Kenza eBookz

Gurbin ido huguma complete - Chapter 27

Gurbin ido huguma complete - Chapter 27

Gurbin ido huguma complete Chapter 27: Gurbin ido huguma complete Chapter 27. "Kana iya tafiya" da wani irin low tune da ya sanya tausayinsa sauka a…

3,326 words

"Kana iya tafiya" da wani irin low tune da ya sanya tausayinsa sauka a zuciyar jabir,yafi kowa sanin yadda shaheeda tayi tattalinsa a lokacin rayuwarsa harma fiye da haka,amma a yanzu duka yayi loosing wannan caring din,dole abubuwan su dinga tabashi,duk da cewa shi yaqi bada wannan damar,yana da hope akan maimunatu shima kamar yadda yaji anni tana fada,ya sake samun gamsuwa akan yarinyar tun ranar da suka zauna sukayi magana ne tsaho a kanta da anni amma ya tattarata ya kaita makarantar kwana,annin kuma ta hana kowa masa magana,tace su xuba masa idanu suga iya nasa gudun ruwan.

A dan shurun da ya ratsa ta tsakaninsu ne tex ya shigo tasa wayar shima,sai ya jawota yana dubawa,qaramin tsaki yaja

"this is nonsense" furucin ya fita can qasan maqoshinsa,idan ba kunne kasa sosai ba ba zaka ji me yake fada ba,kira yayi ya aje wayar saman table bayan ya sakata a loud speaker,bugu biyu ya daga

"Me kake cewa ne?,ace duk gidan a rasa me daukota?" Yace da hisham kai tsaye,lumshe idanunsa hisham yayi daga wancan bangaren kafin ya amsa shi

"Babu yaaya,drivers din duka sun fita tare da abba,yana da baqin da suke zirga zirga dasu,ni kuma nan da minti goma akwai wanda zanwa surgery,kuma emergency ne har mutum biyu,kafin na gama kuma an ja lokaci" katse kiran kawai yayi,ya fara laluban number anty maama.

Itama bugu biyu ta daga suka gaisa

"Driver dinki yana kusa ki bani aronshi?"

"Wai.....ai kuwa yau tun sassafe ya debi yara abbansu yasa ya kaisu qauye"

"Ok" yace a gaggauce

"Akwai wani abu ne?"

"No,ki gaida yaran, thanks "

"Okay" itama ta bishi dashi,tasan halin kayanta fes,bama fadar zaiyi ba

"Waye ya bawa drivers na gidan nan hutu ne gaba dayansu?" Ya jefawa jabir dake nanuqe da wayarsa yana maidawa fatimansa reply na dinta tambayar,sai a sannan ya daga kai ya dubeshi,duk nema neman drivers da yakeyi yana jinsa,ya kuma san dalilin hakan,don kusan da goyon bayansa anni tayi wannan hukuncin

"Hey man,kai ne mana?,ka manta kenan ka zauna ka sani a gaba zaka fara tuhuma?" Tsaki ya sake ja yana tattare files din da suke gabansa

"Bari na fito maka a mutum,duk wannan goce gocen da kake bazai maka bafa,ka tashi kaje dauko yarinyar mutane kawai,three months bata nan amma don zaka bata just thirty to fourty minutes ka daukota a school sai ya gagara saboda adalci irin naka?" Wani kallo ya masa,tunda yaji amsar daya bayar yasan da issue din kenan,sai ya dakata daga hada takardun

"Idan kaji haushi me zai hana kaje kai" dariya ya sake sosai

"Ba dole na bace,ga dole na can tana jirana,kuma inda itace da tuni na tsufa a school din,don bazan bari Allah ya kamani da laifin rashin sauke haqqin dake wuyana ba" yana gama sai ya miqe yana 'yar dariyarsa zai fice daga office din,har ya kusa qofa sai ya tsaya

"Da zaka zo sai mu wuce gida tare ka fara yin lunch kafin ka tafi" ya fada with full caring in his voice,saidai kallo dayan da ja'afar yayi masa ya bashi amsarsa,sai ya kada kai kawai ya fice a office din yana murmushi,ya gode Allah daya bashi juriya da hikimar zama da ja'afar din,mutumin da yake jinsa tamkar cikin mahaifa guda suka kwanta dashi.

Riqe da suit dinsa a hannu ya fito,kana ya sauko kai tsaye zuwa floor din qarshe ya kuma wuce parking lot na ma'aikatar,key dinsa already yana hannunsa,tunda ya sallami driver dinsa,don yau din ya tsara lokacin tashinsa,zai iya kaiwa dare,don haka ya bashi umarnin tafiya idan akai azahar,sai gashi kuma wani abun da babu shi cikin schedule dinsa na yau ya taso masa. [11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: *GURBIN IDO* 37

*AREWABOOKS:HUGUMA* https://arewabooks.com/chapter?id=6364b8542730d61e0981706d ______________

Sanda sukai jarabawar first semester ta goma sha biyar tazo cikin su arba'in,ko kadan hakan bai mata dadi ba,saboda ta saba,har ta gama rayuwar primary dinta bata wuce ta biyar,bata nunama kowa ba sai aminanta kuma roommates dinta,afra ce tace

"Naga qoqarinki ma maimoon(sunan da suka koma ce mata kenan),a wata uku kacal kin doke mutum ashirin da biyar?" Kai ya girgiza sanda take hada kayanta,don a gobe kowa zai wuce gida hutu

"Ina qoqari a nan afreen(sunan da ita dinma take kiranta dashi),bazan iya nunawa kowa result dina ba"

"Zaki iya maimoon,i trust you,duk wanda ya iya arabic,boko bazai bashi wahala ba sam sam sam,boko minor abune akan arabic"

"Next time I will try my best in sha Allah" ta amsa mata tana sakar mata murmushi,tare da jin dadin irin qwarin gwiwar da ko yaushe afra take bata.

Washegari tana ta zuba idanun ganin wanda zayazo daukarta saiga yaa hisham,ya fito suka gaisa dasu afra,ya kuma gabatar musu da kansa da kansa a matsayin yayan maimunatu,sosai abun ya mata dadi,ya girmamasu ya kuma mutuntasu a mazauninsu na aminanta,su kansu sun nuna jin dadin hakan,afra taso su gaisa da 'yan gidansu,suga kuma sabuwar aminiyarta,to amma ya hisham din ya bada uzurin yana da patient da zai gani,dole sukayi sallama suka shiga mota.

Yana qoqarin tada motar ya lura da envelope din hannunta,wadda ke dauke da tambarin makarantar,sai ya miqa hannu

"Duk da ba'ayimin tayin ganin result din ba,nayi shishshigi,a bani na gani" idanu tadan zaro,ta yima kanta alqawarin babu wanda zai gani,har sai tayi abun arziqi,amma tana jin nauyin hisham din

"Ya hisham,don Allah.....ka bari sai next term saina hada maka da wannan din duka ka gani gaba daya" ta fada tana marairaice masa,wanda har ga Allah ita din batasan tayi ba,kamar yadda batasan mugun kyan da hakan ya qara mata ba,har sai daya janye idanunsa da sauri daga fuskarta yana fadin

"Subhanallah" cikin ransa ya furtata a hankali

"Ba matsala,Allah ya nuna mana" yadda taga yayi maganar yana tada motar ba tare da ya sake waiwayowa ba yasa taji babu dadi cikin ranta,sai taji kamar bata kyauta masa ba,don haka ta zaro ta miqa masa,sannan tayi qas da kanta tana jiran jin maganar da zai fada mata

"Kinyi qoqari sosai,ma sha Allah,wannan ne karonki na farko fa?" Ya fada cikin nuna qwarin gwiwa da kuma qarfafata,maganar tazo mata a ba zata,ta kuma bata mamaki,sannan kuma taji dadi gaki da sake samun qwarin gwiwa.

Ta zaci gidan abbi zai kaita,sai taga ya wuce da ita gidanta,bata tambayi dalili ba,bayan ya aje ta tayi masa godiya,ta kuma bashi saqon gaisuwa wajensu anni,tare da roqonsa a kawo mata amna.

Gyare gyare ta shiga yi,irin na mutumin da ya kwan biyu baya waje,sai data gama komai sannan ta sake wanka,ta kuma wuce kitchen ganin azahar har ta gota don ta samawa kanta abinda zataci.

Har zata shiga ta tuna da unaisa,sai taga bai dace tana cikin gida ba amma batasan da dawowarta ba,ko banza ta girme meta a shekaru,wannan tunanin yasa ta karkata akalarta zuwa sashen unaisan.

Knocking biyu aka tambayi waye,kai tsaye ta amsa da itace maimunatu,sai da aka dauki mintuna sannan ta bata izinin shigowa.

Zaune take saman doguwar kujerar falon nata,ta miqe qafafunta akai tana shan lemon fata,da alama tun dazun a hakan take a zaune,kawai dai batayi niyyar bata izinin shigowar bane,kallo daya tayi mata ta canza fuska ta kuma kau da kanta taci gaba da kallonta ga tv.

Koda ta gaisheta sama sama ta amsa

"Na dawo,nace bari na shigo na sanar miki" wata dariya ce ta zowa unaisa,ya tabbata ja'afar din mugun dan rainin hankali ne,hakazalika da biyu ya dauki yarinyar ya kaita makarantar kwana saboda ya raina ajinta da kwanyarta,to amma hakan yayi mata ita din,tunda ko banza kawo yanzun tana dan samun wasu sauye sauyen,duk da cewa ko sau daya bau taba hada dakin kwana da ita ba

"To yayi" tace mata kawai taci gaba da shan lemonta tana kada qafa gami da ci gaba da kallonta,ganin babu wani magana data sake hadasu sai maimunatun ta miqe zata fita

"Agwai" ta kirayeta da sunan da maimunatun tafita sanin me sunan yake nufi,sunan yadan sosa ranta,amma bata nuna ba ta waiwayo tana dubanta

"Am please idan kin tashi girkinki,ki dinga yi iya cikinki,wanda naci a baya ma shahada nayi,don ba abinci kowanne irin mutum nake ci ba,so ina da masu aiki,zasu dinga yin komai" kai ta gyada sannan tayo gaba tana bar mata dakinta.

Ga mamakinta sai taji maganganun unaisa sun dan sosa ranta kadan,abinda tun tasowarta da irin cin zarafin data gamu dashi a rayuwa bata taba jinsa akan kowa ba,ko hakan yana da nasaba da zama dasu afra?,hakan na nufin ta fara sanin kanta da kuma sanin mene ne rayuwa?. Muje zuwa dai.

Tunda ta dawo gidan bataga koda gilmawar J ba,abinda ko sau daya bai ɗaɗata da ƙasa ba,sau tari mancewa take dashi kwata kwata cikin rayuwarta,tasa litattafanta a gaba tana ta haddar hadisan data daukarwa malamin islamiyyarsu alqawarin zata kawo masa su kafin a koma hutu,da kuma izifin data diba shima zata daw da haddarsa,don hatta haddar qur'aninta bata bari ta tsaya ba,tana ganin wannan damar ta roqa alfarma,yake mata qari kuma tana kawo masa.

Ta fannin boko ma litattafan da zasu sake inganta mata koyo da gane turancinta ta karba aro masu yawa daga library din makaranta ta taho dasu,wadan nan abubuwa sune abokan hirarta,kewar da tayi fama da ita zamanta na baya a gidan yanzu duka babu,mantawa ma take da inda take,wani lokaci ma idan tayi breakfast bata sake neman abinci saina dare,batajin yunwa sam idan ta duqufa karatunta,bare kuma ba wani motsi zatayi me yawa ba bare ya zazzage mata cikinta ya jawo mata yunwar ba,tana daki kwance,saman gado idan ta gaji ta dawo falo saman kujera,ba kasafai take shiga kitchen din ba,dalilin da yasa har zuwa sannan batasan ma kalar 'yan aikin da unaisa ke maganar ta kawo ba,don sanda zata shiga da safe basu soma nasu aikin ba,lokacin da zata sake komawa kuma dare yayi sun gama nasu aikin sun bar kitchen din.

To da wannan damar data samu yasa tayi karatu me yawan gaske,wanda ita kanta batasan ta yishi ba,hutun da akazo gida don yinsa nata hutun kadanne.

Randa tayi sati a gidan,tana daga bakin window dinta ne taji cewa ja'afar din tafiya yayi ashe,ta bakin unaisan sanda tayi baqi take rakasu zuwa parking lot na gidan xasu shiga motarsu,saita janye zuwa ciki,ta bude shafin gaba na littafinta taci gaba da karatunta.

Sai da tayi kwana takwas da dawowa sannan su fa'iza suka zo mata,harda amnanta,ranar kamar sallah haka ta jita,sun sameta anata sana'ar wato karatu,amna na jikinta ta dauketa zuwa kitchen don ta sama musu abun sha,kafin tayi tunanin me zata girka musu.

Sanda suka shiga amnan nata mata tambayoyi da zuba mata surutu,tabbacin yarinyar tayi kewarta matuqa,bata lura da unaisa dake tsaye riqe da cup da yoghurt a hannunta ba har sai data kirayi sunan yarinyar,tare suka waiwaya zuwa gareta ita da maimunatun,maimunatun ta dubi yarinyar data zubawa unaisa idanu tana kallonta,duba na rashin sani da kuma rashin sabo

"come-on baby,new mom dinki ce" unaisa ta fada tana murmushi gami da miqawa yarinyar hannu,karon farko da yaro ya burgeta,kasancewarta ba ma'abociyar son yara ba,tsantsar kamanninta da silly mahaifinta din nan ya bayyana,tana fatan batayo miskilanci irin nasa ba.

Kamar kuwa yarinyar tasan me take rayawa a zuciyarta,sai ta noqe kafada tana ci gaba da kallonta

"Zo mu gaisa mana,haba amna,nace miki new mon dinki ce" ta sake maimaitawa dai,sai ta sake maqale mata kafada,wannan karon kallon fuskar maimunatu dake duba lemon da zata dauko musu tayi

"Wannan ce new mom dina,ke ban sanki ba" ba unaisa da yarinyar ta fadawa maganar ba,ita kanta maimunatu taji mamakin maganar,ta dago kanta tana duban fuskarta,waye ya gaya mata itace new mom dinta?,ya akayi ta fahimci haka?,duk da dai yarinyar nada wata muguwar kwanya da kaifin basira,wanda maimunatu tafi tsammanin daga wajen mahaifinta ta gajeta.

Sauke amnan tayi qasa tana dubanta

"Itama new momma ce,kije ki gaisheta kinji" saita gyada kai,duk da bata sake jikinta ba amma haka ta nufi unaisan,abun ya yuma unaisan ciwo sosai,yarinyar ma ba zata zo wajenta ba sai wannan agwai din ta yarje mata,ta kuma yi mata umarni?,ta zabgawa maimunatu harara sanda ta riqe hannun amna,hararar da maimunatun bata ma san tana yinta ba,da hilata ta samu ta janye amnan zuwa part dinta,saidai suna tsaka da hira sai ga daya daga cikin masu aikin unaisan sun dawo da amnan,idanu fici fici da alama rigima ko ma kuka tayi musu.

To hutun kwata kwata na sati hudu ne,suna gama satittikansu suka sake diba suka koma makaranta,maimunatu ta sake dasa yaqin neman karatu,babu ji babu gani,bakin rai bakin fama,su kansu su afrah sunyi mamakin yadda qwaqwalwar maimunatun ta sake budewa daga zuwanta hutu zuwa dawowarta,ta dings musu dariya ganin yadda dukka suke mata duban mamaki,a wani yammaci suna hanyar zuwa islamiyya,bayan ta bada amsar wata tambaya cikin subject din math,shi kansa malamin sai data burgeshi yadda ta amsa question din a gaban allo.

To bata qarasa basu mamaki ba sai da sukaje islamiyyan,duka ta zubewa malaminsu haddar hadisan data yo,a washegari kuma zai karba na qur'ani,wannan yana daya daga cikin abinda ya sake zaburar dasu suma,sannan kuma farat daya sunan maimunatun ya fara tambari cikin makarantar,tun daga juniors dinsu zuwa seniors,cikin watanni shida kacal ta fara zama sananniya,duk wanda kacewa maimunatu abubakar muhammad zaiyi wuya yace maka bai santa ba,dalibai maza da kuma mata,saboda zuwan da tayi da tarin baiwarwarki a lokaci qalilan,kyakkyawar bafulatar usul,wadda ke dauke da wani irin kyau mejan hankali,musamman da a yanzun take zaman makarata,daga dakunan kwanansu sai ajujuwansu na boko sai kuma masallacin makarantar inda a nan suke gudanar da islamiyyarsu,fatarta ta sake wani irin haske,kamar zata tabata jini ya fito,jajayen labbanta da bata sanya musu komai sun sake ja,hakanan idanunta masu wani irin kyau da suke dauke da golden din qwayar idanu,ita kanta takan jima gaban mudubi tana kallon kanta,tare da tambayar kanta ita dince kuwa?,itace maimunatun rugar ummaru?,itace maimunatun inna furera?tabbas ta canza,canji me nisan tazara kuwa.

Duk da cewa gayu da wasu dabi'u nasu afrah sun ratsata,har sun zame mata jiki itama ba tare data sani ba,amma hakan bai hanata yin takatsantsan da kanta ba,qwarai ta sani cewa ba daya suke dasu ba,ita din akwai auren wani a kanta,zuwa yanxu ta sake samun ilimi sani da kuma wayewa kan muhimmancin aure da girman matsayinsa saman kan kowacce diya mace,duk da cewa takan manta sosai da cewa ita din matar wani ce,don shi kansa wanda aka daura mata igiyar ta sanadinsa ba ganinsa take ba,wani lokaci sai taje hutunta har ta dawo baifi su hadu sau daya cikinn gidan ba,idan an samu akasi ne suke haduwa biyu,gaisuwa kusan itace maganar da take gilmawa tsakaninsu,har yau har gobe basu taba wata magana data gota babin gaisuwa da amsa ba.

Tana qoqarin tunawa kanta cewa ita din me aure ce,bawai don damuwa ko soyayya ba,haka kawai cikin ranta takeji bai kwanta mata ba ko kadan,me yasa bai dauko halin hisham ba?,hisham din mutum ne da take matuqar ganin kima mutunci da kuma martabarsa,bata ga alama koda ta kuskure da zata nuna maka yana mu'amala da wani abun maye ko shaye shaye ba,sabanin shi da tun ranar data fara ganinsa tasan cewa mazuqin taba sigari ne,sauran abinda kuma yake sha wannann Allah ne kadai ya barwa kansa sani,tunda ita a nata hasashen,duk wanda yake shan sigari to yana shan komai ma na kayan maye.

Abu na biyu hisham din mutum ne me kimanta dan adam da darajtashi,koda yaushe yana faran faran da ita dama sauran qannansa,a gu daya take ganin kamewarshi da nashi salon miskilancin shima,idan ya fita cikin mutanen da suke ba ahali a garesa ba,ko kuma baqin fuska,a duk sanda zai dawo da ita makaranta ko kuma zai maidata,hira ce me tsafta take wanzuwa a tsakaninsu,yakan bata shawarwari da qarin haske akan karatunta,labarai da suke da nasaba da karatu,kamar labarin lokacin da yake dalibin secondary kamar ta,takan iya sakin jiki dashi kadan yanxu,wannan baquntar da take masa a da yanzu ta ragu sosai,yayin da shi kuma yake girmamata kamar yadda zai girmama dan uwansa,har wani lokaci yakan bata kunya ainun,ganin cewa ya girme mata nesa ba kusa ba,ita yafi cancanta ta bashi wannan girman. [11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 40

Da hannu daya yake driving din,cikin jin wata irin kasala a jikinsa,kai tsaye masallaci da yake sallah idan sallar ya riskeshi akan hanya irin haka ya nufa,ya samu jam'i,ya bada faralin sallar azahar,sannan ya sake fitowa,ya wuce eatery din da yakanci abinci time to time,yayi order din dinner,ya tsaya acan ya tsakura ya biyasu sannan ya wuce kai tsaye zuwa makarantar yana duba lokaci gami da jan tsaki,a yadda jikinsa yayi masa weak a yau,ya tabbatar komai nasa ya rushe,saidai ya barwa gobe kuma,ya fuskanci wani lalaci ne yakeson kamashi a yan satittikan nan,ko zuciyarsa na la'akari da achievements din daya samu take ganin kamar it's time for her to get some rest wanda shi kuma bai shiryawa hakan ba.

Karo na uku kenan dame kula da dakunan kwanansu idan sun tafi hutu ta sake leqowa tana tambaya

"Bai iso ba har yanzu"

"Gashi office din principal din shima a kulle yake,duk dakunan da za'ayi kiran suma a rufe suke" cikin qarfin hali tayi murmushi

"Kada ki damu mr Rebecca,nan da minti goma idan bai iso ba,saiki taimakin mu fidda kayan na samu okada na hau" kai ta jinjina

"Shikenan ba damuwa,fata dai kawai Allah yasa lafiya"

"Ameen" maimunatu ta amsa tana son danne rauninta da fargabarta,tunda ta fara makarantar itace ta farko da take rigasu afrah tafiya gida,ko sau daya hisham bai taba delay na zuwa daukarta ko kawota ba,dalili kenan da yasa yau din da suke mata dariyan zasu rigata tafiya gida bata damu ba,tace musu tasan yana hanya,qila ma kafin su gama ficewa a makarantar ya iso,wannan dalilin yasa suka tafi suka barta,don dukkansu sunsan himmar hisham din wajen daukota,sai gashi abun mamaki duka makarantar an fashe,sai ita daya data rage.

Baya ga fargabar abinda ya riqe hisham din,harda zazzabi da tun jiya takejin somi somin alamun zuwansa,zuwa yanzu kuwa ya fara hade mata har da ciwon kai,abinda yasa ta sake laushi sosai,jimawa kadan sai ga hawaye sun fara layi saman kuncinta tana daukesu,tun ba yau ba dama tasan ita din gwanace wajen saurin kuka,sai gashi dabi'ar tata tana son dawowa,tun tana zaune sai data koma saman gadon afrah ta cure waje daya,tana jin jikinta kamar ana sassara mata shi,hakanan kanta da jikinta kamar an dora mata dutse.

Sanda mr Rebecca ta turo qofar take shaida mata anzo daukarta sama sama take jinta,amma cikin qarfin hali ta amsa mata da to,wani sashe na zuciyarta tana jin ya sake,ta samu sauqin tunanin wani abu me muni ne ya samu hisham din,mr rebacca ce ta dauka wasu kayan tace bari ta fitar mata dasu,ita kuma ta lallaba ta miqe a hankali,saita koma ta zauna,saboda jinta da tayi kamar tana yawo kan iska,ta dafe kanta da hannunta tana jin kamar zai fado

"Kamar yana sauri ne,zan fita miki da sauran kayan,kiyi ki fito" tafadi ba tare data lura da yanayinta ba tana daukan jakarta data rage ta fice.

Agogon gaban motar ya kalla,mintuna kusan hudu kenan yana jiranta?,me ta tsaya yi ya tambayi kansa a zafafe,baya son xaman jira ko qanqani,dabi'ar da yafi tsana kenan,sai ya daga kansa don duba hanyar da zata sadaka da dakunan kwanan nasu,dai dai sanda take fitowa,tana takawa ne a hankali cike da takatsantsan saboda yadda takejin jikinta kamar ba nata ba,iska kuma nason wasa da ita daga hagu zuwa dama,fuskarta tadan tasa kadan wala'alla zafi zazzabi ya sanya hakan,lokaci bayan lokaci tana sanya tafin hannunta tana dafe kuncinta,har yanzu baby face dinta tana nan,saidai ta fara cika,ta kuma fara sauyawa,fuskar shaheeda ce ta fado masa at her age,a irin wannan lokacin datake dalibar secondary kamar haka,a wata rana da yayi mata surprise,yazo daukarta daga makaranta ranar daya samu cikar burinsa a sannan,ranar da ya zama samu shaidar zama cikakken matuqin jirgin sama me lasisi,irin murna da d'oki da ya gani saman fuskarta a sannan

"Ban zaci ganinka ba,har kazo da kanka daukana?" Shine abinda shaheeda tace

"Saboda me?" Ya tambayeta kai tsaye,shuru ta danyi still tana murmushi,da alama tana masa kaara ne akan abinda zata fada

"Uhmmm,say it,say your mind" murmushi ta sakeyi ta girgiza kanta

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull