Bare ki sauƙe haƙƙina…
4,445 words
“In ma ni bakya sona! baki da lokaci na! Bakya buƙatar ganina! Bare ki sauƙe haƙƙina dake kanki, ai ita dai Afreen ƴar kice kuma tana da haƙƙin ta a kanki ko? In kuma kinajin duk kin tsanemu ne baza ki iya rayuwa damu da bamu haƙƙinmu ba, dan Allah ki gaya min ba sai kin zauna kina ta min kuka a cikin gida, kina cutar min da yarinya da yunwa ba, sannan kina tayar min da hankali ba, Ki faɗa min in bakya sona, In sama miki salama kije can ki auri shi wanda kike so ɗin!!!”
Ya ƙare maganar da ƙarfi. Cike da fushi da zafin kishi. Wanda har Ummi dake falon ta jiyoshi. Karo na forko kenan a rayuwar aure su da Shatu da taji yana mata faɗa haka. Jin hakanne kuma yasa da sauri ta kamo hannun Junainah suka tafi ɗakinsu.
Ita kuwa Shatu cikin rauni ta zuba mishi ido tana mamakin fusatarsa da kalaman da yakeyi.
Shi kuwa Sheykh cikin takaici yace. "Na sani ai dama ni na sani bawai sona kikeyi ba, dole akayi miki ko? dama shi kikeso! Wannan abun shi nake gudu da tsoron auren matar da ba sonka takeyi ba. Amman ba matsala kiyi ta sonshi. Nima ina da masu sona, kuma zan aurosu, su kuma kular min da ƴata".
Idanunta da ta zuba masa tad’an lumshe, cikin rawar murya tace. "Yah Sheyk...".
Da sauri cikin fushi da zafin kishin ganin son Ba'ana ne yasata wannan kukan. A faɗa ce ya daga mata hannu cikin tsawa yace. "Da Allah rufe min baki". Yana faɗin hakan ya juya ya fita daga d’akin, still rungume da Afreen akan shoulder dinshi.
Kai tsaye bedroom ɗinsa ya wuce. Cikin tafasan zuciya ya kwantar da ita can ƙarshen gadon nasa. Kana a hankali ya miƙe ya zauna sabida azaban tafasar da zuciyarsa keyi.
Ita kuwa Shatu wasu hawayene, masu sanyi suka zubo mata. Musamman da ta fahimci cewar, zafin kishine ya birkita mata salihin mijinta.
A hankali ta miƙe tsaye, tare da soma takawa ta shige Bathroom. Ruwan ɗumi kawai ta watsa tare da yin Brush kana ta fito daga cikin toilet ɗin. Turaren Oud mai daɗin ƙamshi ta shafa ajikinta. Tare da zura wata royal blue sleeping gown ajikinta mai adon net. Yayinda kuma har yanzu ta kasa tsaida hawayen dake kwance acikin idanunta.
Wasu lallausan sleeping shoe ta zura a ƙafarta, tare kuma da tubke long hair ɗin kanta, da bluesy ribbon. Tana gama kimtsa kanta kuwa, ahankali ta fito daga ɗakin, tare da jawo ƙofar ta rufe. kaitsaye ta nufi Side ɗinsa.
Cikin sanyi ta tura ƙofar Bedroom ɗin nasa tare da yin sallama can ƙasan maƙoshinta.
Ganinsa atsaye da tayi ne kuma yasa, ahankali ta jingina da jikin ƙofar tana kallon yadda yake zirya a tsakiyar ɗakin, shi kadai sai ya kai mari ya kau gouro. Ga wani irin numfashi mai ɗumi da yake fitarwa. Idanunshi kuwa sun kaɗa sunyi jazir.
A hankali ta nufo tsakiyar ɗakin. Cikin sanyi da kuma rauni ta nufi inda yake. Dai-dai lokacin shi kuma ya juyo. Yana juyowa kuwa ta faɗa jikinshi ta rungumeshi tsam a jikinta. Ashagwaɓe ta saki wani irin raunataccen kuka mai kashe jiki da zuciya. Murya na rawa cike da rauni tace.
“Kayi haƙuri Yah Sheykh ka gafarceni, na tuba please, kukana bawai inayi dan na ɓata ranka bane, banason fushinka, Dan Allah kada ka kwana kana fushi dani, I’m very scared dan bazan iya jurewa ba...”
Kasa ƙarasa maganan nata tayi, lokaci ɗaya kuma ta ci gaba da sakin Shessheƙan kuka, tare dasa hannayenta akan chest ɗinsa.
Shi kuwa Sheykh har yanzu fushi yakeji, saboda haka ma gaba ɗaya jikinshi rawa yakeyi dan tsananin takaici kukan da takeyi. Hannunshi yasa ya soma ƙoƙarin ɓanbareta daga jikinsa, murya adaƙile yace. "Ni Sakeni! ki barni!! kuma ki fita harkana!!! Kije can ki gama kukan naki a can ɗakinki, badai kinfi sonshi ba? maza fice min a ɗaki ni ɗakina ba wurin zubda hawayen soyayyar wani ƙato bane."
Jin hakanne yasa, cikin sauri tasa hannayenta ta saƙalo wuyanshi, tare da cusa kanta a ƙirji shi, murya a raunace tace. "Ni banason shi, da gaske Yah Sheykh ka yarda dani bana sonshi, aduniya waye zanso sama da kai? kaine fa Mijina, mahaifin ƴata, sannan kuma Garkuwa ta, tayaya zan so wani bayan kai?”
Da sauri yace. "Eh mahaifin ƴarki ko? Bama mahaifin ƴaƴan kiba, wato irin daga ita shike nan ko?".
Baby face d’inta ta shag’wabe, cikin kasala da kuma son sauk’ar masa da fushinsa tace. "I’m very sorry Zawj mahaifin yaƴana."
Idanunsa yaɗan lumshe, cikin kuma yanayin fara jin sanyi arashin ya tureta ya koma bakin gado ya zauna tare da cewa. "In dai bazaki bar kukan nanba fice min a ɗaki sanida kukanki yana ƙona min rai".
Da sauri tasa tafin hannunta ta share hawayenta. Kana ta matsoshi Ahankali ta kwanta a jikinshi tayi lib, laɓɓan bakinta taɗan tattauna kana a raunace tace. Ok “Please Yah Sheykh nabar kukan, amma ka yafe min, bazan sakeba dan Allah kayi haƙuri". Ajiyar zuciya mai sanyi, ya sauƙe dan ta haɗashi da Allah ta gama zance. Juyowa yayi asanyaye ya fuskanceta, tare dasa hannunsa ya ɗan tallafo kanta, shiru yayi batare daya ce komae ba, sai tsurawa fuskarta ido da yayi. Ganin hakanne kuma yasa ahankali ta sake matsowa jikinsa, wani sassanyan hugging tayi masa, tare da fara sauƙe tagwayen ajiyan zuciya cikin sanyi da taushin murya a hankali tace. "Nifa Bana sonshi, so irin wanda nakeyi maka, nadai soshi matsayin wana jinina, sannan kuma nayi kukane saboda rauni na. Musamman ganin yadda ake dukanshi, da kuma yadda iyayenshi ke kuka. Yah Sheykh Yah Ba'ana shine wanda yayiwa Ummey magani tsawon shekaru biyu ba dare ba rana kafun ta fara magana ta dawo haiyacinta. Naje gidansu dare da rana cikin ruwa da iska na amsowa Ummey na magani, Bai taɓa cutar da niba, Ya soni tamkar ransa, Nikuma na soshi matsayin ɗan uwa musulmi, Shekaran jiya tausayin dukan da akayi mishine ya sani kuka. Jiya kuma tunda Jalal yace min za'a yanke masa hukuncin kisa raunina yasa na kasa tsaida hawayena. Amman bawai dan ina sonsa so na aureba, kawai dai akullum Ina tuna al'khairinsa garemu ne, domin koba komae shid’in yayi taimako agaremu”. Wani sassayan numfashi ya sauƙe tare da, sa hannunshi ya ruggumeta gam-gam a jikinshi. Haka nan yaji duk jikinsa yayi sanyi. Jin yanda yayi hugging d’inta ne kuma yasa ahankali tace. "Nida Allah ya azurtani da miji kamarka, miji na gari! Mumini! Salihi! Mai tausayina! Mai riƙo da ibada! Mai cikakkiyar nagarta! Ta yaya idona zai iya ganin wani ɗa namiji da wata suffar, har in soshi? Nida nake da kai, na shaida Allah yamin kyakkyawan zaɓi! Ina sonka sosai Yah Sheykh nah, Hamma Jabeer, kuma Malam d’ina, ina sonka, zan kuma ci gaba da sonka iya rai da mutuwa, sannan please ka yafe min zuwan da banyi gareka ba, ka d’aukeshi amatsayin ajizanci da kowani d’an Adam keyi, then maganan Afreen kuma kaina ke ciwo shiyasa na barta dasu Junainah, ka yafe min ni bani da sama daku kaida Afreeen kune farin cikina. Kune silar dawowata Nigeria'n rankune ke ajiye dani a masarautar Joɗa". Wani irin sasayyan kiss ya manna mata a goshinta. Cikin kuma yanayi jin sanyi da daɗin kalamanta yace. “I Love you Aysh, I always Love you, I love you so much, Tabbas nayi farin ciki da samun aurenki farin ciki marar misaltuwa, Kece cikon farin cikina My Wife, kece sanyin zuciya da idanuna! sannan kuma har lau kece GARKUWA ta! Duk wani farincikin da zan samu yana tare dake ne, hakika ke HASKE ce acikin rayuwar Jabeer, zan rayu dake har abada!!” Yakai ƙarshen maganan nasa cikin wani irin murya, mai sauƙar da kasala, tare kuma da zame jikinsa, ahankali ya kwanta kana ya jawota ya kwantar da ita ajikinsa. Idanunta ta zubawa kyakkyawar fuskarsa, Cikin kuma yanayin sanyi tace. "Please Yah Sheykh, idan da hali kayi wa ya Ba'ana wata al'farma mana". Kallonta shid’inma yayi kana hankali yace. "Wacce irin alfarma kikeso ayi masa?” Cikin zubda hawaye tace. "Dan Allah kasa a meda case ɗinsa kotun musulunci, a yanke masa hukuncin Musulunci dan Allah". Kansa yaɗan jinjina, cikin yanayin jin rauni da tsananin tausayi kuma yace. “I’m understand My Shatu, but amma kiyi haƙuri kinji, ki daina kuka domin dama tuntuni kotun musulunci aka kai ƙarar, kotun su Abban Yusuf (HUKUNCIN ALLAH) za'a yanke masa Insha Allah" Wani sassayan numfashi ta fesar tare dasa hannu ta share hawayen ta. Kana anutse tace. "Alhamdulillah!” Shiru ta ɗanyi sakamakon jin yanda ya soma yawo da hannnunsa akan waist dinta, akasalance ta ɗago kanta ta kalleshi, wanda shi ɗinma kuma kallonta yake da lumsassun idanuwansa. Ahankali ta matso da fuskarta gab da nasa, tare da zaro harshen ta ta ɗaura akan lips ɗinsa, domin ta fahimci a irin wannan yanayin sam ba buƙatar ace, sai ta jira shi ya fara kissing ɗinta. Idanunsa da suka ɗan sauya kala lokaci daya ya lumshe, musamman alokacin da yaji sauƙan harshenta akan laɓɓansa. Wani irin sha’awa da shauƙinta yakeji, hakanne ko yasa shi buɗe bakinsa, ahankali ta zura harshenta acikin bakin nasa. Wani irin dogon numfashi dukansu suka Sauƙe alokacin da tongues ɗinsu suka had’e waje ɗaya. Azafefe suka shiga kissing din juna, Yayinda kowannensu ke transferring yawun bakinsa wa ɗan uwansa. Kissing ɗin juna sukeyi sosai, Yayinda Aysha’n ke neman zautar masa da lissafi, hakan kuwa shiya sanya azafafe ya zare vail ɗin da ta rufe jikinta dashi. Ganinta da yayi acikin royal blue sleeping gown ɗin da yayi ne kuma, yasa shi jin wani hot feeling ɗin ta. Lokaci guda ya soma sakar mata kiss tako ta Ina. Yayinda daga gefe guda kuwa daddaɗan kamshin Oud dinta ke sake kunna sa. Aninayen dake jere agaban rigar nata ya ɓalle, tare da zare rigar daga jikinta gaba ɗaya, haɗadɗiyar surar jiki dana kirjinta ya zubawa ido, yana me sakejin sonta acikin zuciyarsa. Jikinsa na rawa tamkar wanda bai taɓayin sex da ita ba, haka ya mannata da jikinsa bayan ya zama naked. Atare suka soma fitar da wani irin numfarfashi, saboda yanda duk suka ruɗa juna da salonsu. Zama yayi akan gadon tare da ɗorata asaman jikinsa, lokaci daya kuma yaji numfashinsa na kokarin daukewa saboda yanda yaji Manhood ɗinsa ta samu kekkyawan masauƙi, dumi da kuma daddaɗan sweet da ya samu kansa acikine kuma yasa tunkafun aje ko ina yasoma yi mata wasu kalan sambatun dake nuna yana matuk’ar enjoying mood din. Domin kuwa harji yake kaman zai shiɗe. kaman kuma yanda yake azauce haka itama Shatu’n... After 58minute Bayan kuma komai ya lafa sunyi wanka sun fitone. Ya kalleta da kyau ganin yadda ta lafe ta kwanta lib, da’alama ta ɗan gaji ne. Murmushi yayi sannan ya fice daga cikin dakin, Dinning area yaje. Tea mai kwauri ya haɗa da zafi ya cika ɗan babban kofi kana ya dowa daƙin. Hannunshi ya miƙa mata, ganin haka yasa ta kama hannun, Ɗagota yayi ta zauna, kana shi kuma ya zauna agefenta. Cup ɗin tea din ya kai bakinta. Babu musu kuwa ta buɗe bakin sabida wani irin masifeffen yunwa da takeji, shikansa yasan dole ne ma, taji yunwa, sabida yanda yayi heaven sex da ita yau din, is so special. Tasha tea din sosai, saida ta kusan shanyewa ne kuma ta janye kanta ahankali, tare dayin gyatsa asanyaye tace. "Alhamdulillah". Hannunshi yasa bisa cikinta a hankali ya shafa cikin kula yace. "Shanye shi ko mangana". Ya ƙare maganar yana sa mata cup ɗin tea din abaki. Shanyewa tayi kana ya aje cup ɗin bisa bedside. Sannan yazo ya kwanta ya jawota jikinshi. Washe gari ranar Monday kotu ta yanke wa Ba'ana hukuncin kisa ta Hanyar rataya. Sabida hujja da shaidar daya bayar a kan kanshi. Kana yayi bayanin duk shanayen da yake sacewa daga wannan ƙasar zuwa waccar ƙasar. Ya bada tabbacin duk suna nan. Ya kuma sa yaranshi sun medawa kowa nashi. Domin suma sun musulunta. Bayan kwana biyu aka shirya rataye shi. Bayan anyi komai an fito da shine. Ya kalli taron fulanin Rugar Bani. Cikin zubda hawaye yace. "Dan Allah ku yafe min". Wani irin raunine ya rufesu mai sa zubda hawaye. Kusan a tare sukace sun yafe mishi. Cikin sanyi yace. "Ngd". kana ya juyo ya kalli Sheykh dake gefensa, murya na rawa yace. “Ga dai ƙarshena ni kam, Allah bai nufa zan rayu da Shatu ba. Allah ya ƙaddara matarka ce. Dan Allah ka kula da ita Shatu mace mai rauni da tausayi." Cikin zubda hawaye Sheykh yace. "In sha Allah". Sai kuma ya kalli Bugulu cikin rauni yace. "Mama kin tuna kin min al'ƙawarin zaki musulunta kuma zaki bar sata". Cikin kuka tace. "Nayi al'ƙawari". Da sauri ya kalli Sheykh a hankali yace. "Dan Allah bawa mahaifiyata ƙalmar shahada, a gaban idona in samu in mutu da farin ciki". Cikin zubda hawaye Sheykh yace. "Toh". A nan ya musuluntar da Bugulu. Nan aka rataye shi gaba ɗaya mutane na kuka. Sosai Sheykh da kanshi yayi ta kuka sabida. Amanar kula da Shatu da Ba'ana ya bashi amana. Bayan an rataye shi ne. Droo yayi musu bayanin cewa fa. Ya musulunta tun da dadewa. Hakane yasa Sheykh da kansa yayi masa wonka kana ya limanci sallan gawanshi kana aka kaishi gidansa na gsky.Rayuwa kenan. Shatu kuwa sai dai ta buya tayi kuka, Ummey da kanta tayi tashan kuka. Alhamdulillah bayan rasuwarsa da wata ɗaya. Lamiɗo da kanshi ya shiryawa Sheykh da Shatu da Ummey da Dr Aliyu da Baba Basiru da Galadima su tafi ƙasar Cameroon dan yiwa iyayen Shatu godiya da kuma nemawa Jamil auren Khadijah, dan yana son ranar auren a kuma naɗa Sheykh a matsayin Sarkin Masarautar Joɗa. Alhamdulillah sun gama shirinsu, Washe gari zasu tafine. Batool ta kira Sheykh. Suna zaune da Shatu kiran ya shigo bayan ya ɗagane ta mishi bayani ta ƙara da cewa. "Affan ne ya bani number ka. Alhamdulillah aurena next week Ina gayyatarku ɗaurin aure". Cikin ɗan sake fuska yace. "Masha Allah, Allah ya kaimu in Sha Allah zanzo nida Affan". Cikin jin daɗi tace. "Toh ngd matuƙa Hamma Jabeer". Daga nan sukayi sallama. Da sauri ya sauƙe numfashi ganin Shatu bata kallonshi ma. Ranar litin da yamma jirginsu ya sauƙa cikin ƙasar Cameroon birnin Yahunde. Wasu irin motoci masu tsadar gaskene sukazo suka ɗauke su zuwa gidan Abboi. Suna isa bayan sunyi parking sun firfito gaba dayansu Jamil ne ya ɗan juya....! By *GARKUWAR FULANI*l
*Lamiɗon Adamawa, Dr Aliyu Mustapha jama'ar Adamawa duk suna a gaisheka.😭😭😭 Allah ya jiƙanka da Rahama Lamiɗon Adamawa Dr Aliyu Mustapha. Wannan shafi gaba ɗayan shi sadaukar wane gareka. Jinjina da godiya ga Sarki mai ci Muhammad Barkinɗon Aliyu Mustapha. Allah ya taya riƙe!.!.. Ya juyo ya kalli Shatu dake sauƙe numfashi tare da yin murmushi mai cike da jin daɗin ganin gida. Yah Al'ameen ne ya matso gabansu Sheykh da sauri tare da cewa. "Bismillah mu isa ciki". “Masha Allah” Galadima yace tare da bin bayanshi kai tsaye parlon Abboi na musamman suka nufa. Kana suma saura duk suka bi bayansu. Shatu da Mamey da Ummi da Sara kuwa cikin gida sukayi. Tarba mai cike da mutuntaka akayi musu tare da Kekkyawar mu'amala. Kwana su biyu rak. Suka juyo suka dawo Nigeria, bayan sun gama tsaida batun auren Khadijah da Jamil. Hafsi da Salmanu. Rafi'a da Yah Al'ameen Jalal da Hibba. Bisa mutuntakan da kimar Lamiɗo da tsarin su, na son a ranar za'a naɗa Sheykh a sarautar Sarki Joɗa, yasa duk aka tsara batun ɗaurin auren a Masarautar Joɗa za'ayi shi. Sosai angwayen keta rawar ƙafa abun. Bayan sun dawo da wata biyu. Sosai Afreen ta girma dan yanzu watanta biyar, in ka ganta kace ƴar wata bakwai ce. Rarrafenta ya nuna ko ina zataje, tayi kuɓul-ƙubul gwanin burgewa da ban sha'awa. Kuma yanzu aurensu Jalal saura watanni shida cus da izinin ubangiji. Yau asabar ne, tun safe Sheykh yana gida. Kiran sallan azahar ne yasa ya ɗan miƙe zaune bisa kujerar 3 str da yake kwance. Cikin lumshe ido ya kalli Afreen dake wasanta a tsakiyar falon. Shatu kuwa nata binta zata kamota, ta tubke mata gashin kanta. A hankali ta zauna tare da cewa. "Allah na gaji in biki, nan ki zille can in biki can ki zille nan, na lura sam bakya son a taɓa miki kanki". Murmushi yayi tare da cewa. "Waya sani ko ke ta gado". Da sauri tace. "Sai dai in Junainah ta gado". Miƙewa tsaye yayi yana murmushi. Sai kuwa yayi sauri ya koma ya zauna Kamar wanda aka ture ya faɗi. Da sauri ta miƙe tare da matsoshi cikin kula tace. "Subahanallahi Yah Sheykh lfy kuwa?". Hannun yasa ya dafe kanshi da kai, tare da rumtse idanunshi. Da sauri ta zauna ta jawoshi jikinta, kanshi tasa bisa ƙirjinta cikin sanyi murya tace. "Yah Sheykh baka da lfy ne". Manna kanshi yayi da ƙirjinta murya can kasa, kana ido a lumshe yace. “Ba komai fa Aish kontar da hankali ki". Cikin rau-rau da ido tace. "Ta yaya zan kwantar da hankalina kuma, in ka tsaya kai ɗaya kana shirin faɗuwa na lura da hakan da daɗewa". Ajiyan zuciya ya sauƙe kana a hankali yace. "Lfya ta lau Aish bakiga ma, yadda nake yawan cin abinci ba, bini-bini naci abinci, toh amman kuma wannan karon laulayin da jiri yazo min, musamman in na daɗe a zaune, toh in na tashi tsaye sai inga har duhu yana rufe min ido". Cike da mamaki tace. "Laulayi kuma?". Ta ƙare mgnar cikin zaro ido. Kai ya gyaɗa mata tare da cewa. "Eh mana". Da sauri tace. "Waye mai cikin?” Tashi zaune yayi tare da cewa. "Kece mai cikin mana nine kuma mai laulayin". Da sauri tace. "Na shiga uku Yah Sheykh ciki kuma?nifa tun jinin biƙi ban sake yin jiniba". Kiss ya sakar mata a goshi kana a hankali yace. "Toh kafin wani jinin yazone kuma ciki ya shiga". Cike da al'hini tace. "Yah Sheykh ban ganeba". Cikin tsananin jin daɗi yace. "Allah kuwa Aish kinada ciki, na kimanin watanni uku har ya shiga na huɗu, yana ma gab da fara motsi". Da sauri ta ɗan ja da baya ɗage rigarta sama kaɗan tayi tare da zubawa cikinta ido, ya ilahi ya mujibadda'awati ta faɗa hawaye na kwaranyo mata murya na rawa tace. "Innalillahi Dr. Afreen na da watanta biyar kacal kuma ace ina da ciki, yarinyata zata sha wuya, na shiga uku". Da sauri ya jawota jikinshi ya ruggumeta tsam cikin kwantar mata da hankali yace. “Baki shiga uku ba Aish, al'janna zaki shiga da izinin Ubangiji, aihuwa rahamace Shatu, wasu suna nema ido a rufema Allah bai basuba mu kuma ya bamu. Kuma Alhamdulillah batun Afreen nima da fari hankalina ya tashi so da naga. Ba abinda nonon yayi mata sai ban damuba, ni yamin ma ko kin sani kawai kina ɓoye min ne, sabida kada in sani in nuna farin cikina har Magauta su gane shiyasa baƙi in gaya miki na gane". Cikin zubda hawaye tace. “Yah Sheykh daga haihuwa da kwana arba'in fa kenan na samu ciki". Dariya mai sauti yayi tare da cewa. "Ance miki ni ɗin wasane, bugu ɗaya nakeyi ƙollo ke shiga raga. Gashi kema ɗin ma zalamemmiyace da an baki saiki karɓa. Toh mu godewa Allah kinji ko Mar'atussaliha, muyi farin ciki da abinda Allah ya azurtamu dashi, kiyi Sujjadar godiyar Allah kiyi hamdala sai mu roƙi Allah yasa tagwaye ne, ina kina son ƴan biyu?” Cikin jin sanyi da daɗi tace. "Uhumm sosai ma kuwa Yah Sheykh". Kai ya ɗan ronƙofa ya sumbaci lips ɗin ta kana yace. "Toh Allah ya bamu". Amin Amin tace. Kana yaje yayi al'wala ya wuce masallaci. Ita kuma ta ɗauki Afreen ta wuce da ita. A falo ta samu Junainah ta miƙa mata ita kana ta wuce. Bayan kusan wata biyu kenan lokacin cikin ya cika wata biyar. Sosai ya ɗan fito cas sai kuma tayi yar ƙiba. Afreen kuwa yanzu tana dafa abu ta miƙe tsaye. Aurensu Jalal saura wata 4. Alhamdulillah tana fama da karatunta, kuma wanda yanzu suke shekarar ƙarshe ita da Rafi'a shiyasa ma aka kai bikin da nisa dan Rafi'a ta ida. Tana ruggume da Afreen ta shiga Part ɗin Mamey, dawowarta daga makaranta kenan. Da sauri Mamey tasa hannu. Ta amshe Afreen sai kuma ta kalli Sara dake biye da ita a baya tace. “A'a Sara ya haka, kin barta da jaka da wannan lukutar ƴar tasu". Cikin sauƙe numfashi tace. "Wlh Mamey Afreen na min son inna a soka asha jinin jikinka, wai sai taƙi Sara ta amsheta dole sai ni zan riƙeta". Ta ƙare mgnar tana dungure kanta. Dariya ta karketa kanar tasan abinda akace..ita kuwa Mamey da sauri tace. "Toh Sara ɗauko mata abinci." To tace kana taje ta ɗauko mata. Bayan ta ɗauko ta ɗauki nata ta tafi. Ita kuwa Mamey serilac ɗin Afreen ta dama kana ta fara bata. Tana bata tana kallon Shatu. Sai kuma ta ɗan yi gyaran murya tare da cewa. "Da sauƙi ma ai duk da wahalan karatun da rainon bai sa kin rameba". Kanta ta ɗan sunkuyar ta kalli cikinta cikin yin ƙasa da murya tace. "Toh ba cewa yayi wai inada cikiba". Da sauri Mamey ta danne dariyarta tare da cewa. "Wai ne ma Shatu? Har yanzu a wai yake?". Cikin ɗan jin kunya tace. "Uhum". Nan dai sukayi ta hira daga bisani ta miƙe ta koma Part ɗin ta. Alhamdulillah shirye-shiryen aure nata kan-kama. Tare da shirin naɗin sarauta. Tako ina tako wani lungun da saƙon masarautun gargajiya na Arewacin Nigeria da kudancin, dama maƙotan mu kamarsu Niger, Cameroon, Chadi. Da dai sauransu duk takardar gayyatar naɗin sarautar sabon sarkin masarautar Joɗa ya riskesu. Shiri iya shiri akewa bikin da yake haɗe da ɗaurin auren mutane shida. Cikin Shatu kuwa ya girma ya fito ras, sabida yayi watanni takwas. Afreen kuwa Alhamdulillah tana gudu ko ina yanzu ga gwarancinta ras. Watanninta goma sha ɗaya amman in ka ganta zakayi zaton Yar watanni goma sha biyar ne. Alhamdulillah su Shatu sun kammala karatun su lfy, komai yayi yadda ake buƙata. Hajia Mama kuwa duniya tayi mata atishawar tsaki. Sabida kuturta ya kuma shiga yatsunta na tsuntsayen. A hankali take tafiya Afreen na riƙe da yatsarta. Tana ta gwaranci. "Abba! Abba! Abba!". Murmushi yayi tare da buɗe mata hannunshi da sauri ta tsaki yatsar Shatu ta nufi inda Sheykh ke tsaye, cikin tarin farin ciki yace. "Oyoyo Mamina". Kana ya ɗagata sama. Murmushi Affan yayi tare da cewa. "Afreen sarkin wayo ita kowa natane". Jamil ne yace. "Hmmmm ai ni jiya ta bani mmki. Wai Ance Abbanmu na kiranta zai bata sweet wai sai tace. “Bata so Abbanta a kawo mata". Dariya Ummi tayi tare da cewa. "Kuma daga baya ta bishi da gudu tana Abba cha ciwiut". Murmushi Sheykh yayi kana ya sauƙeta, tare da kallon Shatu dake zaune ta tasa cikinta gaba. Cikin wasa ya kalli Jalal daya shigo yanzu yace. "Jalal ko dai zamu ɗaga bikin kun nanne sai Aish ta haihu zatafi sakewa". Da sauri ya katse wayar da yakeyi da Hibba tare da cewa. “A'a me yayi zafi, tasha zamanta a ɗakinta mun hutasshe ta zuwa bikin". Jamil kuwa kwaɓe fuska yayi tare da cewa. "Uhumm wai a ɗaga". Dariya Affan yayi tare da kallon Sheykh dake musu murmushin wasa nan dai sukaci gaba da tattaunawa kan bikin. Alhamdulillah yau bikinsu Jalal saura mako ɗaya rak. Komai ya kankama. Tuni baƙi sun fara cika masarautar Joɗa tako wani yanki. Hotels din Ɓadamaya Lamiɗo da Sheykh sun kama fiye da rabinsu sabida, sauƙar baƙin da suke tsastsafowa tako wani yanki. Yau jumma'a wanda ya kama sauran kwana bakwai cin a nawa Sheykh rawani jumma'a mai zuwa kenan. Wanda ya kama kuma ranar za'a ɗaura aurensu Jalal tuni su Umaymah da tawagarta sun iso. Tun da safe kuwa yau Shatu ta tashi da ciwon mara, kaɗan-kaɗan. A haka take ta sabgoginta, sabida tana tare da amare duka uku. Sha ɗaya dai-dai na safe Allah ya sauƙeta lfy ta haifi ɗanta na miji santalele. Farincikin a ahlin Sitti ba'a mgn. Bayan an gama kimtsa mai jego da jaririnta kato fari ƙal dashi.
Suna kwance Sheykh ya shigo. Cikin tarin farin ciki dan yana gidan Malam Abubakar ne Yah Jafar ya kirashi ya masa al'bishir.
Cikin jin daɗi ya zauna gefen Shatu. Tare da miƙawa Safiyyah hannu ta miƙa mishi jaririn murya cike da zallan farin ciki yace. "Alhamdulillah masha Allah. Allah na gode maka, da wannan kyauta da kaimin. Ya Allah kasa baɗi iwar haka mu samu tagwaye". Dariya sukayi baki ɗayansu ganin yadda Shatu ta zaro idonta cikin alamun tsoron tace. "Wayyoooooooo Allah na. Yah Sheykh sai kace wata inji". Aunty Rahma ce tace. "Ato ai da alamar hakan zakuyi tunda gashi a shekara ɗaya an samo irin tagwayen Nana Faɗima". Ummi ce dake gefe tana fifitawa Shatu tea tace. "Ko ƴan ukune Allah ya kawosu akwai masu tayaki rainon su. Inji gashi yanzu Afreen tunda aka yayate, sai dai tazo ta leƙaki tayi gaba abinta". Da sauri yace. "Uhumm yauwa Ummi na gaya mata dai". Ya ƙare mgnar yana sumbatar goshin yaron cikin tsananin farin cikin da son yaron. Sai kuma ya kalli Mamey dake shigowa yace. "Mamey da waye yake kamane?".
Matsowa gabanshi tayi ta kalli fuskar jaririn kana tasa hannunta ta tallabo tashi fuskar. Cikin jin daɗi tace. "Da kai yake kama". Cike da jin daɗi yace. "Alhamdulillah".
Nanfa akaci gaba da hidima.
Yau kwana biyu da haihuwar Shatu. Zaune yake agaban Mamey da Abbanshi, kai ya ɗan ɗago ya kalli Abbanshi tare da cewa. "Ummm Abba nace wanne suna za'a sawa yaron?". Murmushi mai cike da jin daɗi Abba yayi tare da cewa. "Na baka zaɓi zaɓawa ɗanka sunan da kafi so". Murmushi mai cike da jin daɗi yayi tare da cewa. "Mamey kefa, ko Jadda kikeso inyi mai suna". Yayi mgnar cikin raha. Da sauri tace. "Mutun da ɗan shi mun baka damarka a matsayinka na uba". Kanshi ya sunkuyar tare da cewa. "Ngd matuƙa da wannan damar". Daga nan ya sallamesu ya miƙe ya fita.
Bedroom ɗinsa ya wuce. Yana shiga ya kira Shatu a waya, ta kawo mishi ɗan. Yayi mishi huɗu ba. Ido ta ɗan zuba mishi tare da cewa. "Me sunanshi?." Murmushi yayi tare da kashe mata ido a hankali yace. "Sai ranar suna zakiji". "Abinma sirrine kenan". Ta faɗi tana murmushi. "Ina da wani sirrine bayan ke, Y.M.D.G na". Ido ta zuba mishi tana mai nazartar baƙaƙen da yake yawan faɗi wasu lokutan. Kiranshi da akayi a wayane yasa ta bar zancen.
Ranar jumma'a, da safe bayan an fito sallan asabu, aka raɗa sunan yaron kana suka nufi cikin gida kowa na mamakin sunan da Sheykh ya sawa ɗansa. A tare suka shiga falon shida ƙannensa.