Gurbin ido complete hugumah - Chapter 18
Gurbin ido complete hugumah Chapter 18: Gurbin ido complete hugumah Chapter 18. A hanya ita kadai kamar ta taune zuciyarta saboda baqinciki,haka ta fitoma…
3,365 words
A hanya ita kadai kamar ta taune zuciyarta saboda baqinciki,haka ta fitoma daga gidan babu wanda ta yiwa sallama,duk irin bautar da khalid din kewa annin har yau bata jin tana masa rabin son da takewa ja'afar,a bakinsu shaffa'u takejin kamar ya soma son yarinyar amma annin ta hanashi ta bawa ja'afar,duk da bata taba jin qaunar yarinyar ba amma taji zafin hakan,hakanan ta hana hafsat ja'afar ta bawa wasu baare daban,wannan babu abinda yake nunawa illa zallar qin da take mata,qwafa taja gami da dogon tsaki,zata gamu da khalid dinne.
"Allah ya sawwaqe,ya yaye miki munubiya" anni ta fada tana jan wayarta
"Shima zan gamu dashi,shegiyar kafiya da riqon abu a rai,wannan wanne irin SO BAYAN RAI ne?,tana nan tana yaqi a kansa bai sani ba,tana ta baqin jini wajen jama'a.
Tana ta bulayin nemansa khadim ya shigo
"Kiramin jafaru da wayarka"
"Allah yasa ya daga,na canza sabon layi" ya fada yana laluben wayar a aljihunsa,sannan ya zauna daga gefan annin yana tambayarta me zaya samu cikin dakin nata
"Ban sani ba,zaka kamomin shi ko sai ka cinye kurwata tukunna" ta fada tana harararsa,don tace khadim din ya cuka kwadayin tsiya,yana qunshe dariyarsa ya dannan kiran ja'afar din,saidai har tayi ta tsinke bai daga ba,sai da ya maimaita kiran ana uku ya dace ya daga,kai tsaye ya miqawa anni wayar ya koma corner falon yayi zamansa yana daukar wayar annin.
Dan madaidaicin waje ne dake bayan gine ginen gidajen nasu,wanda ke shimfide da korran ciyayi,kujerun qarfe ne masu kyau guda uku da table dinsu a tsakiya,saman table din akwai glass cup daya cika da lemo yana kurba time to time,tsaye yake ya baiwa table din baya,hannuwansa riqe da wasu fararen takardu kusan guda shida,wanda ya bada hankali sosai a kansu,da alama akwai muhimmin abu da yake dubawa a ciki,sanye yake cikin shirt da trouser masu taushi duka na kamfanin Louis Vuitton,iskar wajen ta gauraya da daddadan turaren jikinsa tana bada wani yanayi me dadi,wasu slippers ne masu kyau na fata sanye a qafarsa,hannayensa goye a bayansa,lokaci lokaci yakan cire hannun ya shafi tausasan labbansa.
Karamin tsaki yaja sanda wayarsa ta sake qara,karo na kusan uku kenan,sauke takardun yayi daga fuskarsa a hankali,kyakkyawar fuskarsa dake fidda wani irin kwarjini da kuma calmness irin nashi ta bayyana,taku biyu yayi baya ya isa gab da table din inda wayar tasa take,har yanzun wani busar sarewa take me dadin sauraro.
Sai daya kalla screen din some few seconds sannan ya shafa wayar ya karata a kunne
"Assalamu alaikum" ya fadi with husky voice,daga can bangaren anni ta amsa,saiya dan sauke numfashi kadan jin anni ce,ya maqale wayar a kafadarsa yana gyara takardun bayan ya soma da gaisheta
"Lafiya alhmdlh,manya,me yasa kake mancewa da gida?"
"Taya zan mance daku anni?,akwai abubuwa ne da har yanzu bayi settling dinsu ba" haushi ya cikata,koda yaushe maganarsa kenan,to itakam koma meye dai ai ta kawo qarshen abun,don haka cikin kaushi tace dashi
"Kullum maganar dai kenan,tamkar kaine kafi kowa sabga a duniya,to koma dai meye wannan matsalarka ne,mukam ba zamu zauna mu zuba idanu rayuwarka taci gaba da tangal tangal a haka ba,bayan ko talatarka bakaci ba balle laraba,ban sani ba ko dan uwanka ya labarta maka" ta sauke maganar tana jiran amsarsa,dai dai sanda ya gama gyaran takardun ya duqa yana niyyar ajjiyesu saman table din
"Me kenan?"
"Kai kudin aurenka wa 'yammata biyu,nan da sati hudu kuma in sha Allahu kowacce zata shigo gidanka a matsayin matarka,saboda haka ka maida hankalinka,ka tattaro kayo gida,koma meye daga baya zaka qarasashi"
"What a funny story anni" ya fada cike da tantama yanayin fuskarsa na sauyawa zuwa ga yanayi na son yin murmushi,saisai murmushin bai fita ba,saboda yadda yaji labarin yafi masa kama da tatsuniya
"Anni,zancan aure fa kike da mata har biyu" ya fada sounding like dariya zata kubce masa,yanayin da anni tagama karantoshi tsaf,saita hade muryarta itama
"Kafi kowa sanin wacece maryama farouq akko ko?"
Yes,yasan anni fiye da kowa a gidan dama family dinsu,tuna hakan ya sanya duk wani shakku dake ransa wankewa,uwa uba yadda ta kirayi sunanta in full ya sake tabbatar masa she's serious
"Seriously?" Yayi tambayar da wani irin tune,tambayar da baisan dawa yake ba,da anni yake koda kansa?
"Inadai gaya maka,sati hudu kacal suka rage"
"Ya salam ya Allah,anni why?, Me yasa?,mu nawa ke zaune a gidan,amma why me?" Ya fada yana jin wani irin zafi na taso masa har saman fuskarsa
"Bakai kadai ba,wannan karon duk wanda yakai munzali sai ya bar gidan nan ya tafi nasa,abun ya isa hakanan"
"Okay okay fine.....zan dawo zanyi packing komai nawa zan bar gidan,but..... please anni,kada kiyi punishing nawa ta wannan hanyar,bazan iya zama da kowacce mace ba anni please" ya fada cikin kwantar da murya,tare da fatan zai shawo kan annin.
Baki ta tabe daga can,dama tasan za'a rina,tasan halin ja'afar sarai,tasan komai zai iya faruwa,kuma dama bata tarki abun ba sai data shirya masa
"Kaga babu fa wannan zancan,an riga an gama magana da magabantansu,ba zaka maidamu qananan yara ba,kuma ba gidan mukeso ka bari ba,zaman aure mukeso kayi" zaman aure kamar wani mace?, Ya qiyasta hakan cikin ransa
"Anni,ki fahimceni mana,ta yaya za'a auramin mata har biyu bayan babu fahimtar juna a tsakanina da kowaccensu bare azo maganar soyayya wadda already nayi banning dinta"
"Zaku fahimci kawunanku a dakunanku ai" ya zuwa yanzu ranshi ya sake baci fiye da dazun
"Anni!" Ya kirayeta da murya mai kaushi kadan,wanda shi kansa baisan yayi hakan ba "it will not be possible,ta yaya hakan zai yiwu?"
"Ahap gashinan kuwa?" Da gaske take ba zata fahimceshi ba,saidai ma idan bai wasa ba ta sake tunzurashi,don haka sai kawai ya yanke wayar da sauri,sannan cikin wani irin zafin nama yaja kujera guda daya gabansa ya zauna a kai bayan ya jefa wayar saman table din,baya ko tsoron ta fashe.
Dukka hannayensa ya cusa cikin gashinsa yana yamutsawa tare da fadin
"No...no,it can't.....it can't.....am not ready.....am not ready to face it this challenge" ya fada cikin zafi,sai kuma ya sake miqewa,yana buqatar yayi magana da wani,sai ya janyo wayar yana furzar da zazzafar iska daga bakinsa ya soma laluben number ammansa,gab da zata shiga ya sauya shawara ya kashe,sai ya maida kiran kan jabir
"Where are you?" Ya tambayesa kai tsaye,tsabar bacin rai yama manta inda yace masa zaije,tunda jabir din yaji muryarsa yasan cewa akwai matsala,cikin ransa yake fatan Allah yasa ba depression mode dinsa ne ya motsa ba
"Am on my way,is there a problem?"
"Zaka dauki mintuna nawa?"
"Few" ya amsa masa a taqaice
"Okay,am waiting for you, please don't stay long" bai jira amsarsa ba ya katse wayar ya sake jefata inda ya dauko,dukka hannayensa ya zura cikin aljihun wandonsa,yahau kai kawo tsakanin wannan bangaren zuwa wancan,wanne irin hukuncine wannan da zasuyi masa?,wannan auren aiko mace a wannan zamanin ba za'ayi mata shi ba,wadanne irin mata ne su kansu da suka dauki kasadar aurensa ba tare da sun gana dashi ba?,kawai sun amince da auren mutumin da bashi ya nema yardarsu ba?,anni tana tunanin akwai macen da zata cike masa GURBIN shaheeda ne?,babu?,sam babu,yanajin cewa daga kanta an gama haifar diya mace a duniyarsa,wadan nan matan data debo GURBIN IDO ne kawai,fanko ne,ba zasu taba zamtowa IDO ba wato shaheedansa,yayi imani da hakan har cikin zuciyarsa.
Kafin jabir yakai ga isowa ya duba agogo sau babu adadi,a gaban idanunsa cave ta saukeshi,ya fito dauke da niqi niqin siyayya a manyan ledoji,sai a sannan yayi noticing wani abu,kwana biyun jabir fita yake siyayya kusan koda yaushe,kamar wanda ke shirin komawa gida.
Sai daya shiga gida ya aje kayan sannan ya sake fitowa,kafadarsa ya dafa daga baya
"Meye haka ne man?" Waiwayowa yayi ya dubi jabir,idanunsa a sannan har sun kada sun sauya kala saboda zallar bacin rai,wanda ta nan ake iya gane qurewar bacin ransa
"Yanzu kamar ni?,kamar ni anni zatayi forcing dina akan aure?" Tuntuni ya shanshano komai,don yasan da komai din,ya samu labari,saidai baiyi gangancin shaidawa ja'afar din ba,ya zuba idanu yaga ya caftar zata kaya.
Dubansa sosai jabir yayi
"That's right...." Sosai maganar ta baiwa ja'afar mamaki,ta kuma sake qular dashi
"Like how? what are you trying to say jabir?" Ajiyar zuciya ya sauke,shima ya maida hannayensa aljihunsa
"Ja'afar,ka gaza nutsuwa ka karbi qaddarar rayuwarka kayi moving forward yadda ya dace....."
"Yanzu qoqarin me nake?" Ya fada da zafinsa
"Yes,naga canji,kanata qoqarin maida harkokinka yadda ya dace,amma bata iya wannan fannin kawai ya kamata ka maida kai ba wajen gyarawa,ya kamata ka sake building a new family da zasu debe maka kewa,su sake maidaka cikakken mutum,abinda kai ka gaza yi anni ta tayaka ginashi,so bai kamata ka zargeta ko kaji haushi ba,a shawarce ka tsaya ka nutsu,ka yiwa abun kallo na fahimta,don't upset please"
"Okay na gane,kaima kana goyon bayan abinda tayiminkenan?, wait.....waima wa yace musu a yanzun ina sa buqatar wata mace cikin rayuwata?,dolen sai na rayu da wata,a barni nayi rayuwata a haka mana,me na ragu dashi" jabir zai sake cewa wani abu ja'afar din yaja tsaki ya daukin wayarsa a fusace ya wuce cikin gida da sassarfarsa.
25
Kamar jabir din ya shareshi,sai kuma ya kasa,ko babu komai yana buqatar kwantar da hankalinsa kada kuma ya birkice musu a koma 'yar gidan jiya,bayan abubuwan suna danyi kyau ba kamar can baya ba,don haka sai ya kwasa shima ya bishi.
Cikin rashin sa'a ya sameshi ya kulle kansa a dakinsa,yayi ta bugu ya bude masa amma yayi kunnen uwar shegu dashi,ya sani ya qulu sosai,kuma cikin bacin rai yake,haka dole ya haqura,saidai yana fatan kada ya jima a kulle a dakin temper tayi masa yawa.
Komawa yayi ya zauna saman kujerun falon,kam kujerar dake fuskantar dakin,lokaci lokaci yana danna wayarsa yana kuma duban qofar dakin tare da fatan ya bude,saidai har kusan awa guda da rabi ba motsinsa ko alamar budewa,abun da yadan saka jabir yaji shakka a ransa,sai ya sauka daga game din da yakeyi don dama ta fara isarsa,ya kirayi layin anni.
Gaisawa suka fara yi sannan ya gaya mata abinda yake faruwa,duk da taji fargaba itama cikin ranta amma saita dake
"Rabu dashi,zaiyi ne ma ya gama,kayi sabgarka,idan ya gaji ya fito" ta fada cikin dakiya,murmushi jabir yayi,don shi kansa yasan dakiya kawai annin tayi.
Suna gama wayar ya isa ga makunnin kayan kallonsu ya kunna tv din,sannan ya maida channel din dake kai zuwa saudi qur'an da madaidaicin sauti,ya ajjiye remote ya wuce dakinsa ya sauya kayan jikinsa daga shi sai farar singlet da boxer,ya fidda siyayyar da yayo,yakai daki sa,saura kuma ya wuce kitchen dasu.
Abinci ya fara shirya musu,yana aikin amma hankalinsa yana falo,yana yi yana leqawa ki ja'afar din ya fito,saidai har ya gaji da leqan baiga ya fito ba,tilas ya haqura har ya gama abincin.
Yana fitowa daga kitchen din yana qoqarin fidda afron din jikinsa jaafar din na fitowa a dakin,sosai jabir din yaji dadin hakan,ganin fushin baiyi tsaho ba,a yanzun ma ya sake wanka ne don kayan jikinsa na dazun ba sune yanzu ba.
"Ina zuwa?" Jabir ya tambayeshi yana fidda ruwa daga fridge
"Zamu fita da mr mickey,akwai meeting da zamuyi,so if i stay long kada ka jirani"
"Abincin fa?"
"Ka cinye kayanka" dariya ce ta qwacewa jabir,ya sani fushi yake dashi,yaji haushin that's right da ya fada,da kuma goyon bayan anni da yayi,fushinsa ne ya shafi abincinsa
"Cikinka ba nawa ba" ya bashi amsa sanda yake takawa zai fita daga falon,saidai bai waiwayo ba ya fice abinsa,kamar ma baiji abinda jabir din ya fada ba.
Diban iya wanda zai isheshi yayi ya sanya masa sauran a fridge,yasan idan ya dawo zai nema abincin da kansa,don duk abin nan nasa baya wasa da cikinsa ko kadan.
Shirye shirye ake gadan gadan daga gidan dr marwan akko na aurar da ja'afar din,wanda tun ranar da sukayi waya da anni bai sake neman kowa ba,kamar yadda itama annin ta watsar dashi,hakanan daga ita har dr babu wanda ya sake nemansa,shima hakan yayi masa,don kuwa ya riga ya gama shiryama ransa komai,baiga ta yadda yana namiji me cikakken hankali,ba auren fari ba za'ayi masa irin wannan karan tsayen,ya tuhumi kansa da kansa kan ceqa ya bawa anni dama ne da yawa cikin rayuwarsa shi yasa tayi wannan tunanin,bama su da suke nigeria ba,hatta da jabir baibi ta kansa,ya shiryama ransa zai koma nigeria ne a duk sanda ya gama uzurorinsa a nutse.
Ta bangaren jabir kuwa duk da ya damu,yana kuma ankare da abinda ke faruwa amma bai nuna ba,shima shirin tafiya gida yake,saboda a yanzun aurensu su biyu za'ayi,sbi da ja'afar din,anni taso a hada harda su salma amma sai aka samu tsaiko,hisham bai fidda gwanarsa ba,hakanan salma tana kan qadamin kammala nata karatun ita da hafsat da kuma laila,don haka annin tace a barshi zuwa sanda zasu gama din watanni shida nan gaba masu zuwa.
********Dai dai lokacin da suke shigowa farfajiyar gidan sanye da hijabansu na makaranta suna taba hira,motar dake fake a parking lot na gidan ta tsaya,mamallakiyar motar ta budeta ta fito.
Zabgegeyar farar bafulatana,fara tas,wadda kamanninta da haj aishatu ta nuna qwarai,sanye take da wani danyan lace daya kwanta a fatarta,komai na jikinta matching ne,jikinta ba abinda yake sai fidda wani tatausan qamshi,tana rungume da baby boy wanda duka duka bazai wuce shekara daya da watanni biyar ba.
"Auty maama" 'yammatan suka kusa hada baki wajen kiran sunanta,tana rufe motan da key ta waiwayo tana dubansu,fuskarta ta wadatu da fara'a sosai,macace m'abociyar fara'a da kuma kirki,bata debo a qasa ba,ta debo kyawawan halayen mahaifiyarta haj aishatu umar sanda da kuma dr marwan akko
"Yammatan gidan baaba dr" ta fada sanda suka qaraso gaba dayansu,murmushinsuka sako,don dukkansu sunji dadin zuwan nata,saboda akwai shirye shiryen da suke akan bikin gidan,wanda sun tabbatar bazaiyi armashi yadda suka tsara ba saita ce wani abu,a matsayinta na babbar yayarsu,wasu na shirin amsar yaron hannunta,yayin da khadija ta amshi hand bag dinta,suka soma rankayawa ciki bayan sun gaisheta hira ta balle.
"Ina kuka baro maimunatun kuma yau?" Anty maama ta tambaya sanda suke gab da shiga ainihin ginin gidan,inda zao sadaka da qofar kowanne sashe dake cikin gidan,sai a sannan suka laluba suka ga ba maimunatun,da alama guduwa tayi saboda anty maaman
"Tare muke guduwa tayi halan,kinsan halinta,halim fulani ne har yanzu a jikinta,bada kowa yanzu take iya haduwa cikin gidan nan ba,hatta amma wasan buya sukeyi" murmushi ya kufcema anty maama,kunyar yarinyar da kamun kanta yana matuqar burgeta,duk da a cikinsu take amma bata yada dabi'ar kunya ba,har yanzu yarinyar batasan hanyar gidanta ba,da hirar maimunatun suka rakata ta gaida ammi sannan ta isa sassan mahaifiyarta amma,bayan ta aikawa anni da saqon gaisuwa gami da sanarwar ta iso zata shigo.
"Ina duka yaran?" Amma ta tambayi anty maama
"Suna islamiyya,amma for now nasan ma sun taso,nace ma iliyasu driver ya wuce dasu wajen haj,idan na dawo zan biya na debosu"
"Yayi kyau,Allah ya taimaka" amma ta fada,don ba wani dogon hira suke da ita can can ba,kasancewarta diyar fari a wajenta
"Wai maimunatu nita gani ta gudu amma?" Anty maama ta fada tana dariya,sai amman tayi murmushi
"Kyagaji da gani indai maimunatu ce,yanzu ko sassan nan bata zuwa" kai anty maama ta gyada,kamar ba zata ce wani abu ba sai kuma ta magantu
"Allah dai ya tabbatar da alkhairinsa,ubangiji yasa ta zame ma rayuwar ja'afar haske,nafi sanya hope a kanta amma akan samiha gsky,duk da ba'asan maci tuwo ba sai miya ta qare,Allah yasa dai manya ya riqesu da kyau" ajiyar zuciya amma ta sake,don abinda taketa tsoro da fargaba kenan,musamman da yadda kwanaki suketa matsowa,amma bataji.batun dawowarsa ba,koda kuma sunyi waya baya ce mata komai kan dawowar tasa ita kuma bata taba tambaya ba saboda.kara da kuma alkunya,amma dai duk sanda tayi sujjada tana gayawa Allah,wannnan shike bata nutsuwa.
Bata jima sosai ba tace bari taje wajen anni ta fita a sashen.
Bayan gama gaisuwa da 'yar tsokana da wani lokacin take kwasan annin da ita,sai anni ta kirayi sunanta
"Inaso kiyimin total na kayan jere dana kitchen,babanku ya buqata,zai siyawa maimunatu"
"A ina anni" "Oho,wani kamfani ne yace anan da suke kawo kaya daga turkey,da so yayi aje can direct,to kuma lokacin ya qurace,danginta daga can gembu sun nema ya barsu suyi kayan,yace ai diyarsa ce,duk da haka saida suka aiko da kudin kayan,to nace gwara a siya wani abun me daraja da kudin a bata,tunda shi yayi niyyar yin kayan"
"Ma sha Allah,abbi ya kyauta,kuma hakan yayi,ko gold ne sai a siya mata,ba matsala anni" ta amsa mata tana fiddo wayarta daga jaka
"Yauwa,sannan kuma,bashi nakeso ki bani" kai ta daga tana duban anni tana 'yar qaramar dariya
"Me zakiyi da bashi kuma tsohuwa,bayan duka lalitar familyn farouq kumo na hannunki"
"Ke banson iya shege,kiyi ta kanki,magana nake miki ta gaske,aron kudi zaki bayar,amma ni ba kawomin zakiyi ba,lefe nakeso ki hada na maimunatu dana samiha,banason sanya kudina nazo na kasa tambayar jafar,idan nakine sai nafi maida kai ya maida miki kudinki akan kari,so nake komai yayi da kudinsa saboda sai yafi jin auren a jikinsa" dariya anni ta bawa anty maama,ta wani fannin kuma jikin anty maaman yayi sanyi
"Wai har yanzu baice komai ba?,baya cewa komai?" Kai anni ta jin jina
"Eh,amma ki barni dashi,idan yasan wata ai baisan wata ba,kallonsa kawai nakeyi,zai shigo hannuna ne,baisan wace maryam kumo ba har yanzu" ajiyar zuciya anty maama ta saki
"To Allah ya kyauta,ya kuma shiga lamarin"
"Ameen ya hayyu ya qayyumu,jabiru ya turo nasa kudin ta hannun hisham,duk da naji yace akwai wasu kayayyakin daya siya musu shida jafar din,daso yayi ya biya harda na jaafar din na hanashi"
"Eh gwara da bai biya din ba,gaskiyarki anni,gatan sai yayi masa yawa ya gaza riqe abun da muhimmanci"
"Shina gani ai" anni ta fada da qwarin gwiwa,shi yasa takeson anty maama din,saboda tana da matuqar hankali da nutsuwa
"Ba damuwa,naga wasu akwatuna sabbin design masu goma goma,zan siyawa jabir a matsayin gudu mawata,shi kuma zan siya masa set daya,set daya kuma zan saka cikin lissafinsa"
"Yayi dai dai,Allah ha saka miki da alkhairinsa kema,ya qara muku zumunci,Allah ya qara hadamin kanku" anni ta fada cikin jin dadi
"Ameen summa ameen" daga nan suka shiga tsara yadda komai zai kasance daga kan kayan lefen zuwa sauran hidimomi na bikin,harda yadda za'a gyara maimunatu duka anni ta dora saman wuyan anty maama.
Bayan ta gama da anni kuma ta koma bangaren qannenta,a sannan su salma sun shigo,nan suka zauna suka tsara komai bisa tsari da kuma burgewa,saidai har suka ci suka cinye hirarsu babu giccin maimunatu.
Can cikin garden na gidan ta boye kanta,batajin komai a kan auren tunda batasan meye gundarin abinda ya qunsa ba,bata gama wayewa da sanin meye shi ba,bata saba da zabin abubuwa a rayuwarta ba bare tace wannan zabin bai mata ba,kota damu,kawai dai tana jin kunya da kuma nauyin mutan gidan,tunda tasan meye surukuta,ta gefe guda kuma wani lokacin zuciyarta nayin rawa da kuma d'ar d'ar,tunda ta sani cewa kowacce mace tana auren namijin daya ganta yace yana sonta,itama ta maida masa martanin tana sonshi,amma ita nata angon batasan wanne kala bane,daga wacce duniya zaizo?,yaya kuma zai karbeta?,wadan nan sune kawai abubuwan sa takan nanatawa kanta lokaci zuwa lokaci,saidai yadda taga kowa ya daukaki abun a gidan yana bata mamaki,sannan yadda su laila ke sanyata a gaba,suyita gaya mata abubuwa game da angon nata sai ta yita mamaki,don ita bataga alfanun hakan ba,kiyi kaza kiyi kaza,kullum maganarsu kenan,sun canza mata abubuwa masu yawa,kama daga manta turarenta sa sauransu,itakam duka bataga wannan takurar da tsare tsaren na meye ba,badai a daura aure bane kawai a kaita can gidan ba shikenan dai?,amma magana daya biyu sai suce kina da kishiya,saikinyi kaza kinyi kaza,itakam bataga wani abun damuwa da damun kai ba.
********Cikin tsari ilimi da kuma gogewa anty maama ta hada lefe na alfarma,kowacce amarya ta rabauta da akwati goma goma,rana daya aka kai na samiha dana amaryar jabir Aaliya,said kuma kumbo da ammi abokiyar zaman amma ta qarawa kowacce amarya guda hurhudu,shima kowanne shaqe yake da kayan al'adun aure dana zamani,abun dai ya qayatar ya kuma bada sha'awa sosai.
Tarbar girma suka samu daga kowanne bangare na gidajen amaren,suka dawo gida suna yabon tarbar da suka samu,suna kuma tattauna yadda suka fuskanci dangin hajiya Aayah dama ita kanta haj aayah din keji da samiha,kasancewarta diyar fari a wajenta da zata fara aurarwa,su uku kuma kacal Allah ya bata.