Kenza eBookz

Heedayah complete Novel - Chapter 19

Heedayah complete Novel - Chapter 19

Heedayah complete Novel Chapter 19: Heedayah complete Novel Chapter 19. Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very…

2,139 words

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very affordable.... 馃槏 9/12/21, 8:04 PM - ,: Kaka tace "To dama idan ba shi din ba waye xai siyo min Apple manya haka? Ai sai dai Shureen din" Heedayah tace "Ni bai siyo min ba kaka?" Kaka ta kalleta tace "Ke kuma a wa? Ae sai dai in d'an yankar maki idan nayi niyya" Karime ce tayi sallama bakin kofar parlon Mumy ta shiga ciki, Mumy tace "kulle kofar, Sajida ta ga tahowar ki?" Karime ta kulle kofar tace "A'a wanka ta shiga" Mumy tace "Toh mu shiga daki, ba wani aiki bane linki xa kiyi min" Karime tace "Toh Hajiya" Mumy ta shigar da ita bedroom dinta, 'yan kaya ne da basu fi biyar kan makeken gadon dakin, Mumy tace "Ga su nan basu da yawa" Karime ta fara linke kayan, Mumy ta nemi waje ta xauna tana latsa wayarta, ganin Karime har ta kusa gamawa Mumy tace "Hajiyar ta fara sake maki kuwa?" Karime tace "Aa, yau ma tace min tunda Heedayah ta koma gun kaka to idan na gama aikin da xan yi a bangarenta in yi wucewata can dakinmu, ko don d'an kallon da taga Ina yi ne yasa ta fadi haka..." Mumy tace "To banda abun ki ba ga TV a nan ba Karime, duk sanda kike son kallo ki shigo nan kawai, ae xuciyar daban ne, kowa da irin tasa...." Karime tace "Kuma haka ne wllh, ke kam naki daban ne...." Mumy tayi shiru jin ringing din waya a parlonta, mikewa tayi da sauri ta fita parlon, Shuraim ta gani tsaye yana kallon screen din wayarsa dake ring, ya daga ya kai kunne tare da sallama, Mumy ta juya ta koma dakinta da sauri ya bi ta da ido still answering his phone call, alama tayi ma Karime da cewa kar ta kuskura ta fito, sannan ta juyo ta kulle kofar ta dawo parlon ta xauna, Shuraim ya gama answer wayar da yake yace "Mumy xan d'an fita in dawo" Tace "Toh Allah ya kiyaye, yanxu dai kai baxa ka dinga sa manyan kaya ba Aliyu, wllh suna maka kyau amma baka so, even if it's just once a week banda Fridays ka dinga sa wa" Bai ce komai ba ya nufi bedroom dinta, bata san lkcn da ya nufa dakin ba kawai gani tayi ya bude xai shiga, ta mike da sauri tace "Me xaka yi ciki Aliyu??" Tuni ya shiga suka yi ido hudu da Karime, sai a sannan ya juya ya kalli Mumy yace "Gaban mirror xan je" Bai jira tace komai ba ya wuce ciki, Karime dake tsaye kamar munafuka ta risina tace "Ina kwana yallabai" Ko kallonta bai yi ba ya nufi gaban mirror ya tsaya, Mumy dai na tsaye ta kasa bin bayansa, Karime ta fito dakin kamar munafuka tace "Hajiya na gama" cikin daga Mumy tace "Toh dama wani linki ne tun daxu kamar warce na sa kwalemar dakin gaba daya?" Karime ta nufi kofa da sauri ta fita, Shuraim ya fito daga dakin, Mumy ta hade rai tace "Ajiya kayi min a dakin da ka shige min bbu excuse Shuraim??" Yace "Na bar comb dina a nan ai jiya" Yana fadin hka ya nufi kofa, Tace "Shuraim Ina ga fa gwara in sallami mai aikin nan tawa kawai, bbu abinda take tsinana min sai magana ma da take yawan sanya ni, dubi fa wnn yarinyar yaushe ta xo gidan amma na gwammace in sa ta aiki a kan Sajida, cikin dadin rai xata maka komai fess fess, to ni kuma nayi ta kiranta kenan uwar dakinta tayi wani tunanin daban? Yanxu ma nasan uwar dakin nata bata sani ba ta xo, tun safe na kira Sajida ta xo ta min gyaran nan ban ganta ba shine na kira ita wannan din, matsalar ta daya wnn bata da wani wayewa...." Shuraim dai bai ce mata komai ba ya bude kofa yace "Sai na dawo" bin sa tayi da kallo har ya rufe kofar, ta xauna a hankali saman kujera tana naxari.... Mumy ce xaune dakin Hajiya Sadiya, da Hajiya Baturiya, Mumy tace "Sadiya tunda kin sa6a harka da Mutumin nan ki lallaba sa ya rage kudin wllh sun min yawa, duka duka nawa ne a acc din nawa ma tukun? Gaskiya ki yi masa magana a min ragi" Hajiya Sadiya tace "Kinsan Allah, wllh da dubu dari uku da hamsin ma yace, da kyar ya yrda dubu dari biyu da hamsin" Mumy tayi tagumi tace "A kan tsinanniyar yarinyar sai in dawo bbu ko sisi a account dina" Hajiya Baturiya tace "In dai bukata xata biya ba shkkn ba, ke kin hana mu xuwa gun malam to ba sai ki bari ayi me yiwuwa ba" Mumy tace "Toh shkkn, amma fa Ina tsoron kuma kar a xargeni ko da wasa a gidan" Hajiya Sadiya tace "Haba bbu wannan xancen, kaf xa a yashe ki kema har a buge ki, kinga bbu wanda xai xarge ki" Mumy tace "Toh shkkn sai mun yi waya, yamma yyi bari in wuce gida" Har bakin mota Hajiya Sadiya ta raka ita da Hajiya Baturiya, ko wanne ya shiga motarsa suka bar gidan. Kaka na sharan dakinta, Heedayah kuma na saman gado tayi rub da ciki tana sauraron xancen kaka, Kaka tace "Atoh, Shima Sudess din ai ba son yanda yake ganina xaune gidan duniya yake ba, kawai dai bbu ynda ya iya ne tunda ba ubansa ya halitto ni ba, to abinda Allah ba bacci yake ba, sai gashi cikin ruwan sanyi ya kawo min ke duk da dai ke makauniya ce baki da wani amfani kuma bamu hada komai da ke ba, to ai dai yafi babu... Wai d'an agwai da bak'in d'a" Heedayah tace "Waye Sudess din" Kaka tace "Oho haka na ji suna ce masa, jikana ne fa, ni haifi ubansa Umaru, amma cin haram a wajensa ba a cewa komai, yanxun nan xaki ajiye hakkin ki a nan kan ki juyo ya handame, to ina dalili...." Bude kofar dakin aka yi Sudais ya shigo da sallama, Kaka ta saki tsintsiyar hannunta ta mike tace "D'an Halak, yanxun nan nake xancen ka wllh, nace to Sudais anya lafiya kuwa kwana biyu, ni bai ta6a min haka ba" Ya mata wani kallo yace "Ke dai fadi gaskiya...." Heedayah tace "Kaka shine yake cin Haram din?" Juyawa kaka tayi tana kallon Heedayah baki bude, Can ta nufeta ta dunguri kanta tace "A gidan uban wa muka yi haka da ke? Meye kuma Haram, a ina kika ta6a jin wnn mugun kalmar" Sudais yace "Toh an ci Haram din, tunda ina tsoron Allah ai shkkn" Kaka ta juyo tana kallonsa tace "To waye baya tsoron Allah" ya bude hannu yace "Oho, sannan ni bana cin naman mutane, bana gulman mutane" Kaka ta xauna gefen gado ta fara matsar kwalla tana share idonta, ya daga Heedayah ta sauka kasa ya nufi kofa, kaka tace "Dama kar ka sake maido min ita dakina xan koreta wllh, ga kayanta nan duk a fitar min ba ruwana, maganin ciwon idon ma gashi nan na nannadesa da Sabuwar atamfata na saka kasan akwati, kowa ma ya xo ya duba ya kwashe ba ruwana" Sudais ya fita da Heedayah yana dariya kasa kasa, sai bayan da suka fita Heedayah tace "Is she crying??" Sudais ya fara dariya yace "Yess" Heedayah ta kwace hannunta kamar xata yi kuka tace "Ni ka kai ni inje ince mata sannu" Dariya kawai Sudais yake yi, Dai dai nan Mumy ta shigo gidan, ya tsaida dariyar da yake ya gaisheta tayi banxa da shi ta nufi bangarenta, Heedayah da har hawaye ya cika idonta tace "Ka kai ni ince mata sannu mana pls" Ya ja hannunta xuwa parlon Mami yace "Kina xuwa xata maki duka ba ruwana" Shiru Heedayah tayi jin abinda yace, Mami ta fito daga daki jin sallaman Sudais, suka gaisa, tace "Sai yau Sudais" yana murmushi yace "Ina shirye shiryen komawa UK ne, in sha Allah weekend xan wuce" Tace "Ayya, toh Allah ya kai mu lafiya, kaka ta yrda ka fito da Heedayah kenan" Dariya yyi, ya kai Heedayah gun Mami yace "Ehh ta yadda" Mami ta jawota jikinta tace "How are you dear?" A hankali Heedayah tace "Fine, Mami a kai ni wajen kaka" Mami tace "Ohh baki ma son xuwa wajena kenan" Heedayah ta girgixa mata kai, Mami na murmushi tace "Toh bari ku ci abinci, gashi an gama" Kaka na xaune saman tabarma hannunta rike da wayarta tana tunanin wanda xata kai ma ya kira mata Baffa taji dalilin da yasa Sudais ya xo ya dauki Heedayah suka fita, aka bude kofar Shuraim ya shigo da sallama, Kaka ta fara matsar kwalla tace "Yana shigowa kawai ya dauketa bbu wani bayani suka fita, ni ban san Inda ma ya kai ta ba" Shuraim ya tsaya yana kallonta yace "Wa ya dauketa?" Kaka tace "Shine nake son inji ko Umarun ne ya aikosa ya ci min mutunci haka, tana fa kwance muna hira gwanin ban sha'awa ya dauketa ya fice bayan ya gama min rashin kunya har da ce min bani da tsoron Allah ni munafuka ce" Shuraim ya d'an ta6e baki ya nemi waje ya xauna yace "Ina yini?" Tace "Aa wllh ba lafiya ba, ya fi minti talatin fa da fitar min da Deedayah har ynxu shiru" Yace "Toh amfanin me take maki idan tana nan din?" Kaka ta mike da sauri tace "A'a ka iya bakin ka, bata fi min ku ba ma aka ce maka, duk da bata gani kuma bbu dangin iya balle na baba ta fiye min kai wllh" Yace "Toh sai me" tace "Sai bakin ciki ya kashe ka" Junaid ne ya shigo parlon da sallama, Kaka ta washe baki tace "Sannu da xuwa Junaidu, ashe kana hanya" yace "Ehh kaka" ta rike ha6a tace "Wannan zungureren babyn roban duk na Deedayah ne?" Murmushi yyi ya ajiye ledan Babyn hannunsa, Kaka tace "Toh ai dama sai dai kai din, ko Amadu" Tunda Shuraim ya Kalli ledan Babyn ya dauke kansa, Kaka tace "Wannan Mutumin fa na ce ya siyo mata amma kaga bai siyo ba tunda ba wai yana da Imani bane" Shuraim ya mike ya fice daga dakin, Junaid ya bi sa da kallo, kaka tace "Ae kaga irinta, bai siyo ba kuma yana hassada, da ka sani biyu ka siyo ka basa daya tunda bamu san ko bakin ciki yake mata ba" Junaid yyi murmushi yana kallon kaka...... Bayan Magrib Shuraim ya shigo parlon Mumy don rabonsa da ita tun da safe da ya fita gidan, bbu kowa parlon nata ya leka bedroom ya dai ji alamar tana bandaki ya dawo parlon ya xauna ya fiddo wayarsa yana dannawa, wayarta dake jikin caji ne yyi haske alamar kira, ko vibrating wayar bai yi ba sai haske, yana dai xaune har wayar ya katse, aka kara kira, sai da aka kira na hudu sannan ya mike ya nufi Inda wayar yake ya duka ya dauka yana kallon me kiran nata, ya shiga text msg din dake saman wayar, cikin few minutes ya karanta content din, sai kuma ya ajiye wayar ya nufi kofa ya fita ya kulle kofar, a hanya ya hadu da Rabi'ah tace "Ya Shuraim Mumy tana daki?" Yace "Ba daga nan nake ba" daga haka ya wuceta ya wuce bedroom dinsa. Mumy na fitowa parlonta ta nufi wayarta da sauri ganin yana haske alamar ana kira, ta daga ta koma daki ta kulle kofar tace "Yi hakuri wllh na shiga wanka ne, ya ake ciki?" Ta d'an yi shiru sannan ta Kalli agogo tace "Xuwa dai karfe dayan dare shine dai dai" Tayi murmushi tace "Toh shkkn sai mun yi magana...." Daga haka ta katse wayar ta xauna gefen gado tana wani murmushi.... Mami na xaune parlon Abba da Heedayah sai Rabi'ah da Khadijah, aka bude kofar parlon Kaka ta shigo ba ko sallama tace "Ni fa har yanxu ba a shigo min da Deedayah ba lkcn baccinta har ya wuce, idan kuma an canxa wajen kwananta ne sai a sanar min" Bata jira cewarsu ba ta daga Heedayah ta nufi kofa tana kallonsu Rabi'ah tace "Ku kuma gantalallu ga fura can da Junaidu ya kawo min na rage maku" daga haka ta fita, Mami gaba daya bata ji dadin xuwan da kaka tayi ta tafi da Heedayah ba, don ynxu goma ma yyi ta xata kakan tayi bacci ne ta wuce da Heedayahn part dinta don tace xata sha tea, Abba yyi murmushi bai dai ce komai ba amma ya gane Mami wasn't happy, Mami ta mike tace "Toh sai da safe" Yace "Allah ya tashe mu lfya" Su Rabi'ah ma suka yi mata sai da safe ta fita parlon.....

Toh haka Allah yayi da ni yau..... 馃寶

Heedayah isn't free.... It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull