Gurbin ido huguma complete - Chapter 22
Gurbin ido huguma complete Chapter 22: Gurbin ido huguma complete Chapter 22. "Idan kuma naqi haqura fa?" Ya tambayeta yana dage girarsa guda daya,bai kai…
4,469 words
"Idan kuma naqi haqura fa?" Ya tambayeta yana dage girarsa guda daya,bai kai qarshe ba ta sake cewa
"Don Allah" da wata irin murya irin ta yaran dake kukan da babu dalili,sai da ya riqe numfashinsa na wasu sakanni sanda tayi maganar
"Ya Allahu,wacce irin shagwababbiyar yarinya ce wannan?" Ya fada a ransa,gaba daya daga tambaya guda daya shine zata sanyashi a gaba tana masa irin wannan kukan?,me yayi mata?,salon anni ta dawo ta saka shi a uku?,a haka ma ba tsira yayi a wajenta ba,yana ankare da irin kallon tuhuma da bin qwaqwaqwafin da take masa,ya tabbatar idan ta gane wani abu tofa ba dashi zatayi ba,da abbi ko amma zatayi,tasan kuma hakanne zai matuqar daga masa hankali ya kuma bata masa rai.
"Enough.....me akayi miki?,salon a shigo ace na miki wani abu?,stop it" ya fada yana miqewa tsaye,ya matso gaba kadan yana zube hannayensa a aljihunsa,idanunsa kuma a kanta
"Ya isa nace" ya kuma maimaitawa,ganin yadda shagwababbiyar muryarta ke fidda sheshsheqar kuka.
Handkerchief ya zaro ya ajjiye mata agefanta bayan ya duba dakin da idanunsa baiga tissue ba
"Wipe your tears" ya fada mata muryarsa can qasa,ya kuma kauda kansa gefe yana hadiye wani abu,wato ita kuma haka take kenan,babu damar fada ko tsawatarwa kai ko tambaya ma sai ta narke ma mutum?,tako ina anni ta janyo masa jagwal,ta hadashi da waccan data gama zagaye duniya yawon neman karatu,yanzu kuma ga qaramar yarinyar da inda auren qauye yayi tabbas ya haifa kamarta.
Wayarsa ta sake kuka,yaja dan qaramin tsakin da ya sake sanya gaban maimunatu faduwa,ya ciro wayar yana duba me kiran,sai ya koma da baya ya kuma nufi window yana amsa kiran.
Shuru dakin ya dauka,sai sautin muryarsa mai cike da kwarjini dake ratso dakin a hankali,wata irin murya Allah ya bashi me dadin sauraro,ba zaka ce muryar d'a namiji bace,sake goge ragowar lemar hawayennata tayi,tana jin yadda fuskarta ta cika da tattausan qamshin turarensa
"Mugu kawai,kamar mutumin kirki" ta fadi a zuciyarta,hoton sanda yake zuqar sigari ya gifta a idanunta haushinsa na cika mata zuciya
"Ya boye yanata halin banzansa 'yan gidansu basu sani ba,Allah sarki abbi anni da amma" ta fada a ranta tana jin tausayinsu sosai a ranta,ita a nata ganin qarshen qurewar shaye shaye kenan,abinda yasa ta tsani buderi kenan tun farko,ashe zata tadda wannan.
Sallamar anni ta sanyata daga kai da sauri tana jin dadin shigowarta a ranta,don dama neman wanda zaya shigo ya qwacetan takeyi,suna hada ido annin ta sauya fuska tana qure maimunatu da kallo
"Me ya sameki kuma?" Ta jefawa maimunatu tambayar da bata shirya jinta ba,sai tayi shuru ta kasa ce mata komai,saboda batason tayi magana muryarta tayi rawa ta zargi wani abun
"Me kayi mata?" Ta maida akalar tambayar ga ja'afar daya kammala wayarsa yake kuma juyowa,dan tsuke fuska kadan yayi
"Ask her,gata nan ai,ki tambayeta"
"Ke me yayi miki?,da ganin idanuwanki kuka kikayi" kai ta girgiza
"Babu komai anni"
"Ko zaluntarki dama yake cikin gidan?" Kanta ta sake girgizawa alamun a'ah
"Zaginki yayi?" Ta fadi duk da tasan ba dabi'arsa bace,amma ba'a shaidar dan yau,nan ma girgiza kai maimunatu tayi
"Kodai ciki gareki ya nuna bayaso?" Dashi da itan gaba daya Duban anni sukayi,saboda maganar tazo musu a bazata,dauke kansa yayi yana ci gaba da matsa wayarsa,wani sashe na zuciyarsa nason jin zafin maganar,don shi bai taba musu yarinya bama bare tayi ciki,amma kuma sai wani bangare na zuciyarsa ke hango masa qani ko qanwa ga amna,madadin amra data rasa,tunanin ya goge daga kwanyarsa sanda yake deleting saqon daya tura a wayar tashi,don baya barin saqonni.
Shuru anni yayi sannan ta maida dubanta garesa,wanda zaka tsammaci ma baya dakin kwata kwata tunda take maganganunta
"Idan ma jan kunne kayi mata kan kada ta fada ai Allah yana nan,duk abinda mutum yake Allah yana kallonsa ko?" Ji yayi maganar ta masa nauyi sosai,ko menene za'ayi bayason mutum ya hadashi da ubangijinsa,idanu ya zubewa anni yana kallonta ba tare da yace komai ba,koda baiyi maganar ba ta karanci abinda ke ransa,maganar ce kwata kwata baya son a yita,tayi shurun amma kuma taci gaba da qananun mitocinta har zuwa sanda yace ta wuce ya maidasu gida,da farko don tana jin haushinsa cewa tayi
"Kai,kayi ta kanka kaji,ai bakai ka kawoni ba ko?,kaje kaji da kamun da Allah zai maka da diyar mutane" maganar tata ma dariya ta bashi,amma a fuska ba zakaga hakan ba,yaso maida mata amsa,to amma yasan dogon magana zai jawo,qila ma indai anni ce ta barshi da ciwon kai,sai kawai ya barta a haka,tayi mitarta ta qoshi,ya ajjiyeta a gida ya wuce nasa gidan,bayan sun bar baba tabawa a asibitin zasu kwana tare.
Washegari asibitin yadan cika saboda 'yan dubiya da suka dinga xuwa,har abun ya bawa maimunatu mamaki,ganin ciwon bai wani shahara ba,don ma dai likitan yaqi sallamarta ne,yace mai gidanta yace masa a barta saita warke gaba daya,tayi mamakin jin hakan,ja'afar din?,abun kuma yadan farantawa anni,tunda ko ba komai a nata ganin caring ne,a ranar harda abbi a zuwa dubiya da amma da kanta,aka kuma taho mata da amnanta,nan kuwa da dafe taqi binsu su koma,tace duk wanda yazo daga gida last zata biyoshi su dawo tare,hakanan suka tafi suka barta,amna kuwa ta bararraje abunta a gadon asibiti kusa da maimunatun,suna ta shan hirarsu,baba tabawa na daga qasa saman carpet tana tayasu,wani abun taci dariya.
A ranar bai tashi da wuri ba kasancewar Weekend ne,duk da shi ba wani hutun weekend yake ba,ya maida kansa busy sosai fiye da kima,amma a yau din yaji yana buqatar yayi bacci ya kuma huta sosai,don a daren jiya baya dawowarsa unaisa ta bashi ciwon kai sosai,ta sanyashi a gaba tana gaya masa yadda take sonshi da kuma buqatar tasa soyayyar,ya fuskanci kamar a matse take,abinda a nasa ganin bai kamaci a samun hakan daga wajen budurwa ba,baya mantawa shaheedansa dai da ya kusa sati kafin ya samu kanta,shima a haka lallabawa aka dinga yi kafin ta saba,ta jima kafin ya samu ta tashi bayan ya bata zabi guda biyu,ko ya sallameta salin alin,ko taci gaba da haqurin zama dashi har zuwa sanda zuciyarsa zata aminta da zama da ita,surutan da yayi wunin yau duk da ba wai yawa garesu ba suka sa yaji kansa yana ciwo,wannan yasa ya kashe wayoyinsa gaba daya,ya kuma sanyawa qofarsa key don kada ma ta dawo ta dameshi.
Bai farka ba kuwa sai dab da azahar,har sannan bai buda wayoyinsa ba,har sai da yayi wanka ya shirya cikin wani yadi da aka masa ordernsa daga qasashen yarbawa,aka kuma yarfa masa dinkin boda irin nasu,fresh chocolate color skin dinsa tayi luf ta kuma dace da yadin.
Sai sannan ya buda wayoyin yana duba lokaci,zai isa ya samu sallar azahar a gaba cikin jam'i,yana shirin sake kashewa kiran hisham ya shigo masa
"Barka da rana yaaya" "Yauwa,kana lafiya?" "Lafiya lau,akwai kayan da aka maka order ne ka saka phone number dita?" Shuru ya danyi
"I don't think so,but ka kira mr farid,na bashi wani aiki last month,ban san ko shi ya saka number dinka ba"
"Okay yaaya"
"Kaman kana hanya ko?"
"Eh,ina ta wajen unguwarku,naje na duba patient din da na yiwa surgery jiya,sai na biyo wani suya spot"
"Bakaji ko?,kai ne can gobe kaine nan,ka samu standard waje daya ka tsayar dashi duk sanda kwadayinka ya tashi,kaman ba likita ba?" Dan shafa kansa hisham yayi,ja'afar din badai aqida ba,shi kam duk inda yaji taste dinsu ya masa ko yaga abinda yakeso indai ya gamsu da tsaftar wajen zaije yaci
"Am sorry" yace masa a taqaice,don yasan bazai tsaya sauraron dogon jawabinsa ba
"Sorry for your self,ka biyo ta gida ka daukeni"
"Okay" ya amsa shi yana murmushi sannan ya aje wayar,yayan masa is very different and unique,komai nashi ya bambanta dana kowa,shi yake sarawa jabir da suke zaune lumi baka jin kansu. [11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 45
Sosai ta tsorata kamar yadda ta saba,comb din hannunta ya sulale a qass,bugun zuciyarta kuma ya sauya,zuciyarta ta fara tantama shine ko muryarsa ke mata gizo?,don gusar da tantama sai ta waiwayo cike da fatan ya zaman bashi bane.
Ido hudu sukayi dashi sanda yake kurbe kununsa,wannan tsoron dake haifar da wani kyau cikin qwayar idanunta ya bayyana muraran,hakanan yadda gashin kanta ya sauko ya qawata fuskarta ya kuma yi mata ado sosai,ba tare data qara tunanin komai ba ta laluba hanyar toilet,ta manta da cewa qofar toilet din yafi kusa dashi akan inda take tsaye.
A nutse ya dire cup din a saman side drower din dake gefansa idanunsa a kanta yana jiran isowarta,goye hannayensa yayi a qirji yana kallonta har xuwa sanda ta qaraso dab dashi da niyyar wucewa a rude,babu zato kuma babu tsammani taji an ruqo dukka hannayenta gaba daya,sannan kuma ya jata zuwa cikin jikinsa,ya rungumeta ta baya,hannuwansa riqe da dukka hannayenta biyu,rungumar data sanyashi cikin nadama bayan ta samu kyakkyawan masauki cikin jikinsa,gashin kanta ya musu rumfa gaba daya shi da ita,sahihin qamshin hair mist din da yake ji daga nesa bayan ya shigo dakin a yanzun yaji ainihinsa,lallausar fatarta data gama mulketa da wani body lotion mai wani irin sulbi da qamshin rose ta gogi jikinsa,saura kadan yayi missing numfashinsa na gaba,dukka gabbansa suka saki,wani irin yanayi da bai taba zata ko kawowa zaijisa daga kowacce mace ba macen ma irin maimunatu da yakejin zai iya haifar kamarta lokaci daya ya saukar ma kowanne lungu da sawo na sassan jikinsa.
A jikinta ta dinga jin kamar jinin jikinta ke daskarewa saboda tsoro.
Tun daga tafin qafarta zuwa hannayenta dake cikin nasa sunyi wani irin sanyi saboda tsoro da mamaki,kasantuwarta a jikinsa sai takejin kamar cikin wani mafarki take,ire iren mafarkan da suka takura mata kwanakin baya,har ta dinga tsammanin tana da wata lalura data shafi jinnu,amma kuma bayan sun karanta a fiqhu cikin alamun balagar mace da suke nuna kaiwarta munzali irin wannan mafarkin sai hankalinta ya kwanta ta kuma fuskanci abinda ke faruwa da ita.
Tsigar jikinta ce tayi wani mugun zubawa,kanta kuma ya sara sanda hannunsa ya shafi wuyanta a qoqarinsa na tattare gashin nata gefe guda,bata warware ba daga wannan taji ya juyota gaba daya tana fuskartarsa cikin hanzari,tashin hankali!!....ta fada qasan ranta,ta fiddo idanunta dukka waje tana jin yadda towel dinta ya kunce daga daurin data masa,ya kuma fara warwarewa a hankali a hankali,ta kuma yi imanin nan da wasu sakanni zata iya kasancewa tsirara kenan?.
Ta bangarenshi baisan me yake faruwa ba,yadda ta zare idanun nata ya sake haifar masa d wani abu ya kuma gasgata masa tsananin tsoronsa da takeyi
"Why all this fear?Am I a monster?" Yayi maganar yana kafeta da ido,da mugun hanzari ta girgiza kanta,tun kafin ma yakai aya,cikin shagwabarta data zame mata jiki,shagwabar da a baya idan inna furera ta daketa ta fara bata haquri sai tace da ita ba tare da duba da cewa haka yanayinta yake ba tun usuli
"Shegiya karuwa,wannan,irinku ne idan kuka kama mazan jam'a a bariki ba matarsa ba,haar uwarsa saidai ta sallama muku shi"
"Kayi haquri don Allah" maganar ta fito da wata siririyar qwalla daga idanunta,saboda yadda taji towel din naci gaba da ware kansa.
Idanunsa ya lumshe kadan sannan ya sake budesu,hawaye.....hawaye,he hated it,me yasa kuka baya mata wuya?,shagwaba kamar 'yar fari ko auta?,yayi qiyasin hakan a ransa ba tare da yasan ita din bace
"Nooo,dole ki nunan abinda yake baki tsoro a jikina" kai ta shiga gyadawa
"Babu komai"
"It's a lie kuma ban yarda ba" ya fada yana tsuke fuska tare daci gaba da kallonta
"Allah....wayyo Allah daadata!" Ta fadi kukanta yana qaruwa tana kuma neman durqushewa a wajen saboda jin ya fara salube mata.
Dubansa yakai ga jikinta,sai a sannan shima ya karanci meke faruwa,wani mugun shock yaji sanda idanunsa suka kai kan saman rabin dukiyar fulaninta da suka fara fitowa,ba tare da tunani na biyu ba ya sakar mata hannuwanta da gaggawa ya kuma juya mata baya,sannan a hankali ya nufi inda ya aje cup dinsa ya dauka yana ficewa daga dakin ba tare da ya jira komai ba.
Bai samu baba tabawa a falo ba,sai ya fice kawai daga sassan ya kuma wuce parking lot,inda ya samu drivernsa yana jiransa,bai jirashi ya bude masa qofar ba ya bude ya shiga,sannan ya bashi umarnin tafiya.
Sosai yayi relaxing a bayan motar bayan ya kulle idanuwansa yana sauraren yadda bugun zuciyarsa ya sauya cike da mamakin faruwar hakan a gareshi,fuskarta da gifta duhun idanuwansa sanda take kukan,wanne irin tsoronsa take haka?,idan ta bayyana hakan gaban mutane akwai wanda zai yarda dashi kan ba wani mummunan abu yake aikata mata ba?,bude idanun nasa yayi a nutse yana duban hanya,a hankali qamshin jikinta yake yana tashi ta gaban suit dinsa da hannayensa,sai yaja dan qaramin tsaki,yana ji a ransa he's totally wrong.
Ta jima a duqe a wajen tana sharar qwalla,don batasan ma ya fita a dakin ba sai da taji shurun yayi yawa,a hankali ta daga kanta,ta tabbatar baya dakin,sannan taja jikinta daga wajen,tana riqe da towel din nata gam,kamar wadda aka ce za'a qwacewa shi,saman gadonta ta nufa ta zauna,amma sai zaman ya gagareta,wani irin mutuwan jiki takeji da kasala,gaba daya kamar an samu abu an buge mata gabbanta,gefe daya kuma zuciyarta kwata kwata babu dadi,musamman idan ta tuna a yau din wani namiji ya ganta a rabin tsirara,sai wasu sabbin qwallar su sake zirto mata,saidai ta saka hannu ta shafesu.
Ta kwashe awanni masu yawa a haka,ita ba me lafiya ba ita ba mara lafiya ba,bata tashi ta shirya ba hakanan bata fita a bedroom din nata ba,abu daya ne ya tsaye mata a rai yake ta mata yawo,duk juyin da zatayi sai abinda ya farun ya wulga mata a idanunta,hakanan duk motsawar da zatayi sai mayataccen qamshin da ya bar mata ya kada har qwaqwalwarta,tamkar a yanzun ne yake tsaye cikin dakin,tafukan hannuwanta gaba daya sun rune da qamshin wani dan mitsitsin oily pen perfume da yake amfani dashi,idanunta ta lumshe tana shaqar qamshin har cikin qwaqwalwarta,yana silalewa a hankali zuwa zuciyarta,sai ya tuna mata da handkerchief dinsa dake wajenta,d same qamshin da yake jiki kenan,best scent ever data taba ji me wani irin yanayi,duk da yadda zuciyarta keta qyamatar qamshin amma ta kasa daina shaqarsa,daga qarshe bayan ta gama shafe awanninta,haka ta janyo mataccen jikinta ta sauko daga gadon ta nufi toilet ta sake wanka,waiko zata samu ta raba fatarta da mayen qamshin dake qara mata kasala.
Koda ta fito ma tsaiwa tayi gaban mudubi tana duban yadda fuskarta tayi jaa saboda kukan da tayin,ta sauke idanunta saman qirjinta tana tuna a yadda ya ganta,sai ta dan zame towel din tana iya dai dai yadda ya kufce mata a dazun,dukka idanunta ta qwalalo waje,indai towel din yakai haka sakkowa tabbas yaga fiye da rabin jikinta,wasu qwalla masu zafi suka sauko mata,amma kuma sai tayi hanzarin gogesu sanda taji muryar baba tabawa tana knocking qofar gami da tambayarta lafiya ta jita shuru?,ta fito ta karya kada abincin ya huce
"Gani nan fitowa baba" ta amsa mata,sannan taja lotion dinta da hanzari tana sake sabon shafa.
Cikin doguwan rigan wani material mara nauyi ta shirya,ta gyara sumarta ta hadeta waje daya,sannan ta yafa dankwalin kayan,har tayi gaba ta dawo ta dauki wayarta sannan ta fito.
A zaune a falo ta samu baba tabawa,daga kanta tayi da niyyar cewa wani abu sai suka hada ido da maimunatun,tadan zuba mata idanu kadan saboda yadda fuskarta take nuna tayi kuka,kamar zata ce wani abu sai ta fasa,saboda ta tuna dazun,shima taga fitarsa daga dakin da wani mugun hanzari,hakan yasa taji bai kamata tace komai ba,don tsakanin miji da mata sai Allah,fatanta kawai ubangiji yasa ba wani abu mara dadi baje ya faru a tsakaninsu ba,kuma Allah ya kawo daidaito tsakaninsu nan kusa.
Kadan ta zuba abinda baba tabawan ta dafa ta fara tsakura,saida kadan taci ta tashi,saboda tana jin cikinta gaba daya ya cushe,kamar babu wani sauran space na zuba abinci,data dawo saman kujera ma kwanciya tayi,yau ko hirar da sukanyi da baba tabawan jifa jifa ta dinga yinta,tans ankare da ita,lokaci lokaci sai tayi kamar ta tafi tunani,sai kuma ta sauke ajiyar zuciya taci gaba da abinda takeyi.
Kafin azahar jiki da zuciyarta yayi laushi qwarai,sanda ta shiga sallar azahar mamakin kanta ta dinga yi,me yasa abinda ya farun a daxun ya tsaya mata a rai ta kuma kasa mantawa?,me yasa har yanzu take jinta kamar rungume take cikin jikinsa?,me yasa qamshinsa da kamanninsa suka kasa bace mata?,me yasa take hango idanunsan nan take jinsu da nauyi?,saita sake wata irin ajiyar zuciya me nauyi tana tabe baki kamar yaron dake shirin sakin kuka,kafin daga bisani tayi qoqarin daidaita mode dinta ta wuce bandaki don ta dauro alwala.
Iska me zafi ya furzar daga bakinsa yana cire guda daga cikin suit dinsa ta saman,ya kuma saqaleta a suit hanger dake cikin office din,sannan yayi taku biyu ya isa rukunin kujeru masu taushi dake gefe guda a cikin office dinsa,wanda aka tsara wajen tamkar ba cikin office din yake ba.
Opposite jabir dake binsa da kallo ya zauna ba tare da ya daga kai ya dubeshi ba,duk da kuwa yasan shi yake kallo sarai,ya daga qafanshi ya zame qawataccen takalmin dake qafarsa yayi wurgi gefe dashi,ya rage sai socks kawai a qafar tashi
"Wai anya kuwa kasan me dame ka fada wajen meeting din nan?,abinda ka dinga fadi baiyi making sense ba......lafiyarka qalau kuwa yau?" Ya masa tambayar sanda ja'afar din ke tuttulawa cikinsa ruwan sanyi,cike da fatan abinda yakeji ya tsirga masa.
Bai amsa masa ba sai daya qarar da ruwan dake cikin gorar tas yayi wurgi da ita itama,sannan ya sauke idanunsa cikin na jabir,abinda ya sanya jabir din karantarsa,ya kuma sauke boyayyen murmushi
"I know......" Ya amsa masa kai tsaye
"I don't think so" shima ya maida masa da amsa,janye idanunsa yayi daga kan jabir din yana lumshesu sannan ya budesu,kamar zaice wani abu sai ya fasa,ya miqe a hankali yana roller hannun rigarsa zuwa sama don ya samu daman yin alwala,ya taka sannu a hankali zuwa qofar toilet din nasa,ya turata ya shige.
Madaidaicin toilet ne amma ya tsaru matuqa,hakan ya bashi damar lashe kudade masu yawa saboda toiletries da aka zuba masa masu tsada da kyau sannan kuma sabbin design,babban mudubi ne daga wani side daban da zai baka daman ganin kanka sosai,a gabansa ya tsaya yana kallon kansa yana kuma murza sumarsa da hannunsa,ta qasan zuciyarsa yake magana da kansa da kansa,he really made a mistake,ya manta wayeshi.....me ya kaishi kusanta kansa sa wata mace?,to wai hakan ma yana nufin akwai improvement kenan daga depression din da zuciya da ruhinsa ya fada?,tunda har gashi zuciyarsa da gangar jikinsa sun fara neman wani abu daban wanda a baya ko tunaninsa babu a ransa?,hannayensa ya tara a qasan famfo ya cikasu da ruwa ya watsawa fuskarsa,ya sauke ajiyar zuciya yana gaining courage daga can zuciyarsa,yana jin zuwa anjima kadan zai manta komai,komai zai wuce,da wannan ya samu ya daura alwalarsa ya fito,ya samu jabir tsaye dab da rigarsa yana duba takardun da suka gabatarma da juna wajen taron,kai ya daga ya dubeshi
"dude........ina ka samo wannan turaren ne?,but......scent din nasa kamar na mata...,kamar my tee ta taba ban cigiyarsa na kasa samunsa" rasa amsar da zai bashi yayi,yace masa a jikin qaramar yarinya maimunatu ya sameshi?, Ko yace masa rungumeta yayi qamshin ya tabashi
"Ka shiga kayi alwalar muyi salla,lokaci yana wucewa" tuni ya sanya masa ayar tambaya,sai ya gimtse murmushinsa,ya wuce toilet din yana addu'a cikin ransa
"Ya rabb,ya rabb.....ka sanya lokacin nan ya zamo na sauyawarsa".
Duk da miskilancinsa amma shurunsa yayi yawa,haka suke tafe a hanyarsu ta komawa dakin taron,taro yaci gaba kamar yadda yayo announcing business partners din da suka halarci zaman,saidai jabir yana biye dashi,gaba daya kamar ba ja'afar ba yau,ja'afar very energetic person,amma yau din yanata abu kaman mara lafiya.
Biron hannunsa ya aje saman table din bayan yayi singing wata takarda,zai tura file din jabir ya karba yana duba singing din,sai ya zubewa ja'afar idanunsa
"Me yake damunka yau?,kaga abinda kayi jikin takardar nan kuwa?" Ya fada masa da harshen hausa qasa qasa,duk da cewa dukka mahalarta taron babu bahaushe ko daya bare ya fahimci abinda yake fada masa
"it's better to let everyone go.....ka sanya wani time and date din a qarasa abinda bamu gama ba" bai jaa da cewar jabir ba,don a jikinsa yaji yana buqatar hutu,cikin mutuntawa girmamawa da sanin ya kamata jabir ya juya yayi musu bayani gwargwadon yadda zasu fahimta ba tare da jin damuwa ba.
Ko kafij jabir din ya gama sallamarsu tuni ya yima drivernsa magana,don haka ko ta office dinsa bai koma ba ya wuce parking lot driver ya tashi motar sukayo gida,yau ko ta eatery din bai biya ba bare ya samawa kansa abinda zaici. [11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 43
Sai da suka tsaya masallaci sukayi sallar azahar sannan hisham ya sake daukansu wuce asibitin,gab da zasu qarasa ya soma slow da motan,jaafar dake duba wani abu a tab dinsa ya daga kai ya dubeshi
"Uhmmm,ya dai?"
"Naga masu fruit ne,akwai paw paw a ciki,zan siya ma maimunatu" sai ya maida kansa ga abinda yakeyi baice dashi komai ba,har ya buda motar ya fita yaje ya siyo,ya dawo ya tashi motar suka wuce.
Dakin babu kowa,don duka sun yoye sun tafi,daga ita sai amnan sai baba talatu data shiga bandaki zata dauro alwala,tana zaune a saman gadon amna ta zame mata dankwalinta ala dole wai sai ta yi mata kitso,tana ta jagwalgwala mata sassalkan gashinta ta kasa kitsawa saboda sulbi da santsinsa,jikinta akwai sauran zazzabi,an yima likitan bayani yace zai shigo ya dubata,tana biyewa amna dinne kawai don kada yarinyar taji babu dadi.
Batayi zato ba bare tsammani sassanyar muryarsa ta furta sautin sallama hadi da turo qofar dakin gaba daya,tashin farko kuma idanunsa suka sauka a kanta lokacin data rude ta kuma tsorata tana neman dankwalinta,wanda bata sani ba amna ta jefa mata shi qasan gadon,shi yasa ta kasa ganinsa,idanunsa ya dauke ya waiwaya baya inda hisham ke biye dashi
"Wait for a while"
"Okay" hisham ya amsa masa ya kuma ja baya ya tsaya ba tare da yasan dalilin ja'afar na fadin hakan ba.
Koda ya shigo din gaba daya ya maida hankalinsa ga amna wadda ta diro a gadon fa kuma rugo da gudu zuwa gareshi tana kiran sunanshi,haka kawai yaji baya son ganinta haka,ya budewa yarinyar hannayensa bayan ya durqusa yana jiran qarasowarta,zuciyarsa kuma na tuna masa da lokuta irin haka a baya,lokuta mafiya farinciki a rayuwarsa,lokutan da ita da twin sister dinta amra ke rige rigen isowa gareshi,mamansi shahida na tsaye tana kallonsu tana kuma murmushi,sai gashi a yau yarinyar ita daya ta rage masa a cikin guraben farinciki guda uku da yake dasu,tana qarsowa kuwa yayi sama da itama ya cillata kan ya rungumeta cikin jikinsa.
Kafij su gama ganin murnar ganin juna ta lalubo dankwalin da qyar ta yane kanta gaba daya zuwa saman qirjinta,duk da hankalinsa na kan amna amma yana ankare da ita,baisan me yasa take tsoronsa haka take kuma rudewa duk sanda yazo wajen ba,tun ranar daya tsorata tan randa suka baro gembu zuwa gombe,sauke amna yayi a hankali
"Kice da uncle ya shigo yana waje" da dan gudunta ta fice,sai a sannan ya sake maida dubansa kanta,ta nutsu guri guda,wanzuwarsa a wajen tana sata jin kamar wani zazzabin zai sake qaruwar mata,kwata kwata batason ganinsa a waje idan tana nan
"Ina wuni?" Ta fada da muryar nan tata dake da tsananin zaqi da sanyi,shi kansa ya yadda da hakan,idan tayi magana wani sauti take bayarwa na musamman
"Ya jikin?" Ya tambayeta ba tare da ya amsa gaisuwarta ba,yana bin ledar qarin ruwa da aka cire mata da kallo
"Da sauqi" ta bashi amsa dai dai da fitowar baaba tabawa daga bandaki.
"Barka da zuwa,yaushe ka shigo?"
"Yanzu" ya amsata yana waiwaya ga hisham dake shigowa dakin da sallama,kanta ta daga tana amsa sallamar,yadan kalleta ta gefan idanu,akwai dan qaramin murmushi saman lebanta tana dubansu shi da amna,gaisawa shima sukayi da baaba tabawa,ta tayar da sallah,sannan ya matsa inda maimunatu take
"Yanzun don kada a bamu tsarabar boarding shine aka kwanta ciwo?" Shima tana jin nauyinsa sosai,amma ko kwatar na miskilin yayansa me fuskar shanu bai kai ba,akwai dan sabo haka a tsakaninsu,don haka murya can qasa ta yadda take zaton ja'afar bazaiji ba tace
"Kaidai tunda sai yau kk zuwa dubiyan ai shikenan"
"Am sorry.....wallahi ayyuka ne suka yimin yawa kwana biyu,ga teaching hospital da nake zuwa musu sau biyu a sati suma kyauta...."
"Allah ya taimaka" ta fadi duk a darare,ita inda zai fita ya basu waje ma da sai tafijin dadin hakan,ledar gwandar ya tura mata
"Nayi dubiya me kyau,tunda.na kawo miki mutuniyarki ko?" Ya fada yana dubanta yana murmushi,maganar da ta sanya ja'afar karantar fuskarta a fakaice,wanda a zahiri zaka dauka kacokam hankalinsa na ga surutun da amna ke masa,sai yaga fuskarta ta washe sosai,karo na farko da ya taba ganin irin haka tattare da ita
"Na gode sosai,Allah ya saka da alkhairi,ya bada lada" maganar ta tsaya masa a rai,kwatankwacin addu'ar shaheeda kenan duk sanda aka yi mata alkhairi komai qanqantarsa.
Juya gwandar kawai take,tana son sha amma dashi da hisham din duk sun cika mata waje,sanda baba tabawa ta idar da sallar likitan ya shigo,maimunatu ta daga kai a hankali gabanta yana faduwa,ta tuna maganarsa ta jiya,yace indai yazo yau ya samu da sauran zazzabin a jikinta to lallai duk qinta da allura saidai tayi haquri ayi mata ita,a duniya allura itace abu na farko data tsana ta kuma qi jini,daada tafi kowa sanin hakan,don tun kafin rasuwarta akwai sanda bata da lpy,ta takura sai anyi mata takusa shide mata,abinda yasa tun daga ranar bata qara bari anyi mata ba.
"Dr hisham marwan?" Likitan ya fada yana diban hisham,da alama akwai sanayya sosai a tsakaninsu,don shima hisham din yana kallonsa ya kama sunansa,hira suka barke da ita,yana duba file din maimunatu,da treatment din da aka bata daga daren jiya zuwa yau,sai ya daga kai ya dubeta
"Har yanzu da zazzabin?" Kafin ta amsa baba tabawa ta rigata
"Akwai likita,ai har magana aka yo muku dazun"
"Ba damuwa,zai sauka yanzun in sha Allah,qila ma idan akayi wannan allurar basai an sake wata ba" fadin haka kawai sai idanunta ya fara tara hawaye,cikin mamaki a kuma sace ja'afar ke kallonta,bawai tana nufin kiran za'a mata allura ke shirin sanyata kuka ba?,ya hangi zallar tsoro baro baro a idanunta,ta kuma kasa sukuni sanda taga yana hada ruwan allurar waje daya.
Kida wayarsa ta farayi,sassanyar busa me ratsa zuciya,ya cirota ya duba me kiran,sai ya soma takawa a hankali yana ficewa a dakin yana amsa wayar.
Daya daga cikin amintattun ma'aikatansa ne,suke gaya masa motocin da ya siya sun iso,suna lagos,za'a biya kudin clearance da sauransu
"Ayi duk abinda ya dace" "Okay sir" ya amsa masa a ladabce,ya kashe wayar yana juyowa,dai dai sanda baba tabawa ta iso riqe da hannun amna
"Manya inaji fa sai kaje maimunatu zata tsaya,taqi bari ayi mata allurar nan sam" a mamakance yake duban baba tabawa,wanne irin abune haka kamar qaramar yarinya?.