Kawar zuciya Book 2 by takori - Chapter 2
Kawar zuciya Book 2 by takori Chapter 2: Kawar zuciya Book 2 by takori Chapter 2. Suna nan zaune matar na amsa waya lokaci-lokaci, can kuma ta jefa wayar a…
4,455 words
Suna nan zaune matar na amsa waya lokaci-lokaci, can kuma ta jefa wayar a kyakkyawar Jakarta, cike da shishshigi ta dubi Sophie, don taga kalar hutu sosai a jikinta itama, ita kuma dama da irin kalar wadanda take kawance kenan, sai ta hau jan Sophie da hira kadan-kadan babu alamu na bakunta, ko irin yau ta fara ganinta dinnan.
“Baiwar Allah sannu fah. Na ce sannu fah. Halan kema matsalar rashin haihuwa ce ta kawo ki ganin Dr. Galadanchi?”
Safiyyah sai da taji gabanta ya fadi, matar tayi murmushi ganin irin kallon da Sophie tayi mata na mamaki, sai tace,
“yo meye abin mamaki don na canki matsalarki? Ai daidakun mata ne ne da sukazo Standard da ba matsalar data kawo su kenan ba, musamman masu fama da lalurar (PCOS)”.
Sophie ta bita da kallo kawai, don bata ma san menene ‘PCOS’ din ba ita har yau, bata taba jinsa ba, sai a bakin Dr. Muwadda Shinkafi. Ta ce a ranta,
“wasu matan dai Allah ya zuba musu surutu da shiga sharo ba shanu!”.
Matar bata san tunanin da Sophie ke yi a kanta ba, ta cigaba da cewa.
“Alhalin basu san cewa wahalar da kansu kawai suke yi a banza ba. Ni dinnan da kike gani wane kalar asibitine banje neman haihuwa ba, kasashen duniya manya da kanana babu inda bamu taka don neman haihuwa ba nida maigida na.
Mun zubar da dukiya da lokacinmu kamar me a yawon asibiti, duk a banza.
A karshe dole nabi hanyar da ta bulle dani, yanzu haka yara na biyu. Wannan zuwan kuwa na zo ne likita ta rufe min bakin mahaifa in samu in huta da haihuwar haka ko na shekara biyu ne, yarana kuma su kara girma”.
Safiyyah sakin baki tayi tana kallon matar, wadda ta laqawa suna “fadi ba’a tambayeki ba”. Hankalinta ya dan fara daukuwa ga abinda matar take labarta mata, amma bata gane zaurancen hanyar da take nufi ta bi, wadda ta bulle da ita din ba.
Zata so taji wannan kowacce irin hanya ce, da har haihuwar tazo ta isheta tana neman dakatarwa, ko itama ta gwada, ko Allah zai sa ta dace.
Safiyyah sai ta saki jiki da matar nan wadda tace sunanta Ammara, nan suka shiga hirar haihuwa, kamar sun dade da sanin juna, abinki da irin ka gamu da mai irin ciwonka, wanda ya rigaka samun waraka.
Ammara tace “shekaruna ashirin da aure kafin na samu haihuwar yaran da nake dasu yanzu. Kema kinsan mun sha damuwa nida maigidan”.
Safiyyah kuma tace “ita kuma shekara takwas kenan da aure, ko bari bata taba yi ba”. Sai hira ta kara mikawa tsakaninsu akan hakan.
Ammara tace “haka kawai naji kin kwanta min a rai, gaki kyakkyawa ga kuruciya ga hankali, ga hutu, banda haka banida sakewa da bakin fuska sam.
Naga damuwa baro-baro a tare dake, haka kawai yarinyar ki dake zaki bar ciwon damuwa ya kamaki a banza saboda haihuwar da samunta ruwan sha yafi ta saukin sha.
‘Yar uwa ki rabu da wani yawon asibiti ana cin kudinki a banza, kibi hanyar da zata bulle dake kawai.
Rayuwar nan saida dan kaucewa sannan ake ganin daidai”.
Ta kara saka Safiyyah a duhu, har ta kai da tambayarta “dan kaucewa kamar yaya shin? In ji dai ba kauce hanya ta addini ba?”
Ammara tace “kusan hakane, amma ba sosai ba, zauna nan ‘yar uwa kiyita walagigin bin likitoci suna jagwalgwala miki mahaifa suna cika ki da surutan wofi, kuma basu da maganin da zasu baki ki haihun”.
Nan ta bude wayarta ta nuna mata hotonta tare da maigidanta da kyawawan yaransu maza biyu kanana kamar haihuwar kwanika, nan ta kara brainwashing Safiyyah wadda a lokacin nan ba abinda ta dauka a matsayin farin ciki da kwanciyar hankalin dan adam sama da ‘ya’ya.
Haka Ammara tayi ta kwance kan Sophie, tana kara zurmata ga bin irin hanyar data bi ta samu haihuwa. Wadda har zuwa lokacin ta ki fitowa fili ta fadeta sai indirectly take maganar.
Allah sarki Sophie, ita da kanta bata san ta zama desperate ga son haihuwa ba sai yau. Ta yadda har ta dan rasa kyakkyawan tunaninta ta kuma kasa zurfafashi, tarbiyyar shekaru kusan 28 da ilmin addini da mahaifinta Malam ya bata basu sa ta yi tunanin meye ita wannan hanyar da ake ta muku-muku da ita ba’a fito da ita fili an gaya mata ba?
Haka ilmin bokonta duk bai yi amfani a wannan lokacin ba. Biyan bukata kawai take nema.
Ammara tayi nasarar yiwa Sophie famfo mai yawa a wannan danzaman nasu, har take ce mata ta rabu da zancen kawai na mijinta (Zayyan) da yake cewa shi bai damu ba, tace zance ne kawai na mazan da ke son kwanciyar hankalin matansu, karya yake yi yace wai bai damu da haihuwa ba karya ne, maza sun fi mata son ‘ya’ya.
Ta kara jefa Sophie a tagumi da damuwa mai tsanani. Tace “da yawan alfarmomin da take samu yanzu a wurin mijinta (wanda babban dan siyasa ne a jihar Kano) a baya data kasa haihuwa bata samesu ko guda ba”.
Tace mata “saboda matsalar rashin haihuwa taga bala’in dangin miji kala-kala, dana uban miji, don mahaifiyarsa ta jima da rasuwa.
Tace bata samu daidaito da martaba a idon su ba sai bayan data yi musu haihuwar fari, Da namiji, tace uban mijinta ya kafa mata karan tsana, har ya taba yin umarnin da aka saketa saki daya, tace da Safiyyah “a karshe dana ga ba sarki sai Allah sai na bazama, na hada da (dan kaucewa) sannan na samu biyan bukata.
Wadda a halin yanzu ta sayomin kwanciyar hankali a gidana, da zama lafiya da miji na da ubansa da ‘yan uwansa.
Nice tauraruwarsu, tunda na aje masu ‘ya’ya kuma maza”.
Safiyyah wadda a cikin kowanne harafi na labarin da Ammara ke bata soyayyarta da da burinta da haihuwa na karuwa (to an extent), haka tsoron ta da rashin samunta shima yana ta kara ninkuwa. Har taji a ranta ko dai itama ta bi hanyar data bulle da Ammaran, komai tsananinta?
Wadda har yanzu dai bata kai ga yi mata bayaninta baro-baro ba, aka kira Safiyyah ganin likita, Ammara tace zata jirata ta fito itama ta shiga ta fito, sai su karasa maganar.
**** **** ****
Safiyyah a teburin Dr. Galadanci. Bayan ta gaya mata matsalarta na cewa shekarun ta 8 da aure babu haihuwa babu alamarta, likitar tayi mata ‘yan tambayoyi na cewa ko ta taba ganin likita akan matsalar? Ta ce eh, sun je ABUTH da mijinta ba jimawa sun ga gynaecologist, sai Dr Galadanci ta nemi ganin result din ABUTH din.
Sakamakon Safiyyah na ABUTH shi likitar ta karba ta fara budewa, sai taga cewa ba wani banbanci da duka gwajegwajen da itama zatayi mata. Duk da haka Dr. Galadanchi tayi nata binciken yadda ya kamata ta kuma ce Safiyyah ta koma reception ta dan jira fitowar sakamako.
Wannan gap din na jiran sakamako ya baiwa Ammara da Safiyyah damar sake hadewa a waiting lounge suka dora daga inda suka tsaya kafin sakamakon Safiyyah ya kammala.
Safiyyah ta kasa maida kwadayinta kan haihuwa da labarin Ammara, har tace da ita don Allah ta gaya mata kowacce irin hanya ce hanyar data bi ta samu haihuwa, Ammara tace “da dan wuya fa, amma in har kin yarda yafi komai sauki, tunda dai ba a garinnan na Kano kike ba zuwa kikayi kuma a yau zaki koma inda kike, mafi kyau shine a yau muje na raka ki, da zafi-zafi akan bugi karfe ‘yar uwa, daga can zaki samu motar Zaria tunda kan titin Zaria ne kauyen yake dama, ba sai kin dawo ta Kano ba zaki samu mota daga can har Zaria. Tafiyar mintuna talatin ce kacal daga Kano zuwa kauyen na Daka-Tsalle.
“Kauye kuma?” Safiyyah ta tambayi Ammara, ta ce “Eh a can ne malamin yake. Koyaushe aka je kuma ana samun shi saidai layi”. A can kasan ran Sophie taji dan tsoro, ta ji fargaba da darsuwar wani abu, saboda dai ta fahimci komai yanzu, wato ta hanyar bin malamai ake samun haihuwa.
Amma data tuno gore-goren Mama Fatu da ‘ya’yanta, ta kuma tuna cewa ‘ya’ya fa zata samu itama kamar kowa, sannan wadanda su kadai ne zasu dorar da soyayyarta da Zayyan dinta, da kara mata matsayi a zuciyarsa data mahaifiyarsa ta daina kyararta, kuma sune kadai (‘ya’yan) zasu tsaya tare tare da ita a ranar da kowa ya gujeta ko ya juya mata baya ko ranar da bata da karfi ko ta tsufa, amfanin haihuwa da ‘ya’ya yanada yawan da bazai kidayu ba, sune zasu kula da ita idan bata da lafiya, sune….sune…sune komai na uwarsu kamar yadda suka zama sanyin idaniya ga Ammi, aminanta abokan shawararta, itada Sabah, Rayyah da Rayha.
Amfanin haihuwa yanada yawan da bazai lissafu ba, kuma damuwar rashin ta yana da girman da zaisa ka gane dalilin halin yanayin dokantuwa da desperation din da ita Safiyyah ta samu kanta a ciki.
Har sai ranar daya faru gareka, wato ranar daka budi ido shekarunka kusan goma da aure babu ko barin ciki balle batan wata a tare da kai sannan zaka gane irin yanayin data ke ciki.
Sakamakon binciken Dr. Galadanchi dai ya nuna kusan abu daya dai dana Dr. Muwadda Shinkafi ta ABUTH. Bakinsu yazo daya cewa; polycystic ovary syndrome (pcos) shi ya hana Safiyya ovulating.
Fasihiyar Likitar tace “amma ki kwantar da hankalinki ke da mijinki duk kuna da kwan haihuwa, nashi kwan lafiya kalau yake. Amma naki kwan baida kwaliti (inganci) a dalilin cutar ‘polycystic ovary syndrome’.
PCOS cuta ce wadda ‘cyst’ wato ‘maruru’ yake fitowa a cikin ‘ovary’ din mace (wajen kwan haihuwa) wanda yake hana mace ‘ovulation’ har hakan ya haifar da rashin haihuwa. Akwai mata da yawa dake fama da lalurar pcos wadanda basu san sunada shi ba, haka akwai da yawa da alamun pcos ko daya baya nunawa a jikinsu, misali daga cikin alamominsa akwai fitowar gashi a kirji kona kasan fuska da sauransu.
Kinada pcos wanda alamominsa basu nuna a jikinki ba. Kuma babu alamun cewa naki na gado ne. Pcos an fi gadonsa, amma akwai wadanda keda shi ba tareda sun gada ba. Ana kuma iya maganceshi a hankali.
Ta taimaka mata da shawarwarin da suka kamata ta bata, ta rubuta mata magunguna masu kyau da tsada da zasu taimaka mata ta dauki ciki da taimakon Ubangiji dana treatment data dorata akai. Ta kuma bata lambar wayarta don su dinga communicating kai tsaye ta waya ba sai tazo ba, akan duk wani cigaba da aka samu ko akasinsa, tace ta yarje mata kiranta kai tsaye.
Dr. Galadanchi tace ita tana ganin matsaloli na pcos iri-iri daga mata wanda ke hana su haihuwa. Tace “a yanzu dai babu likitan da zai ce miki ga hakikanin lokacin da zaki iya samun haihuwa sai dace, maigidanki na bibiyi nashi results din daga binciken ABUTH ya nuna lafiyarshi kalau, don haka kada ki fidda rai, da taimakon Allah zaki iya haihuwa a sanda Allah ya nufa with treatment, ki dage da shan magungunan nan dana rubuta miki”.
Wannan bayani ya kara jefa Safiyyah cikin damuwa maimakon ya sanyaya mata, har fiyeda damuwar da result din ABUTH ya saka ta. Wannan ya sa ta kara amanna da maganganun kawarta ta Standard, wato Ammara, tun kafin ta baro gaban teburin likitar.
Na cewa ba abinda likitoci zasu iya kullawa wanda baya haihuwa, sai dai su saka ka kayi ta asarar kudinka wajen sayen kwayoyin banza, da surutun wofi mara tabbas wadanda bazasu taimaka maka da komai ba.
A iya hange da tsinkayen Sophie na lokacin sun amince ta yarda da shawarar wannan matar kawai, in dai hakanne kadai hanyar da zata samar da haihuwa gareta da gaggawa, akwai alamun gaskiya sosai a cikin maganganunta, saboda babu alamun karya ko damfara a tare da ita, ko wani alfanu takeson samu daga gareta, face taimako da haduwar jini, don da ganin ta tafi karfin neman komai a wajen wani.
Allah shaidarta ne akan cewa tayi addu’a kuma tana kan yi, ta sha duk wasu tsadaddun magungunan da Dr. Shinkafi ta rubuta mata na tsayin lokaci, wadanda ta duba ta ga duk kusan irin wadanda Dr. Galadanci ta rubuta mata yanzu ne ba wani banbanci mai yawa. Amma Allah bai sa ta dace ba. Watakila mafitar kadai itace wannan da Ammara ta kawo.
Watakila Allah ya nufeta da zuwa Standard Hospital ne yau don ta samu mai taimaka mata, don haka bari kawai tayi kundumbala ta bi shawarar Ammara, wannan dogon bayanin na likitoci ya isheta, bata ko son sake jinsa.
Tana wannan tunanin sai ga Ammara dinma ta fito itama daga ofishin likitar, take gayawa Safiyyah cikin far’a,
“an daure min bakin mahaifa (IUCD insertion), muna iya tafiya yanzu”.
Suka fito tare, Ammara ta bude motarta wata kankanuwar (Peageout 507). Ta bude ta shiga ta kuma mika hannu ta budewa Safiyyah kofar gefenta tace,
“in har kin yarda da shawarata kin kuma yarda bazan cuce ki ba, to kawai ki shigo mu wuce in kaiki Daka-Tsalle. Daga can zan saki a motar Zaria”.
Without a second thought Safiyyah ta amincewa ranta bin Ammara gidan malami. Ta kama murfin mota ta bude tashiga ta zauna ta rufe kofar.
Ammara ta fizgi motar da gudu suka harba kan titi. Suka bullo ta Tarauni suka hau kan Titin Naibawa Zaria Road, wanda titi ne da zai kai ka har garin Kura, ya kuma mike dakai babu shan kwana har Daka-Tsalle.
Suna tafe a hanya Ammara na tuki tana kara yi mata famfo irin na matan masu kudi da suka saba da harka da malaman tsubbu. Take ce mata “ta saki ranta, ta ganta kamar ace “kyat!” ta zura da gudu. Tace ai da yawa yanzu mata wayayyu sunfi ganewa zuwa wajen malaman tsubbu akan duk wasu matsaloli da suka sha musu kai ba haihuwa kadai ba, ke har rashin lafiyar da aka rasa gane kansa da gindinsa malaman kauye sunada maganinsa, hakan yafi musu sauki fiye da su dauwama cikin bakin ciki da ciwon, bacin rai da inferiority complex, irin na rashin daukar ciki da haihuwa kamar na kowacce mace, da kuma bibiyar likitocin da bazasu kulla musu komai ba sai karerayi da surutan banza.
Tace Allah na tuba duk da ana cewa zuwa wajen malaman tsubbu haramun ne, to ai Allah mai afuwa ne mai gafara, bayan bukatarka ta biya kawai sai kayi sahihin tuba, da niyyar bazaka sake aikatawa ba, ba shikenan ba?”
Safiyyah sai ta soma shakkah, ta soma tunanin anya ita a matsayinta na Safiyyah diyar Malam Usman wanda ya koyar dasu Tauheedin cewa ba’a yiwa Allah wayo, kuma ba’a tursasashi, saidai ayi ta rokonsa, anya wannan hanyar ta dace da ita?
Idan ta bulle da Ammara, itama zata bulle da ita ta samu haihuwa?
Ba duka abinda yayi wa ‘A’ ne yake yiwa ‘B’ daidai ba.
Anya ma wannan hanya ta kaucewa kamar yadda Ammara ta kirata ta arziki da Alheri ce a gareta? In Ammi da Malam da Zayyan suka ji ta taka kafafunta wajen bokaye neman haihuwa wane irin hukunci zasu yi mata? Tunda dai taji ana daga baya sai ta tuba ta shiga rudani.
Amma as a desperate and hopeful as she is da haihuwa, sai tace bari dai ta daure, in har zata samu haihuwa shi Allah Gafurun Raheemu ne.
Daidai lokacin da suka isa dan karamin kauyen, daga can nesa Ammara ta faka motar tace gangarawa zasu yi cikin gonar can dake gabansu, har su tadda waccan bukkar da suke hange daga nesa.
Haka suka dage zannuwansu sabida duwatsu suka soma taka tudu da gangare suna shiga cikin gonar.
Cikin sa’arsu basu sha wahalar samun dogon layi bama, mata biyu suka tarar akan layin, don haka suka zauna har suka gama suka fito kafin suma suka saka kai a bukkar.
Jikin Safiyyah ya soma sanyi da ta yi arba da irin abubuwan dake cikin bukkar, da babu kwana-kwana ko wani shatale-tale sun fi kama da kayan tsafi.
Babu Ayar Alqur’ani ko daya ko Gafakarsa, irin na shigifar mahaifinta, wanda shima yake amsa sunan malami kuma ake zuwa wajensa neman taimako.
Nan Qaho ne da kawunan matattun dabbobi, can korrai ne da busassun matattun tsuntsaye, da fatun namun daji babu kyan gani sai doyi suke, korayen cike da wasu bakaken abubuwa marassa kyawun gani a cikin kowacce kwarya suna motsi, wanda hakan ya baiwa bukkar smell mara dadi mai hamami da wari, daga saman bukkar kuma an sakale konannen kan Damisa, abun dai zallah kyankyami. Saida ta hadiye numfashinta.
Wani dukunkunannen mutum ne zaune a kan fatar Akuya, dan tsurut dashi kamar (Dwarf) wato (Wada).
“Ku koma ku shigo da kafar hagu, kuma kada ki kara yi mana sallama.
Tuni ai Tsimbirbira ta san da isowarki Safiyah ‘yar Usmanu da Hafsatu matar Zayyanu”. Bokan yace da Safiyyah cikin fushi.
Saura kadan Sophie ta saki fitsari a wando, ko ta taka da gudu ta koma. Ammara ta gane hakan, sai ta rike hannunta cikin karfafawa ta jata suka koma suka yi yadda yace din.
“Maraba – lale da uwargidan Zayyanu. Magajin Bello Rafindadi masu kashin arziki na gidaje har ‘ya’ya da jikokinsu.
‘Ya’ya tsakaninki da Zayyanu akwai su, saura taki kadan su riskeku.
‘Ya’Ya fal! Har sai kince sun isheki”.
Safiyyah ta kara tsurewa, jin ya ambato sunan wadanda suka haifeta da Zayyan, kuma har sana’ar gadon gidansu Zayyan din ya sani, zuwa yanzu ta fara gayawa kanta gaskiyar lamari gidan BOKA ta kawo kanta, bama na malaman Tsubbu ba, irin masu aiki da aljanu da rauhanai don gani har hanji, wadanda kullum Malam yake gaya musu ziyartarsu don neman biyan bukata halakace babba. Domin mu’amala dasu “shirka ne”.
Suka yi zaman Rakuma a gaban sa, kamar masu neman gafara. Ammara tace da shi “itama dai ba sai na fada ba na sani, tazo neman haihuwa ne itama. Allah ya taimaki Tsimbirbira a taimaka mata, saboda yadda naji dadin taimakon da aka yi min na cika alkawarina na kawo duk mai bukata.
Itama gata na kawo ta Tsimbirbira ta share mata hawaye (wa’iyazu billah). Haihuwa kawai take so, walau mace walau namiji, da gaggawa”.
Tsimbirbira ya fashe da dariya yace “tuni ai labarinta ya iso garemu da bukatarta tun kafin isowarta.
Abu daya zuwa biyu muke bukata daga gareta; jan zakara da jar kaza (fingi-fingi) da za’a hada kwanciya, sai kuma kwan haihuwarta da maniyyin mijinta. Za’a yanka bunsuru a baiwa Tsimbirbira jinin, mu zamu dauki kwan haihuwarta da kanmu, bayan kwana biyu kuma zata dawo ta kawo mana na mijinta, wanda shine mahadin da za’a hada maganin da zan bata.
Shekara bazata zagayo ba sai ta haifi ‘yan biyu maza biyu zar”.
Safiyyah was shocked and frightened yanzu kam, don ta gama amanna ta kusa fita daga addinin musuluncima gabadaya, saboda rashin tawakkalin ta da Zayyan ya jaddada mata karba da muhimmancin yinsa ga musulmi.
Kamar yaya ta bada kwan haihuwarta ta ina za’a dauke shi? Da sperm din Zayyan kuma, ko ta wace hanya hakan zata yiwu?
Don haka ta juya a firgice ta dubi Ammara da fuskar tsoro da firgici mai yawa.
Nan Ammara ta kashe kunya tayi mata bayanin da a baya bata yi mata ba dalla-dalla. Ta yi mata ‘yar rada (whisper) a kunnenta.
“Ai dama na gaya miki sai an dan kauce hanya, sannan za’a samu biyan bukata, ke zaki san yadda zakiyi ki kawo masa duk abinda ya bukata, na jikinki kuwa zaku shiga daga cikin shigifar can ne ya dauka, ta hanyar saduwa dake! Mijinki ba ganewa zaiyi ba”.
Safiyyah ido ya raina fata. Boka ya mike ya shige dan dakin wai yana jiranta, ta bishi da kallon razana da firgici mai yawa cikin kyawawan idanunta.
Ammara ta shiga convincing dinta cikin kyakkyawan lafazi cewa “is just a simple thing, bai fi ya tara dake na ‘yan mintunan da basu gaza biyar ba, kokari zaki yi kawai ki jure ki daure warin jikinsa, don kin ganshi dan tsurut dinnan amma ba karamin fitinanne bane, and you will enjoy him morethan your husband…..”.
A wannan lokacin ne Safiyyah ta samu kalmar “Innalillahi wa’inna Ilaihi Rajioun” ta fado cikin kwakwalwarta, bakinta kuma yayi maza ya kama, ya furtata a fili.
A hankali ta runtse idanunta. Nutsuwarta da tsoron Allahnta suka dawo jikinta. Taji ta tsani haihuwar ma bakidaya in dai son ta ne yau ya kawo ta ga wannan halakar.
Ta tuno tarbiyyar da dattijan iyayenta suka kare rayuwarsu a dorata a kai. Sun kuma sha gaya mata akan damuwarta na rashin haihuwa cewa babu mai baka abinda Allah bai ga damar baka ba.
A yau a bayan idon Ammi, Malam da Zayyan gashi rashin hakurinta ya kawo ta ga halaka har guda biyu; shirka da zina, zinar ma da aurenta….. yau ga inda rashin tawakkalinta, da rashin jin lallashin mijinta ya kawo ta, wai za’a yi zina da ita da aurenta…. kuma da wannan kazamin mushrikin.
Kafin Ammara ta ankara Safiyyah tayi wuf! Ta mike ta kama hanyar fita bukkar. Tana fitowa kuma sai ta taka da mugun gudu. Gudu take da gaske tun karfinta kamar mai gudu akan iska, ita kanta bata san ta iya gudu ba sai yau, domin gani take kamar Bokan zai biyota ko yasa rauhanansa sau daukota su maida masa ita kota wane hali.
Gudu take babu waiwaye har ta samu ta fita daga gonar, ta shiga ainahin cikin kauyen Daka-tsalle.
Jama’ar kauyen na kallonta sai gudu take kamar wani ya biyota, ba tareda ta san inda take jefa kafarta ba, ba kuma ta waiwaye, tana rokon Allah in mafarki ne take yi saboda damuwar rashin haihuwa yayi gaggawar farkar da ita haka daga wannan mummunan mafarkin.
Gudun neman tsira, nadama da ceton Imani Safiyyah ke yi, wanda yafi kama da gudun famfalaki, har ta hau kan babban titin kauyen, ba tare data sani ba. Bata lura ba wata mota kirar Honda ta taho da gudun gaske duk kokarinta na kaucema Safiyyah hakan bai samu ba. Direban kawai ganin Sophie yayi ta fado gabansa, yayi kokarin cin birki ya hango trailer a bayan sa, dole ya zabi bige Safiyyah don ceton kansa da motocin dake bayansa, wadanda cin birkinsa a lokacin zaisa trailer din ta danne su gabadaya.
Haka ya kwashe Safiyyah ya jefar a gefen titi, sannan shima ya gangara gefen titin ya tsaya yana ambaton “innalillahi wainna ilaihi rajioun”.
***** ***** *****
Motocin da ke tahowa daga bayansu duk suka yi wucewarsu babu wanda ya tsaya, yamma tayi sosai, burin kowa ya kai gida ko gari mafi kusa kafin shigowar dare.
Sai tsirarun mutanen da abin ya faru akan idon su ne suka kawo agaji, suka rufu akan Safiyyah da aka wancakalar a gefen titi, suka taimaka masa aka saka ta a motar wanda ya bigeta din. Wani dattijo ya shiga gaban motar don nuna musu asibiti mafi kusa. Safiyyah kwance a bayan motar, aka doshi babban asibitin garin Kura da ita.
Da kyar likitocin suka yarda suka amsheta saboda babu report din ‘yansanda, wanda ya buge tan yace basu hadu da police ko daya ba daga Daka-Tsalle har suka iso Kura, don haka asibitin ne suka kira police aka rubuta report, shikuma ya biya kudin duk treatment din da ya kama za’a yi mata.
An yi sa’a Sophie bata samu karaya ba amma dai akwai gocewar kashin kafa dana hannu, sai kananun raunika da kukkujewa, abinda ya daukesu har bayan isha’I ana mata treatment kafin Safiyyah ta fara dawowa hayyacinta.
**** **** ****
A can kuma Tudun wadar Zaria, wato gidan Anti Dije, hidimar biki data jama’a bata sa Antin ta gane Safiyyah bata nan tun sassafe ba. Sai bayan azahar da Rayyah kanwarta ta gane rashin dawowarta gidan, ta tuno tun safe data ganta tana shiryawa lokacin su Sabah suna barci ita kuma ta farka tace mata zata dan fita ne, amma yanzu zata dawo, to bata dawo din ba.
Kuma har la’asar ta kawo kai Safiyyah bata dawo ba wanda hakan yasa kannenta da suke tare a daki daya duk suka damu, suka soma kiran wayarta ana cewa “not reacheable”.
Daga bisani Sabah ce taje ta samu Anti Dije cikin kawayenta cike da damuwa, a lokacin ana shirin tafiya Mother’s Eve. Tace.
“Anti Dije, ko Yaya Safiyyah ta gaya miki inda zata je ne? Tun safe fa data fita bata dawo ba, kuma bata gaya mana ina zata je ba”.
Anti Dije ma sai a lokacin ta ankara tun safen itama bata ganta ba, jama’a ne suka sa hankalinta bai kai wurin ba, tace
“to ina Safifi zata je haka tun safe bata gayawa kowa cikinmu ba? Amma kira Zayyan ki tambayeshi, bazai kasa sanin ina taje ba, babu inda zata je bada saninsa ba, in kin bibiya ma suna tare”.
Sabah ta kira Zayyan, bugu daya ya dauka suka gaisa yana ta tsokanarta da amaryar robarsa, yadda ya saba tsokanarta don ita ke bin Safiyyah a haihuwa, amma bata biye shi a wasan ba yau, cikin damuwa tace,
“Yaya Zayyan, aunty Safiyyah ta gaya maka inda zata je ne in bi bayanta?”
Yace “kamar yaya? Ba kuna gidan Anti Dije ba?” Sabah ta kara shiga cikin rudu, ta ce “eh, duk muna can, kuma tare muka kwana da ita a daki daya, amma da safennan tace ma Rayyah zata dan fita bazata jima ba, amma har zuwa yanzu karfe hudu bamu ganta ta dawo ba, kuma wayarta bata shiga, Anti Dije tace watakila kuna tare a kiraka a ji”.
Shima ya tuna da safe wajen karfe goma sun yi waya da ita, lokacin isarta Standard Hospital kenan, tace masa “she will call him back” bata jinsa sosai, saboda tana cikin mutane, sai ya dauka ‘yan bikin gidan Anti Dije take nufi. Nan kuwa a lokacin tana magana da kawarta ta kan layin asibiti Ammara ne. Tun daga lokacin kuma bata kira shi din ba, shima kuma yaje Batsari gidan Yayarsa Zubaida ta tsare shi da zance irin nata na kullum, wato na kushe rashin haihuwar Safiyyah har yau. Don ma har yau basu san wanene mara haihuwar tsakanin shi da ita ba, da bai san ya zai kare dasu ba.
Zubaidah tace “sun lura Safiyyah ta tsare gabansa da bayansa, ta hana shi auren diyar kowa, ta shiga rigar arziki tana wadaka son ranta, tana bakin cikin kada wata tazo ta ci, ta hanashi auren da zai karu dashi sai tatse shi suke itada iyayenta kamar hanji.
Ita kuma Safiyyar ta kasa tsinana masa komai tunda har yau ta kasa mayar da shi Uba, cikakken namiji mai iyali kamar kowa.
Tace “kwarai zan so sanin me Safiyyar nan ta taka da take juyaka har haka Baffa, ita ba wani shahararren kyau ba, ita ba aji ba (class) ita kuma ba iya kwalliya ba, kullum ka ganta cikin ragga, wai ita me addini, ko sabida sun saka sunanka a minjaye sun wanke sun baka ka shanye ta bakin Mama?”.