Gurbin ido huguma complete - Chapter 10
Gurbin ido huguma complete Chapter 10: Gurbin ido huguma complete Chapter 10. "Ki buda mana maimunatu kici?,ko bakison irinsa?" Dan qaramin murmushi ta…
3,330 words
"Ki buda mana maimunatu kici?,ko bakison irinsa?" Dan qaramin murmushi ta saki ta girgiza kai,sai ta buda ledar a hankali,laila ta bita da kallo,wani irin kyau fuskarta ke fitarwa fiye da wanda take dashi duk sa'ad da tayi murmushi,janye idanunta tayi,tana gyara zamanta yadda zataji dadin ci gaba da danne dannenta,zuwa lokacin maimunatu ta fara kaiwa cikinta abincin.
Yawan wanda yaci sai yasa ta dinga jin kunyar suga ledar,ita kanta tayi mamaki qwarai,amma kuma daga bisani da taga laila sabgarta take a tab dinta,anni kuma ta koma baccinta sai ta sake itama.
Duk yadda taci burin ganin hanya tun daga adamawa zuwa gombe amma sai da bacci yayi mata tsiya,tana gama cin abincin jikinta ya mutu murus,tsohuwar yunwar data jima a jikinta ta kwanta,tsohuwar gajiya kuma ta shekara da shekaru,basussuka baccin da batasan adadin yawansu ba suka taso mata haiqan,bata shirya ba baccin yayi awon gaba da ita.
*GOMBE STATE*
*_G R A GOMBE_* _DR SULAIMAN KUMO ROAD_
_Dr marwan khalid akko residence_
Katafaren gida ne wanda ya amsa sunansa ta kowacce fuska,irin ginin da aka yishi ba don alfahari fariya ko taqama gami da almubazzaranci ba,gini ne na ma'ana da sanin rayuwa da kuma abinda duniya ke ciki,duba daya zaka yiwa gidan kasan cewa daga zubi da tsarinsa ginin ya zaunu matuqar zaunuwa,hakanan yakan dauki hankalin mafiya yawan jama'a,tun baka ma shiga cikinsa ba.
Gidane dake dauke da sassa guda hudu,biyu na matan gidan,daya kuma mallakin me gidan,yayin da daya bangaren ya zama mallaki ga mahaifiyar me gidan wato haj maryam Farooq kumo.
Gaba daya gidan mallakin dr marwan khalid akko ne,babban limamin gombe gaba daya,shararre kuma sanannen dan kasuwa,wanda Allah ya yiwa baiwar arziqi dama dukiya gaba daya,gami da tarin ilimin addinin islama wanda shi ya kaishi ga zama cikakken dr,hakanan ta fannin boko din ma ba'a barshi a baya ba.
Wani irin mutum ne da Allah ya yiwa baiwar kwarjini da kuma farinjini,mutum ne me amfani da ilimin addininsa ainun,mai yawan taimako sadaka da kuma kyauta ma gaba daya,dukka sirrin nasararsa ya ta'allaqa ne ga mahaifiyarsa,jajirtacciyar uwa da bata daukan raini ko kuma wargi komai qanqani,tsayayya akan 'ya'ya da kuma jikokinta.
Marwan shine babban d'a a wajen haj maryam anni,hakan ya sanya yayi mata matsuguni cikin gidansa tun bayan rasuwar mahaifinsu,kuma dama shi din mutum ne mai matuqar qaunar mahaifiyarsa
da kuma qawa zuci,hakan ya sanya itama haj maryam anni ko cikin yaranta tafi ji dashi,duk da cewa dan fari ne ba auta ba,autansu alhj sagir yaso daukarta ganin kamar shi yafi dacewa,amma gaba daya ya hanasu hakan,yace shi yafi cancanta tunda shine babba.
Matan Dr marwan akko biyu,akwai haj Aishatu,wadda take da yara bakwai dashi,diyarta ta farko macace mai sunan anni wato maryam suna ce mata maama,sai ja'afar d'a na biyu a wajenta,wanda ya zamto halitta mafi soyuwa a wajensu,duka sauran mata ne,salma,hafsa,nadiya,safina,sai autansu namiji khadim,daya dakin kuwa dakin amarya umamatu tana da yara hudu ne,suma din mata ne,fa'iza ce babba,sai khadija,zahra'u,sai mai sunan yuuma rahama suna ce mata baby.
Tsakanin aishatu da suke kira da amma da kuma umamatu da suke kira da ammy zama ne na fahimtar juna da kuma zaman lafiya dai dai gwargwado,yadda Allah ya dorawa kowa son ja'afar haka ammy ke qaunarsa,shi din dan gidanta ne tun farkon zuwanta gidan,amma kuma ta tattara ta miqa mata shi,shima kuma ya dauketa kamar uwa a gareta.
*_Ja'afar marwan khalid akko_*
matashin saurayi kuma matuqin jirgin sama,mai jini a jika,wanda Allah ya yiwa baiwar qira ta jiki,bashi sahun dogaye ko kuma gajerun maza, moderate ne,yana da murjajjen jiki mai siffar qarfi dake nuna shi din ma'abocin gym ne,kalar fatarsa ruwan tarwada ce,wadda ta samu kulawa ta gasken gaske take bada wani irin launi mai daukan hankali matuqa,baya tara suma kamar yadda shi din ba ma'abocin yin aski bane,saidai yadda yake barin sumar kansa zuwa habarsa da kuncinsa abun yana da matuqar qayatarwa da kuma daukar hankali,Allah ya zuba masa wani irin mugun kwarjini wanda yake qara masa kyau haiba da kuma cikar kamala,yana da wani irin farinjini na musamman,bawai a wajen mata kawai ba,a'ah.....hatta a wajen al'ummar gari gaba daya.
Dan gayu ne na gasken gaske,gayu wanda ake kira gayu bawai muna gayu ba,mai tsananin tsafta ne daya tsani qazanta dama qazami,yana da tsari da kuma dokoki da ya sanya ba kowa ke iya mu'amala dashi ba,kamar yadda shima bada kowa yake iya mu'amala ba.
Miskili ne ajin farko,irin miskilancin da zakayi tunani bebe ne ko kuma kurma,magana ko hira bata daga cikin abubuwan dake burgeshi,abu ne mai wuya ka zauna dashi kaji wata doguwar magana a bakinsa,sau tari yafi ganewa amfani da body language,kamar wani me ciwon baki ko kuma mara lafiya,yana da tsananin kamewa da kuma tsare gida,akwai jinin sarauta sosai cikin jikinsa,hakan ya sanya yake da izza da kuma rashin daukan raini,bai yarda da qasqanci ba,yana da neman na kansa sosai,mahaifiyarsa diya ce ga turakin akko,yana da matuqar girmama na gaba dashi,komai qanqantar shekarun daka bashi,duk da mutane da yawa sun masa shaidar wulaqanci da kuma girman kai.
Mutum ne mai tsanani ta fannin so ko qi,bai iya so ba,hakanan bai iya qiyayya ba,idan jininku bai hadu ba ka fita a hanyarsa kawai shi yafi maka alkhairi,yana tsananin son mahaifiyarsa fiye da kowacce halitta a duniya,mahaifinsa da kuma anninsa suke da gurbi na biyu,don yakan kasa tantance cikinsu wa yafi so?,sannan gwaggwo sadiya qanwa ga anni,akwai mutanen da yake ganin kima sosai cikin rayuwarsa da zamantakewarsa.
Jabir shine qawa kuma amini ga ja'afar,d'a ne ga qanin mahaifin ja'afar,mahaifiyarsa ta rasu ta barshi sanda ta haifeshi ko juyawa taga abinda ta haifa bata yi ba,akwai aminci sosai tsakaninta da mahaifiyar jaafar,kuma rana daya aka haifesu,don haka ta dauka jabir ta hada jaafar ta riqesu gaba daya,duk da taso qwarai ta shayar dashi kamar yadda ta shayar da jaafar amma anni ta hana,tace tayi haquri,yasha madara,saboda gudun samun matsala anan gaba,idan hakan ta faru zata haramta masa duk wata 'ya da ita din zata haifa jaafar yace yanaso,ko kuma wata daga cikin 'ya'yan 'yan uwanta,ba'asan kuma me Allah zaiyi ba,dukkansu sun gamsu sun kuma fahimta,taci gaba da bashi madarar,madarar kuma ta amsheshi sosai,ya tashi tubarkall,dashi da jaafar me shan nono babu bambamci,sun tashi tamkar 'yan biyu,don haka ma ake ce musu,akwai matuqar shaquwa da fahimtar juna a tsakaninsu,kowannensu bashi da kamar dan uwansa,dashi yake shawara,shi yake gayawa sirrinsa.
Farinjinin ja'afar ya sanya yake da tarin 'yammata dake hauka a kanshi,saidai ko sau daya bai taba sha'awar bata lokacinsa akan kowacce yarinya ba,a haka kwarjininsa ya sanya mata da yawa sun hadiye kwadayinsu,don basa iya tunkararsa da zancan soyayya kansu tsaye,masu tsaurin idanu ke biyo ta hannun jabir,to shima jabir din yasan waye ja'afar,kuma dabi'un nasu suna dan kamanceceniya,duk da jabir bashi da miskilanci,saidai yana ararsa a duk sanda yaso,hakan yasa sau tari wasunsu baya ko gayawa ja'afar ma yake barin batun yabi iska.
A sannan babban burin ja'afar a duniya shine ya zama pilot,dukka hankali nutsuwa da kuma rayuwarsa ya tattarata ne kan karatunsa gaba daya,sanda yake gab da zama pilot,a lokacin da suke komawa gida hutu daga qasar da yake karatu,a filin jirgin sama shaheeda ta fara ganinsa,d'iya ga shugaban malamai na qasa gaba daya,kuma babban limamin masallacin shugaban qasa dake abuja,yarinyar data bala'in mato masa,saidai tasirin tarbiyya data samu ya hanata bayyana masa,tana da kunya da kuma tsananin kamun kai,amma duk da haka ta kasa kanta sakat,sai data gano waye ja'afar din.
Ta shiga tsananin tashin hankali sanda aka gama karanto mata waye ja'afar?,ta yaya zata shawo kansa?,da wannan tunanin ta dinga rayuwa,haka ta dinga ramewa.
Kwanaki qalilan da ya rage musu su koma gida daga hutunsu suka giwa dr marwan rakiya abuja shi da jabir zuwa taron musabaqa na kasa da ake gudanarwa acan,a ture yaje bawai don yana so ba,don bai shirya zuwan ba.
Cikin hall din kansa yana qasa yanata danne danne a wayarsa,yana jin jabir sunata hira da wasu matasa biyu da suka hadu a can,har zuwa sanda aka fara gabatar da musabaqar,bai daga kansa ko sau daya ba,saidai duk wanda yahau zaiyi karatu har ya sauka yana bibiyarsa a zuciyarsa,yana taya alqalan cin gyaransu,don shima Allah ya bashi haddar qur'ani izifi arba'in cif,sauran kuma biye ne da qur'ani.
Kiran sunan wata daliba da akayi yaji daya daga cikin abokan hirar jabir din yace
"Alhamdlh......ga sister dita din" baiyi niyyar dago da kansa ba,amma jin ana sake maimaita kiran sunanta ganin bata fito ba,sabanin sauran dalibai da kowa ake kiransa sau daya.....shi ya sanyashi daga kansa sanda yaji me kiran sunan ya ajjiye abun maganar alamun ta taso.
Daga rukunin kujerin dake opposite dinsu ta taso,sanye cikin yalwataccen dogon hijabi har qasa,qafarta da hannunta duka safar hannu ne,baka ganin komai nata sai kyakkyawar fuskarta wanda nutsuwa ke kwance samanta.
Kansa ya dauke ya maida ga wayarsa,amma sai ya samu kansa da dakon jin nata karatun,ta daidaita zamanta aka tambayeta wacce qira'a take amfani da ita,ta fada,mai jan karatun ya janyo mata sannan aka bata damar ci gaba.
Gaba daya hall din sai daya dauki shuru sanda tayi bismillah,zazzaqar muryarta ta karade hall din cikin kyakkyawan sauti da qira'a,wanda tunda aka fara ba'ayi mata gyara har ta dire,kabarbarin mutane da yawa data burge suka dinga fitowa daga bakunan jama'a
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 15
*Dawowa cikin labari*
Tafiyar awanni biyu suka qara suka shigo garin gombe,a lokacin anata sallar la'asar,wasu masallatan ma sun idar.
Slow da motar ta fara yi sanda suka qaraso unguwar suka fara gangarowa faffadan layin gidan dr marwan din ya sanya maimunatu farkawa,ta zauna sosai tana murza idanunta tare da kallon sabuwar duniyar da rayuwa ta kawota,murmushi anni tayi
"Lallai kinsha barci maimunatu,harma kin fini jimawa" murmushi tayi cikin jin kunya ta sadda kanta,itama anni murmushin tayi tana maida dubanta ga qofar gidan da suka fara harin tsaiwa
"Marwan dinma yana nan ashe" ta fada tana leqe fa window
"Eh ga motarsa nan,harda baqin motoci ma" hayatu ya amsa mata
"Marwanu marwanu na jama'a,hutun qarshen satin ma shi ba samu yake ba"
"Wallahi haj anni,ai aljanna kawai ta ragewa alhj,amma yana samun yabo da shaida me kyau" kanta ta jinjina cikin jin dadi,ita kanta ta sani,matuqar dai aljanna qasan qafar uwa take,to babu abinda zai hanata dagewa marwanu ya shige.
Kakaf hankalin maimunatu yana ga hanya sanda motarsu take shigewa cikin tangamemen gidan,ba laifi tana da dan sanin rayuwar dadi 'yar mitsitsiya,amma komawarta rugar ummaru ya sake maidata baqauya sosai,don haka ta dinga bin gidan da kallo cikin mamaki su anni,ya akayi su dake rayuwa a guri irin wannan suka iya zuwa rugarsu har sukayi sati guda?,lallai su din nagartattu ne wadanda basu maida duniya a bakin komai ba.
Kafin hayatu ya budewa anni qofa ta fito wajen ya fara cika da mutane,mafi akasarinsu ma'aikatan gidan ne maza da mata,kowa na mata sannu da zuwa tare da qoqarin nuna kulawarsa a gareta,abinda zai nuna maka irin girma matsayi da kuma muhimmancin da take dashi.
Waiwayawa tayi ga maimunatu wadda ke rabe bayan murfin motar da suka fito a ciki,cikin tsoro,kamar xaka ce mata ket ta zura da gudu,sannan ta dubi daya daga cikin ma'aikatan,babba ce aqalla zatayi shekara arba'in da takwas,kuma da alama ita din ta hannun daman anni ce nesa ba kusa ba
"Tabawa riqo min baquwar nan ki shiga min da ita ta qofar baya" ta fadawa tabawan qasa qasa,gyada kanta tayi sannan ta juya inda anni tayi mata ishara,tunda tayi mata magana ta haka tasan cewa wala'alla abune na sirri bataso kowa da kowa ya sani.
Murmushi tabawa ta sake mata sannan ta kama hannunta,ko ba komai maimunatun taji ta sake da tabawa farat daya,saboda yadda ta kama hannunta babu kyama ko alamun kyara ko kuma tsangawa,tana biye da ita har sanda duka bulla wani tangamemen falo,falo ne daya wadata da dukkan nau'in kayan alatu na rayuwa,rukunin kujeru biyu ne a cikinsa saboda girmansa,kowanne color dinsu daban,akwai qofofi a ciki dake nuna alamun dakunan bacci ne,sai wata gajerar siririyar hanya wadda kitchen yake a ciki.
Kitchen ta wuce da ita,wanda maimunatu ga bishi da kallo cike da mamaki,farat daya ta gane kitchen ne,duk da na ainihin gidansu na gembu bai kama koda qafar wannan ba
"Tsaya ina zuwa" tabawa ta fada sannan ta juya ta fita,bata yi koda minti daya cikakke ba ta dawo,tana murmushi ta dubi maimunatu
"Kiyi haquri ko,na barki a tsaye,muje na nuna miki dakinki" kai ta gyada kawai tana maida mata martanin murmushinta,a salube kuma tabi bayanta.
Dakin yafi kusa da kitchen din gidan,don shi daya ne area din,babban dakine da aka shimfideshi da tiles marbles baqaqe masu dishi dishin light blue a jikinsa,yana dauke da babban gado madubu da wardrobe ta jikin bango,gurin ajjiye takalma,da manya bedside guda biyu masu dauke da bedside lamp,tun daga curtains zuwa dan qaramin carpet din dake malale a gaban gadon duka light blue ne,abinda ya qarawa dakin haske da kuma kyau.
"Anni tace nan ne dakinki,ki zauna ki huta sosai,sannan ki fadi abinda kikeso kici,ga bandaki can koda wata buqata zata kamaki,tace zata kiraki idan ta gama" kai maimunatu ta gyada,jikinta a sanyaye,tana ganin kamar taxo inda bai cancanci tayi rayuwa dasu ba,tako ina mutanen nan sunfi qarfinta sun kuma wuce tunaninta,yanzu wannan dakin shi za'a bata a matsayin dakin kwananta?,ita a wa?.
"Me zakici?" Tabawa ta sake maimaitawa idanunta akan maimunatu tana nazarinta,da sassanyar muryarta tace
"Ba komai,banajin yunwa,bamu dade da cin abinci ba" gaskiyarta kuma ta fada,cikinta ya riga da ya zama mara space sosai da bazai iya daukan wani abincin ba bayan awanni biyu,yunwa ta zamar mata jiki
"Shikenan,amma idan kinji kina da buqata,ga waya can ki daga ki kira kitchen,za'a kawo miki duk abinda kike buqata" kai kawai ta sake gyadawa bawai don ta fahimci yadda zatayi kiran ba,sai taga tabawan ta qarasa wajen da qullin kayanta suke tana niyyar dauka
"Kaya na ne" daga kai tayi ta dubeta,murmushi tayi mata sannan tace
"Anni ce ta bada umarnin a daukesu,za'a kawo miki wasu kayan da xakiyi amfani dasu" bata son rabuwa da kayan,kayan suna d matuqar amfani da kuma tarihi a wajenta
"Don Allah ki cewa anni tabarmin su,ina so" fasa dukan tayi,sai ta amsa mata da to,ta juya ta fita a dakin sannan taja mata qofar ta rufe
A nutse ta gama qarewa dakin kallo kusfa kusfa,daga nan inda take zaune tana iya jiyo maganganun mutane sama sama,saidai kuma bata iya rabewa da abinda suke fada.
Daga can bangaren anni kuwa sannu da zuwa jikokinta suke ta shigowa sunayi mata,duk da cewa ba kasafai take wannan wasan dasu ba,amma kuma su din basu qyaleta ba,duk da zafin da take dashi.
Fitowar annin kenan daga wanka bayan ta fito tana zaune a qasa,ta miqe qafafunta da sukayi mata nauyi da kuma tsami saboda zaman mota,man zafi take qoqarin shafawa tabawa ta shigo dakin,dauke da wani qaramin flask din silver da cup guda daya,gefe ta zauna anni ta daga kai ta dubeta
"Sannu tabawa"
"Yauwa hajiya anni" ta amsa mata tana murmushi tare da qoqarin bude flask din ta zuba mata abinda yake ciki,dan yamutsa fuska tayi
"Dakata mana tabawa,yaa daga dawowata zaku hau duramin magani?,ba wani abu me galmi galmi sai magani kamar bugagga?" Dan danne dariyarta tabawa tayi,ita din ba baquwar hutsun anni bace,ta riga data saba da hakan tsahon shekara goma sha
"Ammi ce tace shi xa'a fada baki"
"Ta rasa abun arziqin da zata yimin sai wannan?"
"Abu me galmi galmin yana hanya ai anni,ita da kanta ta karba girkin abinda zakici idan zaki dawo,yanzu haka a kitchen na barta" sai a sannan annin ta saki fuska
"Allah sarkiAishatu,badai qoqari ba....ba daga nan ba" ta fadi tana miqa hannu tare da karbar maganin da tabawa ta zuba matan tana kurba a hankali,ita kanta tana son maganin,saboda yana saurin warware mata gajiya daga jikinta.
Kurba uku tayi aka turo qofar dakin hadi da sallama,matashiya ce sanye da rigar material da aka yiwa budadden dinki,kanta yane da mayafi plain daya dace sosai da kayan jikin nata,tabawa ce ta amsa sallamar tata tana dubanta
"Ina kika shiga tun dazu ga aikinki can an dade da gamashi?" Sai data zauna gefan gadon annin ta yage mayafin kanta sannan tace
"Bari kawai baba tabawa,ai na baje zanci dadi kawai aka kirani daga makaranta nazo ga lecturernmu da yace bazai samu shigo ba ya shigo,mugu ne mutumin nan na qarshe,shi yasa ba shiri na tashi na tafi"
Murmushi tayi
"Ai gashi can a ajjiye"
"Yauwa baaba tabawa.....godiya nake" waiwayawa tayi zuwa ga anni tana murmushi
"Anninmu ta mutunci......barka da sauka,kun dawo lafiya?"
"Lafiya garas na dawo,gashi ma kin ganewa idonki?" Dariyar dake cin salma ta danne,don tasan anni na ciki da ita,domin kuwa ita ya khalid(shine babban jika a wajen anni ta danta na biyu me bin dr marwan)yace ta shirya ta rakata amma ta kawo nata uzurin bata je ba
"Amma nafi kowa jin dadi a gidan nan,Allah da bakya nan duka gidan babu dadi,ai bansan yau zaku dawo ba don munafurci laila bata gayamin ba,da na saka an siyo miki nama a wani suya sport nan bayanmu me shegen dadin tsiya......"
"Ke.....kiyi ta kanki,wato ga kuriya ko?,to ta Allah ba taki ba,bana so" fuska tadanyi qoqarin canzawa,duk a qoqarinta nason gamsar da anni duk da dariyar daketa taso mata,saboda tana da buqata wajen yayansu ja'afar,kuma ta tabbatar da zarar annin ta saka baki anyi an gama
"Allah anni da gaske nake,kar kiso kiji yadda duk naji......"
"Ki rabawa aishatu da marwanu biyar biyar....."annin ta fada tana danqara mata daquwa,wanda babu shiri salma ta miqe ta zari jakarta tana cewa
"Allah ya baki haquri ya huci zuciyarki tsohuwa me ran qarfe" tayi waje,annin bata barta ba ta dora mata
"Sannan kada uban wanda ya sake saka tabawa aiki cikin gidan nan na gaya muku,ba me aikin kowa bace ehe......" Murmushi tabawan tayi bayan ficwwar salman
"Ba wani abu bane hajiya anni,koda aikin gidan nan duka zai dawo kaina indai zan iya zan yishi,keda iyalinki ai kunfi qarfin komai a wajena" kofin maganin ta ajjiye gefe
"Na sani,amma ace duk ma'aikatan dake gidan basu ishesu ba?,ubansu ya lalata su ya dauko masu aiki ya zube musu kamar ba diya mata ba da gobensu a gidan aure zata samesu?,kiga yarinya batasan ta zagi jikinta tayi aiki gidan aurenta ba?,shi yasa suke wayar gari qazamai,ko cikakken tuwo basu iya yiwa miji da zaici kamar ya cire yatsunsa ba......haka yaranmu na karkara suke?" Kai tabawa ta kada tana murmushi
"Sha wuya ne ai wadan nan" furucin na tabawa ya tuna mata da maimunatu
"Kwarai da gaske kuwa,kin tunamin ma,akwai maganar da nakeso muyi dake tabawa" anni ta fada tana gyara zama,tabawa bame aiki anni ke kallonta ba,yar uwa take kallonta kuma abokiyar shawara,bama ita daya ba,kusan duk wanda ya girma ya tashi a gidan kallon kaka yakewa tabawa,mutum ce ita me tsananin mutunci da kuma dattako,bata aikin komai ma cikin gidan,saidai idan anni na buqatar wani abun da sun riga sun saba tabawan kadai keyi,duk da akwai masu aiki sosai cikin gidan
"Kinga yarinyar dana sanya ki kaita ciki ai ko?"
"Qwarai kuwa haj anni" tabawa ta fada tana bawa anni dukka hankalinta
"Yarinyar kyakkyawa sosai,saidai akwai alamunrashin sukuni a tattare da ita da kuma wahala" kai anni ta gyada
"Bama alamu bane,akwaisu" a nutse ta bawa tabawa labarin maimunatu,tare da qudurinta a kanta,labarin da yayi matuqar sanyaya jikin tabawan,tare da saka mata tausayin maimunatu me yawa cikin ranta
"Kiyi nufin alkhairi sosai hajiya anni,kuma dama halinki wannan,Allah ya baki nasara akan hakan,yasan kuma iya bakin matsalar ce,yasa ta zamto masa haske cikin rayuwarsa"
"Ameen,ameen ya hayyu ya qayyumu"anni ta fada tana jin dadin yadda tabawa ta fuskanceta
"Amma kuma wani hanzari ba gudu ba.….."
"Uhmmm,ina jinki tabawa"
"Kinsan akwai matuqar banbanci da tazara me yawa tsakanin manya(sunan da takan kira ja'afar dashi,saboda sunan babban malamin da yaci,kuma wasu sukan kirashi da sunan) da ita yarinyar?,kinsan kuma hali da dabi'ar yaran zamani,musamman shi daya keta qasashe da dama,yaga kuma mata iri iri,inajin kamar idan akace za'a bashi yarinyar nan a haka zai zama da matsala" murmushi anni tayi
"A hakan zaa bashi ita ba kuma a hakan za'a bashi ba" cikin rashin fahimta tabawa ta kalli anni don bata gane hausar ba