Kenza eBookz

Kanwar matata complete - Chapter 17

Kanwar matata complete - Chapter 17

Kanwar matata complete Chapter 17: Kanwar matata complete Chapter 17. Da sauri Sarah ta ƙariso wajen tana faɗin, "Lah, Ai'n kece? Shigo mana kin tsaya a…

3,591 words

Da sauri Sarah ta ƙariso wajen tana faɗin, "Lah, Ai'n kece? Shigo mana kin tsaya a waje kamar baƙuwa. Ke ɗaya ce?" Hanya Khalil ya bata ta shigo tare da faɗin, "Bamu san da zuwanki ba, ashe kina tafe" kai tsaye yayi maganar don har ga Allah bai so zuwanta ba don zata shiga haƙƙinsa na rashin bashi damar kasancewa da matarsa. Da kallo ta bishi tana ji kamar rungumesa saboda ƙaunarsa dake fuzgarta. Shi kuwa Khalil komawa yayi ya zauna tare da ɗaukar remote ya kunna tv ya ɗaura ƙafa ɗaya akan ɗaya. "Ai'n mai zaki ci? Ki zauna mana." Wani kallo Khalil ya watsawa Ai'n ɗin tare da maida kallonsa izuwa ga Sarah yace, "Babe, ba girkin da za kiyi, saboda ban so kiyi stressing kanki shiyasa na fita da kaina na haɗa maki breakfast. Ohh nama manta, akwai sauran abincin da Aunty Maryam ta aiko mana dashi gashi can a dining. She should go and serve herself kamun mu dawo daga cikin gida wajen hajiya. Let go wife!" Ya faɗi hakan tare da kama hannun Sarah ya saka cikin nashi. Kallonta Sarah tayi tare da faɗin, "Aina'u bari muje mu dawo. Hajiya zanje na gaisar in dawo yanzu." Yaƙe tayi tare da faɗin, "Ok sai kun dawo." Suna fita Khalil ya saki tsaki tare da faɗin, "Killjoy?" "Wa?" Sarah ta tambaya tana kallonsa. "Ƙanwarki mana. Bata iya zuwa gidan amare ba. Ita da ake bari sai irin bayan sati biyun nan, duba fa ki gani ko 12:00 bai yi ba. Ni dai wallahi an shiga haƙƙina. Ɗaukar hutun wata guda nayi domin in huta tare da matata, amma naga alama ana son hanani more amarcina." Tsungulinsa tayi a hannu har sai da ya furta, "Auch! Mai nayi maki?" "Duk fa wanda zai zo ba kwana zai yi ba, dole zai tafi ya bar mu tare, to menene abun damuwar bayan we will always sleep together babu mai raba mu?" Cak ya tsaya yana kallonta tare da faɗin, "Haba, dagaske? Za ki biyani duk bashin soyayyar da aka hanani nunawa da ranar?" Dukan kafaɗunsa tayi tare da faɗin, "Wallahi happiness kana da negative mind. Ni ba abunda nake nufi kenan ba." "To ni kuma kinga abunda nake nufi kenan." Faɗin Khalil. Da sauri tayi gaba saboda kunyar da ya bata. Haɗawa yayi da gudu ya isketa tare da faɗin, "Yarinya kina da aiki, wai kunyata kike ji? Taɓ, kina ruwa can gaban breaker." Cak ta tsaya kasancewar sun iso daidai ƙofar part ɗin Hajiya. Shi ya ƙarisa tare da murɗa handle ɗin ƙofar ya shiga bakinsa ɗauke da sallama. Gaba ɗayansu suna parlour ana hira, Hajiya, yaya Abdul-Hakeem, yaya Muhammad Kabir, Aunty Maryam, aunty Khairat, aunty Zakiyyah matar yaya Abdullahi, Nafeesa, Aysha, Laure, Aunty Jamila autarsu uncle Ameeru, sai ƴaƴansu da kuma kaɗan daga cikin sauran mutanen Maiduguri da basu koma ba. Juyawa Khalil yayi tare da faɗin, "Babe, shigo mana." Da sauri Aunty Khairat ta tsunguli aunty Maryam jin sunan da Khalil ya kira Sarah dashi suka bushe da dariya. Ita kuwa Sarah a kunyace ta shigo ɗakin kanta na kallon ƙasa ƙafafuwanta na harɗewa. Har ƙasa ta duƙa tare da faɗin, "Hajiya ina kwana?" Da murmushi a fuskar hajiya ta amsa tare da faɗin, "Zo taho nan kinji ƴata." Zama tayi kusa da ƙafafun Hajiya a kan capet sannan tabi kowa ɗaya bayan ɗaya ta gaida su, kowa ya amsa fuska cike da fara'a babu nuna wani kyara ko wulaƙanci. Khalil ɗin ma gaida waɗanda suka girme shi yayi, wanda ya girma kuma suka gaida shi. "Yayanmu ka iya zaɓe fa wallahi." Faɗin Nafeesa tana ƙara leƙo fuskan Sarah. "Kun san ni komai nawa mai kyau ne shiyasa matata sai da na hanga na waiga na zaɓota zuƙeƙiya gata nan." Aunty Zakiyyah matar ya Abdullahi tace, "Gaskiya Ibrahim baka da kunya, a gaban yayyin naka nake irin wannan magana haka." "To Aunty kuma ni mai nace? Yabon matata fa kawai nayi." Faɗin Khalil yana dariya. "Wai, Hajiya sai kinyi haƙuri don zaki ga rawar kai!" Gaba ɗaya aka kwashe da dariya. Saukowa ƙasa Khalil yayi tare da zama daidai inda Sarah take sannan yace, "Wife, na san baki san kowa a nan wajen ba idan aka cire Laure da tazo ɗakinmu ɗazu. Bari na fara ta kan wannan babbar aunty, (yayi nuni zuwa ga Aunty Zakiyyah), ita ce matar babban wanmu, sojane a Abuja yake aiki. Lokacin da papa yake dai rai, we all are living there duk dani zaman na hutune don a abroad nayi rayuwata kaf, Hajiya ce ta matsa na dawo saboda Allah ya rubuta sai na haɗu dake mun ƙunla alaƙa mai girma. Last year suka aurar da second daughter ɗinsu mai sunan Hajiya ana kiranta little hajjaju, very smart girl don ni ta biyo a kwakwalwa." "Ai ka san mu duka kwakwalan tunkiyoyi gare mu sai kai ɗan gwal" Faɗin yaya barrister. Waro idanu Khalil yayi tare da faɗin, "Ni ba haka nake nufi ba. Mine saurareni kiji." Ya ƙarisa maganar yana kallon Sarah, "Wannan sunansa ya Abdul-Hakeem, wannan itace matarsa Aunty Maryam wacce ta aiko mana da breakfast ɗazu, ƴarsu ɗaya Maimoon... Wannan kuma shine ya barrister, shi kuma kin ga matarsa nan, sunanta Aunty Khairat, ƴaƴansu biyu...." Haka ya dunga nuna mutanan parlour ɗin yana mata bayani. Ita dai kai kawai take ɗaga masa. Yanda aka amsheta kowa na nan-nan da ita ya saka ta mance da wata Aina'u. Shikuwa Khalil yana sane, addu'a kawai yake yi cikin zuciyarsa Allah yasa ta gaji da jira ta wuce gida. Ɓangaren Aina'u kuwa, bayan fitarsu babu inda bata buɗe ta duba ba, sai faɗin, "Kan bala'iiii!" Kawai take yi tana kwafa. Sai da ta gama tsaf sannan ta dawo parlour ta zauna a kan kujera tana girgije-girgije ƙafa, "Wallahi in har sunana Aina'u ɗiyar Lami da Nuhu, wallahi tallahi ba zan taɓa bari kiyi farin ciki ba, ba dai anyi auren ba, enjoy the first week of your marriage before the war begins!" Ta ƙarisa maganar tana mai rausayar da kai. Tun tana ƙirga mintuna har ta dawo awa. A can cikin gida kuwa, kirar sallar azahar ne ya fitar da mazan zuwa masallaci yayin da matan suka ɗauro alwala. Bayan kowa ya idar da Sallah, sai suka haɗu gaba ɗaya a dinning don har an kammala lunch. Kujerun dinning ɗin irin mai sha huɗu ne, kuma sun ɗauke gaba ɗaya don ma yaran an haɗa masu a parlour don suna da yawa. Khalil ƙafa ya tura ya shafo ƙafar Sarah, ɗagowa tayi suka haɗa idanu ya kashe mata idanu, gaba ɗaya a idanun Hajiya komai ya faru amma sai ta nuna kamar bata ga komai ba ta cigaba da cin abincinta. Zumbur Sarah ta miƙe tana faɗin, "Inna lillahi!" Gaba ɗaya aka haɗa baki wajen faɗin, "Mai ya faru?" Khalil kuwa har ya zagaya ta bayanta tare da jan kujeran da take kai baya. "Na manta ina da baƙuwa a ɗaki. Kuma tun ɗazu tana can tana jirana." Hajiya tace, "Laure maza haɗo mata abinci a basket ki tafin mata dashi." Khalil kuwa tsaki yayi a zuciyarsa don bai so ta tuna ba. Shima abincin da bai ƙarisa ci kenan ba yabi bayan matarsa. Kowa Sarah ta murɗa handle ta shiga, a zuciye Aina'u ta juyo zata fara ruwan bala'i sai ga Khalil ya shigo rai ɓutu-ɓutu. Washe baki Ai'n tayi tare da faɗin, "Kun jima, har nayi bacci na farka. Amma dai mancewa kuka yi nazo ko?" Ko kamun Sarah tayi magana caraf Khalil yace, "Ni na ɗauka ma kin wuce ai. Ashe kina nan kina jira." Sarah tace, "Kiyi haƙuri Aina'u wallahi mancewa nayi kina nan. Kinci abincin?" "Ban sani ba shegiya munafuka. Wato kin shigo cikin arziki har kin soma wulaƙanci. Kiyi, lokacinki ne. Nawa na nan zuwa." A Cikin zuciya tayi maganar, amma a zahiri sai cewa tayi, "Naci!" Sama Khalil ya hau yana faɗin, "Love, ɗauko min energy drink a fridge ki kawo min sama." Da "To" ta amsa tare da nufar kitchen ɗin. Da wani irin kallo mai tattare da shauƙi Ai'n tabi bayan Khalil. Sarah kuwa kitchen ta shige ta ɗauko drink ɗin ta dawo parlour tare da faɗin, "Aina'u ina zuwa dan Allah. Bari na kai masa na dawo." Ko tari Aina'u bata yi ba. Sarah kuwa dama bata jira cewarta ba ta nufi sama, kwance ta same shi daga shi sai boxer yana danna waya. Yana jin shigowar ta ya ajiye wayar tare da miƙa mata hannu alamar ta taho garesa. Sai da ta ɗan yi jim sannan tayi taku ta isa gareshi. Janyota yayi gaba ɗaya ta faɗo jikinsa ya saka hannu biyu ya rungume tare da faɗin, "Taho inji ɗumin jikinki matata." Ya ƙarisa maganar yana sunsunar wuyarta. "Dan Allah ka sake ni, Aina'u fa tana parlour." Hannu ya kai ya cire ɗan kwalin kanta ya cusa hannunsa cikin gashinta tare da faɗin, "Duk wacce tazo gidan amare ai ta san hakan zai iya faruwa da ita, ni kuma saboda wata Aina'u ba zan ƙi hutawa da matata ba." Ya ƙarisa maganar tare da murginata yayi mata rumfa yana kallon kyakkyawar fuskanta. "Waiyy! Nauyi gareka, ɗaga ni." Ta faɗi duk da kuwa be sakar mata nauyi ba. Jin abunda tace sai ya ɗan sakar mata kashi talatin a cikin nauyin nasa. Da sauri ta shiga bugun bayansa tana faɗin, "Nauyi, nauyi, nauyi! Wallahi ka sakar min nauyi." "Au haba, dagaske?" Kukan shagwaɓa ta sakar masa tana tsungulin damtsensa. Juyawa yayi ta koma samansa tare da zagaye ƙugunta da hannunsa ya matso da kansa ya haɗe bakinsu ya shiga bata deep kiss, Sarah kuwa sai mutsu-mutsu take zata kwace kanta yayi saurin juyata ta koma ƙasa yayi mata runfa ya shiga bata zazzafan romance, tun tana noƙewa har ta saki jikinta ba tare da ta shirya ba ta shiga mayar da martani. Sai da komai ya kammala ta shiga kukan shagwaɓa tana faɗin zafi. Shi kuwa ya biye mata yana ta lallashi. Tare suka yi wanka wanda a can bayin ma sai da suka ɓata lokaci, suna fitowa daga bayi ana kwaɗa kiran sallar la'asar. Sauri-sauri ya shirya ya fita gudun kar yayi missing ɗin sallah. Turus ya tsaya ganin Aina'u a zaune ta cika tayi faam, shi har ga Allah ya manta da ita a cikin gidan. "Ashe kina nan" shine abunda ya faɗi kawai tare da fita daga parlour. Wani irin kukan baƙin ciki Aina'u ta saki tare da miƙewa a zuciye tayi sama, kamun ta tura ƙofar ɗakin sai da ta tsaya ta goge hawayenta tukun sannan ta tura ƙofar. Juyowa Sarah dake gaban mirror tayi, sai da gabanta ya faɗi ganin Aina'u. "Sarah don nazo gidanki shine zaki min wulaƙanci ke da mijinki? Nagode kuma da izinin Allah ba zan sake zuwa gidanki ba." Tana gama faɗin haka ta juya zata fita. Da sauri Sarah ta miƙe tare da kamo hannunta tace, "Dan girman Allah ƙanwata kiyi haƙuri, wallahi ba wulaƙanci nayi maki ba. Kiyi haƙuri ki yafe min na san ban kyauta miki ba. Dan Allah Aina'u" ta faɗi tana mai haɗe hannunta biyu. "Amma Sarah....." Sarah tayi saurin cewa, "Dan Allah kiyi haƙuri ki bar maimaita magana. Zo ki zauna ina zuwa." Ta riƙo hannunta tare da zaunar da ita a kan gado ita kuma ta isa gaban mirror ta busar da gashin kanta sharp-sharp sannan ta saka riga da skirt English wear sannan ta saka dogon hijjab ta tada sallah. Bayan ta idar da sallar ta cire hijjab tare da nannaɗe dardumar ta ajiye sannan ta zauna kusa da Aina'u tare da faɗin, "Kiyi haƙuri Aina'u, tashi mu sauka ƙasa musha hira." Ta faɗi hakan tare da kama hannun Aina'u wacce ta gama ƙarewa gadon kallo ganinsa a hargitse kuma dama sai ƙarewa gashin Sarah kallo take yi ganinsa jiƙe kamun ta soma busar da kanta. Suna isowa parlour Khalil na shigowa. A gaban Aina'u ya kama kan Sarah tare da sakar mata kiss a goshi tare da faɗin, "Allah ya yi maki albarka!" Sannan ya nufi sama. Baki sake Aina'u ta bishi da kallo har ya ƙule kamun ta zauna tana sakin ajiyar zuciya. Aina'u ba ita ta bar gidan nan ba sai bayan magrib. Washa gari ma ta kuma dawowa, Khalil kamar ya fasa ihu don itace ta soma danna doorbell ko taran safiya bata yi ba kuma sai bayan magrib ta wuce duk ta hana su sakewa. A rana ta uku ce Khalil ya kai bango, don yana buɗe ƙofa yaga ita ce ko amsa gaisuwarta bai yi ba ya juya ya koma sama kuma yaƙi faɗawa Sarah tazo, kuma be bar Sarah ta fito daga bedroom ba ma balle ta sauko parlour taga Aina'un. Ranar har lokacin tafiyarta yayi bata ga ko ƙeyar Sarah ba, shima Khalil ɗin sau biyu ta gansa, lokacin da ya buɗe mata ƙofa da kuma lokacin da ya sauko zuwa kitchen ya dafa indomie da kwai ya koma saman, kuma ko kallon inda take bai yi ba. Sallah ma azahar da la'asar a ɗaki suka yi tare. Tsabar haushin da Aina'u taji, bata san lokacin da tayi wani irin kwallo da magen Khalil ba sai da ta karye a ƙafa sannan ta fizgi jakarta ta fita daga gidan. Tun daga ranar bata kuma dawowa gidan ba. Khalil kuwa kamar zuciyarsa za tayi bindiga ganin Madhu ɗinsa a karye sai kuka take yi. Haka ya kwashe ta zuwa asibitin dabbobi aka gyara mata ƙafar. Satin Sarah biyu a gidan Khalilullah, sun yi sabo da ƴan gidan sosai, kuma kullum da rana idan Khalil ya tafi sallar azahar a side ɗin hajiya take zama ita da Aunty Maryam har lokacin la'asar sannan kowacce ke komawa nata ɓangaren domin ɗaura girki. Sarah ta saba da nacin Khalil yanzu, kullum suna manne da juna babu daren banza. Ba ƙaramin soyayya suke zubawa ba a gidan. Ɓangaren kuwa, ranar da ta bar gidan Sarah keke napep ɗinsu yayi hatsari ta samu gocewar ƙashi a cinya, kuma babu wanda ya sanar da Saran. Wata ɗaya yazo ya wuce, biyu, har uku, Sarah tayi wani irin kyau da ƙiba da haske. Duk wanda ya ganta ya san tana cikin kwanciyar hankali. Yau da take cikin wata uku da kwana goma a gidan miji, Khalil yayi surprising ɗinta bayan gama nacinta akan tana son zuwa gida taga baba dasu Lami. Kamar an sakata a aljanna saboda farin cikin Khalil yace ta shirya zasu je gaida su baba. Wata lafiyayyiyar shadda ta saka kalar ruwan toka wanda yaji stone work iri ɗaya da na jikin Khalil. Sai da ɗauko farin gyale da farin takalmin vinci ta saka. Kaɗan ta fesa turare saboda Khalil bai so idan zasu fita ta riƙa fesa turare sosai. "Wow! Wife kin ganki kuwa?" Hularsa ƙube wanda Hajiya ta ɗinka masa da kanta ta saka masa tare da jawosa ta koma ta gabansa ta kwanto a jikinsa shi kuma ya ɗaura kansa a kan wuyanta, ita kuma tayi masu hoto. Ba ƙaramin kyau hoton yayi ba. "Wai nace ba, wani yare ne ku? Don nasan ku dai ba Hausawa bane." Yan maganar ne a cikin kunnanta. Sai da ta lumshe idanu sannan tace, "Na faɗa maka mu ƴan Nasarawa ne can _Wamba_. Baba yace sunan unguwarmu layin abakwa. Duk cikin mu babu wanda ya taɓa zuwa. Sunan yaren baba _Nindire_. Kuma yana ji sosai. Don akwai abokansa ƴan can, muna ji suna yi idan sun haɗu." "To ke kina ji?" Girgiza kai tayi tare da faɗin, "Ko zo in kashe ka." Dariya yayi shafa cikinta tare da faɗin, "Ɗana dake nan ko ƴata, za suji Kanuri in Sha Allah, zan riƙa yi musu, kuma Hajiya ma nasan za tayi masu." Kallon cikinta tayi sannan ta kallesa tare da faɗin, "To ai ni bani da ciki." "Ni da nayi cikin ai na sani." Ya bata amsa yana dariya. Kallon cikinta dake a shafe tayi, bata san lokacin da murmushi ya suɓuce mata ba tana fatan Allah ya amshi bakinsa. "Muje ko Queen" ya faɗi yana mai nuna mata hanya. Fita tayi ya biyota a baya, ji kawai tayi an ɗauke ta cak, bai sauketa ba sai da ya kawota har ƙofar ɗaki. Ɗakin Hajiya taje domin shaida mata zata gida, ba ƙaramin sha tara na arziki ta haɗa mata ba danginsu sabulai, turaruka, shadda da atamfofi har da manya-manyan zannuwar gado guda biyu. Khalil ta parking ta fito da gudu tayi cikin gida, babu kowa a gidan daga Lami sai Aina'u da ƴaƴansu Na'ima. Rungume Lami tayi tana mai farin cikin ganinta, da idanu tabi Sarah dashi, can kuma ta murza idanunta tare da faɗin, "Sarah! Kece haka?" Ta faɗi hakane tare da kaiwa ƙasa ta shiga faɗin, "Yesu Nagode, Nagode Yesu da kaba yarinyana kwanciyar hankali. Almasihu na koma gareka, ka saka albarka a rayuwar ƴata. In to my heart, in to my heart, come into my heart, Lord Jesus, come in to stay, come into my heart Lord Jesus, ameen!" Ta ƙarisa addu'ar tare da rungume Saran. Baba Nuhu kasa haƙuri yayi Sarah ta shigo, sai gashi ya fito yana farin, da gudu ta ƙarisa tare da faɗin, "Babaaa! Kai ne haka? Kaga yanda ka ƙara lafiya da kyau." Dariya baba yayi tare da faɗin, "Albarkacin haihuwarki ne Sarah, ban san mi zan cewa mijinki ba sai dai kawai ince Allah ya bashi Aljanna. Kullum cikin hidima yake mana. Ba'a haɗa cikakken sati bai zo gidannan gaishe ni ba." Zaro idanu Sarah tayi tare da kwaɓe fuska tace, "Amma shine bai taɓa zuwa dani ba sai yau, kuma baya faɗa min yazo." Murmushi baba yayi tare da faɗin, "Nine nan nace masa kar ya yarda ki soma fita sai kinyi wata uku da aure, shiyasa ko kwanciyar Aina'u a asibiti nace kar a faɗa maki." Zaro idanu Sarah tayi tare da faɗin, "Yanzu Aina'u ta kwanta asibiti baba shine ba'a faɗa min ba? Ni wallahi ba'a kyauta min ba." Dai-dai nan Khalil ya shigo bakinsa ɗauke da sallama. Bayan baba ya amsa yace, "Ke dama tare kuke da Ibrahim ɗin shine baki faɗa ba tuntuni saboda sakarci." Turo baki kawai Sarah tayi tana jin haushin rashin faɗa mata kwanciyar asibitin da Aina'u tayi. Har ƙasa Khalil ya duƙa ya gaida baba sannan ya gaida Lami, baba ne kaɗai ya amsa banda Lami don haushinsa take ji tunda Aina'u ta faɗa mata abunda yayi mata ranar ƙarshe da ta ziyarci Sarah. Ɗakin baba ya shige sukayi ta hira, yayin da Sarah ta shiga ɗakin Lami, tayi tayi Aina'u ta kulata amma ko kallonta bata yi ba. Da Lami kawai suka yi hira. Duba hamsin ta bawa Lami da kuma tsarabar da Hajiya ta bata, Lami kamar ta goyata tsabar murna. Baba ma dubu hamsin ɗin ta bashi da shadda ɗaya da zanin gado, albarka ya dunga saka mata. Anan idar da la'asar suka taho gida. Tun daga wannan rana Sarah ta soma wani irin rashin lafiya, gwajin farko da Khalil yayi mata ya nuna ciki, ɗaukarta yayi zuwa asibitin yayi mata scaning, sai ga cikin wata biyu har da sati biyu. Sosai take laulayi mai zafi wanda yaci uban na farko. Sau uku tana kwanciya a asibiti, abinci kuwa ko ƙamshinsa bata so, daga ruwan bohol sai fanta mai sanyi. Komai Khalil ke yi mata, wanka, wanki da gyaran ɗaki. Idan kuma yana asibiti, Laure ko Aunty Maryam ke yi mata. Wata ranar labara, tana kwance a akan kujera tana maida numfashi taji alamun ana murɗa handle ɗin ƙofa, tana ɗago kai tayi arba da ƙatuwar akwati Aina'u naja. Duk da bata jin ƙarfin jikinta bata san lokacin da ta tashi zaune ba tana bin akwatin da kallo............

*👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262*

*_MATAR SAYYADEE_*

*Paid book 08128755583* [10/5, 11:21 AM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜

*23*

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull