Gurbin ido huguma complete - Chapter 38
Gurbin ido huguma complete Chapter 38: Gurbin ido huguma complete Chapter 38. Sakin spoon din tayi,ta koma da baya a hankali ta zame saman kujerar,sai yaja…
3,353 words
Sakin spoon din tayi,ta koma da baya a hankali ta zame saman kujerar,sai yaja plate daya,ya sanya spoon ya matsar gaban amna
"Uhnnn....bismillah" murmushi ta saka sanann ta dauki cokalin ta soma diban abincin tana kaiwa bakinta,wani murmushin ta kuma yi "Yummy...." Ta fadi tana duban fuskar ja'afar
"Daddy,mucu, you will enjoy it over" murmushin gefan bakin dai ya kuma saki
"Ki cimin amnee,tunda ya miki dadi" qememe ta tubure kan shima fa sai yaci din,ta haura saman table din ta dauko masa wani spoon din,sanan ta tsareshi da idanu,tilas ba don yaso ba ya diba abincin dan kadan ya sanya a bakinsa yana taraddadin abinda zaiji.
A hankali dadin abincin ya fara zagaya harshensa ya kuma gauraye bakinsa gaba daya,sake diban second spoon yayi,sai ya kuma jin real taste din fiye dana dazu,sannu sannu sai gashi yana ta kaiwa cikinsa abincin yana kuma sauraren hirar amnan yana amsa mata da ka,kafin kace meye wannan sai ga plate din wayam babu komai.
Idanu amna ta fitar tana duban ja'afar
"Daddy,a qaro ne?" Kai ya girgiza yana shafa cikinsa,ta wani sashen kuma yana cika da mamakin yawan abincin da yaci,duk da dama shidin bamai wasa bane da cikinsa musamman idan ya samu abincin daya dace da taste dinsa
"No.....am full amnee, thank you"
"Thanks to anty moon,ga kifin dad" sai yayi kamar bazaici ba saboda qoshin da yaji yayi,amma shima yana tabin farko ya bude cikinsa yaci kifin sosai,har sai da sukaci kusan rabi,sannan ya dakata,ya yagi tissue ya goge hannunsa daya baci
"Anty bakici komai ba,ba kyau fa zama da yunwa" sai a sannan hankalinsa yakai kanta,ya kalli plate din abincin nata,kusan babu abinda ta taba a ciki
"Daddy kace mata taci" miqewa yayi ya zube hannayensa a aljihunsa,kana ya saukar mata da dukka nauyin idanuwansa yana kallonta
"Eat it" ya fadi a gajarce
"Daddy yace kici anty moon" saita jinjinawa amna kai
"Zanci amna" a hankali ya janye idanuwan nasa yana mamakin kansa,baisan me yasa ya maida kallonta one of his favorite thing to do ba a duk sanda zasu hadu a muhalli guda,bayason hakan ko kadan,sai ya kama hannun amna suka fice da sassan nata.
Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tana hade hannayenta waje daya da qarfi,abinda take ji cikin jikinta yana qara qarfi,tuni kowacce gaba ta jikinta ta fara amsawa,hakanan launin idanunta suka fara sauyawa,ko kusa ko alama babu wata yunwa da takeji,infact cikinta ma a cunkushe yake,sai ta tashi zuwa bakin fridge ta dauko sassanyan ruwa ta balle ta soma sha tana tsammanin ko zataji sauqin abinda takeji din.
*_UNAISA_*
Tun bayan sallar isha'i ta gama dukkan wani shiri nata na tarbar ja'afar,girke girke tasa aka masa har kala uku,ta kuma fece kwalliya bayan ta sallami dukka masu aikin nata,ta qwame tana jiran jin shigowarsa ko kuma wani motsi nasa.
Lokaci lokaci tana tana duban agogonta,har awannin suka fara nisa,ta fara debe tsammani da xuwansa,wani girman ksi hadi da maganganun da suka fara da haj munubiya suka sauko mata,suka sanya mata wani bala'e'en haushi da takaici,ta kuma shiga safa da marwa amma sai ta kasa daurewa,don haka taja wayarta ta kira anty talatu
"Karkiyi gaggawar zuwa wajensa,ki sake jira daga nan har xuwa sha daya ko sha biyu mu gani,duk wayon ango dai dole yazo hannu ai,yana zuwa hannu kuma ai ya gama yawo,da wannan ta koma din ta zauna tana kada qafa,idanuwanta a kan tv,duk da hankalinta ba'a kai yake ba.
Da qyar ta samu ta tsakura farfesun kifin,saboda abincin bata jin zai shiga cikinta,ta kwashe komai ta maida kitchen,ta gyara ta kuma wanke kwanukan,dukka a daddafe take komai,saboda zuwa sannan gaba daya mararta ta daure tamau,sai danshi da taji tana zubarwa,wanda tayi tsammanin ko period ne yake zuwar mata.
Bandaki ta shiga ta duba jikinta,saidai kuma ba period din bane,wani ruwa ne daban,tsarki tayi tana cije lebe ta fito ta baro toilet din tana takawa da qyar,kayan bacci ta canza tana duba kokaci,amna tana ranta,saidai tunda tasan tare suke da daddynta ba buqatar sai ta dami kanta,sai ta saita freshner din dakin sake fesa kansa da kansa duk bayan wasu sakanni,ta saisaita hasken wutar dakin zuwa dim light,sannan ta haye gadon a hankali taja duvet zuwa qugunta tana cije lebanta hadi da hade qafafunta waje daya.
Ajiyar zuciya unaisan ta saki sanda ta kalla agogo,qarfe goma dai dai na dare agogon ya buga,awanni biyu masu zuwa da anty talatu sai takejin sun mata nisa,ba zata iya bari ba,don haka ta miqe ta nufi bedroom dinta,ta fidda kayan jikinta ta wuce toilet don ta sake shiryawa,ta gama tsara cewa fitar zatayi ta taddashi a duk inda yake.
Hannunsa guda daya yana saman kan amna,yana shafa sumarta a hankali,yayin da dukka hankalinsa ke kan tv yana kallon news a tashar al_akhbaar,yaqe yaqe ne kawai ke tashi tako ina a duniya,abun akwai daukar hankali sosai.
Ajiyar zuciya ya sauke sanda suka kai qarshen labaran,ya janye idanunsa ya maida kan fuskar amna,kallonta yake,sosai take tuna masa da shaheeda,ta wani sashe tana dan diban kamanninta,duk da idonta lips dinsa da skin color irin nashi ne,sai ya tofa mata addu'a sannan ya sunkuya a hankali yayi kissing din goshinta sannan ya miqe ya sabata a kafadarsa ya taka a hankali yana ficewa daga falon. [11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 59
Ya tadda schedules da yawa a company,don yana shiga kamfanin tun daga first floor PA dinsa ke biye dashi yana lissafo masa,yasan cewa laifinsa ne,tun jiya ya kamata ya buda email dinsa ya duna schedules dinsa na yau amma baiyi hakan ba,hakan kuma baya rasa nasaba da abinda ya faru jiyan,ya kuma tabbata da qyar ya tsallake rijiya da baya
"Finally.....you have a trip" dakatawa yayi daga zuba wayoyinsa da yakeyi a muhalli na musamman da aka tanada masa saboda ajjiyesu,ya waiwayo yana dubansa da shanyayyun idanunsan nan dake ma kowa kwarjini
"To where?"
"the construction work of the estate in lagos should be checked sir" juyowa yayi gaba daya yana dubansa
"Did something happen?"
"Kamar akwai qorafe qorafe sir....but sir Jabir will explain to you" shuru ya danyi kana ya kada kai
"Okay....you can go, I need thirty minutes to get ready before entering the first meeting, tell them,and.....send me Mr. Martin"
"Okay sir" ya amsa a ladabce yana juyawa dauke da project planning manual dinsa.
Iska ya furzar daga bakinsa yana murza hannayensa guri guda,yana son duk yadda za'ayi ya fita da amna zuwa wani guri da zai zame mata baqo ko na kwana uku ne,He promised her,kuma duk yadda zaiyi baya yadda yayi mata alqawari ya saba mata,bama ita koma waye zaiyi mu'amala dashi,amma kuma yaga alama kamar dama ba zata bashi damar hakan ba,sabbin sabgogi sai danno kai suke,zai yi qoqari ya duba,koda a wannan karon zata kama ya tafi lagos din da ita ne zaiyi wannan qoqarin.
Shigowar secretary dinsa ya katse masa tunani,dauk da basket din da shi sam yama manta dashi
"Sir,It's your food,you forgot it in the car" duban basket din yayi yana shafa gaban kanshi,daya hannun nasa kuma riqe da biro,kallon saman ido yayi masa yace
"Drop it here" a ladabce ya qaraso ya dora masa shi saman table din nasa saidai kuma daga gefe guda,wai ko xaiyi abinda zai dan wanke kansa a wajensa,saboda yasan me laifi ne shi a wajensa,saidai har yanzu baice masa komai ba,shurunsa kuma bashi da sauqi sam a wajensu.
Dubansa ya sakeyi,kamar zai magana sai kuma ya shareshi yaci gaba da rubutu akan file din dake gabansa,ya danyi jim yaga ko zaice wani abu amma yaga baibai ta kansa ba,sai ya danyi gyaran murya
"Sir,akwai baqi dakeson ganinka...."
"Ka gaya musu,yau bazan samu damar ganin kowa ba,tell them in a polite way,they're our client.....don't repeat it again" J ya fada da kakkaurar muryar dake nuna gargadi da kuma jan kunne ba tare da an fito an maka filla filla da laifin da kai kanka kasan ka aikatashi ba.
A ladabce ya kada kansa
"I will not repeat it sir,am sorry" bai amsa masa ba yaci gaba da aikinsa,shi kuma ya juya ya fita.
Files din dake gabansa ya gama dubawa,wadanda zai sakama hannu ya saka musu,ya tattare takaddun da zaiyi amfani dasu sannan ya shige toilet din dake manne cikin office din nasa.
Yana fitowa jabir na shigowa office din,kai tsaye kamar kowanne lokaci da bashi da shamaki da shigowar
"Good morning" ja'afar ya fada yana sauke hannun rigarsa da yayi rolling up don kada ruwa ya taba
"Morning dude,mun tashi lafiya" jabir ya qarasa maganar yana zama saman kujeru guda biyu dake gaban table dinsa
"Alhamdulillah....ya jikin madam?" Goshinsa ya murza
"To,da sauqi,yau kam ko breakfast ban samu ba,,she can't cook"
"Allah ya bada lafiya" ya fada yana dawowa mazauninsa.
Hannu ya miqa zai dauka wani file,sai ya ture murfin daya daga cikin warmers din,cikin qanqanin lokaci qamshi ya cika wajen
"Wow,wannan fa?,daga ina?" Jabir ya fadi yana leqa warmer din,tambayar ta dan ja hankalin ja'afar,ya daga kai yana kallon abincin shima qamshin na cika qofofin hancinsa,kafin ma yace wani abu jabir ya buda warmers din ya fara serving kansa tare da ja'afar din a different plates,ya kammala ya tura masa gabansa shima yaja nasa.
Ko sau daya jabir ya kasa riqe bakinsa daga yabon abincin,da gaske kuma yake,dadin abincin yakai masa ko ina,duk yadda ja'afar yaso basarwa qamshinsa da kuma yadda jabir keta santi akai yasa ya gaza daurewa,sai ya rufe file din,yaja abincin shima ya fara ci.
Loma biyu kacal ya yadda da abinda jabir din ke fada,saidai ya dake ne ba tare daya nuna ba
"U have a great cooker" jabir yayi furucin yana gyada kai
"what is happening with our Lagos contract?" Ja'afar ya kauda wancan maganar ya sako masa wannan,baice komai saboda yadda girkin ke dibansa,ya fiddo wayarsa yayi dan danne danne ya turawa ja'afar gabansa,sai ja'afar din ya bishi da kallo,ya fuskanci sosai yakewa abincin santi,kaman zai magana sai ya fasa,ya dauki wayar yana duba abinda yake son nuna masa.
Ya jima yana nazari bayan ya tsaida nashi cin abincin,har jabir ya gama ya wanko hannunsa a toilet ya fito
"Da zaka kyautamin yaa J ai da an samin kwano a gidanka kafin my fa'emm ta warware" sai sannan ya dauke idanunsa daga kan wayar,ya watsa masa harara
"Lokacin aiki ne wannan,ba zancan family ake ba yallabai"
"Magana anan fa ta zama dole,kana samun irin wannan kabakin ya kamata a ga canji a jikinka,kadan aje tumbi haka"
"Irinka ne ni da zan kwanta?,so kake wataran ka kasa aikata komai a gad....." Shuru kuma yayi ba tare daya qarasa ba,kaman wanda wuta ta daukewa
"A gado ko?,kuma hakane fa dude,ku da yake expert ne ta wannan fannin zaku fimu sanin sirrin farin shiga" jabir ya fada dariya sosai na kubuce masa.
Karamin tsaki yaja yana tura masa wayarsa da qarfi gabansa,banda jabir din yayi hanzarin saka hannu ya tareta da babu abinda zai hanata faduwa qasa,har yanzu dariyarsa yake kafin yace
"Na duba mana ticket na tafiya lagos jibi in sha Allah"
"Hakan yayi" ja'afar ya fada yana miqewa tsaye don shima ya wanke hannun nasa,ya wuce jabir daketa qunshe dariya har yanzu.
Sai gab da la'asar sannan ya samu kansa,sanda ya dawo office ya taras da miscall har uku,bai iya biba sai daya dawo daga sallah,yana zaune daman cussion yana dan sauke gajiya yabi bayan kiran.
Sosai tayi zurfi cikin tunani lokacin da take kwaba qullin alkubus din data yiwa amna alqawarin yi yau,amna na gefanta tana faman zuba mata surutu kaman yadda ta saba,zaune saman sink daura da tap din dake kitchen.
Tabbas fuskar hajiya munubiya ta gani tana fitowa daga sassan unaisa,unaisan na biye da ita,amma duka ba wannan bane yafi tsaya mata ba a rai,maganganun da kunnuwanta suka jiye mata
"Duk sharrin ammansa ne d wannan makirar tsohuwar,na gaya miki kiyi da gaske,kiyi kamar kinayi,ki kuma zuba ido sosai,zakiga dukka abubuwan da na gaya miki" me amma ta tsare ma haj munubiyan?,me kuma anni itama ta tsare mata?,meye alaqarta da unaisa da har ta zabi ziyartarta a kebantaccen lokaci irin wannan?,bayan basu jima da haduwa a gida ba?,bama wannan ba duka,ame zata zuba ido?,kwata kwata zuciyarta bata kwanta da zuwan haj munubiya ba,duk da bata ganta ba amma ta fita daga gidan ba tare data nema kowa ba.
"Anty moon ana kira,Allah yasa daddy ne" amna ta fada tana tattara hankalinta,ko daya maimunatu bata ma fuskanci wayarta bane saboda sabon ringtone dake kai.
Dab da zata tsinke ta daga,saboda sai data tsaya ta dauraye hannunta ta kuma gogeshi
"Assalamu alaikumm" yarrr yaji tsigar jikinsa ta tashi,sai ya zame kadan yana sake jingina sosai da kujerar,ya kuma dauke dukka qafafuwansa ya dora kan center table din yayi crossing nasu.
Har zata sake maimaita sallamar tata jin shuru,sai tashi muryar ta ratso ta cikin wayar,ta kuma isar da saqo zuwa ga qwaqwalwarta cikin lokaci qarami,har cikin bargonta taji sautin nasa,tsigar jikinta ta zuba itama
"Wa'alaikumus salam" ya amsa mata muryarsa can qasa kamar wanda ya tashi a barci,a hankali ta cira wayar daga kunneta ta juya ta miqawa amna,idanunsa na a lumshe muryar amna ta maye gurbin tata muryar da yake sanya ran ji
"Daddy i missed you, please daddy ka dawo da wuri,anty moon tana maka favourite dinka,daddy zaka dawo?" Murmushi mara sauti ya kubce mata
"In sha Allah amnee"
"Thank you dad,daddy pizza please"
"Amnaaaa" yadan ja sunanta,da sauri ta tareshi
"Please daddy say okay"
"Okay" ya amsa mata kamar yadda taso,sai ta shiga murna tana masa godiya.
Duk yadda yaso ya daure amma sai ya kasa,hakanan ya samu kansa da cewa
"Bata wayar" da sauri kuwa amna ta miqa mata,saita tsare amnan da ido tana son bin ba'asi,murya can qasa da sigar rada tace
"Daddy" amsar wayar tayi,kamar zata sanya a kunneta sai kuma ta latse wayar ta ajeta gefe taci gaba da kwabinta,dubanta amna keyi cikin rashin jin dadi kamar zata saki kuka, murmushi maimunatu ta saki,yarinyar ba zata gane ba,matuqar zata ci gaba da jin muryarsa to akwai damuwa,har yau bata fita daga tarkon maganin data shama kanta ba,lallabawa take
"Daddy yana aiki,ba'a son a dinga disturbing nasa,ko kinaso yayi ciwon kai?" Da sauri ta girgiza kanta
"Okay,budemin ledar can maza a dafawa daddy abinci" sai kuwa ta hau bude mata fararen ledojin,saboda dasu xatayi amfani,cikin ranta tana mamakin tsabar wayo na yarinyar da har ta iya daukan wayarta ta zuba numbers din daddyn nata ta kira,wanda already ta dade da haddace ta.
Daga wayar yayi daga kunnensa yana kallo cikin mamaki,yaji sanda yarinyar ta bata wayar,it means kashe masa waya tayi?,sai yaji wani abu ya tsaye masa a rai,karon farko kenan da wata diya mace a duniya ta taba yi masa hakan,ransa ya sosu sosai,ya furzar da iska daga bakinsa
"me hakan ke nufi?,ta dauka shi sa'anta ne?,she doesn't know who I am" ya fada yana jin zafi har cikin ransa(a hayye,mai yi ne yau akayi masa,ashe dai babu dadi😝). [11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 58
Assalamualaikum
NAFISAT K ABDULLAHI Is an actress in the kannywood industry
She's a singer and can sing all types of songs
You can't afford to miss her newly released song named *KADDARATA* part 1-4 on her YouTube channel *OFFICIAL FEENAT*
You can only click on this link and stand a chance to listen and watch her amazing video
https://youtu.be/t__84EwU7Fo
Dont only enjoy the emotional video but also *SUBSCRIBE* to anable you to be notified when ever she upload another video
Like and drop your comment under the video to encourage her do more of that .
The only way you can support and encourage her is by *SUBSCRIBING* to her YouTube channel below
https://youtu.be/t__84EwU7Fo
She is used to noticing those following and commenting on her videos .
*GUESS WHAT*?
https://youtu.be/t__84EwU7Fo
Click and see for yourself Thank you so much
________________________________
58
Gefe ya janye mata,abinda yayi mugun yi mata dadi kenan,ta kuma bawa kanta tabbacin akwai nasara kenan,sai ta fara takowa zuwa ciki tana kuma sauya salon tafiyarta cikin kwarkwasa da taku d'ai d'ai.
Dab da zata gotashi tayi rangaji ta kuma fada jikinsa,bai tarota ba bai kuma hanata ba,damar data samu kenan ta ruqunqumeshi gaba daya cikin jikinta,duk yadda taso ta daure amma ta kasa,sai ta fara masa wasanni cikin son shagaltar dashi.
Tabbas tayi nasarar sake kunnashi,tunda dama a kusa yake,saidai daga lokacin da ya jata ya fara nuna mata nata salon qwarewar sai al'amarin ya sauya,tun tana iya jurewa irin salon wasanninsa har ta fara gayawa kanta akwai matsala fa,tasan kanta,duk jarabarta akwai iya limit dinta,tana da matuqar rauni ta nan bangaren wanda ba kasafai ta fiya son a dameta ko a zurfafa ba,ko saurayi ne ka fiya nacin manne mata yau gobe jibi zata qara maka wuta,takan ce ita ba riga bace da za'a yita wanketa,daga dukkan alamu yadda yake aike mata da saqo cikin wani irin zafin nama kadai ya isa gaya maka wanne irin kalar mutum ne shi.
Tuni idanunta suka raina fata,ta kuma fara qoqarin guduwa,ta tabbatar ba zata iya ba,ba zata daukeshi ba,don komai zai iya faruwa,qarfinta tattara ta watsala qasan gado tana dafe da lips dinta dake mata radadi kamar zasu yanko su fado,yunquri yayi kamar xai bita abinda ya sanya babu shiri ta miqe ta lalubi hanyar fita da sauri.
Saman gadon ya zube yana fidda wani irin murmushi,shi ya sani ba kowacce irin mace bace zata iya daukeshi ba,ko shaheedansa tasha fama kafin ta saba,saidai da yake mutum ce mai juriya sai ta saba din a hankali,take kuma kula da duk hanyar da zatasan zata sama masa farinciki da nutsuwa.
Ko baya son mutum ba kasafai yake fidda hakan quru quru ba,amma baisan dalilin da ya sanya sam ko sau daya bai taba jin wani abu guda daya daya motsa zuciyarsa a kanta ba,a hankali ya saki tsaki yana saukowa daga saman gadon,sai yaji gaba daya yana qyamar jikinsa bawai don ya fitar da najasa ko wani abu ba,toilet ya shiga ya hada ruwan dumi sosai yayi wanka.
Abu kaman wasa sai gashi gaba daya daren yazo masa a wani irin birkice,sau biyu yana sake wanka,a wannan karon dai wankan ibada ne,tsakiyan dare da kuma kafin sallar asuba,me yasa mafarkinta ya hanashi bacci?,me yasa mafarkinta ya hanashi sukuni?,yana gaban mudubi a zaune yana lissafa tsaho shekaru da watannin daya dauka baiyi rayuwa da mace ba,sai ya furzar da iska daga bakinsa,tabbas wannan abun da ya farun yana da nasaba da dadewar da yayi da nisantar rayuwa dasu,bawai wani abu bane na daban.
Dab da liman zai tada sallar asuba ta buda idanunta,tana budesun abubuwan da suka faru a daren jiya suna dawo mata fes cikin kanta,sannu a hankali ta waarasu cikikin dakin,yana nan a yadda yake har hasken data kunna kafin ta kwanta,saidai sanyin dake busawa ya fara mata yawa saboda iskar asuba data gauraye duniya.
Hannunta ta daga tana shafa saman mararta a hankali,sakayau take jinta,babu wannan ciwon,hakanan babu feelings din gaba daya,sai ta sauke ta juya hannun damanta,idanunta suka sauka akan amna dake baccinta cikin kwanciyar hankali,hannunta ta dora kan fuskar yarinyar da wasu lokuta take mata yanayi da fuskan mahaifinta,batasan ya akayi murmushi ya kubce mata ba,sai ta miqe ta zauna sosai tayi kissing goshinta,sannan ta sake gyara mata kwanciyar gami da ja mata bargon sosai.
Bandakinta ta wuce,ita dinma sai da tayi wanka don bata yadda da kanta ba,sannan ta dawo ta saka prayer jilbab and skart da takanyi amfani dasu musamman a sallar asuba irin haka,ta tada sallarta.
Ko data idar qur'aninta ta dauka,bata wasa da tilawa ko don saboda haddarta,ta buda daga inda ta tsaya jiya ta dora,cikin qaramin sauti da kuma lallausar muryarta dake koyi da qira'ar shaik khalilul khusari.
A nutse ya turo qofar dakin a hankali,sautin karatunta ya baqunci kunnuwansa,sai ya maida qofar kawai ya rufe ba tare daya katse mata karatun ba,ya juya yana barin wajen,sautin karatun yana bin kunnuwansa har zuwa sand yayi nisa a wajen.
"Itama matarka ce" zuciyarsa ta raya masa sanda yake shirin wucewa zuwa saman sa ba tare daya biya sassan unaisa ba,wannan tunanin ya sanyashi sauya akala,ya isa qofar falon ya murdata,sai ya jita a kulle, knocking ya soma,saidai babu alamun za'a bude masa,mutum ne da bai fiya tsawaita abubuwa ba,don haka yana qara biyu ya juya yayi gaba,taku hudu cikin na biyar yaji an bude qofar,ya waiwaya a hankali idanuwansa a kanta.