Kanwar maza 1&2 complete - Chapter 23
Kanwar maza 1&2 complete Chapter 23: Kanwar maza 1&2 complete Chapter 23. Iya tuni ta farka, gwaggo kuwa da ƙyar ta farfaɗo, tunda ta farko take koke-koke…
4,482 words
Iya tuni ta farka, gwaggo kuwa da ƙyar ta farfaɗo, tunda ta farko take koke-koke tana faɗin "Na shiga uku me zance wa uwar yarinyar nan, da na sani na basu 'yar su, ƙaunar yarinyar nan ya sanya na riƙeta, da na san haka zata faru, da na barshi ya tafi da ita. Ni yanzu ina zan saka kaina"
Sai da ma'aikatan wurin suka taru suka yi ta rarrashin gwaggo suna bata haƙuri, amma cewa take "Ni dama tawan suka ɗauka suka bar 'yar mutane, bawan Allah baƙuwace 'yar wa na ce, ban san me zasu yi mata da suka tafi da ita, Allah ka fitar da yarinyar nan ni Shafa'atu ina zan saka kaina, ta ina zan yi wa uwar yarinyar nan bayani?"
Likitan ya ce "Ai uwar yarinyar na tabattar musulma ce, kuma tayi imani da ƙaddara, dan haka ko a gabanta ne za a iya sace yarinyar "
Girgiza kai gwaggo ta yi ta ce "Ba zaka gane ba"
A social media Abubakar ya fara ganin abin da ya faru, kuma ya san da batun an kai ruma katsina, ƙauyen da iya take, duk da yana makaranta. Ba shiri ya kira Aliyu a waya ya sanar masa da a kan lallai ya bincika, su ji ya ruma take, sannan su gaggauta zuwa su ɗaukota.
Usman ma ya gani, dan haka a burkice ya ja Aliyu yake nuna masa abinda ya gani.
Aliyu ya ce "Yanzun nan Yaya yayi mini magana a waya, ina son na kirasu a waya amma tsoro nake ji, babban tashin hankalina kar mai sunan Baba ya ji balle mama, dama ya ce gobe in Allah ya kaimu zai je ya ɗauko ruma".
Usman ya ce "Ka ga ba wannan ba, ka kiras lawalli a waya ka tambayeshi yaya rumaisa take?"
Aliyu ya girgiza kai ya ce "Usman gabana faɗuwa yake yi fa, ance an karkashe wasu an tafi da wasu, kai dai ka kirasu"
Usman ya kira wayar lawalli, amma taƙi shiga, dan haka ya kira ta ɗanlami babban ɗan gwaggo, dan tabattar da abin da yake faruwa.
Sai da ta kusa katsewa sannan ɗanlami ya ɗaga wayar.
Ba tare da sun gaisa ba, cikin zaƙuwa Usman ya ce "Yaya ɗan lami, ya ake ciki ne? Na ji 'yan ta'adda sun kai hari garin su Iya, ya ake ciki ya ya ina ruma?"
Yaya ɗanlami ya ce "Wallahi kuwa, dan kaga gwaggo ma tana gadon asibiti, Baba kawai aka sallamo"
Aliyu ya karɓe wayar ya ce "To Allah ya kyauta, ya ya rumaisa, gobe in Allah ya kaimu yaya umar zai zo ya ɗauketa ya taho da ita, dan Allah a ɗaukota daga garin nan kan ya zo".
"Aliyu sai dai fa mu tsananta addu'a, an samu matsala 'yan bindiga sun tafi da rumaisa!!!"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, me ka ke cewa ne...?"
Usman ya girgiza Aliyu ya ce "Me ya ce maka ne?"
Kan Aliyu yayi magana, suka ga mai sunan Baba a tsaye yana kallonsu, Allah kaɗai ya san iya adadin lokacin da ya shafe a tsaye yana jin su ba tare sun sani ba.
Ayshercool
KANWAR MAZA
BOOK 2 PAGE 5
*Paid book ne, 500 ne via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143, wanda suke ba a Nigeria ba kuma, za su iya saya a arewabooks*
Tsuru-tsuru suka yi suna kallon umar, sai dai yanayinsu ya nuna a razane suke, kuma aka rasa wanda zai yi magana.
Ƙarasawa yayi gabansu, ya karɓi wayar daga hannun Aliyu, ya yi dialing lambar ɗanlami, yana kira ya ɗaga tare da yin sallama. Sai dai ɗanlami na jin muryar mai sunan baba cikinsa ya kaɗa, dan ba ƙaramin tsoron tijarar mai sunan Baba suke ba.
Cikin kakkausar murya Umar ya ce "Me ka gaya musu? Ina ruma take?"
Ɗanlami ya ɗan rikice sannan ya ce "Malam umar a saka addu'a, amma Akwai damuwa, ka san shi lamarin ƙaddarar Ubangiji ba ayi mata shamaki".
Cikin hasala ya kuma cewa"Ba nasiha na ce kayi mini ba, tambayata zaka amsa mini, damuwar me, ka yi mini bayani ina rumaisa take?"
Tamkar an ritsa ɗan lami da bindiga ya ce "Umar wallahi 'yan bindiga sun tafi da rumaisa, kuma ba da ita kaɗai suka tafi ba, amma an sanar da jami'an tsaro za su yi ƙoƙari a kai, za abi bayansu"
Cikin tashin hankali ya ce "Ya isa haka ɗanlami, amma kun san garin nan babu cikakken tsaro kuka tura yarinyar nan? Babu yadda ba ayi ba a kan gwaggo ta bayar da yarinyar nan a dawo da ita gida amma taƙi, ta turata in da ta san babu tsaro, duk yadda ake ciki ku san yadda zaku yi, ni ban san wata magana ba kawai an haɗa baki da ku an yi garkuwa da yarinya ku san yadda zaku yi". Ɗanlami zai yi magana, mai sunan Baba ya kashe wayar ya cillar ya fice a fusace dan gaba ɗaya jijiyoyin kansa sun miƙe saboda ɓacin rai da tashin hankali.
Mama ce ta fito tsakar gida ta na faɗin "Wai babana shi da wa yake ɗaga murya, me kuka yi masa ne yake ta magana sama-sama?"
Cikin sanyin jiki Usman ya ce "Saɓani ne aka samu, kin san halinsa da zuciya da saurin fushi"
Mama ta ce "A'a ai kuwa bai fiye yin magana ba, sai an ƙure shi, wani abun dai ku ka yi masa, ko kuma faɗa kuke a tsakanin ku" gani tayi sun jeru basu ce mata komai ba, sai dai fuskokinsu ɗauke da damuwa, kamar a firgice suke.
Ta dubi Aliyu da kyau ta ce "Gadanga wai menene, na ganku duk wani iri me yake faruwa ne, ko akwai wata matsala ne?"
Aliyu ya dake ya ce "Babu komai mama, ni bari na fita zan sayo omo na yi wanki".
"Ban da omon da babana ya sayo shekaranjiya ya shigo da shi kaya guda, kusan kayan, wane omon kuma ka ke nema ko ka manta ne?"
Ya dafe kai ya ce "Ohh na manta, aski zani, ai na manta shaf da Oman ne, idan na dawo daga askin sai na yi wankin" yana yin maganar yayi waje, Usman ya rufa masa baya.
Gaba ɗaya mama ta kasa gane kansu, kuma ba wanda yayi mata bayanin wani abu. Kawai ta share ta cigaba da sabgoginta.
Duk yadda usman ya so dakewa abu ya gagara, a soro ya durƙusa ya fashe da kuka, shi ya riga ya karaya ya san ubangijin da ya halicci ruma ne kawai zai fitar da ita.
Aliyu ya rungumo shi ya ce "Haba usyy so ka ke sai mama ta gane ne? Dan Allah ka jure kan mu san abin yi, kar mu bari ta gano akwai matsala idam ta gane, ka san tana da hawan jini, yanzu zai iya tashi"
Usman ya ce "Wane abun yi da me zamu karɓota? Me muke da shi? Mutanen da ba imani ne da su ba, 'ya mace ce fa, Allah kaɗai ya san me zasu yi mata, gara ace mutuwa ta yi ga gawarta da wannan tashin hankalin, wa zai kula da ita?".
Aliyu da tasa zuciyar ma ke daf da karyewa ya ce "Na sani, amma addu'a ba ta bar komai ba Usman ita zamu dagewa, kayi haƙuri tashi ka daina kuka kar mama ta zo ta samemu" haka yayi ta rarrashin Usman.
Mai sunan baba kuwa ji yayi duniyar ta yi masa zafi, ina ma shi aka ɗauka aka bar ruma. Yaya mama za ta ji idan ta samu labarin an yi garkuwa da rumaisa?. Zuciyarsa ta din ga zafi yana jin da zai ga gwaggo sai yayi mata rashin mutuncin da bata taɓa tunani ba, dan yana jin zai iya mangareta dan duk ita ta janyo wannan masifar, duk da tana ƙanwar mahaifinsu, cewar da aka yi tana gadon asibiti jininta ya hau bai dameshi ba, dan da jinin tasa uwar ya hau ko wani abu ya samu ruma, gara duk abin da zai faru ya faru.
*** Zuwan takawa a Abuja a wannan karon ya sanya ya samu abubuwa masu muhimmanci da bincikensa bai kai masa ba a baya, sai dai zuciyarsa na ta azalzalarsa a kan lallai ya koma gida, jinsa yake tamkar a kan wuta, idan bai bar garin ba kamar wani mummunan abu zai faru da shi, dan haka babu shiri, ya tattara kayansa ya taho Kano, dama ga Ammi na ta waya dan duk a tsorace take, saboda yanayin jikinsa, Jabir ma duk ya addabeshi a kan nan kano ma akwai aiki, dan haka ya haɗa kayansa ya koma kano.
Sai ka ce a wannan karon ya fara tafiye-tafiye, Ammi sai hamdala take a kan dawowarsa gida lafiya, dan ba ƙaramin tashin hankali ta shiga ba, da yayi tafiyar nan dan sam ji ta yi ba ta son tafiyar ta sa.
A gidan Turaki suka haɗu, da takawa, da Jabir da kuma Jamil da ya kasance wa ga Samha kuma cousin ɗin sa. Hira suke yi sosai, suna tattaunawa a kan rayuwa. Jamil ya zunguri Takawa ya ce "Kai, wai me kake nufi da ni ne, ba fa ka taka gidana ba, ranar da na tare ma ko rakiya ba ka yi mini ba, kuma ba ka zo ba sai harkokinka kawai kake"
Ɗan shiru Adam yayi, tun daga lokacin da ya ji muryar ruma a ranar ya rasa nutsuwarsa, kilisar ma da ƙyar aka ƙarasata da shi, tunani ya fara yi ko zuwa unguwar su zai yi. 'Ka je ka yi mata me?' wata zuciyar ta tambayeshi. Tsaki yayi wanda ya fito fili bai sani ba.
"Tsakin me kake kuma?" Adam ya tambaye shi.
Girgiza kai yayi bai ce komai ba.
Jabir ya ce "Yauwwa Takawa, ina mutuniyarka kuwa wannan yarinyar?"
Haɗe rai Adam yayi tare da basarwa, Jamil ya ce "Wace yarinyar, budurwa yayi ne? Kai ka isa ka yi wa ƙanwata kishiya?"
Jabir ya ce "To bana ce ba, wata 'yar figigiyar yarinya ce mai kama da bainu, ban taɓa ganin yarinya mara mutunci da rashin tsoro irinta ba".
Adam a ransa ya ce "Ai ba ka san mara mutunci ba, sai ka ga wasiƙar da ta rubuta mini' amma a zahiri yayi shiru kamar ba da shi suke hirar ba. *** "Ina sonka Adam, so bana wasa ba, so mai tsananin gaske son da nake jin zan iya komai domin na mallake ka, duk da na rasa dalilin da ya sanya bana gabanka, ko da yake ba rasa dalili na yi ba, nafi kowa sanin dalilin da yasa bana gabanka, kuma ina daf da magance komai domin in samu miƙaƙƙiyar hanya ɗoɗar ta cimma muradina na rayuwa da kai, ko baka aureni ba ina son kasancewa da kai na rayu ƙarƙashin kulawarka. Ban sani ba ko zuwa nan gaba asirina ya tonu duk da bana tunanin faruwar hakan, amma idan ma ya farun ka yi mini uzuri soyayyar ka ce ta janyo mini hakan" tamkar taɓaɓɓiya haka samha ta saka hoton Adam a gaba ta na surutu, hoton yana sanye da kaya ne na sarauta, ya ɗan sauke rawaninsa yana murmushi, wanda aka ɗauka da hawan wata salla. Sai da ta gama soki burutsunta, ta mayar da hoton ma'ajiyarsa, ta tashi ta ƙarasa shirinta ta fice.
Mummy ce tare da aminiyarta zaune a ƙuryar ɗakin Mummy suna tattaunawa.
"Wai hajiya Lubabatu babu wani zazzafan malami ne, abubuwa kamar sun tsaya mini, sun ƙi cigaba kamar yadda nake so".
"Haba Jamila, ke kin san an daɗe muna haƙa rijiya, rijiyar da muke saka ran samun ruwa a kowane lokaci, mun shirin da idan balli ya tashi akwai rikici, ke dai mu cigaba da haƙuri".
Mummy ta girgiza kai ta ce "Ya ci ace burina ya gama cika, nifa da dai da mintuna biyar bana son ruhin Binta ya kasance cikin kwanciyar hankali da farinciki, so nake ta dauwwama a baƙin ciki har ƙarshen rayuwarta".
Dariya Hajiya Lubabatu ta yi ta ce "Haba Jamila, ai ko a haka kika barta wallahi ta yabawa aya zaƙinta, kuma ta ɗanɗana kuɗarta, amma ki cigaba da haƙuri ai mun ɗana tarko daban-daban".
Mummy ta jinjina kai ta ce "Shikenan, bari mu ga zuwa yaushe, na cigaba da sanya musu ido, duk wani motsinsu uwani na gaya mini, kuma na ce lallai ta kawo mini maganin da waccan 'yar tsintuwar ke shafa masa".
"To shikenan, to bari mu ga yadda abubuwa zasu kaya". *** Har azahar babu wanda ya kula su ruma, masu kuka na yi masu addu'a na yi, ga yunwa ta addabeta a gida wataran ƙarfe bakwai ta karya, amma har bayan azahar babu wanda ya kulasu balle ya basu wani abu. Tashi ruma ta yi ta samu ɗaya daga cikin 'yan bindigar ta ce "Bawan Allah yunwa nake ji, ku bani abinci na ci"
Wani mugun kallo ya yi wa ruma ya ce "Zo ki cinyeni, an gaya miki nan wurin hutu ne da jin daɗi?".
"Ai ni ba mayya bace da zan cinyeka, idan ma cin ne ban ga abin ci a nan ba, idan ba za a bamu abinci ba meyasa zaku kawo mu nan?" Ta na rufe baki yana hankaɗeta sai dai faɗi ƙasa ya saita ta da bindiga "Idan ki ka yi mini hauka, yanzu na lahira zasu yi maraba da ke".
Ruma ta kalli yadda ta faɗi ƙasa, wata irin zuciya ta harziƙota ta miƙe tsaye ta sake kallonsa ta ce "Na faɗa a bani abinci yunwa nake ji, ai daɗinta idan ka kasheni ba a wuta zaka sakani ko aljanna ba, hisabi na Allah ne, to na faɗa a bani abinci yunwa nake ji, harbeni maza kai kuma a ƙara maka kwanakinka a duniya" Babu alamar tsoro ko shakka a tare da ruma, kowa sai da ya Zubo mata ido, saboda ƙarfin halinta.
A fusace ya tashi yayi kan ruma, amma wani ya riƙe shi, ya ce kar ka kuskura, ƙyaleta idan ka yi mata wani abun za'a iya samun matsala, ka bari oga ya zo ya faɗi ya za ayi".
Huci ya din ga yi yaso ya tattaka ruma, ko ya keta mata haddi a gaban mutanen wurin, ya kawo ƙarshen harshenta.
"Ni baka kyauta mini ba da baka bari ya kasheni na huta ba"
"Wato ke dai bakinki ba zai mutu ba ko?"
"Idan har so ku ke na yi shiru, to ku kasheni ko ku mayar da ni gidanmu, wannan ai zalunci ne ni yunwa nake ji" tayi maganar tana share hawaye.
Dattijon nan ne dai na jiya ya ce "Yarinya ki yi shiru da bakinki, kar su citar da ke, wannan mutanen ba ayi musu haka".
"To ni yunwa nake ji" tayi maganar har cikin zuciyarta.
Duk wani kurari da zare ido ruma taƙi yin shiru, kamar ma da gayya take yi dan ta tunzurasu su yi mata abin da za su yi mata.
*** Har dare mama ba ta san abin da ya faru ba, kuma an rasa wanda zai gaya mata, sai mita take musu cewar ita fa ta kasa haƙuri ta kira gwaggo idan an dawo da ruma ta haɗata da ita, amma wayar gwaggon ba ta shiga. Sun yi mamaki da duk jin rediyon mama ba ta ji batun kai harin ba. Ganin tana ta surutu ita kaɗai ba wanda ya tanka mata, ya sanya ta magantu "Wai ba zaku gaya mini meke faruwa ba ne? Duk cikinku fa yau babu wanda ya ci abinci, kun ƙi walwala kun ƙi magana, kuma kun ƙi gaya mini menene?"
Usman ne ya tashi ya ce "Mama sai da safe, ni dai bana jin daɗi ne".
Babu wanda ya bawa mama amsa, a hankali duk suka watse daga tsakar gidan, mama ta sha jinin jikinta ta fara tunanin menene ya faru haka, da basa son gaya mata?.
Babu wanda ya saurari su ruma sai bayan la'asar, aka zo da wasu kuloli a kan babur, aka rarraba musu wata busashshiyar gurasa, gaya guda ɗai-ɗai, sai pure water ɗaya tamkar mabarata. Ruma ta kalli gurasar nan, duk uwar yunwar da take ji, amma a rasa me za a bata sai wannan takurarriyar abar a bushe, babu mai babu komai a jiki. Gashi duk ta bushe kamar ƙanzo.
Ruma ta gasta ta fara ƙoƙarin haɗiya, amma ta kasa haɗiyewa, da ƙyar ta dannata da ruwa, daga gutsura ɗayar nan ba ta ƙara ba ta shanye ruwanta ta yar da ledar, sauran kuwa tuni kowa ya kama gurasar nan suka cinye.
*** Duk wata tattaunawa su Usman da sauran 'yan uwansa sun yi, amma sun rasa ta ina zasu ɓullowa lamarin, duk in da zasu buga sun yi, amma babu wani labari game da in da su ruma suke, gashi da wani ya ce zai je katsinan mama za ta gano akwai abin da yake faruwa, dan a yanzu haka ma duk ta tsargu, mussaman yadda suka daina walwala ga kuma ta fara shiga damuwa rashin shigar wayar gwaggo. Su huzaifa ma sun gano abin da yake faruwa, sai dai yanayin ruɗewa da Huzaifa da Yasir suka yi, ya sanya mama cigaba da jefa musu zargi da kuma kokwanto.
Yau ƙarfe tara na safe taga duk sun fito daga ɗakinsu sun jeru a tsakar gida, kamae kullum babu wanda yake walwala a cikinsu, kuma babu mai sunan Baba a cikinsu. Mama ta girgiza kai ta ce "Koma menene Allah yayi muku maganinss, tunda ni dai ina tsakaninku ba zaku gaya mini ba".
Ta fito daga banɗaki kenan, Abubakar yayi sallama ya shigo da jakarsa ta makaranta, sai dai kallo ɗaya tayi masa shima ta ga tsananin tashin hankali a fuskarsa.
Mama tayi saroro tana kallonsa, cikin ƙarfin hali ta ce masa "Kai kuma me ya dawo da kai yanzu?"
Suka haɗa ido da Aliyu, Aliyu ya sunkuyar da kai, Yasir kuma ya hau goge hawaye.
"Saddiƙu, dan Allah kai ka gaya mini menene? Ku daina ɓoye mini koma menene, na kasa nutsuwa sun ƙi su gaya mini abin da yake faruwa, na rasa gane kansu, dama har akwai abin da ban cancanci in sani ba?"
Abubakar ya ajiye jakarsa ya kamo hannun mama ya ce "Mu je ɗaki mama sai mu yi magana"
Mama ta buge hannunsa ta ce "Ba in da zani, ku yi ta riƙe abin ku a cikinku nima bana son ji, idan abin da bana ƙauna a rayuwata bai wuce ganin fuskokin da ba sa son damuwata in gansu cikin damuwa ba, ko ba zan maganta muku ba ai na yi addu'a" ta juya za ta wuce ɗakinta.
"Mama ruma ce" ya furta a hankali, cak mama ta tsaya ta kasa gaba ta kasa baya, ta ji maganar ta sa kamar bai faɗeta dai-dai ba.
Ba tare da ta waiwayo ba ta ce "Mutuwa ta yi?"
"An yi garkuwa da ita, a garin su Iya, a cikin harin da aka kai ƙauyen har da ita aka ɗauka".
Innalillahi wa Innalillahi raji'un, mama za ta iya cewa ko mutuwar iyayenta ba ta girgizata kamar wannan abu da ta ji yanzu ba, ji ta yi kamar ba a hayyacinta ta ji maganar ba, tamkar an mata yayyafin wuta, Rumaisa a hannun 'yan biniga, gara ace kashe mata ita suka yi, ta tura a ɗauko mata gawarta, amma ruma 'ya mace ƙarama a hannunsu a tsakiyar dajin Allah, Allah kaɗai ya san me za su yi mata, ga halin ruma da ta sani na rashin kunya da surutun tsiya, tsaf za su illata ta. Jikin mama ne ya hau rawa, ta sake ƙare musu kallo, Huzaifa da Yasir suna ta kuka, Aliyu kuma ya sunkuyar da kai, haka Abdallah, Usmsn kuwa barin tsakar gidan ya yi, babu mai sunan Baba ko ba a gaya mata ba ya tafi katsinan ne.
Ta yinƙura da niyyar ɗaga ƙafarta, ta tafi luuu gaba ɗaya suka yi kanta suna kiran sunanta
Ayshercool
*Paid book ne, 500 ne via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143, wanda suke ba a Nigeria ba kuma, za su iya saya a arewabooks*
Sosai suke girgiza mama, amma ko motsi ba ta yi, a gigice Abdallah ya ɗebo ruwa ya din ga shafa mata a fuskarta Usman ya ɗauko mafici yana yi mata fifita. Aliyu ya kalli Usman ya c "Usman wani ya je ya samo napep mu kaita asibiti da sauri".
Usman ya ce "Ko nan da zaure ba zan iya fita gani nake komai zai iya faruwa kan na dawo, sai dai ko su Yasir".
Yasir da yake riƙe da hannun mama ya ƙara ƙanƙame hannun, ya ƙi tashi yana kuka.
A hankali mama ta yi tari, ta fara motsawa tana Innalillahi wa Innalillahi raji'un. Babban fatanta Allah ya sa idan ta buɗe idanunta ace mata mafarki take yi.
Sai dai tana buɗe ido ta kalli fuskokin su Huzaifa, hakan ya tabbatar mata a zahiri ne, ruma an yi garkuwa da ita.
Sannu suka din ga jerwa mama, amma ta kasa amsa musu, a hankali ta ce "Ku kira babana, dan Allah ya juyo gida kar ya je, mu bar wa Allah komai".
"Amma mama meyasa?"
"Kar yaje ya tayar musu da hankali ko shi ma wani abun ya same shi, zuwan nasa babu abin da zai ƙara ku kira mini shi a waya, ya dawo gida dan Allah".
Jiki a sanyaye Abubakar ya janyo wayarsa a aljihunsa ya kira lambar Umar.
Mai sunan Baba na ɗagawa Abubakar ya ce "Akhi mama ta ce ka dawo gida, bata yarda ka je ba?"
A hasale Umar ya ce "A kan me zaku gaya mata, kun san ba cikakkiyar lafiya ce da ita ba dan me za a gaya mata? Wannan ai ba yi ba ne, idan wani abu ya sameta fa?"
Shima Abubakar da zuciyarsa ke a kusa ya hayayyƙo masa "Kai saurara ni ka ke wa shouting? Da wanne zan ji ne? Har zuwa yaushe zamu cigaba da ɓoye mata. zamu dawo mata da rumaisa ne idan bamu gaya mata ba? zaka din ga yi mini hayaniya kai kaɗai kake cikin damuwar ne? Duk ta shiga damuwa ba mai cin abinci kowa baya walwala kuma an ƙi sanar mata abin da ke faruwa, zuwa yaushe za a cigaba da ɓoye mata, idan ka ga dama ka dawo idan ba ka ga dama ka je ka yi abin da ka ga dama" Umar yayi wa ɗan uwansa uzuri, damuwa ce ta sanya ya sauke masa, dan Sadik ba dai haƙuri ba. Suna gama wayar Abubakar yayi cilli da wayar zai tashi mama ta riƙe shi.
Cikin tawakalli da ƙarfin hali ta ce "Yi haƙuri, kar ka yi fushi dan Allah, ka lallaɓo mini shi ya dawo ka san halinsa"
Abubakar yayi ajiyar zuciya zai yi magana wayar mama ta fara ringing a ɗaki, Yasir ya je ya ɗauko, mai sunan Baba ne yake kira. Mama ta karɓa da sauri ta kara a kunnenta ta ce "Babana dan Allah ka dawo gida" tayi maganar muryarta na rawa.
"Ki yi haƙuri mama, daga sallar asuba na wuce, ina Katsina yanzu haka na kusa ƙarasawa ki yi haƙuri ba abin da za zan aikata, zan je wurin jami'an tsaro ne, ki kwantar da hankalinki in sha Allah za ta dawo lafiya ".
"To" kawai mama ta ce ta saki wayar, tana wata irin ajiyar zuciya, zuciyarta sai wani irin zafi take yi mata, amma idonta ya bushe babu hawaye.
Su ruma kuwa yau kwana na huɗu kenan suna hannun 'yan bindiga, ba wanka ba wanki, ga azabar yunwa ruma ba ta iya cin abin da ake bata, ruwan nan ɗaya idan an basu da shi take sha idan tana jin fitsari ta yi. Duk azabar kashi irin na ruma, ta matse abin ta ba ta yi. Tun da ruma take ba ta taɓa kawo tsintar kanta a irin wannan halin ba. Ga duka da wasu lokutan ake yi wa wasu, duk da ita babu wanda ya taɓa dukanta, amma ana dukan wasu ciki har da mata, 'yan bindiga su dake su su taka su da ƙafa. Wani tarihi ruma ta tuna da aka taɓa basu a islamiyya, a rayuwarta tana son malaman da suke basu tarihi, dan duk abin da take zata nutsu ta saurara. Akwai ranar da malamin yayi musu tarihin Annabi yunus da kifi ya haɗiye shi, ya karanta *La'ila ha illa anta subhanaka inni kuntu mina zalimin* Har ruma ta ce "Kai malam amma kifin da ya haɗiye annabi yunus, dai yayi girman duniyar nan?"
Malamin ya yi murmushi ya ce "Meyasa ki ka ce haka? Kin san girman duniya kuwa?"
"To ai malam kifin da inuwa mai kifi yake sayarwa, da wanda ake talla ko ɗan tsako ba zasu iya haɗiya ba, amma na ji ka ce kifi ya haɗiye mutum"
"Kifi ne dai babba ruma, amma ba kamar girman duniya ba, kuma ba a gaya mana girman kifin ba a Alqur'ani, abin da nake son ki riƙe yanzu shi ne, falalar wannan addu'a da annabi yunus Alaihissalam ya karanta, a duk lokacin da kika shiga wani mawuyacin hali, ko ki ka shiga hannun wasu azzalumai to kema ki karanta Addu'ar da Annabi yunus Alaihissalam ya karanta *La'ila ha illa anta subhanaka inni kuntu mina zalimin*"
"To malam, in Allah ya yarda zan din ga yi, to wace addu'a zan yi idan na yi wa mama laifi kar ta yi mini faɗa ko ta saka mai sunan Baba ya sakani kama kunne?" Jik tambayar da ta yi, ya sanya 'yan ajin suka kwashe da dariya.
"A'a ai dole idan ki ka yi laifi ayi miki faɗa ko a hukunta ki, amma a duk lokacin da kike fargabar haɗuwa da wani, mugu ko maƙiyi sai ki karanta *Allahumma inni as'aluka min nuhurihim, wa'auzubika min shuriruhim*"
Ko da ruma ta tuna da wannan tarihin da malaminsu ya yi musu sai ta fara nanata "*La'ila ha illa anta subhanaka inni kuntu mina zalimin*"
Ihun wata mata ne ya sanya ruma waiwayawa taga ko dukan na ta ake, amma taga ɗaya daga cikin mutanen yana jan ta tana ihu, tana a taimaka mata. Babu wanda ya tanka mata mutumin yayi cikin dajin da ita.
Ɗaya daga cikin 'yan bindigar ya ce "Ai gara hakan, tun da 'yar matsiyata ce ba za su biyan kuɗin da aka ce su karɓeta ba".
Kusan awa biyu mutumin ya dawo ba tare da ita ba.
Ta ji wasu a kusa da ita suna magana ƙasa-ƙasa "Innalillahi, ita ma sun mata fyaɗe sun kasheta" Ruma ji tayi kamar ta tambayesu meye fyaɗe, tunowa tayi lokacin da take tambayar mama meye fyaɗe su Aliyu suka din ga hantararta.
A take ta fashe da kuka, saboda yadda take kewar gida, duk suka juyo suka kalleta.
"Ke meye haka?"
"Mama" ta faɗa cikin kuka.
"Yi mana shiru ko in taka ruwan cikinki"
"Wallahi ba zan yi shiru ba, wayyo Allah mama yaya Aliyu yaya usy dan Allah ku zo ku ɗaukeni zan mutu, wayyo Allahna" kuka take sosai kamar wadda wani iftila'in ya afkawa.
Wata mata ce ta din ga rarrashin ruma tana bata haƙuri da ƙyar ta yi shiru, ta cigaba da nanata addu'ar nan.