Idon nera by mamuhgee Complete - Chapter 16
Idon nera by mamuhgee Complete Chapter 16: Idon nera by mamuhgee Complete Chapter 16. Wayeshi dazai shigo rayuwarsu Yana neman lalata musu suna cikin sanyi...
4,482 words
Wayeshi dazai shigo rayuwarsu Yana neman lalata musu suna cikin sanyi...
Me mommy take tunani dazata Bari aci gaba da cin mutuncin IDON NERA's akan AQEEL ASAD wadda Rana tsaka ya shigo rayuwarsu.
Kiran Hayat ne yasake shigowa wayarta ta jefarda wayar gefenta tana sakin qaramin saki sbd Hayat din Yana qara Mata ciwon kai da Kiran wayarsa dayaketa yimata tin safe.
Bude idanuwanta tayi akan hotunansu dake kan jaridar ranta na qara soyuwa da kalmar da Yan jaridar sukai amfani da ita Wai uwar ko 'yar.
Jan motarta tayi Kai tsaye ta nufi office din mommynta Dan gwara ta yanke alaqarta da AQEEL ASAD da wuri batason alaqarsu kawai. ##MAMUH# #LOVE/HOTLOVE/AQEEL ASAD/AMAL SANDA #IDON NERA
*_ZAFAFA BIYAR_*
*RUMBUN K'AYA*π₯ Hafsat Rano
*DAUDAR GORA*π₯ Billyn Abdul
*IDON NERA*π₯ Mamuhgee
*A RUBUCE TAKE*π₯ Safiya huguma
*KI KULANI*π₯ Miss xoxo
Littafi daya---400 Biyu---600 Uku----800 Hudu-----1k Biyar din duka----1200
ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN
0022419171 Maryam sani Access bank
Shedarka ta 09033181070
MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN
09166221261
π³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺ *Ina yan uwa 'yan nijer?* *Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+22799643131
Littafi daya---450CFA biyu---650CFA uku----850CFA hudu----1050 CFA Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!* *Thanks for choosing us*π₯ *_Arewabooks@Mamuhgee_* 32 Tunda safiyar ranar shikuma Hayat gidansa aka tashi da fitina Mai qarfi tsakaninsa da Nafee wadda itace kadaice tasan da yasaka a bibiya AQEEL ASAD akan tabbatarda shine yake zuwa IDON NERA's,
Tajisa alokacinda yake maganarsa dakuma lokacinda aka tabbatar Masa da AQEEL ASAD dinne,
Batareda tunanin Aminyarta ba kokuma mutuncin AQEEL ASAD da kusancinsu ta fidda labarin Wanda Daman neman tabbacin jita jitar Media keyi Dan Haka tun a Daren ta fitarda labarin Tunanin nata Mijin ya fita tarkonsu.
Yana cin karo da jaridar yasan Nafeen ce Dan Haka ya tinkareta Kai tsaye ta tabbatar Masa da itace.
Fada da tashin hankali sukai sosai Wanda yasa yace tabar gidansa Takoma gidansu sai tayi hankali Kuma kada ta yarda ta fadawa kowa itace tafidda zancen.
Kukan tashin hankali da Dana sani taringa Yi gashi ita kanta tana tsoron Bilkees taga labarin Bare hartasan itace ta fidda zancen,
Sanin wacece Bilkees da tsananin zafin kishinta yasa tashiga sabon tashin hankali karshe ta Dole saidata Kira Bilkees din tana kuka ta sanar Mata Hayat ya koreta akan IDON NERA..
ba shiru Bilkees din ta iso gidan tana yiwa Idon Nera adduar dibar albarka da fatan su hadu da nasu masifar datafi Wanda suka saka Aminyarta.
Koda ta Isa Haka suka zauna suna jajanta lamarin Bilkees cikeda tausayin Aminyarta ta baro bayan ta rarrashin Amrah dataketa kukan rabuwa da mahaifiyarta.
A hanyarta ta komawa gida Traffic light ya tsaidasu cikin lafiyayyar motarta da ake tuqata,
A cikin Dan qaramin cunkoson holdup din dasuke tafara qosawa da jiran ta Dan dago kanta tana kallon wajen motar cikin mummunan tsautsayi idanuwanta suka sauka kan hoton kyakkyawan mijinta a shafin farka na jaridar da wani me siyarda jaridu yaketa dagawa Dan a siya.
Ajiyar zuciya me sanyi ta sauke tana jin son AQEEL ASAD dinta me tsananin girma na sake mamayeta musamman tunaninta na koda yaushe akan nata dinne ita kadai.
Take tausayin Nafee da aurenta yabi duk ya wargaje sbd masifa ya dawo ranta.
Murmushin farin ciki ta sake tana sake kallon fuskarsa a jaridar tareda saka hannu handbag dinta tana lalubo wayarta Dan kiransa taji murmuyarsa.......
Dakatawa tayi daga dauko wayar cikin Jakarta tana Dan tsayar da idanuwanta akan jaridar lokacinda me jaridun ya matso har gaban gilashin motarsu Yana sake tallata sanaar tasa.....
Ras ta bude ido da kyau ta karanta bayanin dake rubuce baro baro gameda mijin nata da hotonsa yake Kai,
Duk tsananin ilimin addinin datake dashi Kuma a matsayinta na matar wadda yakeda sani a addnini sosai bata iya kamo salatiba a bakinta sbd mummunan faduwa da rawar da kirjinta yayi, cikin tashin hankali da tsoro hannuwanta na rawa tace"
Wayyo Allah na Nashiga uku, Meye wanna nake gani?
Murya na Yar rawa ta kalli drivernta tana cewa,
"Habibu karantamun abinda yake jikin jaridar Nan Dan Allah Kaga nakasa gane mena karanta...
Me jarida kuwa yana ganin hankalinta sosai akan jaridarsa ya sake matsowa sosai Yana sake Nuno mata jaridar Yana cewa,
"Jaridar yau ce Haj.
Ahankali habibu ya bude idanuwansa akan jaridar ya karanta abinda yake rubuce a gurin hoton maigidansu.
*_DR sheykh MUHAMMAD AQEEL ASAD Former COA, HN Spk/MADAME IDON NERA._* *_Work(aiki) Or busness(kasuwanci)????_* *_Mother(uwa) Madame haj zainab IDON NERA or Daughter ('ya) AMAL Sanda IDON NERA???_*
Sake karantawa yayi dakyau ya tabbatarda dai Maigidansu ake nufi wato Dr Aqeel sheykh.. To meya hada sunan dr sheykh da wannan hamshaqiyar matar data bawa karuwai cikakken yanci da gata???
Me ake nufi da uwa ko 'ya?.....
Cikin Yar shaqewar murya bilkees tace"
Habibu fassaramun dakyau nagane Mana Ka karanta kayimun shiru kabarni Ina jiran bayani.
Shiru yayi yana Dan kaucewa kallon jaridar a natse yace"
Hajia shirme ne da neman lalata suna irin na Yan jarida fa Amma bakomai ban.....
A rikice ta zaro kudin da batama San nawa bane daga Jakarta ta sake glass din motar ta miqawa me jaridar ta karba da qarfi tana sake ware idonta sosai akai tana sake karantawa.....
Innalillahi,kenan dai abinda ta karanta dinne da farko ba kuren karatun bane...
Innalillahi na shiga uku na lalace, Kodai sunan SSG zasu saka suka saka na Sheykh sbd a iya saninta babbar masifar data tarwatsa farin ciki da gidan SSG a yanzu ba kowa bace face IDON NERA, Saidai bata saniba Yar ce ko uwar ake magana yanzu akan AQEEL ASAD dinta..
Mezai hada mijinta me tsananin qyanqyamin sunan zina ma bare karuwan dake aikata zinar har a hada sunansu a jarida.....
Zuciyarta taji tana doka wani irin tsalle da rawar firgici,
Nashiga uku bana gane komai wlh, IDON NERA kuma? Dr shaykh Dina Kuma??
Zufane yaketa karyo mata tako Ina cikin doguwar jallabiyar dake jikinta,
Ahankali numfashinta yafara yin sama sama sbd tsananin firgici da abinda takeji a zuciyarta,
Zuciyarta wata irin zafaffiyar zuciyace akan mijinta, Tanada wani irin mugun rauni agurin kishi sbd abu kadan ne yake sakata shiga masifaffen hali sbd kishin Mijinta Wanda ya kasance abin so ga Mata da yawa,
Me ake nufi? Taje ta kaso rigimar gidan Nafee shine masifar zata bullo akanta... Cabdijam, Wllh gwara da wurwuri masifar Takoma inda ta fito wato gurin Hayat din Amma baa kan AQEEL ASAD dintaba..
kishinta rinjayar iliminta yakeyi sosai aduk lokacinda ta hararo mace a rayuwar Mijinta shiyasa take wahala sosai da zuciyarta gameda Mijin nata,
Wani gumi take sake fesowa tana Jin zuciyarta na tsalle,
Ganin mawuyacin halinda tashiga yasa habibu qarawa motarsu gudu suka iso gida a rikice sbd ganin kamar zata shide bata hayyacinta.
Yana parking ko Jakarta a juye ta daukota tana tafe Yan wasu abubuwa ciki suna zubewa batareda ta ankaraba.
Kai tsaye hayar shashen umma ta nufa idanuwan ko gani basayi sosai sbd rikici.
Daqyar da wahala ta iya Dan seta kanta kadan sbd sanin doka da halin ummar na rashin son rawar jiki da tashin hankali da rashin nutsuwa.
A Palo ta taddata zaune kan doguwar kujera tana karanta sako a waya,
Kasa riqe kanta bilkees din tayi sbd gab take da Dora hannu akai tayita birgima tana qwala ihu da wannan mummunan abin datake neman me yimata budadden bayani akan ba gaskia bane abinda aka rubuta din.
Hannunta na wata irin rawa ta miqawa haj maryamah jaridar hannunta tana sako wasu irin hawayen tashin hankali da shiga uku...
Kafin tayi magana Hameeda ce tashigo palon itama hankalinta atashe riqeda jaridar ko gabanta bata gani sosai itama tana cewa"
Umme B menene yake faruwa zaa lalatawa daddyna suna?
Wannan IDON NERA fa ake magana akai,
Meya hada sunan daddyna da suna hamshaqan karuwai dasuke lalata zaman lafiyar gidaje?
Meya hadata da daddynah?
Meya hada sunansu guri daya?
Wace tambayace suka rubuta anan din????
Wurgi tayi da jaridar tana sakin hawaye itama Dan wlh bazata iya muguwar tsanar datayiwa AMAL IDON NERA ba, Ta tsaneta Haka kawai tsana Mai tsanani sbd ta lalata rayuwar gidan uncle SSG.
Haj Maryamah kuwa da aduk duniya idan akwai kalmar datafi tsana a fada gabanta to itace kalmar karuwanci,
Ta tsani kalmar sunan tsana mafi muni da qyama Wanda kusan kowa yasan hakan shiyasa shima Dr shaykh Aqeel ya tsani kalmar sunan a baya batareda yasan dalilinta na tsananta tsana da tsananta qyamar sunanba,
Ajiye wayarta tayi agefe tareda kallonsu daya bayan daya gabanta na Dan nauyi ganin yanda hankalinsu yayi masifar tashi gashi suna ambatar wannan munanniyar kalmar hadeda sunan AQEEL dinta.
Hannu takai a sanyaye ta dauki jairidar ta saukar da idonta akai tana kokarin nutsar da kanta ta karanta.
Jimmm tayi tana sake maimaita karanta kalmomin daya bayan daya bugun kirjinta na Dan sauyawa ahankali.
Sake kallon hotonsa dake kan jaridar tayi ta tabbatarda AQEEL ASAD dinne 'danta qwalli daya ake magana,
Komawa yayi tasake karanto zancen dalla dallah kusan so hudu...
Ahankali ta saukar da idonta akan lafiyayyan hoton Zainab dake gefe da 'yarta inda aka rubutasu da sunansu da manyan baqi.
Innalillahi wainna ilayhi rajiun Innalillahi wainna ilayhi rajiun
Balkees na ganin haka tasake shiga mummunan tashin hankali tafara nanata sunan IDON NERA a bakinta cikin rikicewa tana cewa"
Wayyo Ni Allah wace ranace wannan?? Innalillahi wainna ilayhi rajiun..
Miqewa Haj Maryamah tayi zata bar gurin sbd zuciyarta dake bugawa ba daidaiba Amma tana tsayuwa qafafunta suka kasa riqeta ta sulale zuciyarta na daukan wani irin nauyi da harbawa take BP dinta ya haye sama.
Kanta sukayo cikin tashin hankali da tsoro suna Kiran sunanta hankali tashe.
A office duk yanda yaso samun damar fitowa hakan Bai samuba saima wani babban abin daya taso Masa Dole zai tafi Abuja da yamman tareda baqin nasa.
Dole ya hakura da zuwa gidan Maminsa Amma gabaki daya hankalinsa nakan AMAL dayake buqatan gani Ido rufe sbd ya tabbatarda itace little MARYAMAH.
Labarin jaridar tuni ya yadu kamar wutar daji da kuwa tunda ya fito koina labaran akeyi,
Wayoyinsa Dole ya kashe sbd masu kiransa danjin idan bacin sunane a dauki mataki,
Baida abinda zai fadawa kowa ayanzu Dan Haka ya zabi yin shiru bazaice komaiba yanzu din.
Gida Kai tsaye ya wuce Dan daukan abubuwan dazai buqatan a kwana biyun dazaiyi Abujan ya dawo.
Yana Isa Kai tsaye Saida yaje ya hada karamar Louis Vuitton luggage ya miqawa malam Rabiu yasaka mota kafin ya nufi bangaren ummansa sbd yasan Bilkees na can.
Yana shiga yagansu hankalinsu kamar baa jikinsuba su dukan,
Qarasowa yayi cikin takun nutsuwa Yana kallon haj maryamah dake kallonsa cikin tashin hankali,tsoro,fargaba da babban tunanin Ina ya hadu Zainab,Kuma tun yaushe.
Kenan bayan tsawon shekaru yagano zainab din shine ya boye Mata?
Wace qaddarar ce wannan? Zainab tazama masifar rayuwarta.
Innalillahi wainna ilayhirrajiuni Tayaya zaace itace?
Rintse idanuwanta tayi tana cewa"
Ya Allah kada ka dawo da Zainab rayuwar tsaftataccen 'dana AQEEL,
Ya Allah ka hanasu sake haduwa sbd rayuwarsu ta bambamta,
Shi Mai tsaftane ya Allah,
Kowa yaje yayi rayuwarsa da abinda Allah yabasa 'dana mai tsarki itakuma 'yaya Masu daudar najazar uwa karuwa Wanda itama tanada tabbacin 'yar karuwace a yanzu...
IDON NERA??
Meya kawo sunan da ko tsarki da dadin ji da fada babu acikin rayuwarsu??
Da gaske
Shin Zainab dince ma idon nera kokuwa 'yarta data bar gida da ita kokuwa 'yar data haifa a karuwancin??
Mezaisa AQEEL ASAD dinta ya yarda ma ya kalli inda IDON NERA's din suke sbd tsananin taka tsantsan dinsa da kiyayewarsa ga kusantar qazanta??
Yasan Zainab itace idon neran shiyasa yaje kokuwa wata qaddarar ce takaisa har aka samu damar lalata mutuncinsa da sunansa..
Maganganunta dashine kadai yasan maanarsu yankar zuciyarsa sukeyi, Bayason tayarda duk wani zancen ayanzu sbd bazaiso Jin mummunan sunan akan Maminsa ba daga bakin kowaba a gida.
Yanayinta dayake tsanani yasashi kasa cewa komai suka dauketa zuwa asibiti sbd numfashin nata neman tsayawa yakeyi.
Bilkees ma neman sumewar takeyi sbd numfashinta dayake neman toshewa Dan Haka da taimakon mufeeda itama ta Dan samun riqe numfashin suka Isa asibitin da umma. ##MAMUH# #SISTERS#BLACK AND WHITE LOVE# LOVE/ROMANCE #HOTLOVE/MARRIAGE
*_ZAFAFA BIYAR_*
*RUMBUN K'AYA*π₯ Hafsat Rano
*DAUDAR GORA*π₯ Billyn Abdul
*IDON NERA*π₯ Mamuhgee
*A RUBUCE TAKE*π₯ Safiya huguma
*KI KULANI*π₯ Miss xoxo
Littafi daya---400 Biyu---600 Uku----800 Hudu-----1k Biyar din duka----1200
ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN
0022419171 Maryam sani Access bank
Shedarka ta 09033181070
MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN
09166221261
π³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺ *Ina yan uwa 'yan nijer?* *Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+22799643131
Littafi daya---450CFA biyu---650CFA uku----850CFA hudu----1050 CFA Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!* *Thanks for choosing us*π₯ *_ArewabooksMamuhgee_* 33 Suna Isa asibiti aka karbeta kasancewar tareda shine akazo asibitin take aka karbeta cikin gaggawa da kulawa..
Bp ne yayi sama sosai Dan Haka take suka fara Mata allurai da wasu daga cikin magunan dazai sauko dashi zuwa normal cikin gaggawa.
Zama yayi akan tattausan sofa kushin dake lafiyayyan Amenity room din tareda Dan rufe idanuwansa ya bude Yana sakin numfashi a ahankali.
Bilkees ce ta dawo gefensa ta tsaya idanuwanta gabaki daya sun canja Masifa da tashin hankali ne kawai ke Mata tsalle da rumfa tako Ina,
Dr menene abinda yake faruwa Ni kwata kwata bana gane komai A gurinka kawai zanji dalla dallah nagane me ake nufi?? Me Kuma yake faruwa??
Ni wlh halinda umma tashiga Wasa ne, Zan iya haukacewa Dr idan kacemun Dagaske kaje IDON NERA's,
Gawurtattun kar.....
Cikin wani mummunan kallon dayasata rikicewa ya dago ya kalleta gabaki daya annurin fuskarsa ya tashi daga damuwan halinda umma take ciki zuwa mummunan bacin Rai da fushi..
Ahankali ya bude Baki tareda dauke idonsa akanta yace,
"Sunan Idon Nera ma karki sake ambata a bakinki bare wani sunan daban" Dokace hade da umarnin..
Wani jiri ne ya dibeta sbd buguwar da zuciyarta tayi da karfi,
Muryarta na rawa ta qara matsowa gabansa sosai Wanda ya sashi sake kame fuskarsa batareda ya dago ya kalleta ba.,
"Banganeba, Na Dena fadan sunan sbd qazantars......
Miqewa yayi tareda rabata ya wuce sbd akwai mutane tako Ina asibitin da ake tsakanin ganin girmansa da mutuncinsa tareda girmamasa bazaiso Ransa ya baci ba a irin gurin.
Bin bayansa tayi da kallo tana qarasa firgicewa,
"Menene yake faruwa Wai ma tukuna??
Wlh Bata yardaba , Takasa yarda da Mijinta AQEEL ASAD guda zai iya ko kallon gidan Wainnan karuwan bare ya iya kusantarsu ya shiga,
Neman auren Hayat yaje kokuwa?
Rawa qafafunta suka farayi da sauri mufeeda ta qaraso itama a rude take da abinda keta Shirin faruwa su sunkasa gane komai.
Abu daya suka sani shine Daga Idon Nera din har 'yarta sunyi kadan su lalata musu farin ciki,
Idanma da gaske angansa dasu suka lalata auren SSG da Idon Nera din bare nata Mijin.
Motarsa ya Isa aka bude Masa yana shiga wayarsa tafara vibrating na baqin dake jiransa,
Dauka yayi yacewa Al-Amin baqin su wuce zai biyo flight din safiya da wuri insha Allah.
***Amal na Isa office din mommynta datake gudanar da harkokin businesses dinta apart from harkanta ta Daban da ake kira da karuwancin.
Ajiye jaridar tayi Kai tsaye gaban mommyn tana kallonta cikin Bata rai tace,
Mommy kina ganin alaqarki da wannan AQEEL ASAD din bazai kawo baci Rai da ninkin bacin sunaba akanki?
Mommy koma menene alaqarki dashi gabaki daya hakan Bai kwantamunba, Shi kansa Bai kwantamunba,
Meyasa Zaki ringa tattala duk wani zancenza saikace shi din yafi sauran abokanan kasuwancinki,
Mommy idan akwai wani alaqar daba business ba a tsakaninku inason sani sbd Shi kansa dabiarsa akanki tayi hannun Riga kwata kwata da sauran kowace dabiar.
Mommy......
Katse Haj Zainab tayi cikin kulawa da kwantar Mata da hankali tace,
"Amal breath please, Wannan rumours da bacin sunan ba yanzu aka fara ba,mun Saba,.ba komai bane, Banajin komai akan hakan, Damuwata dayace akaro nafarko akan irin wannan iskancin na Yan jarida shine sunan AQEEL ASAD dayake ciki,
Bantaba musantawa ko tankawa akan ire iren hakan sbd bana buqatan yiwa kowa bayanin halinda rayuwata take ciki Amma bazan iya Bari su Bata sunan AQEEL ba,
AQEEL ASAD shine Wanda raina zaiyi matukar baci idan suka lalata sunansa akan nawa sunan...
Mamakine ya sake shigar AMAL tana kallonta tace,
"Mommy?kinji abinda kike fada kuwa? Mutuncinsa yafi naki ne? Idanma sunansa ya baci shine ya kawo Kansa idan na tina,
Mommy please ki Dena fadan hakan kina sake sakamun zafinsa araina, Tayaya shi din yasamu wannan mahummancin a gurinki?
Yanda ran Amal din yake a cakude yasa mommyn kokarin danne nata bacin ran akan lamarin Amma bawai Dan nata sunanba sai Dan mutuncin AQEEL dinta dakuma uwa uba babbar rigimar da hakan zata bullo sbd wanan jaridar zata tabbatarwa da duk inda uwarsa da kakarsa suke cewan itada AQEEL sun dawo rayuwar juna kenan, Abinda Kuma ta guda din kenan sbd riqo da alqawarinta na cewan ta yanke duka wata alaqa dake tsakaninta dasu har abada Kuma tana Nan akan bakanta,
Idan Kuma suna Nan a yanda ta sansu to tabbas aduk inda suke zasu nemeta su sameta sbd isarda sakon zuciyarsu kaman Yanda suka Saba... Hakan na na nufin Amal da siddi zasusan su din su wanene,.abinda Basu taba tambaya daga garetaba bakuma su damu da tambayarba Koda su din shegu ne Basu damuba tunda uwar data haifesu din tana taredasu kamar yayan sunna.
Shirunta tareda zurfi cikin tinani yasa Amal zuba Mata fararen idanuwanta tana kallonta cikin mamaki,
Amma koma menene batajin zata dauki cin fuska da sabon bacin suna ga mahaifiyarta sbd itace duniyarta gabaki daya.
*****Awar Haj Maryamah hudu a asibitin BP dinta ya dawo daidai saidai zuciyarta takasa Dena bugawa da sauri bp dinma tasan ba jimawa zaiyiba zai ringa hawane Yana sauka sbd ita kadai tasan yanda zuciyarta take bugawa tareda kasa Jan numfashin nutsuwa.
Daga ita harsu Bilkees Babu Wanda yake cikakken hayyacinsa,
Ita Bilkees da mufeeda hoto ne kawai a kawo umma asibitin Dan kusan Bilkees din tafi kowa ficewa hayyacinta a tsaye kawai take Amma Sam Bata gane komai sai an maimaita Mata abinda aka fada din.,
Kallo daya Haj Maryamah tayiwa AQEEL ASAD din alokacinda ya shigo ta fahimci Babu wata magana dazai iya saurara akan Zainab,
Kamewar da yayiwa fuskarsa ce ta tabbatar Mata da abinda taketa qin yarda dinne dai ya tabbata wato Zainab dai tadawo rayuwarsa Kuma yana sane da abinda ya sakata cikin wanna halin kenan shiyasa yaqi Bata fuskar yin maganar....
Innalillahi wainna ilayhi rajiun,
Wace sabuwar masifar ce wannan,
A bayan ma da Zainab takeda tsarki Bata barta da 'danta ba Dan haka babu ta yanda zata bari 'danta ya sake ko kallon inda qazantarsu takeba bare ya kwaso najasarsu,
Bazata taba yarda wannan karon 'danta Mai tsarki tsarkakakke ya kusanci inda sukeba,
Kome zatai zatayi Amma wlh Zainab bazata dawo rayuwar 'dantaba itada 'yarta, Wannan karon kome na dukiyarta zata watsar akan 'danta ya tsaya gurinta bazai sake kallon zainab bama bare wata 'yarta wadda itama take baqin cikin fadar sunanta da aka sakawa 'yar gashinan ta qare a rayuwa irinta uwarta,
Sake kallon AQEEL din tayi idanuwanta da zuciyarta na sake daukan zafi da ciwo,
A natse cikin kamewa yagama tabbatarda Babu wata matsala zasu iya tafiya da umman gida.
Bilkees data gap da faduwa sbd tiririn da zuciyarta take ciki itada mufeeda,
Bata tafi gidaba itama saida aka duba bp dinta daya kusan haura 200 daqyar akai Mata controlling dinsa tayo gida a gigice saidai cikin rashin saa tana isowa akace AQEEL din yabi jirgin dare ya wuce Abuja.
Cikin tashin hankali ta kalli umma wadda itace ta matsa Masa akan ya tafi din taji sauki sbd tanada buqatan barinsa a garin na kwana biyu Dan tabbatarda abinda tasani,
Zainab tazama masifar rayuwarsu itada ummanta da 'danta,
Tayaya zata fuskanci wannan tashin hankalin dayake dawowa musu???
Bilkees data kasa gane kan umman ta qaraso gabanta hankali baa kwanceba tana jiran Jin ta bakin umman tukuna tasan ta inda zata fara da lamarin.
"Idon Nera" duk sunan ya fado a ransu sai anrasa tsakanin zuciyar haj Maryamah data Balkees wacce tafi girgiza dashiga mummunan yanayi,
Tashin hankali da rikicewar Balkees a zahirin bayyane yake ga duk Wanda ya ganta yasan tayi kololuwar fita hayyaci da tsananin kishi da tashin hankali akan lamarin tun lokacinda idonta ya kyallo jaridar,
Ga AQEEL ASAD din yaqi tanka kalma ko daya akan lamarin bare a bude zancen komai Susan matsayarsa saima kaman harda bayason zancen yasashi tafiya a Daren,
Idan AQEEL ASAD baiyi niyar magana akan abu ba Sam ko fuskar a tayarda zancen baya bayarwa Amma wannan ma yafi kowanne yanayin qin bada damar saima wata irin tsananin rashin bada Dama ko fuskar da zatai tashin hankali da aibata Idon nera,
Haj Maryamah kuwa sake juya zancen takeyi a ce Zainab idon Nera, qanwar mahaifiyarsa wadda itace yakewa kallon uwa sbd itace tasan wahala da dawainiya dashi tun Yana cikin mahaifiyarsa take dawainiya da wahala dasu harya fito duniya ta renesa tamkar itace ta haifesa haryayi girman dasuka rabu,
Itace macen da a duniyarsa mahaifiyarsa data haifesace kawai tafita haqqi akansa Amma shaquwa da kaunar zahirima tafi girma a tsakaninsa da ita, ta sadaukar da rayuwarta da kuruciyarta gabaki daya gurin kulawa dashi,
babban abin firgicin shine 'yarta daya a duniya itace wadda yakejin kamar yayi failing malaminsa akan rashinta,
Ko a cikin mafarki ne kunya,baqin ciki, takaici da qyamar fadan tasan Zainab ma zatayi bare a zahiri,
Duka wannan bayanin idan duniya taji mutuncin AQEEL dintane zai zube, Tayaya zata Bari asan alaqarsa da Zainab Idon Nera, Bazata yardaba.
Kwanan baqin ciki da zullumin tunani sukai aranar wadda sukaga safiya daqyar.
**** Haj Maryam kusan tafi Balkees shiga qunci da damuwa tareda baqin cikin bayyanuwar wannan Al'amarin sbd kaman 'dacin zuciyarta tun na quruciya ne yake Shirin dawowa idan bata datse wannan alqar tasuba da wuri,
Idanma 'yar Zainab dince IDON NERA duk baqin cikin daya ne sbd girman Zainab a zuciyan aqeel ganin takeyi ya wuce nata itada ta haifesa saidai batajin har abada zata iya karban Zainab da itace qurjin zuciyarta,
Aqeel tsarkakakke ne itakuma yanzu najaza ce abar qyama daga ita har 'yarta.... Babu ya yanda AQEEL zai iya ko kallon Zainab din bare dawo da matsayinta na uwa a zuciyarsa matuqar itace IDON NERA din Koda 'yarta ce IDON NERA AQEEL saiya qyamacesu..
Qarin abin kunya da baqin cikin da zubewar mutunci da darajarsu zai fara ne daga lokacinda duniya tasan ita din yayar Idon nera dince, Jininsu daya, Mutum daya ya haifesu..
Haka zalika girman MUHAMMAD AQEEL ASADULLAH a duniya zai rangwanta a idon mutane idan sukaji Karuwar da kowa yasani IDON NERA qanwar mahaifiyarsa ce, Jininsa ce, Marikiqiyarsa ce wadda yake Kira da uwa.
Babban tashin hankali da tsoronta yace zaiyi yunqurin dawo da Zainab rayuwarsu wadda AMAL IDON NERA itakuma itace babbar tashin hankali da masifar datake girgiza bilkees da duniyarta gabaki daya sbd daga lokacinda tasamu damar ganin hotunan IDON NERAs din a Media kiris ya hanata samun shanyewar rabin jiki badan mufeeda tayi gaggawar taimaka mataba.
Abinda ya sumar da Balkees shine bayan gama qarewa hotunan haj IDON NERA kallo shine Ido biyu da hoton AMAL Idon Nera wadda duniya ta shedar da mutuwar so datakewa mahaifiyarta haj Zainab Idon Nera.
Ganin Amal yasa bilkees daga kwanciyar hankalin gidan gabaki daya akan lamarin sbd son sanin asalin meke faruwa...
Haka zalika batajin ko gida jaridar daya wallafa wannan jaridar zata qyalesu mataki zata dauka tako Ina sbd ko wannan qazamtaccen zancen Adena yadawa bare wani abin ya biyo baya,
Dan Koda zata rasa komai da kowa a duniyarta bazata taba yarda asake hada sunan tsarkakken sunan mijintaba da sunan IDON NERA Koda uwar Koda 'yar. ##MAMUH#
ZAFAFA BIYAR 2023
*RUMBUN K'AYA*π₯
*DAUDAR GORA*π₯
*IDON NERA*π₯
*A RUBUCE TAKE*π₯
*KI KULANI*π₯
*_uhmmmm_*ππππππππππ
*Nasan zakuce ya da murmushi haka?*
*Wanda bai shigo ba bazai gane ba*
*Sai kin shigo daga ciki zaki gane me nake nufi*βΊοΈβΊοΈ
*KE DAGA JIN SUNAYEN LITATTAFAN MA KADAI KASAN CEWA AKWAI WANI BABBAN ABU MAI MATUQAR JAN HAKALI TATTARE DASU*
*KINA NEMAN INDA ZAKI HUTAR DA KWANYARKI?*
*KI SAMU ZUNZURUTUN NISHADI DA ILIMI?*
Littafi daya---400 Biyu---600 Uku----800 Hudu-----1k Biyar din duka----1200
*ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN KI ANTAYA JIRGIN FITON ZAFAFA BIYAR*π₯π₯π₯π₯π₯
0022419171 Maryam sani Access bank
*MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN*
09166221261
π³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺ *Ina yan uwa 'yan nijer?* *Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+22799643131
Littafi daya---450CFA biyu---650CFA uku----850CFA hudu----1050 CFA Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!* *SIYAN NA GARI KUMA MAIDA KUDI GIDA!* *_Arewabooke@Mamuhgee_* 34 Wayar umma Haj Maryamah ta Kira Saida takusa katsewa umman ta dauka,
Wani irin kukan da Bata taba fashewa dashiba ta fashewa umman dashi zuciyarta na tafarfasar da kunci da bacin Rai harma da baqin ciki.,
Zaune umma ta tashi daga kwacen datake akan doguwar kujerar dakinta ta hutawa hankalinta na tashi Dan Bata taba jin kukan Maryamah dinta ba tun bayan rasuwar Mijinta na farko, Ko mijita na biyun daya rasu batai wani kukaba saidai hawaye Amma yau din lamari ya girmama,
Maryamah?? Lafiya? Waye ya rasu? Ina AQEEL lafiyansa kalau kuwa? Ya matarsa da 'yarsa Suma lfy dai?? Meyene ya faru gayamun kafin hawan jinina yayi sama.
Kasa magana Haj Maryamah tayi sabd takasa riqe kukanta akan Zainab datake riqewa shekaru, Yau tasamu abinda yake makoshinta akanta ya fashe shiyasa kukan yakasa tsayuwa.
Kukane takeyi dayake fitowa can qasan zuciyarta da ranta,
Umma daga zaunen qarasa miqewa tsaye tayi tana sake ambatar sunan maryamah din hankalinta na tashi.
Saida tasamu ta danne zuciyarta ta cusawa kanta dauriya da taurin Rai kafin ta share hawatenta da tissue ta sauke ajiyar zuciya ahankali tukuna ta bude baki tareda Dan gyara muryanta datayi nauyi takoma daidai ranta na quna tace,
"Umma Zainab tadawo rayuwar AQEEL, AQEEL yaga Zainab da 'yarta, Zasu Bata suna da mutuncinsa a Idon duniya, Zainab magajiyan k.....umma Ni bama Zan iya fadan qazantaccen sunan da bakina Mai tsafta ba..
Umma AQEEL zai koma gurinta ya sake juyamun baya,
Me nayiwa Zainab data zabi shiga tsakaninsa da rabani da 'dana daya danake dashi a duniya??
Umma wannan karon wlh bazan iya daukaba......
Zama umma tayi a hankali tana shiga nata mamaki da tashin hankalin itama sbd abune da Bata taba kawo tunanin shine zaa fada ba wato dawowar Zainab rayuwarsu,
Tun tana qaramar karuwarta sun samu sun yakiceta sun rabu da ita rayuwarsu ta huta sai yanzu zata dawo rayuwar 'dansu tana shahararriyar karuwa, Me take nufi da hakan?
Rayuwar ta bare Mata ne kokuwa?
Cin mutuncinsu da barnar suna zatai musu kome?
Baqin ciki da damuwa zata dawo musu dashi bayan sun samu nutsuwa da salama tareda dangana ya shiga AQEEL ASAD baya rashinta shine yanzu tunda ya zama babban mutum Mai fada aji zata bullo Dan tozartasu da kawo musu sabuwar masifa...
Wani 'daci ta hadiye a makoshinta bayan Haj Maryamah ta zayyana Mata komai na bayyanar Zainab harma da yarta..
IDON NERA??" itama ta mamaita sunan a bakinta tana Jin ranta na tsananta soyuwa da bacin Rai da tashin hankali...