Kurkukun kaddara book 1 - Chapter 39
Kurkukun kaddara book 1 Chapter 39: Kurkukun kaddara book 1 Chapter 39. Jin haka yasa ta daidaita natsuwarta, ta kasa kunne tana jiran Jin me zasu Ce,…
3,315 words
Jin haka yasa ta daidaita natsuwarta, ta kasa kunne tana jiran Jin me zasu Ce, wanda take tunanin shine team leader ɗinsu, wanda ke zaune saman Sofa 2 seater akanshi ta tsayar da idanuwanta, wata irin ƙirar ƙarfi ce gare shi, taban al'ajabi, mai matuƙar jan hankali da tsoratarwa, kai daga ganin wannan babu wasa acikin lamuranshi, baƙaƙen kayan sun zauna mashi sosai, sun bayyanar da zazzafar surarshi, tayi tunanin shi zai yi mata magana amma sai taji yayi shiru,
Takun tafiya ta kuma jiyowa ta can 6angaren, Wani ƙaton ne Ya fito sanye da bakaken Kaya, Hannunshi a ruƙe da plate me ɗauke da Glass Cup, ruwan sanyi ne aciki, a saman table ɗin dake a kusa da sofa ɗin da aneelerh ke a zaune ya ɗaura plate ɗin, Cikin girmamawa yace mata"Zata iya sha" ya ambaci hakan tare da juyawa Ya bar falon, duk fa waɗannan Garadan mazan na a kewaye da ita, Da farko taji tsoron tasha kada ace An sanya mata wani abu, amma daga baya saita kai hannu ta ɗauka ta ɗan kur6i ruwan, sanyi gare shi ga daɗi, bayan ta ajiye Glass ɗin, Sai ga wannan katon daya kawo mata ruwa, Ya dawo Cikin falon hannunshi ruƙe da Laptop Tsadaddan gaske, Adai dai gaban aneelerh Ya ajiye laptop ɗin saman table gefen plate ɗin da ya kawo mata ruwa,
Daddana laptop ɗin Ya shiga yi Cikin ƙwarewa, Aneeelrh dai ta zuba ido tana jiran ganin me za'a nuna mata,
Bakomai bane Ya bayyana akan screen ɗin Laptop ɗin nasu, Face Hotonsu da su kayi ranar birthday ɗin Angel, Su Huɗu, Angel ce a tsakiyarsu, Taj yana agefenta ya zuƙunna, Aneelerh da Uzair Suna atsaye fuskokinsu ɗauke da murmushi,
Tsananin mamaki ne ya kama Aneelerh ganin wannan hoton, duk da tasan Zasu Iya samun shi a social media, saboda sunyi share ɗinshi a insta da Facebook, twitter da tiktok, hada videos na birthday ɗin angel,
"Kin gane su"? Muryar mutumin ce ta katse mata tunaninta, da sauri tace"Eh, ƴan uwana ne," ya nemi ta yi masu bayanin menene alaƙarta da su" da hannu ta nuna mashi hotonta dana uzair tace mijina ne, wannan kuma ɗan uncle ɗin shi ne, Sunan shi Tajuddeen, Ita kuma yarinyar Ɗiyarshi ce, sunanta Unaisa amma muna kiranta da Angel,'
Jinjina kai ya yi tare da cewa"Mu jami'ae ne masu zaman kansu, muna da interest akan case ɗin 6acewarsu, that's the reason why muke Bibiyarki, saboda sanin cewa ke kaɗaice zaki Iya bamu bayanan da muke so, Zamuyi maki tambayoyi, da zarar kin amsa mana zamu sallame ki ki tafi, kuma bazaki sake ganin mu ba," ta amsa ma shi da toh,
Tambayoyi suka shiga yi mata, tun daga kan alaƙar dake tsakanin su tajuddeen da Uncle abdallah har izuwa kan Alhaji ubaid, da ita kanta hada iyayenta duka saida su ka yi mata tambayoyi a dangane dasu, hatta Benazir sai da suka yi mata tambayoyi akanta, duk ta amsa masu wanda ta sani, abunda ya ɗaure mata kai hada ƙawarta Aisha suka Yi mata tambayoyi akanta, game da yarda akai mahaifinta yayi mata korar kare daga gidan shi, Lamarin ya ɗaure ma aneelerh kai, taya akai suka san kowa da take atare da shi? Su wanene waɗannan jami'an masu Uniform baƙaƙen Kaya, Taso ta tambayesu daga ina suke, amma sai suka ce mata, basu bata iznin tambayar komai agame dasu ba, Sannan suka ce ta sawa ranta cewa a mafarkine Ta haɗu dasu, kada tayi tunaninsu kuma kada ta kuskura ta yi gigin faɗa ma wani agame da su,
bayan sun kammala Yi mata tambayoyin har bakin motarta suka rakota, ta buɗe ta shiga, suka yi mata godiya taja motar ta fuce daga Cikin gidan, Tana cikin yin driving saman titi Junaid Ya farka yana ta tsala kuka, a dole ta kashe motar daga gefe ɗaya ta rumgumo shi ajikinta tana lallashinshi, yace mata Yunwa yake Ji, ta bashi abinci yaci," tunawa da madararsa da ta ajiye mashi a backseat na motar yasa ta juya ta kai hannu ta ɗauko mashi ita, acikin bottle take, ta cire murfin ta kafa mashi abaki yana sha, yayin da ta shiga zurfin tunani, abun ya tsaya mata aranta, ita gaba ɗaya rayuwar duniyar tsoronta take ji, meya faru dasu uzair? Shiru ba labarinsu kusan shekara huɗu? Sannan ga wasu mutane suna Bibiyar rayuwarta da sunan jami'ae ne, Anya kuwa bazata gudu tabar ƙasar nan ba, na wani lokaci? Gani take kamar zata rasa ɗanta ne, kamar yadda ta rasa mutun ukun nan masu mahimmanci, tana cikin yin wannan xancen zucin junaid ya fashe da kuka yana faɗin"tasa mashi madara a hanci," da sauri takai idonta kanshi, fuskarshi ta 6aci da madarar, batasan ya akai ta janye robar daga bakinshi ba ta kwafa mashi a hancin shi, rufe bottle ɗin tayi tare da ajiyeta gefe ɗaya, ta zaro hanky cikin ƴar purse ɗinta ta shiga goge mashi madarar, bayan ta kammala ta maida hanky a cikin purse ɗin, Ta rungumeshi ajikinta tana lallashinshi, har saida yayi shiru lamo ajikinta tukunna ta tashi motar ta miƙi hanya ta nufi gida,
Lokacin da ta koma Gida, a palour ta taras da Mami da wasu ƙawayenta suna fira, sai da ta fara gaishe su, suka amsa mata, tare da miƙa mata hannu ta basu junaid, Ita kuma ta wuce cikin ɗakinta, tana shiga ta rage kayan jikinta ta faɗa toilet tayi wanka, ta fito waist ɗinta a ɗaure da towel tana kokarin zama saman mirror chair, alert ya shigo Cikin wayarta dake ajiye saman mattress, da sauri takai hannu ta ɗauki wayar, kamar a mafarki take ganin credit alert ɗin da aka turo mata via dollar account ɗinta, wanda a kuɗinmu na nigeria kuɗi ne bana wasa ba, har saida ta dafe ƙirjinta da hannu ɗaya, ta shiga ruɗu akan wannan kuɗin da aka turo mata, bayan ita ba wanda ta ba acct number ɗinta, Shi kanshi dollar account ɗin ta jima bata yi amfani dashi ba,
Komawa ta yi gefen gadonta ta zauna hannunta ruƙe da wayar tana kallonta, wani saƙonne ya kuma shigowa cikin wayarta, cikin harshen turanci aka rubuto shi, karantawa tayi kamar haka
_mun gode da haɗin kan da kika bamu_
Nan take ta gane cewa Jami'an nan ne suka Turo mata da kuɗin, ajiyar zuciya ta sauke tare da jefar da wayar saman pillow, Ta gyara kwanciyarta saman mattress ɗin, Yayin da idanuwanta ke fuskantar ceilling, zuciyarta a cunkushe take da tunani kala kala duk akan Jami'an nan, Su kuma ko daga ina suke? Waye ya sanya su bibiyar case ɗin su tajuddeen? amma tasha ruwan mamakin Irin Ƙirar jikinsu, especially wannan ɗayan daya zauna saman sofa wanda take tunanin shi ne team leader ɗinsu, Kamar shi ya ƙera kanshi, daga gani dai jami'ae ne su bana wasa ba, ita dai fatanta Allah ya tabbatar da alkhairi akan bincikensu dana su Uncle bash,
Ta yi zurfi acikin tunaninta, tajiyo muryar baby junaid yana faɗin"Mommy kizo inji mami, " daga kwancen da take ta juya tana kallonshi, ya ruƙe qugu abakin ƙopar ɗakin, yana ta faman zumbura baki yace"Bake kika sanya mun madara a hanci ba, ae na faɗa mata, tace zata rama mini"
Yadda yayi maganar ne ya bata dariya, har fararen haƙoranta suka bayyana, Miƙa mashi hannu tayi"zo nan My baby boy" maƙe kafa ɗa yayi"Ae baki sona, Tunda kika sanya mun madara a hanci," saukowa tayi daga saman gadon ta wuce wurin closet ɗinta, Jallabiya ta ɗauko ta zura ta ajikinta, kafin ta dawo ta nufi inda yake a tsaye, ta zuqunna agabanshi tare da kai hannu tana shafa sumar kanshi tace"My baby boy, nifa mommynka ce, ni na haife ka, bani da tamkarka aduniyar nan inasonka fiye da kaina, jinka nake kamar bugun zuciyata,' takarasa maganar tare da sanya hannu ta ɗauke shi, kafin ta mike ta wuce cikin falon,
A lokacin ƙawayen Mami sun tafi, A zaune ta same ta saman Sofa, Riga bubu ce a jikinta, idonta na akan plasma tv, tashar arewa 24 take kallo
Takun tafiyar aneelerh ne ya janyo hankalinta, ta juyo tare da kallonta, fuskarta asake tace"My daughter Kinyi mana laifi, Junaid ya faɗa mini abunda kika yi mashi acikin mota, ashe dama shirin kashe shi ki kayi"? cikin zolaya tayi maganar, Fuskar aneelerh ɗauke da murmushi tace"Kuskure ne mami bansan nayi mashi haka ba, kuma fa har hakuri na bashi amma shine bai kar6i uzirina ba," takai karshen maganar a yayin da take zama saman Sofa tare da junaid, Ya manne ma jikinta,
Kallon shi mami tayi"ka yafe mata ko in rama maka"? Ashagwa6e yace"nayi mata amma idan ta ƙara, afaɗa ma uncle bash ya sanya gun ya harbe mata kai," gaba ɗaya suka kwashe da dariya aneelerh tace"amma baka da mutunci junaid, uwar taka zaka sa a harba da bindinga? Idan na mutu ya zaka yi"? Watsa hannu yayi tare da cewa"Shikenan, sai aje kasuwa asiyo wata uwar" tuntsirewa su kayi da dariya, mami tace"Aku sarkin ɗumi, Kwanan nan xan sanyaka makaranta, tun da bakinka ya buɗe, ga surutu" Aneelerh tace"nima tunanin da nake yi kenan, ko islamiyace a fara sanya shi yana zuwa kafin asanya shi ta bokan," fira suka cigaba da yi har baby junaid yayi bacci a jikinta, aneelerh bata fada ma mami game da abunda ya faru da ita ba, kamar yadda jami'an suka gargaɗeta akan ta manta da komai nasu ta ɗauka tamkar mafarki tayi shiyasa taja bakinta tayi shiru gudun kada taja ma kanta,
*Back to Prison*
After One Day👌
Wani irin narkakken Jini ne mai kauri da ƙarni yake gangarowa ta cikin ƙoramar ruwan dake Gudana, Sassan Jikin mutun ta gani gunduwa gunduwa tsulundum acikin Jinin, Hannu tasa ta dafe kanta tare da fashewa da matsancin kuka na fitar hayyaci,
A firgice ta farka daga baccin da take yi sakamakon bugun ƙafarta da aka yi, wata irin Zabura Ta yi tare da miƙe wa zaune, Tana binsu Da Kallo, ɗaya Bayan ɗaya, Suna a kewaye da gadonta, Batool Hanna hibba, Azeeza, yasmin, eve, javed Sai kiran sunanta suke Yi suna tambayarta lafiya? Me take ma kuka? Abunda ya faru suna a kwance saman gadajensu suka soma Jin shessheƙar kukan angel, Hakan yasa suka yi gaggawar zuwa gaban gadonta don suji dalilin yin kukan nata,
"Angel meya faru ne? Duk kin bi kin ruɗe? ko kinyi mummunan mafarki ne"? batool ce ta jefa mata tambayoyin,
Ƙanƙame Jikinta Ta yi da hannayenta, wata irin zufa Ce ke tsastsafo mata ajikin fatarta, Sai faman zazzare Manyan idanuwanta take Yi, gaba ɗaya bata Acikin hayyacinta, tayi matuƙar tsorata da mafarkin da tayi, muryarta na kerma ta soma Magana"Ina parveen? ina rubina da Deeja an dawo dasu? Ko kuwa har yanzu? Takai ƙarshen maganar tana kallonsu Batool,
*Domin neman ƙarin bayani 08103884440 ko 08169856268 Text on whatsapp only banda phone calls, Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, Ga wanda ya shirya yin payment, zai iya yi mini magana, a ƙarshen wannan watan free pages zasu ƙare na Takun farko, zamu nutsa Cikin labari*
share fisabilillah❤👌*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*
*Daga alƙalamin Boss Bature✍️*
*Dedicated to Aunty kubra❤*
*Gargarɗi!!!*
_Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na book din nan ba ta kowace siga, ko a karanta mini shi a Youtube, ba tare da an nemi izni a wurina ba. Ko a haɗa mini document, idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi mini haƙƙina!_
E30-31
💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫
*_ALBISHINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE, SHAHARARRA KUMA K'ASAITACIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO DR MAMAN YUSUF LIKITAR MATA SOKOTO TANA FARINCIKIN SANAR DAKU CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE A FADIN NIGERIA DA NIGER HARMA DA WASU K'ASASHEN BAKI DAYA, KU SANI A DADE ANAYI SAI GASKIYA KUMA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI , INA MARABA DA MASU SIYAN DAYA KO SARI_* .http://wa.me/+2347069711327
*_munada zafafan kaya kamar haka ,_*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
*Hadin amarya budurwa ko zawara*
*Hadin uwar gida Mai taken (Maida tsohuwa yarinya)*
*Maijego package (virgin gain)* 📦
*Hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji*
*Sahihin maganin sanyi na Maza Dana Mata Wanda yake fatattakar sanyi cikin Dan lokaci*
*Maganin gyaran nono Wanda zai gyara maki nononki cikin Dan lokaci komai lalacewarsa*
*Maganin hips Wanda zaisa shape dinki ya fita kiyi kyau kema ki shiga jerin Mata masu aji*
*Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko kiyi kiba yar dai dai misali kema adinga binki da kallo Idan kin juya Sam rama batayi ba yar uwa*
*Hadin mallaka ba boka ba malam , akwai taimakon da muke bayarwa ga Mai butsarin namiji Wanda cikin ruwan sanyi Zaki dinga juya abunki , haka akwai Hadi na musamman Wanda komai rowar namiji sai kin samu alkhairin a wajanshi,*
*Muna da kalolin gumbuna masu Saka ni'ima sha'awa da dandano* *Kalolin garrika mash gyara gaban mace da jimawa ajiki* *Kalolin Zuma masu saukar da ni'ima Nan take da gamsar da maigida* *Kalolin tsumi Wanda cikin sauki zasu Baki ni'ima da dandano irin wadda akeso* *Kalolin matsi Wanda suke ciko da gaban mace matse gaban mace da bata Wani irin dadi da dadano* *Akwai set kala kala Wanda yawansh ya wuce na zayyanasu anan ga Mai bukatar kayana zata iya mun magana Kai tsaye ta hanyar danna wannan blue rubutun* 👉🏻 http://wa.me/+2347069711327
*Muna dahuwar zabo ,dahuwar kaza ,dahuwar kifi ,dahuwar zuciya ,dahuwar Yan shila ,dahuwar tsoka Tara ,dahuwar Kwan mallaka, dambun nama ko na kaza Wanda yake saukar da ni'ima da jimawa sosai ajikin mace*
*Idan nace zan rubuta komai da komai to wannan page din ba zai isheni ba ,Amma ga masu sha'awar siyan kayana Zaku iya mun magana Kai tsaye ta wannan number, haka masu sha'awa su dinga ganin kalolin kayana a status sumin magana ta wannan number sai nayi seving numbers dinki ta hakan ne Zaku dinga ganin kalolin kayana idan na daura* http://wa.me/+2347069711327
*Ina maraba da Mai siyan Daya ko sari Dr maman Yusuf likitar mata sokoto*
*❤❤❤PRISONERS❤❤❤*
"Angel Still ba'a dawo dasu ba, Abincin da muka rage musu tun jiya ya riga da ya lalace, da mun sani mun cinye shi," Hanna ce ta bata amsa, Azeeza tace"Yanzu shikenan baza adawo mana da su Parveenar mu ba? sun tafi kenan"? Muryarta a sanyaye tayi maganar, Hibba tace"Pls Azeeza stop sayin that bana jin daɗi, kuna karya mana zuciya, Tsohuwa fa tace za'a dawo dasu da zarar Sun samu lafiya," Eve ce ta kalli Hibba da tayi maganar tace"Hib kin manta lokacin baya? Ƴan uwanmu da muke atare dasu? Wasu in an ɗauke su ba'a dawowa dasu sun tafi kenan"? Idon angel akansu tana sauraronsu, kwata kwata bata acikin natsuwarta, tana matuƙar jin tsoron ta yi mummunan mafarki, saboda Xaiyi wuya mafarkinta yaƙi xama gaskiya, kafin zuwanta gidan kurkukun ƙaddara saida tafara mafarkin kasancewa acikin shi kuma sai ga shi ta tabbata, ta tsinci kanta acikin shi,
"Yakamata mu daina wannan maganar, Muna ƙara tayar wa junan mu hankali, Idan muka kwantar da hankalin mu, za'a dawo dasu ne," acewar Javed, yasmin tace"Yanzu me zamuyi toh? Ni nagaji da zama zugudum, " fuskarta a yamutse Tayi maganar,
Azeeza tace"Muna da abunyi mana, Angel zata Wanke mana gashin kanmu, ta kuma gyara mana shi, " tunkan takai karshen maganar, yasmin ta harare ta"Kefa matsalarki kenan, Sai ana magana ta hankali ki wani soko wa mutane Shiririta aciki," zum6ura baki Azeeza Ta yi tare da murguɗawa mata shi tace"To me kike so Muyi? Wanka ko motsa Jiki? Ko kuma bacci? Ko giants xamu Jira su kawo mana abinci"? Banza yasmin tayi da ita, Zama batool tayi a gefen gadon angel, ta ruƙo hannun angel acikin nata tace"Sister, na lura sam bakya acikin hayyacin ki, Ki faɗa mini, me kika gani acikin baccin ki wanda ya tsoratar dake"? Idanuwan angel cike tab da ƙwalla ta ɗago ta kalli fuskar batool, bazata Iya faɗa mata ainihin abunda ta gani acikin mafarkin ta ba, Saboda Bata son ta tayar mata da hankali, Kuma faɗin baida amfani, sannan ma babu kyau mutun yayi mummunan mafarki ya faɗi ma wasu,
Don haka tace mata"bakomai batool Just bana Jin daɗin Jikina ne,"
"Ko zakiyi wanka ne? May be kiji daɗin Jikin ki," cikin sanyin murya tace"eh, xanyi, " tana rufe baki Azeeza tace"Angel me zamuyi yau"? Murmushi angel ta ƙaƙalo, yayin da take kallonta tace"Little Kome kike so Shi za'ayi, " ashagwa6e Azeeza ta bubbuga ƙafar tare da cewa"Ni kidaina ce mun little bana so," gaba ɗaya su kayi dariya, Hanna tace"Ae gaskiya ta faɗi, kallarki fa? Wata ƴar ƙarama dake, Ko kafaɗarmu baki kai ba, banta6a ganin wadda bata cigaba ba acikinmu irin ki, Duk yawan abincin da kike Ci sam baki ƙara auki, ba ƙiba ba tsawo," dariya suka saki gaba ɗayansu, Rai a6ace Azeeza Ta zuƙunna kasa tana yin kukan ƙarya, Angel tace"pls kudaina janta, Nima na faɗi ne kawai don ayi nishaɗi, amma azeeza ae itace babbarmu," ta yi maganar tana ƙyaftawa musu ido, atare suka haɗa baki wurin cewa"hakane Azeeza itace babbarmu, muma wasa muke Yi mata, don kawai ayi raha ne" Sunsan azeeza da son girma, jin wannan maganar tasu yasa ta miƙe tana gumtse dariya abaki,
Angel tace mata"Me kike so Muyi yanzu? "Ki wanke mana gashin kanmu, Kuma ki gyara mana, keda batool kamar yadda ku kayi mana ran nan kin tuna'? Zaro ido angel tayi"Azeeza Baki ga yadda na farka ba yau, sam babu natsuwa atare dani, Taya zamu Iya wanke maku wannan uban gashin kan naku, Kuma mu gyara shi,? Ta6e baki azeeza ta yi, Itafa in taso abu to ayi mata kawai, idan ba haka ba yini zatayi tana faman tur6une musu fuska duk da tana da yawan fara'a kamar Gonar auduga, "Kada Ki damu sister azeeza, Koda angel bata samu damar tayani ba, Ni xan gyara maku gashin kanku, Mu barta ta huta, tun da bata Jin daɗi, Kuxo muje toilet," Batool ce ta yi maganar, Ta juya ta nufi toilet suka bi bayanta,
Bayan tafiyarsu Cikin toilet, Angel ta sauke ajiyar zuciya, tare da jingina bayanta Jikin bango, Gefe ta juyar da kanta tana kallon Gadon danish, kamar dai kullum yana a kudundune Cikin bargo, Haris da mubeen da Javed hada naufal duk basu farka daga Bacci ba, sakamon daren da su kayi jiya batare da sun runtsa ba, Suna Xaman Jiran adawo musu ƴan uwansu,
Saƙe saƙe ta shiga Yi acikin zuciyarta, game da wasu tambayoyi da suka cunkushe mata kwakwalwarta, sun hanata sakat, idan ta takura kanta akan tunaninsu Har wani matsanancin ciwon kai take ji, tabbas tana son Yin magana da tsohuwa duk da tasan zaiyi wuya tsohuwa ta amsa mata tambayoyinta, amma zata jaraba tunkararta, Yau ɗin nan,
A6angaren su Batool, sai da tabi kowannan su ɗaya bayan ɗaya ta wanke musu sumar kawunansu, Baƙaramar wahala tasha ba, domin kuwa Dukansu tsayin gashinsu Ya zarce midback ɗinsu, Ga uban yawa dake gare shi, bayan ta kammala wanke musu gashin, Sai da kowannan su Yayi wanka, Kafin suka dawo Cikin ɗakin, Kamar yarda suka bar angel zaune saman gadonta haka suka sameta, ganin sun fito daga wankan Yasa itama ta miƙe domin zuwa yin wankan, Shigarta da ƴan mintuna ta fito, A lokacin Danish dasu Mubeen duk sun farka daga bacci, saukowa su ka yi daga saman gadajen su, Atare suka Nufi Toilet domin suma suyi wankan ko sunji daɗin Jikin su.
A zaune ta samu batool gefen gado ta ruƙe Comb, Zata Gyara musu gashin kansu, hakanan taji tana sha'awar Tayi musu Kitson kalaba Guda Biyu akansu don ta Iyata, Kallon batool tayi tare da cewa"Ki bari In yi musu kitson Kalaba, Nasan ba'ata6a Yi maku ba, Yau zan jaraba mu gani idan zan iya" Cike da Jin daɗi Batool ta mika mata Comb ɗin, Tasa hannu ta kar6a, tare da samun wuri gefen gadon batul ta xauna, Ta ɗago ta kalli su Azeeza dake ta murna za'a gyara musu gashi tace Su zazzauna a ƙasa, zata fara gyarawa azeeza nata idan ta kammala mata zata Kira ta gaba da zata yi mawa,