Kenza eBookz

Gurbin ido huguma complete - Chapter 15

Gurbin ido huguma complete - Chapter 15

Gurbin ido huguma complete Chapter 15: Gurbin ido huguma complete Chapter 15. "Yayi kyau" yace yana ci gaba da cin abincinsa,sai dinning din yayi…

4,500 words

"Yayi kyau" yace yana ci gaba da cin abincinsa,sai dinning din yayi shuru,kasancewar dabi'ar abbi din,ba kasafai yake cin abinci kuma yana magana ba,har sai ya kammala,shurun da ya sanya ja'afar ciro wayarsa,yanajin abbin da jabir suna magana jefi jefi,wanda kusan duka kan tsare tsaren bikinsu ne.

"Bismillahi" abbi ya fada yana zama saman kujerun falon,yayin da jabir da kuma ja'afar kowanne yayi matsugunni a qasa

"Kai jabir alhmdlh,mun gama duka maganar da zamuyi dakai.....am ja'afar,abinda yasa na kiraka" abbi ya fadi yana gyara zamansa sosai,gami da cire hularsa ya aje gefe

"Inason in tambayeka......wacece ta haifeni?" Girma maganar ta yiwa ja'afar sosai,har sai daya dago suka hada ido da abbi,kana ya maida idanunsa qasa

"Anni ce abbi"

"Ma sha Allah,to ban sani ba,ko ka manta ne,dani da umar da sagir da abbas da usman.....dukkaninmu anni ce ta haifemu,kuma qarqashin ikonta muke damu da dukka abinda muka mallaka,ba zanyi magana me tsaho ba,saboda nasan kasan matsayinta a wajenmu,hatta da mahaifiyarka zabin anni ce idan baki sani ba,shi yasa ta zamto ta musamman a wajena,na kuma yi dacen da maza dubu basuyi ba,dukka hukuncin da anni ta yanke a kanka yatabbata,kuma ba komai bane ya janyo hakan ba ina da.imanin qauna ce da kuma damuwa da halin da kake ciki,Allah yayi maka wata iriyar zuciya data banbamta data kowa,amma ka sani,jajircewa da karbar al'amura a yadda sukazo suna iya kawo sauyi,hakanan lokaci yana iya warkar da kowanne irin ciwo komai girmansa,duk wani abu da zakayi a yanzu akan aurenka shizai nuna dai dai matsayin anni a wajeka,idan ka wulaqantata ko ka watsa mata qasa a idanu to ni ubanka marwan ka yiwa haka,idan ka karba abun da kima da mutunci,ka kuma riqeshi da daraja to ni ubanka marwanu ka mutunta,saboda haka zabi ya rage naka,dan halak dai shike rama halacci,anni kuwa halacci tayi maka ba butulci ba,zanga dame zaka sakawa mahaifiyata".

Maganganu ne gajeru marasa dogon zango,saidai nauyinsu yafi qarfin wani ma'auni ya iya gwadasu,shigen shigen magana irin wannan bata taba hadashi da mahaifinsa ba sai a wannan karon,nauyin maganganun da har dr ta sallamesu basu bar dukan sassan jikinsa ba,har sun kusa fita ya sake kiransa

"Ka shirya daga yau zuwa gobe,kaje gidan minister ka gana da unaisa"

"Unisa?" Ya fada cikin ransa,yana jin he knew the owner of the name UNAISA,to amma a ina?, somewhere..... somewhere,for sure,indai gidan minister ne,bu he may not remember ainihin inda yasan ta din.

Dukka wannan shi da zuciyarsa yake wannan tadin,wanda tuni ya riga yace da abbi "To" yabi kuma bayan jabir sun fice.

"Ya?,yau din zamu wuce?,don inason naje naga fatima gaskiya,i missed her badly" yana jin iya maganarsa ta yau ta qare,so saboda haka bashi da abinda zai cewa jabir din,saidai ya masa wani kallo,yana shirin yi gaba jabir din yasha gabanshi

"Shawara guda daya J.pls and pls,kayi qoqarin bin maganar abbi,indai har kai din masoyin shaheeda ne da gaske,na tabbatar da tana raye itace mutum ta farko da zata fara tursasaka kabi abinda dukka magabatanka suke so,for the first and last time may be da sukeso kayi musu wani abu cikin rayuwarka,we will see if you can do it" jabir yakai qarshen maganar yana duba yanayin ja'afar,duk da cewa ya bashi baya,kamar yadda ya zata din,baice masa komai ba sai gaba da yayi ya barshi a wajen.

Sassansu ya yanke ya koma kawai,saboda kansa gaba daya ya gama daukan zafi,tako.ina abbi ya gama daureshi,tun jabir baice komai ba dama ya riga daya yankema ransa dole ya tsaya ya fuskanci komai,zaiyi duk yadda abbi da anni keso for the sake of them.

Ya jima a haka kafin yayi qoqarin dai daita nutsuwarsa,ya daga waya ya turama hisham tex kan ya kawo masa amna,ba jimawa sai gashi da ita,ya dire masa ita ya juya.

Jaka guda ta kayan wasan daya jima yana siya ya tura mata,duk sanda ya fita yaga wani abun wasa saiya tuna da ita,sai kuma ya siya ya ajjiye,murna ta ishi amna,ta dauki wancan ta ajjiye,ta dauko wannan ta ajjiye,komai sai data nuna masa,kamar ba shi ya siyo ba.

A gaba ya sanyata yana kallo kawai,iya wannan farincikin nasa ya sauke kaso mai yawa daga cikin nashi bacin ran,abu na qarshe da yarinyar ta fada shi ya tashi zaman nasu,ya kuma dawo da mutuwar shaheeda da twin sister dinta amra danya a ransu duka su biyun,kewa da maraicin shaheedan ya kamasu

"Daddy.....mommy taqi dawowa,taqi kawomin amra muyi wasa,daddy yaushe zasu dawo?,zanyi fushi fa daddy" cikin jikinsa ya rungumeta,yana shafan gadon bayanta

"Kada kiyi fushi,kita musu addu'a kinji?,zamu hadu dasu in sha Allah sooner or later"ya fada yana qoqarin hadiye wani abu mai tauri daya tsaya masa a wuya.

Ta jima a haka kwance a jikinsa,yana jin yanayin saukar numfashinta da yadda ta qara nauyi a jikinsa ya tabbatar tayi bacci,sai ya miqe sabe da ita,daya hannun nasa kuma yana riqe da jakar kayan wasanta yayi sassan ammansa da ita.

Yana shiga tana shigowa itama falon daga ainihin qofar baya na sassan nata da zata sadaka da masaukin baqi na gidan,ita da masu aikinta su biyu,lili da laraba,suna dauke da jibga jibgan duvet da ana fiddosu yawanci a lokacin taro irin wannan musamman saboda baqin.

Jikinta sanye da Egyptian hijab daya saukar mata har qasa,duk da dare ne amma akwai eye glasses tare da ita,wanda takanyi amfani dashi lokaci lokaci idan taji bata jin dadin idanuwanta.

"Karbeta lili,ki kaimin ita dakina,idan kin shiga ki rage qarfin acn nan,don naji kaman mura nason kamata" a ladabce ta amsa,ta dauki amna da ja'afar ya shimfide mata saman kujera ta wuce ciki

"Manya" ta kirayeshi da sunan da takan kirashi dashi don ba kasafai zakaji ta kirayi sunan nasa kai tsaye ba

"Zauna muyi magana" kamar yadda ta umarceshi haka yayi,ya koma ya zauna din yana bata hankalinsa

"Kayimin wata alfarma man" sosai yake duban amman tasa,abinda yasa ta fahimci tambaya yakeson yi kan alfarmar data ambata

"Don Allah na roqeka,ka daure ka karba qaddararka a duk yadda tazo maka,kada kayi wani abu da kasan cewa ba dai dai bane,ka riqe amanar da aka baka bisa gaskiya da na sanka da ita,don Allah"

"Ku daina roqata hakanan amma,kunfi qarfin haka a wajena" ya amsa mata yana bata assurance din haka ta cikin qwayar idanunsa,ta san yana da qoqarin bin umarnin na sama dashi daman,saidai sanin halinsa yasanya mata shakku kadan,amma a yanzun hankalinta ya gama kwanciya gaba daya

"Allah yayi ma rayuwarku albarka,shikenan sai da safe"

A daren gaba daya ya gama lissafa yadda zai tafi da komai,yadda zaibi umarnin mahaifansa ta gefe guda ba tare da rayukansu sun baci ba,hakanan ba tare kuma da matan da aketa qoqarin liqa masa sun dameshi ba,don haka a washegari bayan ya shirya ya fito,ya nema ma'aikata daga cikin kamfaninsa,ya tsara musu abinda yakeso.

Cikin gidaje hudu da yake dasu ya zaba daya,wanda yake dan nesa kadan da nasu gidan,yasa aka hau aikinsa baji babu gani,don dama gidan kusan an gama komai nasa,fenti da saka qwayaye da sauran kayan qawata gidanne kadai ya rage,abinda yasa yayi saurin yin hakan,don bayason abbi ko anni wani yace su zauna a ainihin gidansa dakegovernment house road,don yafi kusa da nan gidan nasu,gidane iya gida,wanda ya amsa sunansa,kuma ya ginashi ne musamman a sannan saboda shaheeda,a sanda ta haifa masa twins,ya zuba musu komai da komai,sanda zasu tashi zuwa gidan suturar jikinsu kawai suka dauka,kuma ko bayan rasuwar shaheedan babu abinda ya bari aka taba cikin gidan,hatta da suturarta,da anyi maganan kwasan wani abun sai a rasa kansa,sai aka yanke shawarar a jinkirta ko yana kan tsinin zafin mutuwar ne,saidai har kwanan gobe komai yana nan a muhallinsa,a baya cikin gidan yake rayuwarsa,saidai yadda yake dada komawa yasa anni ta yanke shawarar ya tattaro ya dawo gida cikin jama'a,a kulle wancan gidan ko za'a samu sauqin wasu al'amuran,an dan samu din,saidai babu abinda ya canza shaheeda daga zuciyarsa har kwanan gobe ita da amransa *SO BAYAN RAI*

Gidan daya zaba din gida ne sama dake da babbar haraba da zata iya daukan motoci goma,akwai balcony da zaka shiga wanda yake dauke da babban falo,hagu da dama na bangon falon qofofi ne guda biyu,kowacce qofa akwai babban falo hade da bedroom a cikinsa, kitchen daya ne wanda yake falon,saidai babba ne,babu wanda zai takura wani,hakanan side biyu gareshi,a falon akwai stairs da aka qawata da wasu irin makarai masu kyau,marbles ne zube har zuwa saman,inda zai sadaka shima da falo babba ne dakuna guda uku ne a saman kowanne manne da toilets dinsa,sai wani balcony din daga sama wanda zai baka daman ganin ainihin harabar gidan fetal,a qasan akwai spare din daki guda daya,sai dakunan baqi maza da na me gadi daga can wajen gidan.

Gidan yana da girma,don kowanne daki da falo babbane qwarai,hakanan yadda aka tsara ginin ya bada sha:awa ainun,saidai jabir da ya gani yaga gazawar ja:afar din,a matsayin da Allah ya bashi,duba da gidan da zai dauko unaisa

"Idan gidan bai mata ba saita fasa dani ta zaba wani fine,iya abinda zan iya kenan" ya gayawa jabir,kamar shine unaisan.

Duka kudin anty maama na lefe ya tura mata abinta ba tare daya sake wani musu ba,hakanan dukka wata zirga zirga ta samarwa da baqinsu masauki tare dashi aka yita,saidai sau tari har suje su dawo ba zakaji yace kanzil ba,lokutta mafi yawa wayarsa na a hannunsa ne,cikin abokansu guda biyun da suketa zirga zirgan tare babu wanda ya kawo komai ransa,saboda sunsan wayeshi,captain j din haka nan dabi'arsa take sun sani tun ba yau ba,magana ko surutu shine assignment mai wahalar cinyewa da zaka hadashi dashi.

Sai daya qara kwana biyu sannan ya samu ya sukunin saka time na zuwanshi gidansu unaisa kamar yadda abbi yayi masa umarni,ganin yadda yake shiga cikin sabgogin yasa abbi bai tanka masa,don yana ganin sauyi muraran da kuma qoqarin bin umarni daga wajen ja'afar din.

A ranar yayi zamanshi a sassansu kamar bashi da plan na zuwa ko ina,tab ce saman cinyarsa yana duba wasu abubuwa,sanaye yake da bawin boxer wanda ya fidda ainihin qirar tsayayyun qafafunsa dake cike da tarin gargasa,jabir ya turo qofar dakin ya shigo,a shirye tsaf cikin shadda,sai yaja turus ya tsaya

"Me zan gani?,J baka duba agogo ne?"

"What happened?" Ya tambayeshi a nutse abinsa,kamar ma baisan meke faruwa ba

"You are very stubborn manya,me yasa kakeso ayita maimaita magana daya?,just simple instruction amma ka kasa bi" idanu ya watsa masa bayan ya kashe tab din

"Yaushe na gaya maka fasa zuwa na?"

"Ai banga alama ba"

"Kamar?" Ya tambayeshi yana shafa dan qaramin gemun dake manne a habarshi,ya kuma hade da zagayayyen gashin dake kumatunsa zuws qasan hancinsa

"Gashi nan kuwa ina gani,you are sitting properly,dafa'an kamar babu inda zaka?" Yatsansa ya sanya yana bin tsahon karan hancinsa daga sama zuwa qasa,ya lumshe idanunsa kana ya budesu yana furzar da iska,sai daya sauke qafafunsa qasa daga samam glass table din da take kai sannan yace

"Okay,so kake kazo ka sameni ina ihu guri guri ina announcing ma mutane zanje naga hurul'een ko?" Idanunsa ya lumshe yana sake girgiza kai alamun a'ah

"You should remember.....ita din ba kowa bace a wajena face GURBIN IDANUN da ba zasu taba zamowa idanu ba,koda zasu shekara miliyan anan din" daga haka ya miqe a nutse yana ajjiye kayan hannunsa ya nufi toilet

"Oho dai,no matter how dolenka kaje,na baka minti ashirin ka taddani falo,idan kuma ka wuce hakan....,basai na qarasa ba"

Kusan sai da jabir yayi dana sanin fadin wannan maganar,saboda sai da ja'afar ya ninka ashirin sau uku,don sai daya dauki awa daya cif sannan ya fito,saidai ya dauki kyau iya kyau yadda ya kamata,sanye yake da wani lallausan farin yadi na maza dake da shara shara,takalmin qafarsa baqi ne dan qasar Italy,hular dake kansa tun daga nesa take qyalli kamar farin tangaran,sosai kwalliyar tabi jikinsa,ta kuma dace da yammacin,hatta jabiru sai daya yaba da adon,amma sai ya fake da qorafin dadewa da yayi,bai kulashi ba,saima seat mai zaman banza da yayi zamansa,ya fidda wayarsa yana aikawa wani client dinsu saqonni,ya kuma turawa saubam secretary dinsa saqon ya sameshi a wani eatery goben yanason su tattauna.

Cikin wata farar Rolls-Royce ghost v12 mallakin ja'afar din suka fita,suna cillawa saman kwalta jabir ya qarawa motar gudu sosai,bayan ya cikasu da ac kamar yadda suka saba amfani da ita,basa ko ji ga jikinsu. [11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 27

*********Sosai maimunatu takejin dadin zama gidan bappa sule,saboda tana samun kulawa qwarai da gaske,ga kuma 'yammatan 'ya'yansa da suke kusan sa'anni da ita,hanne da hauwa,sun fita wayo da kuma gogewa,don inda suke din ba za'a kirashi da karkara ba,maraya ce,jininsu ya hadu sosai saboda kirkinsu da yadda suke nuna mata qauna da janta a jiki,nan da nan shaquwa ta shiga tsakaninsu,abun na yiwa maimunatu dadi,ashe dangi dadi garesu,koda ace batasan dangin mahaifinta ba,amma a qalla samun wadan nan a kusa na dauke mata kewa da fargabar rasa dangin mahaifi da kaso hamsin cikin dari.

A lokacin maimunatu ta sake tabbatarwa kanta lallai inna furera shigo shigo babu zurfi tayi musu,a duk sanda tazo gembu ashe nuna musu take komai lafiya lau,sannan maimunatu najin dadin can shi yasa taqi biyota nan ganin dangi,abunda yayi matuqar baiwa maimunatu mamaki,kasancewarta miskila ba kasafai takan buda baki tacewa inna furera zata bita b,saidai ita kanta takan karanci tsantsar yadda maimunatun ke son biyotan,don tasha gwaba mata baqar magana kan cewa duk ta gama nacin da qwallafa ran,wataqila ita da gembu sai idan taje yawon arba'in idan ta haihu gidan buderi,wani lokacin saidai ta sakaye taci kukanta,wani lokacin kuma har hanya take bin inna furera cike da fata da kuma burin zataji tausayinta ta tafi da ita,saidai ko sau daya bata taba sauyawa ba,daga bisani data qara wayo sai ta tattara ta qyale,ta sanyawa ranta dangana da haquri.

A sannan maimunatu taga kara ta dangin mahaifiyarta da zumunci,kowa da abinda zai kawo bisa al'adar auren fulani,basu duba cewa DR yace abar komai zai mata ba,cikin qaramin lokaci aka tara mata kayan amfanin kitchen irin nasu kala kala,wanda ba lallai a sameshi a can ba.

**********Biki ya rage saura sati guda kacal,tun a lokacin hidima ta balle daga kowanne bangare,gidan dr da kuma gidan minister harda gidansu amarya ga jabir wato fatima,saidai hidimar da ake gidan minister zata baka mamaki,kai kace bikin yara shida za'ayi ba yarinya daya ba,tun a kwanaki bakwai din da sukayi saura gidan ya fara karbar baki.

*********Katafaren beauty parlor ne,wanda aka tanadeshi musamman saboda gyaran jiki,turara jiki,fidda duk wata dauda,tada komada da maida tsohuwa yarinya a zamanance,waje ne na wane da wane,waje ne na idan ka isa ka shiga.

Daga cikin wajen fira ce ke tashi,da alama mata an hadu,kuma an samu abunda ake buqata,qawayen amarya samha ne,kowacce da abinda ake mata a wajen,wasu gyaran manicure and pedicure,wasu gyaran gashi,wasu kuma lalle ake zana musu,yayin da wasu kuma ake musu gyaran fuskarsu don su sake kyan gani a wajen bikin.

Gefe guda amarya unaisa ce cikin wata irin riga data lullube jikinta da ita,sai kanta kawai ake gani,hayaqi dake cike da qamshi ne yake futowa daga wuyanta,magana suke qasa qasa ita da wata matashiya kamarta dake gefanta,wanda hayaniyar da sauran keyi yasa ba zaka iya jin me suke fada din sosai ba saika matsa kusa dasu

"Na samu information.....jibi zai dawo nigeria"

"Na rasa wanne irin so kike masa samiha,ta ya zaki auri mutumin dako zance bai taba zuwa wajenki ba bare ayi maganar so?" Murmushi ta saki tana girgiza kai

"Ba zaki gane ba husna,ja'afar na daban ne,irinsa ba'a jiran sai sunzo zance kafin su cancanta a auresu,na musamman ne shi,sabodashi naqi aure har sai da na samu cikar burina ta hanyar daddy,na nace duk da yayi aure,har Allah ya qaddara rabona ne,matarsa da yake matuqar so ta rasu,saboda shi naqi auren unais naqi auren ahmad naqi auren hanif ke da duk wanda kika sani" kai husna ta jinjina

"Amma wanne qwarin gwiwa kk dashi na cewa zai soki?,da har zaki auri mijin matacciya wanda yake cikin halin SO BAYAN RAI?" Murmushi ta sake saki

"Karkiji komai,duk abinda kk so baka gajiya dashi,soyayyar da nake masa ita zata ja mana ragama,i will do all my best naga ya soni,kada ki manta,ni ba qaramar mace bace,na hada komai da kowanne namiji zaiyi sha'awa ya kuma burgeshi"

"But kin manta kina da kishiya kenan" murmushin dake nuna hankalinta a kwance yake ta saki

"Kusan hakan gaskiya,yarinya ce qarama wadda ta fito daga ruga,kinga yaushe zata tsoratani?,beside ma kuma itama hadi ne,rigima ce irin ta kakanni kawai,abun ma dariya yake ban idan na tuna,namiji irin ja'afar da wannan a matsayin mata idan banda rigimar tsofaffi?very classy guy,har na fara imagining yadda zai fatattaketa wlh a kurkusa duk sanda suka fara haduwa da ita" ta qarashe fada tana sakin dariya,don ta tabbata abinda zai biyo baya kenan,wannan shine yaqini bisa hasashenta.

Ita kanta husna data hasaso ja'afar din,ta kuma san wayeshi da yadda yake,sai taji hasashen unaisan haka yake,'yar ruga?,ba shakka kam bazai iya zama da ita ba,kamar yadda tayi amanna ba zata iya goga kishi da kyakkyawa kuma me aji irin qawarta unaisa diyar minister ba.

_ba'asan maci tuwo ba sai miya ta qare,muje zuwa_

**********Ƙarfe hudu na rana agogon turkey,biyu na rana agogon nigeria jirgin Turkish airline ya sauka a filin sauka da tashin jirage na malam aminu kano,dauke da tarin passengers,ciki harda jabir usma khalid akko da ja'afar marwan khalid akko.

Dukkansu sanye suke da wasu lafiyayyun Italian suit,kalolin da suka dace da gayu aji da kuma kyansu,duk wanda ya kallesu sai ya maida kansa ya dada kallonsu,zaratan fulanin samari guda biyu,wadanda ilimi hutu da kuma kudi ya ratsa kowannensu,jikoki kuma jinin khalidu akko.

Zaman jiran jirgin da zai tashi zuwa gombe sukayi,wanda duka duka bai wuce awa guda ba suka daga zuwa gomben.

Ta gefan idanu jabir yaketa karantar ja'afar tunda suka sauka a qasar,fuskarsa kadaran kadaham take,babu walwala hakanan ba wata fara'a bace saman fuskar tasa ba,hannunaa guda daya yana soke a aljihunsa,har zuwa sanda suke nufar motar da tazo daga gidan Dr marwan domin kaisu gida.

Muslimu driver din abbi shine yazo daukansu,cikin wata baqar range Rover,ko ba'a gaya maka kasan cewa sabuwa ce,sai qyalli take da daukan idanu,jabir yayi tsammanin samun masu tarbarsu bayan muslimun da zai tuqa su,saidai babu kowa saishi din,sai ya alaqanta hakan da shakkar ja'afar da sukeyi,don ba kasafai ko a baya zasuyi tafiya tare a samu masu tarbarsu ba.

Cikin matuqar girmamawa da jin dadin dawowarsu muslimu ya gaidasu,sannan ya sanya jakankunansu a mota,ya shiga ya tada motar suka dauki hanya.

Tunda suka hau hanyar idanunsa na bisa titunansu,yana qiyasta watanni da ya share bashi qasarsa,watanni ne masu dan dama,dashi kansa baisan gudun da suke ba sai yanzu.

Tazarar dake tsakanin gidan dr marwan akko da airport din ba mai yawa bace,dalilin da yasa basu dauki wani lokaci mai tsaho ba suka isa gidan.

Bin ginin gidan nasu yake da kallo kamar wanda a yau yafara arba dashi,ba komai yake kallo ba sai sabon fenti da yaga anbi gidan dashi duk da girma da fadinsa,cikin qanqanin lokaci yaji zuciyarsa na masa qunci,da gaske shirin bikin suke kenan,sai ya dauke kansa daga inda yake kallo din,ya sanya hannu ya bude murfin motar ya fito ya biyo bayan jabir.

Tun a harabar gidan tarin ma'aikata dake aiki a qarqashin gidan suka fara musu maraba,kusan da jabir ya barsu,dama shike da wannan juriyar,ya sanya kansa zuwa cikin gidan,a yau din da yake a cikin gidan,sai yaji wani irin kewa da zumudi mai yawan gaske nason ganin mahaifiyarsa ita da gudan jininsa amna,baisan yayi kewarsu kamar hauka ba sai yanzu da yake a kusa dasu.

Da tattausar muryarsa mai zurfin nan yayi sallama cikin falon nasa,haj aishatu dake nutse saman kujerun alfarma da aka yiwa falon nata qawanya dasu ta daga kanta daga duban farar takardar dake dauke da rubutu a hannunta tana amsa sallamar tasa,idanunsu suka gauraya da juna,ta saki boyayyar ajiyar zuciya mai nauyi

"Alhmadlh ya rabb" ta fada can qasan zuciyarta,sai ta dubi matar da suke tare

"Ki shiga ciki kice ina samra?,ta baki waje kici abinci,zan kiraki mintuna kadan" miqewa tayi tana godiya,sannan tabi hanyar da zata sadata da farfajiyar sassan haj aishatun da take kamae qaramin tsakar gida mai siffar garden da aka wadata da wasu fararen duwatsu na wuta.

Ci gaba yayi da takowa cikin falon,yayin da amma wannan karon tayi qoqarin ajjiye kunyar dake tsakaninsu

"Maraba lale,ashe kuna gab da isowa?" Wani dan qaramin miskilin murmushi ya subuce masa,ya qaraso gabanta ya zube ya soma gaisheta,tana amsa masa itama cikin kulawa tare da karantar yanayinsa.

Baiyi wata qiba ba sam,saidai jikinsa a murje yake kadan,sai kuma fatarsa data sakw fresh da kuma haske,alamin weather din qasar data karbeshi,akwai maganganu masu tarin yawa dake ran amma,saidai a yanzun kamar yayi wuri tace komai,don haka ta barwa lokaci na gaba idan suka gama warwarewa daga gajiyar tafiya.

Yadda ja'afar ya zube mata haka jabir,don marabarsa da ja'afar din daukan cikinsa ne na tsahon wata tara ne kawai batayi ba.

Kusan shi ya fara fita yabar jabiru da amma,wanda dama koda a baya abun kusan haka yake,hirarsu da amman bata qarewa,zaka sauka jabir ya haifa ba ja'afar ba.

Yana fitowa sukayi kacibus da ammi,kana kallonta kasan an fara shiga hidima,daga boys quarters na gidan take,taje ta duba yadda aka gyara gami da tsara wajen saboda saukar baqi 'yan biki.

"Oyoyo,saukar yaushe?,ina ta ciki ban jiku ba?" Murmushin gefan baki yayi,ya gaidata itama a girmame kamar yadda suka saba

"Me zakuci?,don gidan gaba daya a hargitse yake,banjin zaku samu kalar abincin da kuke so"

"Ki turo mana hisham kawai ammi" muryar jabir dake tahowa daga baya ta bata amsa,don yasan halim ja'afar din sarai,tsaf zai iya cewa

"We are okay" bayan shi magana ta gaskiya yunwa yakeji

"Banajin zaku samu hisham cikin gidan nan jabir,gidan yau kusan babu kowa sai baqi,yana can hidimar saukar nasu baqin"

"Ba damuwa zan kirashi" jabir ya fada suka soma gaisawa sannan shima yabi bayan ja'afar wanda ya wuce sassan anni,ammi tayi gaba tana tunanin abinda zata sa a samar musu me dan sauqi da zasu iya ci.

Sanda ya sanya kai falon har yayi kamar zai koma saboda muryoyin baqi da yaji sai kuma yaci gaba da cusa kai,sai daya shiga din sannan ya fuskanci su waye a falon,anty maama ce,sai ummi badi'a matar uncle abbas.

Qaramin tsaki yaja qasan ransa,su kadai amma sun cika falon da hayaniya kamar mutum dubu,dukkansu maraba suke masa banda anni da taja bakinta ta tsuke,ya qaraso ya zauna saman hannun kujera yana amsa marabarsu,kafin dukansu su biyun su miqe anty maama tana cewa

"Anni bari muje,nan da awa biyu idan bamu dawo ba don Allah hayatu ko muslimu suje su debomin yaran nan"

"Zan gaya musu,amma kada kuje ku zauna kuma"

"Muna samo abinda mukeso zamu dawo"

"Allah ya tsare" suka amsa suna ficewa,sai falon ya rage saura shi da annin.

"Barka da warhaka" ya fada cikin rusunawa "Barkan ka" ta bashi amsa a taqaice tana bata fuska,saidai a yau din baiji bata fuskarta ya dameshi ba kamar yadda suke da ita a baya,yana jin a wannan bigiren shi yafi cancanta ya bata fuska akan kowa

"Ina wuni?" "Daban wuni ba zaka ganni?,ai da zamanka kayi a sassanka,ni yafi cancanta nazo na gaisheka ai,tunda yanzu ka zama uban kowa,sai abinda kakeso ka tsara zamu dinga bi,tunda kaika haifi kanka" kyawawan idanunsa ya lumshe kana ya budesu,ita tsohuwar batasan abinda yakeji bane?,batasan irin qunci da ciwon data haddasa masa ba haka siddan yana zaman zamansa yana lallaba rayuwarsa?

Muryoyin sallamarsu ta katse anni daga ruwan tijarar data debo ta shirya sauke masa su tas yau a kansa,duka 'yammatan gidan ne suka shigo,wansa dawowarsu kenan daga gyaran gashi.

Da hayaniya suka shigo saboda yadda sabgogin bikin suka fara musu dadi,amma suna hada idanu kowacce sai tayi turus,ta kuma saita bakinta,kudin goro ya yiwa gaisuwarsu ya amsa su gaba daya,babu wadda tayi gigin zama dukka suka juya suna barin sashen,daidai lokacin da amna wadda aka yiwa kanta gyara na musamman take rugowa cikin falon riqe da leda a hannunta cike da kayan qwalam tana qwalawa anni kira gami da cewa tazo suci.

Cak ta tsaya sanda tayi idanu hudu da mahaifin nata,sai kuma ta watsar da ledar hannun nata,ta take da gudu tayo wajensa tana kiran

"Dadddyyyyy...." Qasa ya sauko ya tanqwashe qafafunsa,ya kuma bude mata hannayensa gaba daya,yana jin wata irin qauna da qarfin jini dake tsakanin uba da diyarsa yana fusgarsa,ta kuwa iso ta fada jikinsa,ya sanya hannayensa gaba daya ya rungumeta cikin jikinsa yana sauke ajiyar zuciyaSosai ta qanqameshi itama kamar zata koma jikinsa

"Daddy" ta sake kira tana sauke ajiyar zuciya bayan shuru da tayi na wasu sakanni,dukka gaba dayansu shida annin sai tausayinta ya lullubesu,ya dagata sosai ya sake tallafarta yana dubanta

"Amnee" ya kirata da sunan da shaheeda kadai take kiranta da shi

"Daddy....kaima shine ka tafi ka barni?,mommy ta tafi,amra ta tafi,kaima haka?" Kai ya girgiza yana shafa sumarta da tasha gyara tana ta qyalli

"Am sorry my little angel......daddy yana neman afuwa,bazai sake tafiya ya barki ba" fuskarta ta washe sosai,da alama taji dadin maganarsa,sai kuma ta sake cune fuska

"Adda maimoon ma ta tafi,har yanzu bata dawo ba,daddy zaka je ka dauko min ita?" Anni ya kalla da alama yana da buqatar qarin bayanin sanin wacece ita,kamar kuma ya jijji sunan a bakin annin da ammansa,ganin anni bata bashi wani hint da zai gane wacece ba sai ya gyada kai kawai

"Zan dauko miki ita lil princess" qanqameshi tayi tana murna

"I love you daddy"

"Love you more amne na" sai ta shige jikinsa tana sauke ajiyar zuciya dake nuni da samun cikakkiyar nutsuwa.

Karamin tsaki anni ta sake

"Kalli.....wannan daukar hakkin har ina?,Allah ya kyauta wannan banzar zuciyar taka data kasa daukan kalar tata qaddarar" bai tankawa annin ba,don yasan jiqaqqiya ce tsakaninsa da annin,kuma ba zata qyaleshi ba tabbas sai ta maida masa kai tsaye ko kuma a fakaice.

Koda ya tashi tafiya qin yarda amna tayi ta sauka daga jikinsa,tana maqale dashi,da ita yatafi sassansa,ya samu.jabir har ya fito a wanka,yanata fama da wayoyin al'umma. [11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 30

Ko sau daya bacci ko gyangyadi basuyi nasarar fusgarta ba,hakanan ko qwaqwaran motsi batayi tsahon a wannin da suka dauka suna tafiya,hakazalika motar haka ta kasance shuru,ba zata ce ga ainihin abinda yake faruwa cikin motar ba,sai daga bisani ne tadan janye mayafin dake kanta kadan saboda ta samu damar kallon gefan hanyoyin da suke wucewa da mugun gudu.

Taraba suka wuce kai tsaye saboda su raba tsahon tafiyar,uwa uba kuma yammaci tayi lis,babu security ace sunyi tafiyar dare,don haka suka yanke sauka a wani hotel dake kan babbar hanyar da zata sadasu da gombe,kafin su iso ma tuni jabir yayi booking dakuna,don haka suna isa kowa key na dakinsu aka bashi.

Itakam tana zaune cikin motar,har zuwa sanda anty maama ta qaraso ta fiddota,ran anty maaman cike da haushin ja'afar din,ta yaya sunsha wannan doguwar tafiyar xai fita yabar diyar mutane cikin mota?.

Yana tsaye a tsakiyar dakin yana amsa waya sanda anty maama tayi knocking,ya qarasa bakin qofar ya murza handle din ya bude mata ba tare da ya tsaya tambayar waye ba,kana yaja da baya yana ci gaba da amsa wayar.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull