Heedayah complete Novel - Chapter 56
Heedayah complete Novel Chapter 56: Heedayah complete Novel Chapter 56. Heedayah isn't free, you read for free 馃し馃徎鈥嶁檧锔忦煠佛煆烩€嶁檧锔�
4,490 words
Heedayah isn't free, you read for free 馃し馃徎鈥嶁檧锔忦煠佛煆烩€嶁檧锔�
it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah
Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788.... 9/12/21, 8:04 PM - ,: Kashe wutan gidan yyi gaba daya snn ya dawo parlon ya dau wayarsa ya kunna fitila ya wuce sama, a hankali ya bude dakin dake kallon wanda Heedayah ke ciki, ya shiga ya rufe, kusa da kofar bathroom ya isa ya duka ya daga foot mat dake kasa ya daga tiles din da aka daura kawai a wajen, sai dai idan mutum bai lura ba baxai gane daura tiles din kawai aka yi ba xa a iya dagawa, wani karamin under ground ya haska a wajen bayan ya bude wani box, ya ciro bindiga guda daya cikin bindigogi biyar dake nan snn ya dura bullet dinsu dake wajen su ma, ya mayar da tiles din ynda yake ya daura foot mat din ya mike ya saka bindigan a aljihunsa, ya fita dakin ya kulle kofar gently, har xai sauka sai kuma ya kalli kofar dakin da Heedayah ke ciki ya dawo ya bude kofar shi ma gently yana kallon cikin dakin, all with the aid of his phone flash, kwance ya ganta ta dukunkune waje daya tana bacci, ya karasa cikin dakin ya bude press dake ciki ya fiddo babban blanket me laushi ya lulluba mata, still yyi sai kuma ya kashe flash din da wuri ganin ta gyara kwanciyarta, sai da ya tabbatar ta ci gaba da baccin snn ya tafi gun curtains xai gyara ya hango mota biyu sun tsaya dai dai gate din gidan don ta window din ana yi ganin wasu bangare daga surrounding din street din, kallon motar yake har bayan kusan minti goma shi dai bai ga alamar an sakko daga ciki ba, wanda idan ma an sakko din ma ba sani xai yi ba sbda jikin wall din gidan motar ya tsaya, nan kuwa mutane biyar har sun sauka daga motar xuwa bakin gate din nasa, daya daga mutane biyar din da suka diro daga motar ya tafi ya durkusa bakin gate din gidan yana haska fitilar wayarsa ko xai ga tambarin tayar mota da xai yi nuni da mota ta shiga gidan, mikewa yyi yana kallon sauran yace "Yes yana ciki" dayan cikinsu yace "Cikin darkness?? da yana ciki ai xa a ga wuta a cikin gidan, but no light and akwai wuta a anguwar ai" Bindiga wanda ke kallonsa ya daura masa a fuskarsa strictly yace "Ka raina kitabar Brainiac kenan? Tunda har baya gidansa na asokoro, baya can gida, to yana gidan nan, coz he have no business with the other gender ballantana ace yana hotel, baya ma kwanan hotel, so now you guys should just find a way da xa mu shiga gidan nan in hukuntasa" Mutumin yace "Talent dinsa na yanda yake shiga gidan mutane in every operation xa mu yi amfani da yanxu" Tuni Khaleel ya fita dakin da Heedayah take ya sakko downstairs ya fito compound, ta jikin bango ya dinga bi har ya iso gate ya manne da bangon pillar din gate din, nan kuma duk ya dau muryoyinsu, A karo na farko Maska yace "We should bother our self not..... finding a way in, I have his spare keys, stole them from Zayyad" Khaleel yyi grinning teeth dinsa bai kara second daya a wajen ba ya koma cikin gidan da sauri, a karo na farka a rayuwarsa ya ji he is disturbed about something, ya ji gaba daya hankalinsa ya tashi, baya son abinda xai tsorata Heedayah ko kadan, ya san kuma dole xa su shigo gidan ya san tunda makulli na gun maska xa su shigo, da ma shi kadai ne xai sama ma kansa way out cikin few minutes but not with Heedayah, yana shiga parlon ya ji suna bude gate din, ya sa makulli kofar parlon leaving the key jikin kofar duk da ya san it's of no use cos he knows all the trick, they knows all the trick, they are expert users of his talent and experiences, sama ya haura ya tsaya nan corridor patiently waiting for them, yana jin suka bude kofar parlon bayan wasu mintuna, haka kawai a sannan ya dinga jin faduwar gaba, and with just a blink of an eye sae ga wuta ya haska ko ina, wato sun kunna wutan gidan yasan kuma aikin Maska ne, Fago na nuna ma Oga Arne takalman Heedayah dake parlon yace "This is the root of the problem, mace ce ta shigo rayuwarsa shine take yaudararsa yake misbehaving yake raina ku" Arne ya rike ha6arsa yana gyada kai convincingly yana kallon takalmin da mugun mamaki, a hankali yace "Ohh I seeee, mace ce ta shiga rayuwarsa farat daya, abun ka da ba sabon ba" Fago yace "He risked his colleagues life sbda matsiyaciyar mace da xan harbe yanxun nan" Arne yyi wani dariyar bossawa lkci daya kuma ya daina dariyar yace "To wllh wllh a gabansa xa a aikata lahira, snn sai ya san yayi fatali da umarnin manyansa yau, shi ya mance a yanda muka daukesa kenan, I am more of his father than Boss, ni ne uwarsa nine ubansa ynxu haka a duniya" Khaleel dake jin duk abinda suke cewa ya manne da bango hannunsa rike da bindigarsa ya saita dai dai gwiwar Fago cikin few seconds ya saki bullet din, bayan ya tabbatar ya samu kafar ya bude dakin da Heedayah take ciki ya shige da sauri ya sa makulli, wani ihun axaba fago yayi ya xube kasa jini na malala daga gwiwarsa ta dama, ko wannensu har Arnen suka samu bango duk suka manne suna xaxxare ido, A firgice Heedayah ta mike xaune saman gado tana kallon Khaleel, ya boye bindigar hannunsa a bayansa, ya sakar mata murmushi da iyakarsa lips, kokarin sauka ta fara yi daga saman gadon looking very afraid tace "Meye yyi wani karan, what's that, is that a gun????" Ya nufeta trying his best to calm her down yace "No sound, may be... May be... We have visitors, probably armed robbers, bandit, kidnappers...." Ta wani xaro ido ta fasa wani shegen ihu ta mike tsaye, rikicewa yyi ganin yanda ta tsorata ya isa gabanta not minding she will see the gun in his hand yace "Noo Heedayah, I will protect you by all means bbu abinda xai faru dake, I promise you this" Ta wani xaro gaba daya idanuwanta ganin bindigan hannunsa ta kara saka wani kara me karfi, jawota yyi jikinsa yace "I am protecting us with it, they have guns also, I mean no harm Heedayah" ta kankamesa tace "Wayyo ni tsoro nake ji, plsss take me out of this house, don Allah ka tafi da ni daga nan, tsoro nake ji" Jikin window ya nufa holding on to her tightly, ya bude window din dakin ya saita bindigarsa up the sky ya saki bullets uku that sounds so loud a anguwar, Heedayah bata ta6a tsorata irin na wannan dare ba tunda aka haifeta, tana son kwace kanta kuma amma ya ki saketa, ya kara harba bindigar, dai dai nan Maska ya bude kofar dakin, sun kai su shidda ko wanne na nuna masa bindiga kamar yanda shi ma yake nuna ma Arne, Duk ynda Heedayah ta so juyawa taga wa enda suka shigo Khaleel bai bata wannan daman ba sbda yanda ya rungumeta, Arne ya dinga kallonta yana nuna mata bindigar hannunsa, shi kuma Khaleel na pointing dinsa da nasa bindigar, Arne yace "Ka sauke bindigar ka ko in harbeta har lahira ynxu" Girgixa kai Khaleel yyi yace "Same will happen to you right now" Arne yyi wani shegen kara yace "Genius dama sbda mace kayi disappointing dinmu ka janyo mana rasa Salim????? Ka janyo mana asara da yawa, duk sbda yar kwailar nan? Wato a cikin kankanin lkci ka gurbata rayuwarka ka fara harka da mataaa, a kaf duniyar nan dama kana da sama da ni???" Cikin tsawa ya kare maganar yana huci, sai kuma ya nufesa still pointing the gun to Heedayah, Khaleel ma na nuna sa da gun dinsa fuskarsa a daure, lkci daya Siren ya cika anguwar Arne ya juya da sauri yana kallon yaransa yana xaro ido, Maska sake xare ido shi ma yace "Policemen...." cikin daga murya Arne yace "Get set, back to the cars now, help Fagoo out, immediately now" Duk suka juya suka fice daga dakin da sauri, Arne na komawa da baya bai fasa nuna Heedayah da bindiga ba yana kallon Khaleel cikin kaushin murya ta mugunta yace "Wllh wllh idan baka dawo hanya ba nine ajalin ka Khaleel, nine ajalin wannan yarinya, nine ajalinku ku biyu billahh, sae na yi maka kisan walakanci, ita kuma in harbeta cikin ruwan sanyi, kasan wanene ni Khaleel, kasan wanene Manga, kasan wanene Barau, kasan wanene Bala, forget you are a Genius idan aka hada mu hudu mun fi Genius, we will make life a dirty miserable for you before sending you to ur early grave, yanxu muka fara harka da kai, baka isa ka kara bijira mana lkci daya ka janyo mana matsala ba, Kai din namu ne" yana fadin haka ya fice daga dakin in a haste, har sannan siren na tashi a anguwar loudly, Khaleel ya sauke wani ajiyar xuciya a karo na farko ya kalli Heedayah that he is holding so tight a jikinsa don ya san she passed out from the moment she heard their voices, kwantar da ita yyi saman gado yana kallon kyakkyawan fuskarta cikin sanyin murya yace "Heedayah...." Su Arne da tawagarsa na isa titi suka jiyo jiniyar yan sanda so far away alamar a lkcn ma Yan sandan ke tahowa, and they wondered wani siren ne ke tashi a anguwar haka, not minding that.... a mugun guje suka yi wucewarsu da motocin su kafin bayyanar motar yan sandan, Knocking Khaleel ya ji ana yi downstairs with voices, ya mike tsaye da sauri ya ajiye bindigar hannunsa karkashin pillow ya fita, corridor din dakunan ya hadu da matasa just like him guda biyu sai dattijai guda biyu, daya dattijon yace "Hope you are safe brother?" Khaleel ya kirkiro murmushi yace "Alhmdllh" Daya matashin yace "Babu abinda dai suka yi ko, don naga pool of blood downstairs" Khaleel yace "Ni na caki daya daga cikinsu da wuka, har suka gudu sbda karan Siren wukar yana jikinsa, I battled with them" A tare suka hada baki suka yi hamdala, Dattijon yace "To matar taka fa?" Khaleel da kamar baxae ce komai ba sai kuma yace "Ta dai tsorata ne kawai, and I think she passed out...." Daya daga matashin yace "Can I meet her in and check on her" Dattijon yace "Ehh likita ne shi, either ya dubata ko kuma a wuce asibiti kawai" komawa dakin Khaleel yyi ya isa kusa da Heedayah ya durkusa ya dau dankwalinta da ya fadi a kasa ya rufe mata gashinta da shi snn ya gyara mata skirt dinta, ya koma gunsu yace ma likitan xai iya shiga, makotansa ne su din gaba daya, iyakarsa da su haduwa a masjid din anguwar yyi masu gaisuwar mutunci yyi wucewarsa that is if yana Abuja, though a wata ya kan yi sati uku a Abuja, xamansa a Kaduna lkci lkci ne, Siren din da ya dinga tashi a anguwar kuma daya daga matashin wanda ya kasance soja ne ya kunna kuma yyi kiran office a turo masu yan sanda tun farkon harbin da Khaleel yyi sau uku, neighbors din nasa na nan har yan sanda suka iso suka d'an yi investigation dinsu suka wuce, sae kusan karfe biyu da few minutes duk neighbors din suka bar gidan Khaleel, bayan likitan ya tabbatar Heedayah is fine, kuma bacci take. Har kusan asuba Khaleel na xaune gefen Heedayah bayan ya gyara parlon duk ya share blood stain din, ya jinginar da kansa da gado yana kallon saman dakin, juyawa yaga tayi, ya sauke idonsa kanta da sauri yana kallonta, a hankali ta bude idonta suka yi ido hudu da shi, mikewa tayi xaune tana kallonsa sai kuma ta bi dakin da kallo, ya kamo hannunta kafin yace komai ta fashe masa da kuka tsoro karara a fuskarta tana komawa baya, yyi kasa da murya yace "You are safe Heedayah, 'yan sanda sun xo sun tafi da su" ta fashe da kuka sosai xata sauka saman gadon, ya riko duk hannunta biyu yace "Nace maki yan sanda sun tafi da su, don't cry plss" cikin rawar murya tace "I am still afraid, why were they here?" Yyi kasa da murya yace "To Rob" ta dinga bin dakin da kallo tana hawaye, yace "Stop crying plss" tace "Kaina na min ciwo" da damuwa yake kallonta, can ya mike don Dr Farouq ya dauko mata magani daxu daga gidansa ya kawo kafin su tafi, Khaleel yace "I'm coming" sauka tayi da sauri daga kan gadon ta tsaya kusa da shi tace "Nooo kar ka barni" kama hannunta yyi suka fita dakin xuwa downstairs ta makalkale masa don duk a tsorace take, kitchen ya shiga tare da ita, ya dau bottle water a fridge ya xuba a kettle ya kunna, ya lumshe ido jin yanda taki basa breathing space standing so close to him, Bai bari ruwan ya tafasa ba ya dauraye mug ya xuba kayan shayi a ciki snn ya xuba ruwan ya dau spoon ya juya, kashe wutan kitchen din yyi suka fita, yana rike da cup din shayin tana makale da shi suka koma sama, yana kallonta tana shan shayin bai san sarkin shan shayi bace har ta shanye tass, yace "You need more?" Girgixa masa kai tayi, ya bata ruwan gora da paracetamol ta amsa ta sha, bayan few minutes ta kwanta saman gadon tayi shiru tana kara tunanin abinda ya faru, she is still shock, kallon agogo dake nuna karfe uku da few minutes yyi sai a snn ya fara jin bacci, ya lumshe idonsa ya bude yace "Did you need anything Heedayah?" Girgixa kai tayi tana kallonsa, yace "Xan tafi in kwanta...." Da sauri ta mike xaune tace "Where?" Yace "Dakina" kuka ta sakar masa tace "Noo kar ka barni ni kadai pls, wllh tsoro nake ji" Shiru yyi yana kallonta, can ya mike ya bude press ya ciro wani bargon ya shimfida a kasa ya dau pillow ya ajiye snn ya kashe wutan dakin ya kwanta kasan bargon yace "Good night" edge din gadon ta dawo ta inda yake kwance yanda xata dinga ganinsa yana daga kasa tana daga sama tayi lamo gabanta na faduwa, ba a dau lkci ba bacci ya dauketa, shi kuma duk baccin da yake ji sai ya samu kansa da kasa yi.... A idonsa aka yi kiran sllhn asuba, biyar da few minutes ya mike ya shiga bandaki yyi alwala ya fito ya bude kofar dakin a hankali so careful not to wake her sannan ya fita. Bayan ya dawo masallaci a parlor ya kwanta nan da nan bacci ya daukesa, cikin bacci ya ji ana tashinsa, ya bude idanuwansa a hankali ya ganta durkushe kusa da shi tana kallonsa, murya can kasa tace "Babu Hijabin da xan yi sllh" ya kuma lumshe idonsa snn ya bude ya mike xaune, ita dai kallonsa kawai take da idanuwanta da suka kumbura, tashi yyi ya wuce sama ta mike ta bi bayansa, ya shiga wani daki sai gashi ya fito da hijab a linke, ya mika mata, tace "Na waye?" Murmushi ya sakar mata yace "Pray Heedayah" daga haka ya koma downstairs, ta shiga dakin ta dauko darduman ita ma ta dawo kasa, har ya koma bacci ta samesa a parlon, ta jima xaune saman darduman bayan ta idar da slhn don har gari ya fara haske, daga karshe ta kwanta saman darduman nan da nan bacci ya dauketa. Karfe takwas saura mintuna Mami ta shigo garin Abuja, tun hudu da wani abu na asuba hakurin Maman Fadil ya kare ta kirata don tayi ta kiran Junaid wayarsa wasn't going through a daren, nan dai ta sanar ma Mani halin da ake ciki with tears, daren ranan daga ita har Farida bbu wanda ya rintsa, I don't want to talk about shuraim cos he saw no sleep too, ya kuma fi su shiga tashin hankali, Tun da Maman Fadil ta sanar ma Mami abinda ke faruwa, sllhn asuban ma sai da Mami tayi consoling kanta na gaske snn ta iya yi, she have never been down lkci daya kamar ynda tayi jin news din nan ba, she felt so sick at once, ba training din da tayi ma Heedayah ba kenan, baxata taba tafiya tare da saurayi ba kamar yanda Dinar ta sanar mata, Mami was so confuse and shock to the highest, wanda bata san lkcn da hawaye ya hau mata xarya ba gashi junaid baya gidan sai dai bata yi yunkurin kiransa ba, tana idar da sllhn Asuba sai da ta sha magani ko xata d'an ji saukin abinda take ji, snn ta saka Hijab dinta har kasa ta dau hanyar Abuja, not minding the road tare da driver dinta, she just can't hold it anymore, a motar ma banda addu'o'i bbu abinda take ta yi, tun auren Maman Fadil sae ranan Mami ta taka gidanta a karo na farko, daga Farida har Yayarta bbu wanda ya iya ce ma Mami komai, sae Maman Islam makociyar Maman Fadil da ke parlon da wata neighbor dinsu Maman Safwan ne suka iya gaisheta da yi mata sannu da xuwa ganin kamaninta da su farida, Mami ta amsa cikin sanyi, ta nemi kujera ta xauna don bata jin xata iya ci gaba da tsayuwa tana kallon Maman Fadil tace "Deenar me ku ka yi ma Heedayah?" Cikin sanyin murya Maman Fadil tace "Haba Mami me xa mu yi ma Heedayah, karfe nawa suka iso a jiyan ma balle ayi mata wani abu, wllh bbu abinda aka yi mata" sae kuma ta fara kuka sosai, Mami ta dafe kanta ita ma hawayen har ya kawo idonta, ta shiga kiran Allah a xuciyarta, Abba kawai da kaka suka fado mata a wnn lkcn, where is she to start from now, Maman Fadil na share idonta tace "Abun da mamaki sosai, ko da ta fita gurin saurayi ae xata dawo sai in wani abu ne ya faru, kuma gashi bamu san waye saurayin ba, wllh Mami sneaking tayi ta fita ni da Farida bbu wanda yasan ta fita, da na sani ai babu abinda xai sa in barta ta fita waje, mu uku kadae ne gidan sae Fadil fa" Farida dai hawaye kawai take ta kasa cewa komai, Mami ta daure ta mike tace "Nearest police station a ina yake?" Maman Fadil tace "Aa tun asuba Shuraim ya kai kara can, he is still not yet back ma" Maman Islam ta sauke wani ajiyar xuciya tace "Allah ubangiji ya takaita wahala da tashin hankali, ya bayyanata cikin aminci da yarda" A hankali Maman Fadil tace "Ameen" Mami ta dau wayarta ta shiga kiran Shuraim. Karfe tara saura Heedayah ta farka, ta mike xaune tana bin katon parlon da kallo, har sannan Khaleel na kwance saman kujera yana bacci, ta mike ta isa kusa da shi ta durkusa tana kallonsa, hancinsa ta kafe da ido, can ta kalli dogon lashes dinsa snn lips dinsa, ta kuma kallon hancinsa, sosai gabanta ya fadi, lkci daya ya bude ido ta koma baya da sauri har tana neman faduwa tana kifta ido tace "Tell me who were those people of yesterday" ya mike xaune yana shafa kansa yace "Armed Robbers, good morning Heedayah" shiru tayi tana kallonsa, ya lumshe idonsa ya bude yace "May be sun ga ina gari and they've been targeting sae jiya suka xo" a sanyaye tace "How did they leave?" Yace "My neighbors helped, they alerted the police" Tayi shiru tana kallonsa, sauke dogayen kafafuwansa yyi kasa yace "I've slept for so long, you need to get back home Heedayah, kar ki ci gaba da daga hankalin wa enda suka rike ki da aminci, I am taking you back home now idan kinyi breakfast" lkci daya mood dinta ya canxa tayi shiru tana kallonsa, ya mike yace "Ki tafi sama ke ma ki shirya, take ur bath I will get you something to wear now" da kallo ta bi sa har ya wuce upstairs ba a dau lkci ba ya sakko da makullin motarsa, yace "Toothpaste, toothbrush, sponge, soap towel duk suna nan na ajiye maki saman gado, I will be back soon" ta mike da sauri kamar xata yi kuka tace "Ni tsoro nake ji wllh" yace "No harm Heedayah, ba dadewa xanyi ba kuma, I will be back soon" daga haka ya fita parlon tana ji ya fitar da motarsa daga gidan, xancen da yyi mata kafin na karshe ne ke yawo a kanta, she needs to get back home, but she never wants to go back, shiru tayi tana tunanin kilan dole yace sai ya kai ta gida, ita kuma bata son ta je, hawaye ya kawo idonta ta wuce sama da sauri ta dauko veil dinta snn ta sakko kasa, ta sa takalminta ta nufi kofa, gwara ta tafi kawai kafin ya dawo ya ka ita gida. Murda kofar tayi ta ji a rufe, kamar xata yi kuka ta dinga kallon kofar, ta sake murdawa bai buduwa ba, a hankali ta juya ta koma sama duk jikinta a sanyaye ta dau abubuwan da ya ajiye mata saman gado ta shiga bandakin, ko da ya dawo bata fito ba ya ajiye mata ledan hannunsa kan gadon sannan ya fita dakin ya wuce nasa, har ya sakko wajen karfe goma bayan yyi wanka ya shirya Heedayah bata sakko ba, sai kallon agogo yake don ya kagu ya ga ya mayar da ita gida, daga karshe ya mike ya wuce saman, karo suka kusa ci xata sakko ya koma baya yana kallonta, sosai bakin abayar yyi mata kyau kamar ya aunata kafin ya siyo, ya sakar mata murmushi yace "U look cute" Ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, yace "Taho kiyi breakfast lkci na wucewa" bin bayansa tayi suka koma kasa, ya hada mata shayi ya bata fried Irish with egg and ketchup da ya siyo, yace "Do you take bread?" Ta girgixa masa kai, shayin ta fara shanyewa gaba daya, ya buda ido yana kallonta yace "Why?" Tace "Haka nake yi" yace "You need more?" Ta girgixa masa kai, jawo plate din Irish din tayi ta fara ci a hankali, ya d'an yi murmushi ya hada shayinsa da iyakarsa bai kai rabin cup ba ya fara sha, yace "Ina xa ki ce ma Guardians dinki kin tafi idan na mayar da ke yanxu Heedayah?" Ta kallesa bata ce komai ba, lkci daya ta kasa ci gaba da cin dankalin, ganin hakan yace "Why are you not eating" bata ce masa komai ba ta ci gaba da ci without appetite, har cikin ranta bata son xancen gida, daga karshe ta tura Irish din ganin ya fice a ranta gaba daya, ta koma saman kujera ta xauna ta jinginar da kanta da kujeran, da ido ya bi ta yace "What's wrong Heedayah?" Ta girgixa masa kai tace "Nothing na koshi" Kafin yace komai tayi saurin cewa "Wannan shayin ne xai isheka?" Yace "Baxan ma shanye ba" Tayi shiru tana kallonsa bata ce komai ba, a hankali kuma tace "I saw u with gun yesterday, waye ya baka" kallonta yyi da sauri coz her question came unaware, sai kuma ya sauke idonsa kasa cikin cool voice dinsa yace "My father, you know.... he is a soldier, da naji barayin sun shigo shine na tafi dakinsa na dauko bindigar" Yana iya ganin tsoron da ya bayyana fuskarta lkci daya, ya ajiye sauran shayin da ya rage ya mike yace "I need to get u back home Heedayah, nasan hankalin kowa ya tashi yanxu, ki saka kayan ki da kika cire a leda ki sakko da shi mu tafi" Shiru tayi tana kallonsa ko kiftawa babu, gabanta na faduwa kuma sosai, ganin jiranta yake tace "Na saka a leda...." yace "To dauko su" tayi narai narai da ido cikin tsigar shagwaba tace "Ni baxan iya xuwa sama ba kuma, my legs a paining me, ka dauko min" ya kai minti daya yana kallonta can yyi murmushi ya wuce saman ta bi sa da kallo har ta daina hangosa, mikewa tayi da sauri ta tafi ta saka takalminta ta fice daga parlon da ya bari a bude bayan shigowarsa daxu, kusan da gudu ta isa gate shi ma lock kawai ta bude ta fice daga gidan gaba daya, mota ce tayi parking dai dai gate din gidan, tana kallo har wanda ke cikin motar ya sakko, kallonta ya dinga yi, taki yarda su hada ido ta nufi hanyar da take tunanin xai fitar da ita daga anguwan da sauri, da ido ya bi ta har tayi nisa snn ya shiga gidan, ya bude parlon ya shiga, daga kitchen Khaleel ya fito yana neman Heedayah, ya tsaya kallon wanda ya shigo parlon, Zayyad yyi masa wani shegen kallo sai kuma ya kyalkyale da dariya yace "I am happy for you frnd, ko ba komai kai ma xaka bada labarin wacece mace tunda ka kwana gida daya da mace yau, sai dai you are in great risk Brainiac, Mu ma ba wai bama harka da mata ba, but we still concentrate on our goals, kai kuma da yake sabon shiga ne, it's causing you much distraction, ga mata iri ri sai warce ka xaba ka darje a gari, don't be afraid of loosing this one....." Wani kallo Khaleel ya jefa masa xai koma sama neman Heedayah and idan ma ya ganta baxai bari ta fito ba har Zayyad ya wuce, Zayyad yace "Na samu labarin artabun da kayi da su Oga daren jiya, you chop liver Genius... and probably my text message helped, yanxu dai tunda har gari ya waye har kuma yarinyar ta kama gabanta sai mu je ka bada hakuri, I don't want to imagine anything happening to you Brainiac..... But isn't that girl I saw too young for u, anyway sweet sixteen, and she is damnnn pretty with the perfect curves...." Har Khaleel ya fara hawa stairs ya dakata ya juyo da sauri fuska daure yace "And where did u see her??" Zayyad yace "Mun hadu bakin gate xata wuce yanxu" Wani tsalle Khaleel yyi ya duro maimakon sakkowa few stairs din da ya hau yace "Ta tafi Ina?????" Zayyad ya tsaya kallonsa, Khaleel ya nufesa da sauri yace "Answer me plss Zayyad, Ina ta tafi" Zayyad yace "Wahala be like bicycle, I just met with her outside ynxu da xan shigo and tayi hanyar titi how will I know inda xa ta" Khaleel yace "Nooo, why did u let her" Zayyad ya saki baki yana kallonsa yace "Ikon Allah to nasan inda xa ta ko nasan me ya fito da ita" Khaleel ya warce car key din hannunsa ya fita waje da sauri almost running, Zayyad ya bi bayansa with much surprise.