Gurbin ido huguma complete - Chapter 46
Gurbin ido huguma complete Chapter 46: Gurbin ido huguma complete Chapter 46. A haka ta dinga zuba idanu taji yayi mata zancan ta shirya komawa makaranta…
3,361 words
A haka ta dinga zuba idanu taji yayi mata zancan ta shirya komawa makaranta amma shuru,ko kadan shima bai sake tunawa da wata maganar makaranta ba,yana shiryawa zai fita gaida su amman wayar anni ta riskeshi,tace yazo shi da maimunatun takeson gani,amsa mata yayi da to,don bai kawo komai cikin ransa ba,gefe daya tun jiya zuciyarsa ke cike da mamakin unaisa?,ina taje?,ita dai ba qaramar yarinya ba bare ace bata tayi ko kuma an saceta,hakanan baiyi da ita zata fita zuwa ko ina ba,saidai duk da haka zaisa a bincika masa ko gida ta tafi.
Sanda yace ma maimunatu ta shirya zasu gidan muraran farincikinta ya gaza boyuwa,nan da nan ta buda kayanta na lefe,ta hada kaya sosai da zata kaima su annin da sunan tsaraba,ana zaune a mota yaga fitowarta,idanunsa suka dinga yawo a kanta saboda mugun kyan da tayi masa,yana zaune harta qaraso,sai ya bude murfin motar,ya zuro qafafunsa waje,ya kama hannunta ya jata zuwa ciki,bata musa ba tabi bayansa cikin fargabar kada dai yace an fasa zuwan,tuni ta narke fuska idanuwanta suka fara tara ruwan hawaye.
Closet dinta ya bude,ya fidda wasu kayan daban,sannan ya fara ware na jikin ta,hannunsa ta riqe gam tana dubansa,sai ya girgiza mata kai sannan ya zare hannunta.
Shi ya sake shiryata tsaf,ya isa da ita gaban mudubin yana tsaye a bayanta,dukkansu shi da ita suke kallon mudubin,ya sakar mata tattausan murmushi yana duban qwayar idanuwanta,yaso ya rage kyau da kaifin kwalliyar data yine,shi yasa ya shiryata da kansa,amma kuma ya gaza yin hakan,wani kyau na daban ta sakeyi.
Da wani irin zafin nama ya juyo da ita suna fuskantar juna,don har ta tsorata tana dubansa,hannunta saman kafadarsa, idanuwansa ya sauke kan jajayen lips dinta,wanda koda bata saka mishi jambaki ba iya man lebe ya wadatar ya fidda kyansa,miyansa ya tsinke,ya hadiye wani abu ta maqoshinsa,sannan yakai bakinsa saman nata a hankali yana lashe lips din nata hade da wani zafafan kisses.
Sai da ya gama kashe mata jiki gaba daya sannan ya dauke bakinsa yana sauke numfashi a hankali,sakinta yayi sai tayi taga taga kamar zata fadi saboda rashin qwarin jikinta,da sauri ya tallafe ta yana kallonta,a karon farko yaga yadda tayi laushi,don har ta cikin idanuwanta hakan sun nuna,sai ya ajjiyeta gefan gado sannan ya wuce toilet dinta a hankali.
Minti.biyu kawai ya fito yana goge fuskarsa,ya miqa mata hannunsa ta dora nata a kai sannan suka fice zuwa motar,cikinsu ba wanda ya sake cewa komai.
Yau kai tsaye sassan abbi suka fara dira,saboda khadim da suka hadu dashi yace amma da ammi duka suna can,tamkar ta nutse haka maimunatu ta dinga ji,sai take ganin kamar kowa yana karanto komai daga jikinta.
A matuqar kunyace ta gaida abbi sannan ammi,amma tana bedroom din abbin tana gyara masa gami da hada masa ruwan wanka,sai data fito ta gansu,sai ta shaidaws abbin ta gama tana qarasowa cikin falon.
Yau fuskarta dauke da wani irin murmushi da farinciki,ta qaraso tana amsa gaisuwar maimunatu gami da sanya hannunta dukka ta dagota,sai kawai ta rungumeta
"Ashe ke din jinin sa'adatu ce maimunatu?,na jima jikina yana bani kamar na sanki,kamar nasan wani da yake da.nasaba dake,ashe diyar matar dan uwana ce ke, alhamdulillah" ta qarashe maganar tana maimaita hamdalarta,yayin da kunya suka yiwa maimunatu qawanya.
Shiko jabir yana zaune qafafunsa harde da juna yana kallonsu,wani farinciki yana ratsashi,shaheeda ta tafi ga wata shaheedan,komai da yake qiyastawa na shaheeda wanda yayi missing nasa ya sameshi a wajen maimunatu,harma abinda ita din bata dashi.
Su laila nata kai kawo suna son samu space suyi hirar yaushe gamo da maimunatun amma kowacce idan ta shigo sai ta wayance da wani abun ta fice ganin ja'afar na wajen,sai da amma ta cikata da kayan ciye ciye a sassanta,amma ta kasa cin komai saboda kunyar amman da takeji
"Maimunatu,diyata ce ke yanzu ba surukata ba, maimakon ki sake sakin jikinki sai kuma ki sake dararewa?" Matsowa gaba kadan ja'afar din yayi,ya buda dukkan abinda amman ta ajjiye ya zuba mata,kafin ma ya gama amma ta miqe ta matsa a wajen.
Shanyayyun idanuwansa ya sauke mata
"Ko sau daya ban taba ganin kinci abincin kirki ba.....oya matso muci" ya fada murya can qasa,narkewa tayi kaman zata saki kuka,a shagwabe tace
"Nafa qoshi" idonsa ya lumshe yana cije labbansa,tana kasheshi.....har baisan iyakar illar da take masa ba idan tayi wannan shagwabar tata,tana jefashi a wani yanayi,har yana jin kamar bazai iya jurewa ba.
Kaman baiji me tace ba ya matso ya dauki spoon ya saka musu a ciki,ya tsareta kuma da idanunsa,dole ta dauka ta fara motsa abincin kafin takai bakinta,a spoon na biyu kuwa hannunta ya kama yakai bakinsa,idanu a waje tayi galala tana kallonsa,bayajin kunya ko tsoron kada wani ya shigo?,saidai shi ko a jikinsa,ci gaba yayi da tauna abincin,yana jin yana masa dadi a baki fiye da kullum,ko don da hannunta ta ciyar dashi?.
Wasa wasa sai gashi sunci abincin shi da ita ba laifi,shigowar anty maama yasa suka fara wucewa sassan anni ita da ita,kafin ya bisu a baya.
A nutse anni tayi mata kyakkyawan kallo guda daya,a take kuma ta fahimci komai ya kankama
"Anzo wajen,haka dama nakeso,zakaci qaniyanka" ta fada a ranta,tana amsa gaisuwa maimunatu,wadda ta duqa gabanta tana duban qafan annin data sake motsawa da ciwo,sannu take mata,tana jin ciwon annin yana taba ranta, tsohuwar nada kima da martaba a wajenta,sai ta karba man da take shafawar taci gaba da shafa mata,annin na tayata murnar na haduwarsu da sa'ade,da kuma maida zancan yadda abun ya kasance,anty maama na saka musu baki,itama har cikin ranta tana jin dadin kasancewar hakan
"Ni kaina na jima ina ganin yanayinta da anty sa'adah da fareeda,musamman fareeda,muryoyinsu kusan daya ne,duk sanda naji muryarta sai na tuna dasu,ashe jini daya ne"
"Ikon Allah kenan,ga abinda kaketa nema ashe yana kusa da kai baka sani ba" anni ta fada rana jin zuciyarta na mata dadi,abu daya ya ragewa maimunatu a yanzun shine bayyanar mahaifinta,wanda shima ta fara shirya yadda zata tunkari ja'afar da maganar,don ya kamata ayi wani abu a kai, lokaci yana dada ja.
Dai dai lokacin da yayi sallama ya shigo,kamar kowanne lokacin idanuwansa suna kan maimunatu,duk inda zaya shiga ita yake fara gani,muddin tana waje.
Qasan carfet yau din ya zauna,dab da anni da kuma maimunatu da jikinta yayi week tun shigowarsa,batason yayi wani abu da zai bata kunya a gaban anni,don haka tana gama shafawan ta ajjiye man ta matsa daga wajen.
Gaida annin ya fara yi yana mata sannu da jiki,ta amsa tana dubansa,kafin ta dauke kai tace
"Sannunku da hanya matafiya,ya gajiyar tafiya"
"Alhamdulillah" ya amsa mata hankalinshi kwance,kamar bai fahimci da gatse tayi maganar ba
"To ma sha Allah,ba wata doguwar magana bace,dama so nake na gaya maka,da Allah kayi da jiki ka maida yarinyar mutane makaranta,tunda dai amana na dauko,kai kuma alqawari ka dauka,to ya kamata ka sauke" ya manta rabon da yaji gabansa ya fadi sai yau,yadan lumshe idanuwansa sannan ya budesu yana duban anni
"Wacce makaranta?" Dubansa take saboda yadda taga zai raina mata hankali
"Makarantar da ubanka marwanu ya bude" dauke kansa yayi daga inda take,yasan anni,zata fadi fiye da haka ma,don haka ya fito mata shima a ja'afar dinsa sak
"Na cireta anni,wata zan canza mata"
"Dalili?" Ta tambayeshi harda riqe qugu tana qare masa kallo
"Kawai" ya amsata yana sassauta daurin agogon dake hannunsa,don a take yaji kamar ya matseshi ma.
"To uban maryamu,to billhuwallazi la'ilaha illa anta baka isa ba,uban kuturu ma yayi kadan ballantana na makaho,kaiiii ja'afaru,kayi ta kanka wallahi,bakasan wace maryamu ba hala,mu zaka mayar qananun mutane?,wanne irin zabine baa baka ba amma ka kafe can zaka kaita?,shine zaka tsire cireta a makaranta kanason yi mata walagigi da karatu?,to kayi qarya ka kwana da yunwa" boyayyar ajiyar zuciya ya saki,yana jin cewa ya shiga uku yau,tijarar anni ta dira a kansa
"Lemme explain you mana anni....."
"Lamma ma taci qaniyarta,kayi ta kanka fa,idan hausa hausa idan fillanci fillanci" hannunsa yasa ya dafe goshinsa da kyau,anni bata da kyau idan ta tubure,gashi jabir baya kusa ballantana ya tayashi,shi kuma bai iya daukan hayaniya da yawa ba har haka
"Relax.....relax,ba daina karatu zatayi ba,inaso ta koma day ne,i mean jeka ka dawo"
"Baka isa bafa,ita ka fara zaba mata ita zata ci gaba da zuwa,idan kaga ta daina saidai idan itace tace bata so....." Maida dubanta tayi ga maimunatu dake zaune,tayi shuru yana sauraren dambarwar tasu
"Ke maimunatu.....kinason komawa makarantarki......ko kin zabi dadi miji ya sauya miki wadda yaga dama?".... [11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 70
Seat din kusa da ita fareeda diyar sa'ade ta barwa maimunatu,dukkansu suna ta kallon maimunatu cike da zumudi a zukatansu,saboda suna da.labarinta sarai,sannan ita fareeda tana dan tuna wasu abubuwa da suka faru,tunda da dan wayonta suka bar gembu.
Cikin tafiyar awannin da suka cur hannun sa'ade yana cikin na maimunatu,kaf maimunatu ta labarta mata dukkan abinda take da buqatar sani,saade ta lumshe idanu hawaye masu dumi suna fita akan fuskarta
"Wata shari'ar sai a lahira,inno taci amanata taci amanar shatu,Allah ya jiqanki 'yar uwata,matsala na samu akan dukka abinda ya shafi bayanaina,aka samu wasu suka dauka sukayi amfani dasu suka aikata laifi,ya zamana ni ake zargi aketa nema,wannan dalili yasa abbansu yayimin kyakkyawan boyo,sannan akaci gaba da bincike,don yasan muddin ya fiddani aka kamani babu mai fitar dani sai Allah,wannan dalilin ya hanani dawowa gareku,saidai duk da haka nayi amfani da abbansu nayi aike gembu,waya kudi da kaya,ina amfani da wani boyayyen layi ina yawaita kiran inno akan yaya kuke ya lafiyarku?,koda yaushe nunamin take kuna nan lafiya,bana jimawa akan waya shi yasa bana samun damar cewa a bani ku,aike nake akai akai na kudi da kaya ashe baya samunku,ashe sun gama shirya abinda suka shirya,ashe sun cutar min da shatu na,sun kuma cutatar dake kema" sai suka sanya kuka gaba dayansu hannuwansu cikin na juna.
Dogon numfashi ja'afar dake daga can bayansu ya saki,tunda suka zauna hankalinsa da nutsuwarsa tana kansu,duk da baijin abinda suke fada amma yana iya fahimtar kuka suke,yana kuma ji a zuciyarsa maimunatun kuka take da gasken gaske,yana ta son ya daure amma ya gaza,yana jin kukan nata yana tabashi sosai
"Please,ka gaya mata ta daina sakata kuka haka" ja'afar ya fada idanuwansa a kansu,kallonsa jabir yayi baki galala
"Kai,surukarka ce fa,sannan kuma mamanka ta wani fannin,ita za'a cewa ta daina saka matarka kuka?,bazan iya ba" shuru ya ratsa tsakani,kawai sai ganin ja'afar jabir yayi yana miqewa tsaye,da alama zuwa zaiyi kenan ya shaidar mata da kansa.
Saurin damqoshi jabir yayi,don yasan tsaf xai aika
"Haba mana,kayi haquri mana romeo,dole fa suyi kuka,don bakasan komai bane" da mamaki ya juyo ya dubeshi,duba na son sanin abinda bai sani din ba,ba tare da yace komai ba jabir ya karanceshi,sai yace dashi
"Zauna na fada maka" ba musu ya koma ya zauna din,ya kuma tattara dukka hankalinsa ga jabir,yayin da jabir ya soma magana a nutse,dama.ya jima yana fatan zuwan wannan lokacin da ja'afar din zai san labarin maimunatu,yasan halinsa sarai,yana da wani irin tausayi na daban q zuciyarsa,sanin labarin nata zai sake haifar da wata alaqa mai girma a tsakaninsu,inda a baya ne,yasan halinsa......bazai taba tsaya ya saurareshi ba,coz bashi da interest,idan kuma yayi loosing interest akan abu babu mai sanyashi dole face mutum biyu zuwa uku a duniya,anni abbi da amma.
"Ashe nesa a kusa take?,ke din matar ja'afar ce,ja'afar kamar d'a yake a wajena,saboda dan qanwar abbansu fareeda ne"
"Amma?" Maimunatu ta fada tana dan fidda idanu cikin mamaki,a karon farko sa'ade ta gyada kai
"Qwarai,wala'alla banda matsalar dana samu.....wadda sai yanzu ta warware,dani za'ayi bikinku,nasan anyi bikin,amma ban san amaryar ba,don a sannan ba cikin hayyacina nake ba,yau sati daya kwata kwata da bayyanar gaskiya,aka kuma damqe wadanda suka aikata laifin,wanna shine ya bani 'yancina" kai maimunatu take jinjinawa,lallai soyayya ta gaskiya abace mai kima daraja da kuma wahala,ta jinjinawa abbansu fareeda da yadda ya bata dukkan kariya,duk da cewa basa a qasarsu,amma ya tsaya mata kai da fata don ganin ya kula da amanar da aka bashi
"Yaranki nawa diyam dita?,duk da nasan ba zai wuce guda daya ba tunda baku fi shekara da auren ba,saidai idan kinyo gadon dangin tamu daadar masu haifar twins" kunya ta kama maimunatu,saita kifa fuskarta a kafadar sa'ade,tana jin kamar ita da daadarta suke magana
"Babu ko daya" murmushi tayi tana gyada kai
"To Allah ya kawo masu amfani da albarka,yasa kiyita haifa mana bibbiyu,zuri'ar shatu na tayi dogon baya" tayi maganar cikin rauni dajin zafin mutuwar 'yar uwarta,wanda bata sani ba gaba daya sai kwanan nan.
Hawayen fuskarta ta dauke,ta waiwaya kadan baya inda su ja'afar suke
"Amma naji dadi da naga yadda ja'afar yake miki,da alama akwai tsaftatacciyar soyayya a tsakaninku" a kunyace ta saki murmushi tana yin qas da kanta,sai takejin kamar umma sa'aden tana iya karanto abinda ya faru tsakaninta da ja'afar din kwanaki biyar din da suka shude,don har yau bataji tafiyarta ta koma dai dai ba yadda take ada,sannan kuma ta fahimci akwai sauran dan ciwo ciwo a jikinta.
Jin bata amsa ba sai ta dora
"Haka nake fata,ki samu mijin marainiya,kuma ina da cikakken fatan cewa zaki samu haka daga ja'afar,indai yaro yana gadon dabi'u daga mahaifiyarsa,aishatu mutum ce nagartacciya,kawai qauna mai tsafta tsakanina da ita,bansan yaya zataji ba sanda labarin KE JININA CE ya risketa" sa'ade ta qarashe maganar tana gyada kai murmushi na kubce mata.
Duk yadda umma sa'ade taso ja'afar yabar mata maimunatu su wuce gidanta ko kwana daya suyi amma ya murje idanunsa,bai ma yarda ta ganshi ba,don tuni ya isa motarsa yayi zamansa a owners corner yana jiran isowarta,awannin data dauka ba tare dashi ba sai yake jinsa kamar wanda ya rasa wani sashe na jikinsa,ya sauke hannunsa da yake duban lokaci dai dai sanda take takowa zuwa gaban motar,fareeda da umma sa'aden suna biye da ita.
Sosai ya zuba mata idanu ransa yana motsuwa,yana kuma tuna labarinta da jabir ya bashi,wani irin nau'in tausayi na musamman na ratsa zuciyarsa kamar zai narkar da ita,how she survive?,rayuwa ba uwa ba uba?,babu yaya babu qani?,ba soyayya ba kulawa?.......tabbas ta cancanci samun komai,ta cancanci ta samu duk wani abu data rasa a baya,sai ya lumshe idanunsa sanda suke gab da motar,yana daukarma kansa wani alqawari,wanda ba wanda ya gayawa,tsakaninsa ne da ubangijinsa kawai.
"Ina fatan za'a kawomin ita ko ni ayimin alfarma nazo na ganta ko yallabai?" Sa'ade ta fada tana murmushi,kai ya jinjina mata da nashi miskilallen murmushin ya amsata a taqaice
"In sha Allah" tasan halinsa ba tun yau ba,don haka itama bata wani damu sosai ba,ta maida qofar ta rufe musu tana musu fatan sauka lafiya,kafin itama ta juya zuwa motocin da suka zo daukarta,zuciyarta cike fal da kewar maimunatu,wanda inda so samu ne su kasance tare,su kwana gado daya tana sake jin labarin rayuwarta.
Bata gama dai daita zamanta a cikin motar ba ta tsinci hannunta cikin nasa,ya daga hannun nata a hankali ya cusa cikin qirjinsa yana lumshe idanuwansa.
Shuru tayi kamar yadda shima yayi shurun,tana jin yadda zuciyarsa ke bugawa fat fat da qarfi bisa qaramar tazara sosai a tsakani,mintuna kusan uku suka kwashe a haka sannan ya bude idanuwansa ya azasu a kanta
"Awa shida kawai?,ta yaya zan jurema wasu awannin da suka fi haka tsaho da yawa?" Ya fada da mugun taushin,salon maganar daya haifar mata da wata kasala da kuma wani yanayi na daban a zuciyarta,saidai ta share ta kuma danne,taso ta zame hannunta amma ya hana hakan faruwa,yaci gaba da riqon hannun nata cikin nasa.
^^^^^^^^^^Ajiyar zuciya mai nauyi ta sauke sanda ta fito daga wanka,gajiyar da bata jita ba a daxun yanzu tana sauko mata,ta bata kusan awa uku,tunda ta shigo dakin take waya da 'yan sannu da zuwa gami da zolaya a fakaice,su laila harma da afra,wanda wayar tasu ta sake qara mata kwadayin komawa makaranta,saboda ta bata labarin yadda aketa zuba karatu,don ba zasu jima ba zasu zana jarabawar qualifying su wuce zuwa ss three kai tsaye.
Tsaye tayi gaba mudubi sanye da towel hoodie robe fara tas,idanuwanta nakan kayanta data gama shiryawa tsaf na komawa makaranta tun kafin suyi wannan tafiyar,tafiyar data zame mata mabudi kuma mafari na kalolin rayuwa iri daban daban.
A hankali yake saukowa daga samansa hannunsa riqe da wayarsa yana dannawa,shima yayi wanka ya canza kayansa zuwa wata lallausar over size shirt da three quater wanda ya tsaya masa iya qaurinsa.
Karo na uku idanuwansa suka sauka a sashenta,ya sake canza akalar tafiyarsa zuwa qofar sassan,yayi knocking na wani lokaci,sannan yasa hannu ya murda handle din amma sai ya jishi a riqe gam,hannunsa ya daga yana kallon tafin hannunsa da ya danyi qura,mamaki ya kamashi,jikinsa kuma ya bashi lallai wajen ba kullewar dazu ko jiya bane,amma ina ta fita ba tare da izninsa ba?,ina taje?,bayan ya bar mata digits din da zata nemeshi?,bashi da wannan amsar,don haka ya juya yana barin wajen zuciyarsa na sosuwa,ransa kuma fal da bacin rai.
Samun kansa yayi da nufar sashenta,ya buda qofar ya tura,wannan sassanyan qamshin nata da ya kama sashen har yanzu yana nan daram,sai ya lumshe idanu yana nufar qofar dakin da yake jin tana ciki,tunda dashi tafi amfani.
Har ta gama igiyar robe din ta soma kwancewa taji an turo qofar dakin,sai ta tsaya cak cike da mamaki tana dubansa,don batayi tsammanin ganinsa a dai dai lokacin ba,tana ganin lokacine da zata sake tunda zaya zauna a sassansa.
Yana kuma kallonta yana sake takowa zuwa ciki,wani abu kuma yana narkar masa da zuciyarsa,wankan da tayi ya sake sawa fuskarta tayi fresh sosai,akwai sauran lema a gashin girarta da kuma gaban kanta,zuciyarta ta shiga bugawa sanda taga yana nufota direct,amma kuma sai ta gaza daga qafafuwanta har ya cimmata.
Dab da ita ya tsaya wanda taku daya zaiyi ya hade duk wata tazara dake tsakaninsu,a nutse ya daga hannunsa ya dora saman igiyar rigar,jaa daya yayi mata ta ware,rigar wankan ta fara ware kanta da kanta, tunda dama igiyar ke riqe da ita.
Cikin gigita ta sanya hannunta ta damqe gaban rigar,qaramin murmushi ne ya subuce masa yana duban idanuwanta da suka hautsine da tsoro,har yanzun da sauran aiki kenan ya raya a ransa,yana ci gaba da kallon nata ya zura hannunsa ta tsagar gaban rigar,bata ankara ba ta tsinci sassanyan tafin hannunsa saman cikinta saitin cibiyarta.
Cak numfashinta ya dauke na wucin gadi, kafin ta samu nasarar fusgoshi kuma hannunsa ya fara yin sama,har ya samu nasarar isa muhallin da taketa bawa kariyar,sai ji tayi ta ratsa hannuwan nasa a tsakaninsu da wani salo da ya sanyata dauke wuta.
Qugunta ya riqo da kyau sanda qafafunta suka soma rawa,ya matso da ita jikinsa sosai yana sanya hannunsa ya zare hannuwanta dake riqe da gaban rigar,sannan a hankali ya hada tafin hannunsa da ainihin fatarta mai santsi da laushi ya fara zame rigar gaba daya daga jikinta.
Qanqameshi tayi da kyau don hana faruwar hakan,ta tabbatar idan ya samu nasarar rabata da rigar komai zai iya faruwa,don babu wani abu daya rage a jikinta sai ita,cikin rarrabewar numfashi da yadda laushin fatarta ke shirin zautar dashi ya dora bakinsa saman kunnenta
"Don't scare,baccin gajiya kawai nazo muyi" sake qanqameshi tayi tsigar jikinta na tashi,bakinta na rawa tace
"Ammm.....bar.....bari na saka riga" dago fuskarta yayi da kyau yana duban tsakiyar idanuwanta da idanunsa da suka soma kaduwa,kamar bazaiyi magana ba sai kuma yace
"Waye ya gaya miki saka riga ya halatta a irin wannan lokacin?,this is unfair....kamar ha'inci ne fa?,ya zaki lullubemin abun rufar da babu kamarsa a duniya da wata suturar da bata kama qafarsa daraja ba?" Ya fada cikin wani irin shauqi da baisan gana bayyana ba,ya kuma juye mata dukka nauyin maganganun hade da nauyin qwayar idanuwansa,gaba daya jikinta sai ya saki,ta runtse idanuwanta,tana sauraren yadda yake rabata da rigar gaba daya,sannan ya dauketa kai tsaye zuwa kan gadon bayan ya sauke dukka labulen dakin ya kuma rage hasken qwayayen dake ciki,sai dakin ya bada wani ni'imtaccen yanayi.
Sosai ya manne fatar jikinsu waje daya,ya boyeta cikin faffadan qirjinsa,kusan tare suka saki ajiyar zuciya,ya sanya hannunsa saman kanta a hankali yana shafar sumarta,idanunsa a rufe yana jin bugun zuciyarta,kana daga bisani kuma yaji ya sauya,alamun dake nuna bacci ya dauketa,hannunsa ya dauke daga saman kan nata,ya jata jikinsa sosai yana jin kamar ya bude qirjinsa ya sakata a ciki,babu jimawa shima wani daddadan bacci yayi awon gaba dashi.
*Arewabooks:Huguma*
#gurbin ido
❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥