Kenza eBookz

Kamar da wasa complete novel - Chapter 33

Kamar da wasa complete novel - Chapter 33

Kamar da wasa complete novel Chapter 33: Kamar da wasa complete novel Chapter 33. Duk da wannan maganganun da yayi mata bata yarda ba azatonta wai barazana…

3,116 words

Duk da wannan maganganun da yayi mata bata yarda ba azatonta wai barazana ce yayi mata shiyasa taci gaba da yi masa maganar itafa zubar da cikin nan zatayi ji yayi gaba daya auren yafita akansa daga bilkisun har asma'un fushi yake dasu saboda kowaccensu mai laifice awajensa, ita kuma husnah kishi da rashin wayo yarufe mata ido takasa ganin sudden changes din dake tattare da bilkisu itafa kawai idonta yarufe gani take bilkisu da biyu taki haihuwa saboda karta tsufa irin rashin dabarar da matan yanzu keyi wai aki haihuwa gudun kada atsufa. Ranar laraba yazo kano kuma aranar yake son komawa daga bilkisun har husnah sama sama yagaisa dasu dan ita bilkisu ma ko ganinsa bata yiba tana can wurin aiki sai awaya yakirata, ita kuma husnah tana gida, shi baida dabi'ar binciken wayar mutane amma yau yayi akan husnah saboda yana zargin kamar zugata kawayenta keyi ai kuwa zarginshi yazama gaskiya dan yaga chat dinsu da Fa'iza tana tambayarta wai cikin yazube tace a'a wannan maganin baiyi mata aikiba sai ciwon mara da yasata shine fa'iza ta tura mata sunan wani wai ta gwadashi mana yafi wancan karfi, ranar husnah ta raina kanta domin yi yayi kamar zai dafata yacinye nama danye saboda masifa daga karshe yace wallahi idan ta zubar da cikin nan abakin aurenta kuma kar su Ruky da Fa'iza su kara zuwar masa gida, da bacin rai yakoma kaduna itama bilkisu fushin take yi akan nada wai yazo ko yaje yaganta yayi tafiyarsa, washe gari da rana ya kirata wai dan Allah tayi masa taimako duk ranar da kawayen husnah sukazo ta fada masa da to ta amsa masa amma acikin zuciyarta tace babu ruwanta bazata zama munafuka ba. Bilkisu fa kiba kullum karuwa takeyi ga haske sannan fatarta har wani kyalli da sheki takeyi yanzu duk kayanta dakyar suke shigarta tun bata daukar maganar khulsum dagaske na wai cikine da ita har tafara dauka dan taji period dinta shiru gashi har pad tasiyo guda biyu ta ajiye amma kemadagas yaki zuwa gabanta ne yafara faduwa wanda sam bata San dalili ba, acikin satin fahad yazo nan dinma aranar zai koma fada sukayi kaca kaca da husnah akan cikin nan bilkisu na jinsu kamar zai doki husnah tsabar ransa yabaci bai ko yiwa bilkisu sallama ba yayi tafiyarsa abinda yasake kular da ita kenan, yana tafiya husnah ta aiwatar da kudurinta ta zubar da cikin ai kuwa tasha wuya kamar zata mutu dan azaba, ranar friday sai gashi lokacin husnah bata gama warwarewa ba daga ta'asar da tayi shiyasa yayi saurin ganewa tun kafin ya tambayeta tafara shirya masa karya wai kawai mafarki tayi wata mata mai kamada bilkisu tana dukan cikinta da tabarya tana farkawa taji tana bleeding sai kuma ciwo yasata agaba, fada fahad yashiga surfawa yana cewa kar ta yarda tasaka bilkisu cikin shirmenta ta hada kayanta tatafi gidansu shi yagaji da wannan masifar tata ai dama yafada mata karta zubar da cikin nan amma saida ta zubar. Bilkisu na daki tana jinsu amma bata fitoba saboda ba asata cikiba kar ace munafurci ne, aranar itama tayi gwaji da pt strip din da tasiyo tun kwanaki biyu da suka wuce amma tsoro yahanata yi, tun agwajin farko yanuna mata ciki baro baro, rufe baki tayi tana mamakin to meyasa takasa ganewa tun farko? Yanzu shikenan tayi abun kunya wai itace dauke da cikin fahad ajikinta to ko itama zubarwar zatayi? Masifar da yayita yiwa husnah ce tafado mata nan tsoro yashigeta to ai ko babu komai ma lokacine yayi wanda zata nunawa husnah cewa ita ba juya bace sannan babu abinda yasamu mahaifarta ras take tunda gashi tadau ciki. Duk da cewa husnah ta tafi yaki sakar mata fuska dan tun lokacin da ya bukaceta tahanashi yake fushi ita kuma yanzu tun ranar da tayi pregnancy test dinnan take jin wata matsananciyar bukatarshi kamar me amma ko cikin dakin nata bai kwanaba afalo ya kwana haka yabarta da juye juye da kwalla kun san mai ciki idan taso abu bata samuba.....

*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:22] Hafsat Rano: *Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*

55****Washe gari da safe tana jinsa afalo yana harkar dake gabansa ahaka ta tashi tayi wanka ta dan shirya sannan tasake kwanciya cikin net,har wurin 9 sannan yashigo cikin dakin kai tsaye bathroom yawuce yaje yayi wanka yafito tana nan dai inda yabarta kwance tana satar kallonshi, ganin bai san tanayi ba yasata maida kallon nata gaba daya kansa, koda wasa ita bata taba zaton zata tsinci kanta cikin wannan yanayin ba wai yau itace ke yiwa fahad kallo na daban lumshe idanuwanta tayi wadanda kasala ta cikasu, tana ganinshi ya kammala shiryawa yasa dogayen kaya kalar ruwan siminti yana kokarin fesa turare yaji atishawar ta, juyawa yayi ya kalleta,

"Sannu.... Ko mura kikeyi ne?"

Jijjiga kai tayi idanuwanta na taruwa da kwalla,

"Ayya sorry...., idan zan dawo zan taho miki da magani"

Batayi magana ba taci gaba da binsa da kallo ji take kamar ta janyoshi amma bazata iyaba, har yakarasa shiryawarsa ya juyo ya kalleta batayi motsi ba,

"Ni na fita... Akwai wani abune?"

Shiru tayi masa tana matse kwallarta,

"Wai meyake faruwa ne? Ke kam sai kace dan ke kadai aka halacci kuka? Haba bakida aiki sai koke koke.... Dan Allah kirage yawan kukan nan....."

Tashi zaune tayi tana kallonsa amma batayi magana ba,

"Bari naje shago.... Nadawo aljihu na babu nauyi ne duk na kashe kudadena wallahi....."

Juyawa yayi yafita jin batace komai ba yana fita ta rafka tagumi tana shafar cikinta da hannunta guda daya, tunani take yi kila abinda ke cikinta mace ce kila kuma namiji ne, ohh Allah mai iko shi kadai yasani, tashi tayi tafita ta shiga kitchen domin dafaffen kwai take son ci, bayan ta dafa tafito tana kallon dakin husnah kwana biyu duk sai take jin gidan yayi shiru da yawa da husnah bata nan yanzu da ace tana nan tasan tana nan tana aikin yar mata da magana, har zata zauna tajiyo karar wayarta, ciki takoma ta dauko wayar tafito ta daga sannan ta nemi wuri ta zauna,

"Labour wai yau baki zuwa aikine? Waye kika ajiye wanda zaiyi miki voicing din labaran rana?"

"Haba kawata dama fa ina nemanki yanzu nake shirin kiranki.... Yau bazan shigoba bana jin dadi"

"To wallahi ki zo dai ki karanta labaranki domin yau copers din da kika saba jibgawa aikinki suyi miki duk basu zo ba..... Nikuma kinga ni nayi nasafe bazai yuyu asake jin muryata a na rana ba MD zaiyi magana"

"Dan Allah kawata kiyi min wallahi ina cikin matsala ne bazan iya zuwaba dama kuma ina nemanki fa.... Ina son mu tattauna"

"Shikenan Allah yakara sauki, wasa nake yimiki zanyi miki news din, anjima idan natashi zan shigo...."

Sallama sukayi ta dan kishingida tana bare kwan da ta dafa guda uku, daga karshe wai ta dan kunna kallo ko zata debe kewa. K'arfe biyu saura khulsum ta karaso gidan lokacin bilkisu na kwance kan kujera, zama khulsum tayi tana cemata,

"Bani abinci yunwa nakeji..."

"Ai kuwa sai dai kisha tea dan ban girka komai ba, bana jin sha'awar girki wallahi"

"To shikuma fa?"

"Shima tea din yasha kadai yafita"

Dariya khulsum tayi,

"Kina shagalinki kawata, wato girkima sai kin gadama zakiyi, koda yake bake kadai bace ai..."

"Nida waye da?"

"Au ina kanwar taki?"

Yamutsa fuska bilkisu tayi sannan tace,

"Bata nanfa kwana biyu, amma may be zata dawo... Ke ni ba wannan ba dan Allah shawara nake so kibani...."

"Allah yasa zan iya labour... Meya faru?"

Dan shiru tayi na wasu sakanni sannan tace,

"Kinga wannan cikin da wata dabi'a yazo min wallahi.... Wai karfi da yaji kulawar fahad nake nema"

"Banfa ganeba.... Yimin gwari gwari"

Harararta tayi sannan tace,

"Ina nufin ina bukatar mijina, shikuma fushi yake tayi akan last time da yazo na hanashi kaina saboda munafurtata yayi.... Dan Allah tawacce hanya zan janyo ra'ayinshi batare da yagane ba...."

Khulsum najin haka me zatayi inba dariya ba, dariya tafara yi harda buga kafa akasa,cikin jin haushi bilkisu tace,

"Ya ina yimiki serious magana amma kina nema ki mayar da ita abun dariya?, dagaske fa nake yimiki..."

"Kin san me yabani dariya? Zamanku da fahad na burgeni, ke son girma shikuma Jan aji.... Labour kenan wallahi Allah ne ya kamaki, kin tuna lokacin bikinku, cewa fa kikayi ni yaron nan da yadage sai ya aurene me zai bani idan munyi auren?, wai ma tsaya idan aka ajiye masa ni ta ina zai fara?, yaron da ko gama balaga baiyi ba...."

"Dan Allah ni ya isheni, yanzu dai zaki bani shawara ko dariyar zaki cigaba da yimin? Kin dai san bani kadai bace cikina zai iya samun matsala idan har bai samu abinda yake bukata ba...."

Shiru khulsum tayi ta daina dariyar da takeyi,

"Kin san me labour? Ai ke yakamata kisan hanyar da zaki bi wurin janyo hankalinsa saboda kinga kowanne namiji akwai ta inda ake kamashi.... Wani ta girki, wani ta kwalliya, wani ta magana, wani ta kamshi ma kawai zai zo hannu... Yanda maza suke kala kala haka hanyoyin kamasu ma yake kala kala.....amma ke me mijinki yafi so?"

"Shima yana son abinci kuma gaskiya yanada son kamshi...."

Tsaki khulsum tayi sannan tace,

"Ashe ke da kin san ma abubuwan da yafiso shine bakiyi ba? To yanzu tashi zakiyi ki shirya masa lafiyayyen abinci sannan ki turare gidanki da dakinki da ke kanki da kamshi kinga yana dawowa sai kuyi evening show kawai...."

Dariya bilkisu tayi cikin murna tace,

"Yawwa mutuniyas kokefa.... Nagode bari natashi nabada himma...."

"Yakamata kam, yau dai ga ranar yaro tazo...."

Daga haka ta sabi jakarta tafita tana dariya. Bilkisu zagewa tayi ta gyara gidan tsaf ta turareshi da turaren wuta da freshener mai sanyin kamshi, shi kansa bedroom din ma yadda ta gyarashi abin kallo ne tasaka wani bedsheet pink colour da zanen heart atsakiya abin gwanin burgewa sannan ta danyi kwalliya da net din dake makale jikin gadon ta tattare shi yabada design mai kyau sannan gefe daya ga turaren wuta na stick mai masifar kamshi yana ci sai hayaki mai kamshine yake tashi ahankali. Ita kanta yau kwalliya taci cikin materia red colour dinkin gown gefe daya ta shirya lafiyayyen girkinta soyayyiyar shinkafa da salad kawai fahad take jira. Tana kwance kan doguwar kujera tana kallon wani film atashar African magic mai suna things i hate about you fahad yashigo, fuskarshi babu yabo babu fallasa ya nemi wuri ya zauna yana kallonta, matar nan fa dagaske kiba take hadawa bata wasaba,

"Sannu da zuwa...." Tafada idonta nakan tv amma fuskarta asake take sosai wanda har hakan yaso bashi mamaki, cikin basarwa yace,

"Yawwa ranki yadade...."

"Ga abinci can fa..."

"Ok sannu da kokari bari na dan watsa ruwa tukunna..."

Daga haka yamike yawuce ciki nan tabishi da kallon sha'awa tana jin kamar tabishi, tana nan zaune yafito sanye da kananan kaya dukansu bakake daga rigar har wandon hannunsa rikeda p cap, wani bala'in kyau taga yayi mata ba kadanba bata taba sanin cewa fahad kyakkyawa bane sai yau,kallonshi kawai ta zauna tana yi sai take ganin kamar ma da biyu yake yimata wannan yangar da jan class din domin sai wani yatsine yatsine yakeyi kamar mace, da yake yau acikin shaukinsa take shiyasa take ganin komai nasa yau kyau yake yimata yana burgeta. Tana zaune tanata aikin satar kallonshi yagama cin abincin yamike yana kallonta shi fa yau yakula da fara'a ta tashi amma baisan dalili ba,

"Zan fita...."

Taji yafada, ji tayi kamar ta dora hannu aka tafasa ihu dan tsabar haushi, batayi masa magana ba yasa kai zai fice har yaje bakin kofa taji yajuyo yace,

"Amm namanta..., gaskiya yau dakinki yayi kyau.... Da ke dinma kanki, style din da aka yiwa dakin is something amazing..... I like ur style hajjaju..."

Daga haka yafice daga cikin falon, tana jin alamun tafiyarshi tafara kwalla, cikeda damuwa da bacin rai takira khulsum tana fada mata, dariya khulsum tayi sannan tace,

"Ohh my God.... What a funny.... Wato darling fahad yagano mu shine bazai bada kai bori yahau da wuriba har sai yabamu wahala? To inyasan wata ai bai san wata ba.... Bari inyi miki text, insha Allah bazai tsallake wannan tarkon namu ba"

"Are you sure...?" Inji bilkisu,

"Am 100% sure dear... Kijirani yanzu"

Daga haka takatse wayar tana jiran text din khulsum babu jimawa kuwa saiga text din yashigo, murmushi bilkisu tayi tana bawa kanta tabbacin zatayi fiyeda yadda khulsum ta shirya mata.

Har karfe 9 fahad bai dawoba sai wurin 9:30 sannan taji shigowarshi, tana kwance cikin net a kunnenta yashiga wanka yafito sannan yafita falo daga shi sai short nicker wanda tabada tabbacin abinci yaje yaci, yana shigowa yaji kamar nishin bilkisu da sauri yanufi gadon, kwance yaganta shame shame tanata faman sakin wahalallen nishi cikin wata atamfarta dinkin riga da skirt gaba daya kayan sun matseta sosai, dagota yayi yana tambayarta cikin rudewa,

"Bilkisu menene? Meke faruwa...?"

Kirjinta ta nuna masa da hannunta alamun ciwo yake yimata,

"Ciwon kirji kikeyi?"

Kai ta daga masa tana sake dago kirjinta tana sakin nishi, gaba dayanta ya dauketa ya saka ajikinshi yana cewa,

"Ai dolema dama kiyi ciwon kirji... Kallifa yanda kayan nan suka matse ki...., bari acire kawai"

Runtse idanuwanta tayi tana sake sakin wani nishin kamar gaske dan sai ka rantse da Allah ciwon takeyi irin sosai dinnan, baiyi wata wata ba yazuge zip din rigar yacire sannan yazuge na skirt din shima yacire shi kamar yadda yayi expecting daga ita sai pant yarasa meyasa bilkisu bata shiri da bra kamar wacce take mintsininta, kasa kawar da kansa yayi yadai yi kasa da murya yana cewa,

"Zaki sha maganine infita insamo miki?"

Kai ta girgiza masa cikin dakiya da muryar wahalar ciwo tace,

"A'a.... Kayi massaging dina may be i will be ok...."

Babu bata lokaci yafara abinda tace amma kuma bai dade da farawar ba shi kansa yaji al'amarin yafi karfin daurewa irin tashi shiyasa kafin ya farga har yasoma shiga cikin wani yanayi, daga shi har ita yau kowa yabaje basirarsa wurin kulawa da dan uwansa da samar masa da nutsuwa, bilkisu kam kasa kallonsa tayi daga karshe ma ta tsiri baccin karya tana jinsa yana yimata magana akan tatashi tayi wanka amma tayi shiru. Yau kam tayi baccinta cikin nutsuwa domin tasamu abinda take muradi dan ko juyi batayi ba saida asubah tayi sannan fahad yatasheta, wanka tayi tai salla shikuma fahad yafita masallaci, abin mamaki lokacin da yadawo kwance ya isketa kan rug din salla tana faman haki da nishi kamar wacce tayi race, yanzunma abinda yafaru daren jiya shine yasake faruwa, shar da ita ta shirya ta shiga cikin kitchen bayan takashe kan 80,tana tsaka da soya doya fahad yafito cikin shirinsa, manyan kaya yasaka shadda ash colour amma babu hula, a kofar kitchen din yatsaya yana dan kasa da idanuwanshi, daga ita harshi kunyar juna sukeji ta lura,

"Good morning sweetheart...."

Taji yafada ahankali,

"Morning, how was your night....."

Jin abinda tace yasashi dan murmushi yana shafa keya,

"It was amazing....."

Shiru tayi tana dan murmushi batareda ta kalleshi ba,

"Yanaga kafito bayan gashi ina preparing break fast?"

Dan satar kallonta yayi suka hada ido,

"Ni ai azumi nake...."

Dariya abinda taji yafada tayi tajuya ta kalleshi,

"Dama ana daukar azumi bayan alfijir ya keto?, malam bakada azumi kawai katsaya kayi breakfast"

Murmushi yayi ya karasa shiga cikin kitchen din yatsaya abayanta yana taimaka mata, tare suka zauna sukayi breakfast din sannan yafita, tun da tasamu wannan dabarar shikenan kullum da ita take aiki babu dare babu asubah sannan babu rana sai yanzu take gasgata maganar khulsum da take cemata itafa ta godewa Allah da tasamu yaro sharaf ta aura wallahi zataji dadi domin duk lokacin da take son kasancewa dashi zai saurareta kuma bazai kosaba amma manyan mutane sai ahankali ga shekaru ga basir duk yagama dasu, yanzu kam ta yarda 100% auren yaro akwai advantage aciki kamar yadda shima auren babban akwai nasa advantage din. Koda fahad yakoma makaranta ma baya sati daya baizo gidaba saboda Bilkisu domin baya son ta bukaci wani abu shikuma baya nan, kullum yana hanyar kano wani abun mamaki har lokacin shi bai san ciki gareta ba. Ranar da yayi wani zuwa da yamma yan uwan husna sukazo suka kwashe kayanta ita bilkisu ma lokacin bata nan tana wurin aiki saida tadawo ta iske falon yayi wani fadi duk sai taji babu dadi, fahad ta kalla wanda ke aikin goge mata tiles din dake cikin falon saboda yau haka tafita bata dauke ko tsinke acikin gidanba,

"Wai bazaka dawo da husna ba kenan? Haba kai kuwa anayin fa fiyeda hakama kuma adawo ashirya.... Dan Allah kaje ka dawo da ita..."

"Bakiga laifin da tayi min bane?, to be honest with you, she highly disappointed me and ban jin zan sake zama da ita gaskiya...."

"Duk da haka u have to be patient... U have to forgive her... Remember bature yace without sins there is no forgiveness.... Dan Allah kayafe mata..."

Tsayawa kawai yayi yana kallonta, zuwa can yanisa yace,

"Ai yanzu ba laifina bane, itace lokacin da taje gida ta hada karya da kareraye ta fadawa mahaifinta shikuma yayi fushi akan wai zaluntar yarsa nakeyi dan haka tagama zaman aure dani.... Kin gani da ace time din ta fadi gaskiyar abinda yafaru may be idan aka bani hakuri bayan na huce zan iya dawo da ita amma sai taje ta harhada karya ta fada.... Gashi dai tana sona tana son zama dani har gobe amma babu hali.... Aurena da husna kawai mubarshi a matsayin kaddara"

"Allah yasa hakane yafi zama alkhairi...."

Daga haka ta mike tashiga bedroom din tausayi taji yabata saboda ganin yanda ya gyara dakin ya kintsa komai harda su turaren wuta, gaskiya fahad abokin rayuwa ne yanada halin manya komai nagidan yayi mata harda su wanke wanke, washe garin ranar yaje yasiyo babbar katifa mai round kamar gado yasaka adakin husnah ai bilkisu nagani tafara daure dauren fuska wato raba daki zaiyi da ita da zai wani kama yasiyo katifa? Wallahi bazai yuyu ba ai kuwa bai yuyunba, kwanansa biyu yakoma Kaduna bai dawoba sai ranar da ake sunan matar ya Abba wato nusaiba wacce ta haifi yaronta namiji, kasancewar exam yakeyi saida ya dan samu interval sannan yadawo gida sai ranar yasan bilkisu nada ciki saboda cikin yafito sosai ita kuma tasake kiba tubarkalla gaba daya kayanta sunki shiga dan dakyar tasamu doguwar rigar da ta shigeta, bra kuwa duk sunyi mata kadan sai wata kwaya daya itace take iya sawa itama tana dawowa zata figeta ta yar,

"Wannan rigar ai ta matseki..."

Cikin jin haushi ta kalleshi,

"To ya zanyi? Kana ganima ahakanma ita kadaice ta shiga jikina"

"Allah yabaki hakuri, fito mutafi"

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull