Kenza eBookz

Gurbin ido huguma complete - Chapter 41

Gurbin ido huguma complete - Chapter 41

Gurbin ido huguma complete Chapter 41: Gurbin ido huguma complete Chapter 41. Zaune take saman three sitter dinta,tana sanye da doguwar rigar atamfa,sai…

3,318 words

Zaune take saman three sitter dinta,tana sanye da doguwar rigar atamfa,sai dankwalin kayan dake aje a gefe,kanta dake cike da gashin doki da aka yiwa kitso tamkar nata yana a bude,ta miqe qafafuwanta tana kadasu,hannunta dafe da wayarta da alama chart takeyi,gefanta teburin glasa ne dake hargitse da ragoyin abinci gorar ruwa data lemo dukka da tasha.

Sosai tayi mamakin ganinsa a sassan nata,karo na farko kenan tsahon zamanta a gidan,duk yadda taso ta danne farinciki da mamakinta amma sun gaza boyuwa,tana daga zaunen tace masa

"Bismillah ga waje....." Ta datsi maganar tare da qwallawa dayan ne aikin nata dake cikin bedroom dinta tana gyaro mata shi kira,sai gata jiki na rawa,ta zube itama tana gaidashi,da hannu kawai ya amsa mata ba tare da ya dubi sashen ta ba

"Ki hado masa abinci da abun sha" ta bata umarni kai tsaye,sai ta miqe da hanzari ta fice,cikin zuciyarsa yake jin qyanqyamin maganarta,yar aiki?,ta kawo masa abinci da abin sha?,definitely batasan shi ba,batasan komai a kansa ba,ta yaya zai fara tsara zama da irin wannan?.

Daga kai tayi ta dubeshi still yana tsaye hannayensa saye a aljihunsa

"Have a seat" ta sake maimaitawa,tana jin wani dadi da izza tana shigarta,ko har ta fara cikin nasara ne ya biyota da kansa?,indai ko hakane lallai zata nutsu ta yanka qa'idojinta da sharudda wanda zasu dace da rayuwarta ba matsi balle takura.

Baice mata komai ba,yafidda hannuwansa daga aljihu tare da daurin kudi sabbi ya matsa gaba kadan ya ajjiye mata su

"I don't have your account digits....zan xanyi tafi....so koda zaki buqaci wani abu" sai ya ciro dan qaramin qawataccen complimentary card dinsa milk da aka yiwa ado da zaiba ya aje mata

"You can contact me" dauke idanunta tayi daga kan card din ta mayar fuskarsa,wani abu na mata yawo a zuciya,wannan tafiyar da yake fadin zaiyi a qa'ida ace da ita zai tafin,amma sai wani girman kai ya taso mata,meye nata na damuwa ko nuna zakwadin tafiya?,bayan sun zagaya duniya da kyau,kudi sosai daddynta ke fitar musu duk sanda suke son su fita wata qasar,kada ma tayi magana ya rainata yaga kamar so take yaje da ita ne, shikenan sai ta amsa tayin da haj Aaya tayi mata na zuwa inda itama kafin sun dawo,don haka ta koma ta jingina da kujerar tana cewa

"Allah ya kiyaye hanya" labbansa kawai ya motsa alamun amsawa,sannan ya juya yana ficewa daga sashen hadi da bar mata qamshin turarensa.

Ajiyar zuciya ta sauke sanda ya ida ficewar,ta lumshe idanu tana zuqar daddadan qamshin nasa,ashe yadda take hangensa da tsada daga nesa yafi haka wuyar samu ma daga kusa?,amma dai ko yaya ne ita ba zata sake bada kanta ba,zata ci gaba da amfani da girma da martabarta,har sai ya fahimta ya kuma kawo kanshi.

*******Tun da ta farka da safen amna ta kasa komawa barci,wai batason tayi barci daddy ya tafi ya barta,tunda yace flight din safe ne zasu bi, maimunatu nata mata dariya tana kuma shirya mata kayanta,dai dai da yadda tace haka daddy yake shirya musu idan zasuyi tafiya,ba wasu kaya masu yawa ba masu.kuhimmanci kawai ake dauka,sauran abinda basu da,yafi ganewa ya siya musu a can.

K'arfe tara da minti ashirin ta kammala komai harda break fast dinsu,ita dince kawai.batayi wanka ba,tun jiya bata ganshi ba,tana daki dai ya shigo sunyi magana da amna,kafin ta fito sun gama ya fita,kamar ta shareshi amma sai taga bai kamata ba,kodon diyarsa dake qaunarta,don haka ta dauki kwando ta shirya komai dai dai da yadda amnan zata iya dauka

"Muje na rakaki ki kaiwa daddy" daman zaman jira take,ta kuwa sauko da saurinta,maimunatu ta dauki kwandon suka fito tana tsokanar amna,kada dai ace daddy ya tafi ya barta,ta qyalqyale da dariya

"Daddy baya fadin alqawari fa ya saba anty" kai ya jinjina tana murmushin yadda yarinyar tasan halin mahaifinta,duk da shekarunta basufi hudu ba.

Daga second matattakala ta biyu ta tsaya ta miqa mata kwandon,sai ta tsaya tana duban amnan tana ci gaba da haurawa har takai qarshe sannan ta sauke idanunta daga kanta tana juyowa don barin wajen taje ta qarasa abinda batayi ba.

Waiwayowar da zatayi suka hada ido ta ita,sanye take cikin wanu straight leg trousers da shirt spaghetti hand,siriryar silver chain ne a wuyanta da qaramin dan kunne barima, qafarta high hill ne,fuskarta ta wadata da makeup sosai.

Kallon kallo suka yiwa junansu,sa'annan unaisan ta zarce da yima maimunatu kallon qurilla daga sama har qasa.

Wasu soft nigh gown ne a jikinta farare tas tas kamar ba dasu ta kwana ba, gashinta mai laushi da santsi nannade cikin wata hula me zubin shower cap,kwantacciyar qananun sumarta ta gaban goshinta zuwa qeya dukka ta fito ta sake qawata fuskarta kamar ba daga bacci ta tashi ba,jikinta na fidda qamshin turaren baccinta data jima da warewa musamman saboda bacci kamar yadda afra ta koya mata,fararen santala santala hannunta dukka a waje suke saboda yanayin hannun rigar dan qarami ne sosai, tsintsiyar hannunta cike suke da duwatsuntan nan asalin wadanda ta gada daga daadarta,ko sau daha bata taba sha'awaf ciresu daga hannunta ba,sai suka kuma sake mata kyau suka haske farar fatarta dake luwai luwai fes kuma jajir da ita,kullum duwatsun kamar sake gogesu akeyi saboda sheqin da sukeyi,qafarta wani farin slippers ne mai taushi da aka yiwa wani adon gashi gashi daga sama.

Da qyar unaisa ta hadiye wani abu me tauri,haushi sosai ya cikata ganin yadda maimunatun tayi gaggawar dauke idanunta daga kanta tayi gaba kamar batasan wacece ita din ba.

"Agwai" ta kirayeta da sunan da tasan zai bata ranta,sai tayi kamar bata jita ba ta sakeyin gaba

"Hey dake nake magana" nan ma shuru,taci gaba da takawa zuwa sassanta,zuciya ta ingiza unaisan,sai tayi saurin takawa ta kuwa sha gabanta

"Don baki da kunya kina ji ina miki magana?,wato kin samu sake saboda kina zaton kin hada miji dani ko?,mijin da kike hoto a wajensa?,ba kowan kowa bace ke illa 'yar qauye mazauniyar riga,ki kiyayeni wallah,bakisan wacece unaisa ba,diya ga ministern ilimi" wani kallo maimunatu ta watsa mata,karon farko tun zuwanta gombe da taji wani ya bata mata rai,har ran nata ya sosu har haka

"Duk da nike bafulatana amma ban taba daukar tallan nono ba har kawo rana irin ta yau,kiwo kuwa wannan ado ne ga dukka cikakken bafulatani,koda ma ace nayi tallan nono ai ba aibu bane ba kuma gazawa bace,saboda dan halak baya manta tushe,tushiya kuwa masomin dukka wata daawa ce da tayi tsiro ta fito al'umma ke kallonta......" Daga wannan ta kewaye unaisa ta qarasa shigewa falonta ta kuma rufe qofar ta abinta,take unaisa ta sake hasala,sai ta juya zuwa stairs din ja:afar,sai kuma ta sake ja ta tsaya,idan ta hau tace masa me?,kada mutuncin ta ya zube a idanunsa,bari,zatayi dealing da yarinyar a cikin gidan da kanta,dole tayi.laushi,kuma dole tayi mata biyayya,badai tafiya zaya yi ya barsu ba su biyun a gidan ba?. [11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 64

Da murmushi suka dubi juna ita da fatiman,ta bata hannu sukayi musabaha sannan suka fara gaisawa,fatima na matsa mata gefenta ta zauna,amna na saman qafafunta.

Cikin mintunan da sukayi suna jiran lokacin tashinsu ta sake sabawa sosai da fatima,kamar su dauki shekaru tare,tana da sauqin qai da kuma yawan hira,ta dauki maimunatu kamar mate dinta,duk da ta bata aqalla shekaru uku,don ita ta rufa shekara ashirin,wannan yasa maimunatu ta sake sosai,suka shiga hira da fatiman,suna baiwa juna labarin makaranta,duk da fatiman ta gama secondary school,yanzun haka tana 200level ne.

Tare da fatiman suka shiga jirgin,sai itama ta duba jikin boarding pass dinta kamar yadda taga fatima tayi ta laluba seat number dinta.

A hankali take dubawa har ta iso gurin,tuni daya kujerar wadda ita ke bakin window me ita yana zaune akai,saita juya tana duban inda su fatima ke zaune,ita da amna ne seat number dinsu daya, jabir kuma da ja'afar wadanda seats daya ne suka rabasu,batasan tsarin jirgi ba,tunda ba sabawa tayi da shiga ba,don haka ta zame qaraman jakar dake kafadarta ta zauna saman kujerar bakinta dauke da bismillah.

A hankali ya waiwayo yana dubanta,matashin saurayine wanda duka duka bazai wuce shekara ashirin da bakwai ba,kana kallonsa zakasan wayewa da hutu sun ratsashi,unexpected ya ganta a kusa dashi,sai ya tashi ya zauna sosai idanuwansa a kanta,duk yadda yaso basarwa amma ya gaza,cikin muryarsa dake nuna zallan iyayi yace

"Sannu 'yammata" a hankali ta waiwaya ta kalleshi,sai ta dauke kanta tayi gyaran murya kawai ba tare da tace komai ba, shima sai yayi shurun,amma kuma lokaci lokaci yana waiwayowa ya kalleta,saidai ta basar,ta kuma tsuke fuskarta da kyau,kamar yadda ko sau daya bata waiwaya ta dubeshi ba.

Tunda ta zauna a seat dinta ya fuskanci wanda yake abokin xamanta hankalinsa ya gaza kwanciya,kunnuwansa naga jabir ne dake ta masa bayanin wasu receipt da suka biya kudin wasu clearance a wajen custom's,saidai dukka hankalinsa yana kanta.

A hankali yaji kamar ana matsa zuciyarsa sanda ya fahimci saurayin yana yawan juyawa yana kallonta,ya dinga qoqarin dannewa da kuma kauda hankalinsa amma sai ya gaza,agogon hannunsa ya daga ya kalla,akwai awa kusan biyu a gaba kafin jirginsu ya sauka a lagos,sai yaja wani dogon tsaki,abinda yaja hankalin jabir kenan,sai a sannan ya fahimci bama fahimtar bayanin nasa yake ba,yakai idanuwansa inda ja'afar din ke kallo,sai a lokacin ya gane abinda ke faruwa,cikin taqaitaccen lokaci jabir ya qare masa kallo,hatta zamansa bai zauna properly ba,kamar wanda taushin kujerar bai masa ba,amma da alama duka bai fuskanci hakan ba shi.

Gimtse dariyar dake son qwace masa yayi,ya buda baki zaiyi magana dai dai lokacin ja'afar din ya dunqule hannunsa ya buga a hannun kujerar da yake kai

"It can't" ya fadi yana miqewa zumbur,ya taka a hankali ya fito daga inda yake ya nufi wajensu.

Cikinsu ba wanda yasan da wanzuwar tasa a wajen,dai dai sanda saurayin ke qoqarin miqa mata tissue ganin ta rufe bakinta atishawa nason fita,ido hudu sukayi da ja'afar dake tsaye a kansu,ya goye hannuwansa a qirjinsa ya zuba masa wannan idanun nasa dake saurin ladabtar da kowa,wasu kibiyoyi da baisan suna fita a idanunsa ba nata spark.

Sosai kallon da yake masa ya dakeshi ya kuma yi masa kwarjini,sai ya janye tissue din bakinsa na subucewa da cewa

"Lafiya?" Cikin fargaba tare da tunanin qila matar aure ce kenan,tunanin da baizo ransa ba sai a lokacin,maganar da yayin tasa maimunatu daga kanta,suka hada ido,sai ya mata inkiyar ta tashi,yayi gaba,ta miqe tana sake saqala jakarta ta biyo bayansa.

Kafin su iso jabir har ya miqe yabar mususeat din,dariya kaman zata kasheshi,ya koma inda ta taso din,saidai koda hakan shima ya taya J dinsa kishin da yaketa qaryata kansa bashi yakeyi ba,ya dubi matashin

"Ku dinga hankali da matan mutane" ya fada yana jifansa da wani kallo me kama da harara,don shi din dama yafi ja'afar magana.

Shi daya ya dinga quncin rai,yaja tsaki yafi a qirga,ita dai bata dashi komai ba,har awannin da suka rage musu ya cika jirgi yayi landing a lagos cunkus dakin tsumma.

Motar kamfaninsa ta nan lagos ce tazo daukarsu wadda aka tanadar masa saboda irin haka dama sauran mamyan baqi da sukeyi daga qasashen waje abokan kasuwancinsu,already jabir ya musu booking na dakuna a daya daga cikin five star hotels,wanda kuma yafi kusa da inda sukazo duba ayyukansu,ciki da falo ya kamawa su ja'afar saboda amna,shi da fatinsa kuma single room.

To tun saukarsu lagos basu samu zama sosai ba,idan motar company tazo ta saukesu tun safe sai dare,wannan ya bawa su maimunatu damar yawo sosai cikin garin lagos,jabir yasa wata motar daga company musamman take zuwa duk sanda suka gama shirinsu ta daukesu tayita zagayawa dasu guraren shaqawatawa kala daban daban,ya tura musu enough kudi ta account din fatima,ga kuma bandir da J ya ajjiye mata itama,basu da wata matsala ta komai,duk yadda maimunatun tayi tsammanin ba zataji dadin tafiyar ba sai abun yazo mata akasin hakan,taji dadin garin fiye da zatonta,sunyi yawo sosai,hakanan fatima ta musu siyayya mai yawan gaske,musamman maimunatu da batazo da wasu kayan ba,saidai kuma ita fatiman kusan duka qananun kaya ne siyayyar nata,sai sakakku da zata iya fita dasu cikin gari,don haka maimunatu ta ware kowanne jaka daban,wandancan da takejin ba zata iya fita dasu ba,da kuma wadanda zata iya sakawa.

Duk yadda garin ke mata dadi amma bata mance da lissafin lokacin komawarsu makaranta ba,sunyi waya da afrah itama tana sake tuna mata

"Allah ya nuna mana,amma bana gida ma,muna lagos,kuma banga alamun dawowarmu ba" dariya sosai afra ta sake

"Wannan abu yayi min dadi,tsuntsun soyayyar ya fara sauka kenan,honeymoon aka tafi ne?" Kamar tana gabanta saita saki harara

"A'ah milkmoon aka tafi,tare fa muka tafi da amna,harda su fatima"

"To sai me?,bikin magaji zai hana na magajiya ne?,amna ina ruwanta?,zatafi kowa son a bawa daddynta kulawa,fatima kuwa na tabbatar saidai ta tayaki,kuma nasan ba daki daya kuke ba,kidai zauna garin kallon ruwa kwado yayi miki qafa"

"Mtsweew,Allah ya shiryeki afrah,gwara hajja tayi miki aure ta huta"

"Wallahi ko gwara a aurar dani a huta,idan ba haka ba......."

"Ba'a kunne na zaki qarasa wannan zancan naki ba,ya girmi kunnuwana" saita datse wayar tana dariya.

A hankali ta aje wayar a gefanta

_ki tsaya dai kallon ruwa kwado yayi miki qafa_,wai me yasa kowa maganarsa kan ja'afar ne,kowa kusan abinda yake fadi mata kenan idan irin wannan zancan ya hadusu,sai ta sauke ajiyar zuciya,idanuwanta na hango mata kalar soyayyar jabir da fatima,wata irin soyayya me nuna zallar kulawa da kuma shaquwa,ita kanta abun yana burgeta,sau tari idan ya kirata bayan ya fita tunda yawancin lokutta suna tare,sai tayi kasaqe tana sauraren kalar hirarsu,ta fahimci ita kanta fatiman ta gano kalar zamansu,don wani lokaci ta taba cewa da ita

"Shi namiji da kike gani,babu abu mai sauqi wajen sarrafawa irinsa,sau tari dama suke nema ko jira ka basu,mijinki ko?,hmmmmmm,astagfirullah,soyayyarsu ta dabance,duk sanda suka tashi nunawa mace soyayya za'a sha mamaki,saidai suna da wani irin aji da kamewa,wanda zaisa ki gaza fahimtar inda suka dosa" ajiyar zuciya ta sauke tana gyara kwanciyar rub da cikin da tayi saman kujerun falon,amna na daki tana bacci,dama a ciki suke kwana ita da ita,shi ya canjesu a falon.

Qarar security na jikin qofar taji,kafin kuma ta ankara an murda handle din an turo qofar,sai ta daga kai da sauri don ganin wanda ya shigo din,saboda ta san wannan ba shine lokacin dawowarsu ba,zata iya cewa tun zuwansu tsahon kwanaki takwas yau,sau uku kawai suka hadu ita dashi,tana qunshe a daki sanda zai fita,kafin ya dawo ta tattare tayi kwanciyar barci abinta.

Tun kafin ya saki handle din idanunsa ke manne a kanta,wata gown ce a jikinta ta wani material maras nauyi,wannan yasa kwanciyar rub da cikin da tayi ya bayyana mazaunai da qugunta sosai.

A hankali idanuwansa suka kai kai,ya lumshe idanunsa tsigar jikinsa na zubawa,sai ya juya ya maida qofar ya rufeta,sannan ya soma takowa cikin dakin bakinsa dauke da sallama.

Tuni ta miqe ta zauna kanta a qasa tana wasa da yatsun hannunta,itakam dawowarsa a yanzun kamar takura ce a wajenta,dole saidai ta koma daki tayita zama

"Sannu da zuwa" ta fada a hankali tana miqewa tsaye duk da bataji ya amsa ba,taku biyu tayi taga ya babbake gaba daya hanyar wucewarta,idanuwansa a kanta,yau din kallonta tsakiyar idanuwanta yake kansa tsaye,ya karkatar da wuyansa gefe daya yana son hukuntata da idanun kamar yadda ya saba

"Am...zan zan wuce" ta fadi muryarta nadan rawa,saboda jiki da zuciyarta da taji sun fara amsawa

"Idan naqi fa?" Ya amsa mata yana hade fuskarsa,mamaki amsar da ya bata ta bata,sai ta dan tsuke bakinta kadan kafin ta sakeshi,idanuwansa suka kai kai,ya sake jin wani abu na sauka a dukka sassan jikinsa,yana kuma gauraya da gajiyar daya kwaso,idan yace pink lips dinta basa burgeshi yayi qarya,qara taku uku yayi qwarara sai gashi a gabanta jikinsu na gogayya waje daya,kafin ta qara wani tunani ya sanya hannuwansa ta baya ya dorasu saman mazaunanta,take a kuma lokaci guda kowanne numfashinsa ya fara barazanar daukewa na wucin gadi,namiji ne shi tsayayye,ita kuwa mace mai rauni,wannan yasa fa gaza tsaiwa a muhallinta ta fada jikinsa gaba daya,kafin ta samu ta fusgo numfashin nata,ta fara qoqarin raba jikinta da nashi,amma tayi latti,don ya zagaye bayanta da hannuwan nasa gaba daya.

Ji yake kamar an jan jininsa da na'urar lantarki mara zafi,wani irin shock yakeji sosai,gudun zuciyarsa ya fara rawa

"Hope ba da irin wannan kayan kike fita ba?" Yayi maganar yana dagata daga jikinsa,muryarsa na wani irin fusga,kamar zata narke a wajen haka takeji,kanta a qasa ta gyada masa kai,fiye da rabin hankalinta yana kan qofar daki,kada amna ta fito,ilai kuwa sai ga qaran qofan bude dakin,ba tare daya juya sashen ba yaja da baya ya sulale saman kujera

"Hadamin ruwan wanka" ya bata umarni karo na farko kenan,don da kansa yake hadawar.

Kamar qafafunta ba zasu iya daukanta ba haka ta jasu tayi ciki,amna kuma ta fito tana masa sannu da zuwa,a jikin bangon toilet ta jingina bayanta bayan ta kunna ruwan tana jiran na dumi ya sauko,kowanne sashe na jikinta ya zama week,wai me yasa?,me yasa irin hakan ke faruwa da ita?,tuno irin wani sassanyan qamshi gami da laushin daya ratsa fatarta tayi lokacin da ta isa ga jikinsa,kawai sai ta goye hannayenta aqirji tana matse jikinta waje guda kamar me jin sanyi.

Ta gama hadawa ta juyo ta kama handle din da nufin bude qofar sai aka rigata shigowa,ja'afar dinne,sanye da trouser dinsa da fara qal din singlet dinsa kamar ba'a sanyawa jiki ita,ya cika qofar ya kuma taho gaba daya,so babu wani space da zata rabeshi ta fice,dole ta janye da baya har ya shigo,idanuwanta na kallon qasa,don ba zata iya kallonshi a haka ba,tsoro yake bata,gaba daya dantsensa wasu irin muscles ne dake nuna yadda ya qware wajen motsa jiki da kuma daga qarfe,daga hannuwansa zuwa qirjinsa duka sun bayyana albarkatun gargasar dake tattare da wajen.

Ta dauka zai janye mata ne,sai taji ya maida qofar ya rufe,ya kuma fara zare singlet din da tayi saura a jikinsa,da saurinta ta qara gaba tana yunqurin bude bandakin,saidai ya saka lock a jiki,ta saka hannunta zata murza ta bude,ta tsinci husky voice dinsa na mata gargadi

"Karki sake ki budeni,am taking bath" tashin hankali,sai taja da baya ta sake jingina da bangon zuciyarta na wani irin bugawa cike da tsoro,to wanka zaiyi itama wankan akace masa zatayi?,tsoro ya sake kamata ganin yana zare trouser din jikinsa,ta rasa a wanne side zata tsaya ba tare da taga kominsa ba?, kowanne sashe na bandakin glass ne da zai baka damar ganin abinda ke faruwa a kowanne bangare da bandakin,kota juya ma gabanta glass ne,idan kuma tace shi zata fuskanta ba?,inaa,ba zata iya tsaiwa gabansa bama,sai ta runtse idanuwanta gaba daya hawaye na taruwa cikin idanun nata.

Rufe idanuwan nata ya bashi damar kallonta son ransa,ba abinda yake fuskarsa irin qirjinta dake cike sosai,ya kuma zauna ta cikin rigar saboda wata tattarar roba da aka yi mata daga sama, qaramin murmushi na gefan baki ya sake sanda ya fidda trouser din saboda yadda yaga ta cuno baki gaba,komai nata akwai childishness a ciki,some times ba abinda take tuna masa illa lokacin amarcinsu irin wannan shida shaheeda,tana tuna masa abubuwa masu yawa tattare da ita,ko a yanzun sai yake gani kaman ita dince.

Rataye trouser din yayi,pants na maza ne kawai ya rage a jikinsa

"Miqomin sponge" kamar ya mata tsawa a tsakiyar kanta haka taji,ta yaya zata iya bude idanuwanta ta kalleshi a haka?,sake maimaita mata yayi,sai ta fara tattakawa a hankali tana lalube ba tare data bude idanunta ba,qaramin murmushi ya qwace masa ganin ta saba hanya,tana ta lalube har arean da yake tsaye,sai ya zuba mata ido ya rabu da ita,baice mata komai ba har zuwa sanda ta damqi hannunsa.

Saki taso yi da sauri amma cikin zafin nama ya riqeta,ya kuma janyota cikin jikinsa gaba daya,yayi mata rumfa da yalwataccen qirjinsa,ya kuma lullubeta da tattausar fatarsa,matseta yayi sosai cikin jikinsa wani numfashi mai nauyi yana qwace masa ba tare da ya shirya ba,wani irin body contact ya samu da ita irin wanda bai taba ba,tudun mazaunanta ya taba sashe mafi kima a jikinsa.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull