Kanwar maza 1 and 2 Complete - Chapter 57
Kanwar maza 1 and 2 Complete Chapter 57: Kanwar maza 1 and 2 Complete Chapter 57. Ta ƙarasa ta zauna, safarta tayi futu-futu saboda tafiyar ƙafa, ta zauna…
1,674 words
Ta ƙarasa ta zauna, safarta tayi futu-futu saboda tafiyar ƙafa, ta zauna ta ce "Tun safe nake tahowa, da ƙyar na zo gidan nan, dan na ga sabir, amma da na zo aka hanani shigowa, wai ya ce idan na zo kar a sake barina na shigo, sai kuma na ganshi ya zo wucewa zai shigo gidan nan, tare muka shigo na bar shi a waje, amma kuma da na shigo na ganshi a nan a zaune, a waje da ƙanan kaya na ganshi, amma kuma a nan na ganshi da wasu kayan". Tayi maganar tana kallonsa.
Adam bin rumaisa ya yi da kallo, yana mamakin anya kanta ɗaya, jin ta ce da ƙafa ta taho, kuma yanayinta ya tabattar da hakan.
Ammi ta ce "Ohh Mahmud ya shigo gari kenan?"
"Waye Mahmoud? Ba shi na gani a waje ba kenan?".
"Ba shi ki ka gani ba" Ammi ta bata amsa.
Rumaisa ta gyara zamantaz tana shafan kan Sabir, sannan ta yi ajiyar zuciya ta ce "Allah sarki, Allah ya sa idan na fita na ganshi na bashi haƙuri ban san ba shi bane ba, na yi ta masa masifa*.
"Amma rumaisa ba makaranta zaki je ba na ganki da uniform?".
"Makaranta zani, amma na kasa jurewa, ba bu abun da nake so sai in ga sabir, amma na zo wai an hanani shigowa, ban da dalilin sabir ma ni mai zai kawoni gidan nan, ina ga ma alhakin yaran mutane da nake cin zali ne ya kamani, Allah ya jarrabeni da son yaron da ake wulaƙanta ni a kansa, bakomai wataran sai labari"
Maimakonsa ammi ta ji maganganun rumaisa sun yi tsauri, sai ma wani irin tausayinta da ya kamata, lallai rumaisa tana cikin jarrabawa ta gaske saboda sabir.
Ammi ta riƙe hannunta ta ce "Rumaisa, babu mai wulaƙantaki a kan sabir, sabir ɗanki ne, ki yi haƙuri zan ɗau hukuncin da ya dace a kan Adam, amma daga yanzu duk lokacin da ki ke son ganinsa, akwai lambata a wayar mamanki, ki kirani ni kuma zan saka a kawo miki shi, ko na kawo miki shi da kaina, kin ga yanzu kin yi missing school, bari ya mayar da ke gida, tun da dama wurin aiki zai koma"
Rumaisa ta girgiza kai ta share hawaye ta ce "A'a, zan koma gida da kaina, kuma ba zan sake zuwa gidan ba, balle masu gadi su ci mutuncina a waje kamar yadda aka yi mini yau kamar ƴar maula" tayi maganar tana sake fashewa da matsanancin kuka.
"Kiyi haƙuri, in sha Allah hakan ba zata sake kasancewa ba, babu mai sake wulaƙanki a kan sabir, ko shigowa gidan nan, tun da gidanku ne, bari a kawo miki ruwa ki sha, ki ci abinci sai ya mayar da ke gida".
Ta girgiza kai ta ce "A'a na gode, dama sabir kawai nake son na gani, ban ci wani abun ba balle yayi tunanin ina fakewa da son ganin sabir ina zuwa kwaɗayi". Kalaman rumaisa ya tabattarwa da ammi rumaisa ba wauta da ƙuruciya kawai ta iya ba, ta san mutuncin kanta, kuma tana girmama kanta.
Ta ce "Ai na baki haƙuri, kuma na gaya miki zan ɗau mataki a kansa, kuma ko me zai ce ki rabu da shi, abun da ki ka yi masa a rayuwa bai isa ya biyaki ba, ladanki yana wurin Allah, tashi mu je ki sha ruwa ki sake karyawa, wannan tafiyar da ki ka yi na san kin gaji sosai" da ƙyar rumaisa ta amince ta tashi ta bi ammi, dan tana ganin mutuncinta da darajarta, amma ba dan haka ba, sai ta ce ko iskar gidan ba zata shaƙa ba balle ruwa, saboda cin mutuncin da aka yi mata.
Ammi ta kai rumaisa falonta, ta saka a ka kai mata abinci, ta fita ta bata wuri dan ta ci, ta dawo ta tarar da Adam a falo.
Rai a ɓace Ammi ta ce "Ban ji daɗin abun da ka yi ba ƙwarai da gaske, muzanta yarinyar nan da aka yi a waje, a kan me zaka ce kar a sake barinta ta shigo?"
Cikin ladabi Adam ya ce "Tuba nake, ba na yi haka ne domin ɓata miki rai ba, amma yawan zuwanta gidan nan akwai matsala, bana son ta shiga cikin wani hatsari saboda ni ko ayi amfani da ita wurin cutar da waninmu"
Ammi ta ɗan yi shiru ta ce "Ban ƙi ta taka ba, amma a ƙuruciya irin ta ta, da irin ƙaunar da take nunawa gudan jininka bai kamata a ɗauki wannan matakin kai tsaye a kanta ba, ba tare da bin wasu hanyoyi da ba zata ga an wulaƙantata ko cutar da ita ba. Tana da matuƙar wayo da kaifin basira, dan haka abun da ka yi mata dole ta kirashi da wulaƙanci da tozarci, kar ka sake yanke makamancin wannan hukuncin ba tare da izinina ba".
Ya risuna ya ce "In sha Allah"
"Ka biya ka fara ajiyeta a gida, ka sanar musu halin da ake ciki, don a saka ido sosai a kan ta ta daina missing makaranta, kuma kar ta sake yin wannan doguwar tafiya haka a ƙafa ita kaɗai"
Ya jinjinawa ammi kai.
Rumaisa ta fito, idanun nan sun yi ja ta ce "Ammi zan tafi".
"Maman Sabir har kin gama, bari ya mayar da ke gida" rumaisa ta kalli Adam sannan ta kalli ammi za ta yi magana, ammi ta girgiza mata kai ta ce "Ba'a jayayya da umarnin giwar galadima" Ammi ta yi mata maganar cikin gargaɗi, haka ya tilastawa rumaisa yin shiru.
Adam ya miƙe yayi gaba, rumaisa ta durƙusa ta sumbaci goshin sabir, sannan ta bi bayan Adam.
Kamar yadda ransa yake a haɗe, haka ita ma ta tsuke ta ta fuskar, babu alamar wasa da yarinta.
"Laa ka ga, bawan Allah" Adam ya ji maganar rumaisa, tsayawa yayi ya waiwaya bayansa, da gudu ya ga ta nufi jikin bishiyar dabinon da ke tsakiyar harabar gidan. Mahmud ne a tsaye yake waya, amma ya katse wayar ya zubawa rumaisa ido yana jiran ta ƙaraso.
Ta ƙarasa tana ɗan haki ta yi murmushi ta ce "Ashe ba kai ne shi ba?"
Mahmud ya ce "Shi wa?"
Rumaisa ta nuna masa in da Adam yake.
"Na zata shine da na ganka ɗazu, idona ya rufe sosai da ɓacin rai, ga gajiya kuma kuna kama sosai da sosai, dan Allah ka yafe mini na yi maka rashin kunya a gaban mutane"
Yayi murmushi ya ce "Kin ga jaririn naki?"
"Na ganshi, Allah ya saka maka da alkhairi da ban ganshi ba yau, da ina ga mutuwa zan yi. Ɗa na ne fa anty aisha ta bar mini shi, amma ya ƙwace shi kuma wai ya hana ni shigowa gidan nan"
"Wace aishar?"
"Kai baka san ta ba? Kai ba ɗan nan gidan bane?".
"Eh ɗan nan gidan ne, amma bana ƙasar jiya da daddare na dawo".
"Au ho, to in gaya maka sace ni aka yi a katsina, sai aka sato anty aisha matarsa, ta haihu ta rasu ta bar mini jaririn na kuɓuto da ƙyar, bayan na yi kwanaki ina wahala, amma ya ƙwace ɗan kuma wai idan na zo kar a sake barina na shigo, dan Allah wannan ba mugunta ba ce ba?"
Mahmud ya yi murmushi ya ce "Bai kyauta miki ba gaskiya"
"To kai baka taɓa zuwa sashin ammi ka ga jaririn ba, au ashe fa ka ce jiya ka dawo, ba ka ga ɗan nawa ba, mai kyau tubarkallah, ai na san ammi zata nuna maka shi ma, tunda a gidan nan ka ke"
"Eh a gidan nan nake, amma ni ba a sashinsu nake ba, ni ɗan Mummy ne".
"Wacece kuma hakan?" Ta tambayeshi tana ɗan gyatsine fuska.
"Babata ce, ko baki san mata biyu ne a gidan nan ba? Anyway na ga kamar jiranki yake yi, ki je kar ya zo nan wurin ya karairayaki, shi yafi masa komai sauƙi"
Cikin fitsara rumaisa ta ce "Wallahi wuce nan, na gode sosai ba zan taɓa manta taimakon da ka yi mini ba yau, kuma ka na da kirki fiye da wancan mutumin, dan Allah ka je ka ga ɗana a wurin ammi, sunanshi Mahmud ana ce masa sabir" tana maganar ta yi gaba tana murmushi.
Turus Mahmud yayi ya bi rumaisa da kallo, Adam ya sanyawa ɗan sa sunan Mahmud? Ya tambayi kansa, dan abun da mamaki.
Wurin motar adam ta nufa, da tuni ya kunnata, ya fito ya saka ana karkaɗewa motar ƙura.
Ya ƙarewa rumaisa kallo ya ce "Bawanki ne ni da zaki shanya ni ki tafi yawon surut?".
Ta kalleshi ta ce "Ba yawon surutu na tafi ba, godiya na je yi masa na bashi haƙuri. Ya nuna mini karamci saboda ni ɗan adam ce bai koreni ba ɗazu da na rasa nutsuwa ta ina kuka ba, ya taimaka mini na samu abun da nake so". Ta yi maganar irin ko maganar ta yi masa daɗi ko kar ta yi masa bai shafeta ba.
"Tun daga lokacin da ki ka sake shigowa rayuwata, ki ke ta wasu irin halayya da son nuna lallai akwai wani abu a tsakanina da ke, ina ɗaga miki ƙafa albarkacin yaron nan da kuma ƙuruciyarki, idan ki ka cigaba da wannan abubuwan ki ka shiga trap ɗi na zaki sha wahala na gaya miki, and as from today kar ki sake zuwar mana gida, abun da ki ka yi Allah ya baki lada, bana buƙatar sake ganinki a cikin gidan nan da sunan kin zo ganin yaron nan, idan kuma ki ka cigaba da zuwa zan nesanta shi da ke, nisantawa mai tazarar gaske da ba zaki iya cimm masa ba, dan haka idan ma wani abun ne a ranki ya sanya ki ke bibiyarsa, ki saka abun da na gaya miki a ranki. Idan har zaki cigaba da bibiyar yaron nan, za'a iya amfani da ke a cutar da shi, dan haka bana buƙatar sake ganinki a kusa da shi" yayi maganar cikin kashedi.
Cak ta tsaya ko ƙwaƙwƙwaran motsi ba ta yi, sai wasu irin hawaye da suke zubowa daga idonta.
Ayshercool