Kwai cikin kaya book 2 complete - Chapter 15
Kwai cikin kaya book 2 complete Chapter 15: Kwai cikin kaya book 2 complete Chapter 15. auna a kujerar dake gaban tebirin ɗin. Hannu ya miƙa masa sukai…
4,372 words
auna a kujerar dake gaban tebirin ɗin. Hannu ya miƙa masa sukai musabaha, murɗe hannu Jay yay har saida Jabeer yay ƴar ƙara, ya fisge yana hararsa da faɗin, “ALLAH kai mugune na bugawa a takarda, ciremin hannun zakayi boss”. Murmushi Jawaad yayi yana miƙa masa key ɗin motarsa da faɗin, “Gobema ka sake yin gulma”,. Jabeer ya sake hararsa yana juya hannunsa, “Kasan ALLAH Jay, yau da ace ba sunan momine da itaba da akanta zan rama, ALLAH ya ceceta kuwa”. Murmushi Jay yayi yana taɓe baki, yace, “Kaje ka rama mana ina ruwana, Am sorry jiya na maka tsawa, rainane duk a jagule kaikuma kazo zaka sake cazamin kai da naka shiriritan”. Murmushi Jabeer yay yana shafa kansa dajin ƙaunar abokin nasa cikin rai, “Ni dama ban ɗaukesa komaiba, nasan wanene Jay ɗinmu idan yay fushi, ina fatandai itama Momin tamu ka bata haƙuri, dan na koma office ɗinka kusan 3:45 na isketa tana kuka”. Haɗe fuska da lumshe idanu Jay yayi yana sauke numfashi, “Ai yarinyarnan bata da kunya. manta da zancenta, ina fatan su Hafiz sun iso, dan inason muyi magana”. Kamar yanda ya buƙata sai Jabeer ya bar zancen bily, ya amsa masa da, “Okey bara na kirasu to, nasan duk sun iso yanzun”. Gyara zama Jay yay, yayi shiru har Jabeer ya gama kiransu. Babu wani jimawa sai gasu duk sun shigo, saida suka gaggaisa sannan kowa ya nema wajen zama, Aliyu da idonsa ya sauka akan yatsan Jawaad dake naɗe da bandage yace, “Boss miya samu hannun kuma haka?”. Hannun Jawaad ya kalla yana ƙaramin tsaki, “Wlhy Aliy wani ɗan ciwo naji, shinefa Alhaji baba yaymin wannan naɗin”. Dariya duk sukayi, Hafiz yace, “Shi ka kaima fushin jiya kenan?”. Hararsa Jay yayi amma baice komaiba. “Kunga ku ajiye shiritarnan taku muyi magana yau inada aiki a office saboda jiya banyi komaiba”. Duk hankalinsu suka maida gareshi, Jabeer ya direma kowa kofin coffee daya haɗo, “Thanks ” Jawaad ya faɗa yana ɗaukar kofin, suma su Hafiz sukai masa godiya, Jawaad yakai kofin bakinsa sanan ya janye idonsa a kansu, sai dai yay matuƙar canja fuska saboda maganar da zaiyi tana zafarsa a cikin rai, “Guys dolene yarinyarnan tabar cikinmu a wannan karon, bazan iya cigaba da zama da itaba ta isheni haka nan”. Kallon juna suka shigayi kowa da tsoro akan fuskarsa, Aliyu yay ƙarfin halin faɗin, “Wa kake nufi a cikinsu boss? Kasan yanzu sun zama su biyu”. Kallon Aliyu yayi tamkar bazaice komaiba, sai kuma cikin takaici yace, “Rose nake nufi”. Shiru sukai duk suna jinjina zancen a ransu, kafin Hafiz yace, “Banƙi ta takaba Boss, sai dai hakan zai iya zama wata matsala daban, duk da bansan ainahin abinda tai makaba na kula tanason takurama rayuwar mami ne, abinda kuma na fahimta itafa gani take son Mami kake gaskiya shiyyasa take duk waɗanan abubuwan”. Tsaki Jawaad yaja yana yamitse fuska cike da takaici amma baice komaiba. Suma shirun sukai basu damu da rashin bada amsarba, dan a ganinsu idan son Bilkisu yake wataran ai dole ta fito fili ko. Jabeer ne ya katse shirun nasu da faɗin, “Gaskiya boss hakan ba shine mafitaba, na farko Rose tasan sirrikanmu da yawa, yaƙi take akan soyayyarka a yanzu, idan kace ta barmu zaitai amfani da wannan fushin ta koma cin dunduniyarmu, munada muhimman ayyuka a ƙasa waɗanda munyi zurfi sosai na kaiwa ga nasara, sune zata fara harin ɓatawa, karka manta zagaye muke da maƙiya, ƙaramar ƙofar da za'a kutsa cikin mutuncinmu kawai ake nema dama, magana ta ƙarshe kuma Rose zatabi duk hanyar da zuciyarta ta ƙawata mata ta cutar da mai sunan mom batare da munsan tayaya ta shirya hakanba, kaga kuwa tako ina korarta ba mafita zata bamuba, domin iyakar gudunmu dai bai wuce kabi ta ƙasa kasa aimata transfer ba, duk nisan da kake tunanin zatayi damu ALLAH saita dawo koda ta hanyar saka wanine yay mata aiki kuwa”. Dukansu sun gamsu da maganar Jabeer. Aliyu yace, “Maganar Jabeer fa gaskiyace Jay, sawa tabar cikinmu ba mafita bace, gara ace muna ganin duk motsinta, sannan ni a ganin idan kanason Mami ɗin miza hana ka fito ka bayyana mata kawai a wuce wajen, da zafi-zafi ake bugun ƙarfefa a wannan zamanin”. Fuska sosai Jawaad ya haɗe, cikin nuna halin ko in kula ya wani taɓe baki yaƙi cewa
komai a karo na biyu kan maganar Bilkisu. Duk idanu suka zuba masa na mamaki, sun rasa miyake ɓoyewa. Sai da ya shaƙi iska dan kansa sannan yay magana, “Kuna ɓatamin rai da shirmennan naku, kunefa dalilin shigowar wannan yarinyar cikin tawagarnan, amma miyasa kuke son maida zancenta wani abu daban, to inagama ba rose bace ta cancanci yin nesa damu, Miemaa zansa aima transfer, ince dai shikenan”. Da sauri Hafiz yace, “Ba shikenanba, yarinyarnan yanzune ta fara aiki, ƙwazon data fara nunawa yana buƙatar a cigaba da horar da ita akan gaskiya, munji ba sonta kakeba, kuma insha ALLAH babu mai sake maka wannan maganar, inaga kawai mu zauna dasu ita da Rose kajama Rose dogon gargaɗi akan wannan haukar tata mara tushe, domin munutsu mu fuskanci sauran ayyukan dake gabanmu, yanzu aikinan da muke wlhy yanada matuƙar sarƙaƙiya da haɗari, amma gashi muna wasa dashi, sai dau ku yaya kuka gani?”. Jabeer dake wani shegen murmushi yana satar kallon Jay yace, “Hakan yayi nidai a wajena, gara a bar mana Miemaar mu muyita kwasar albarkacin sunanta”. Hafiz da Aliyu sukai dariya, dan sunsan shaƙiyancin Jabeer ne ya motsa, Jawaad kam uffan baiceba, saima miƙewa da yayi yay musu sallama ya fita. Yana fita duk sukayi dariya, Aliyu yace, “ALLAH Jabeer kasama boss ido da yawa, nakula son ƙureshi kake kawai,, ka barshi yasha iskar duniya malam”. Nanma dariyar sukayi, Hafiz yace, “kunga nima bara na koma Office, gayenan addu'armu kawai yafi buƙata”. “Hakane kam” cewar Aliyu dake miƙewa shima.
Fitowar Jay daga office ɗin Jabeer yay dai-dai da fitowar Bilkisu daga motar Qaseem suna murmushi ma juna, dukda a sama yake kuma ta glass yake ganinsu hakan bai hanashi ganin murmushin yamata ƙyauba, dayake ba yawan ganin murmushin nata yakeba sai yazam idan tayi yakan kasance na musamman, ya taɓe bakinsa yana barin wajen. Bilkisu kam da batasan yanayiba rakkiya tayoma Qaseem dake bata labarin maganar da sukai akan aurensu jiya da Dad. hakan sai yasani jin daɗi da raguwar nauyin da zuciyarta tayi tun a daren shekaran jiya, a ganina garama nai auren na huta, dan na kula zamanmu a haka haɗarine babba a gareni, maganganun Dad na jiya akan fyaɗen mai aikin su Nazifa ya mugun tsaya mani a rai, inada yaƙinin irin wannan ƙaddarar ta afka tsakanin ni da ƴaƴansa to wlhy nikaɗai zanyi kukana, dan tabbas zai goya musu bayane, a yanda kuwa Yah Qaseem ke kaima jikina hari da halayyar Salman da batai minba komai zai iya faruwan, to maganin ayi kar a fara kawai. Saida nai masa rakkiya har office ɗinsa sannan na juya na sauka namu, saida na gaisa da kowa sannan na zauna mazaunina, Computer ɗin gabana na kunna domin duba gajeren video da boss ya bani nai sharhi akan abinda na fahimta ciki, gaba ɗaya hankalina na maida akan aikin har Ummie data makara yau ta shigo, gaisuwa tayi da sauran sannan ta matso inda nake ta bani hannu muka gaisa idonmu akan video mu duka. “Bily jiya wai miyasa kika gudu bayan kinsan magana mai muhimmanci muke tattaunawa a group?”. Murmushi nai mata ina cigaba da control ɗin mouse ɗin Computer a hannuna na haggu, na damar kuma ina riƙe da pen ina rubutu a takarda. “Hankalina ne yay masifar tashi Ummie, al'amarinne akwai ruɗani a ciki, dan na fara zargin mai aikata ɓarnarnan ba mutum ɗaya bane sai dai ƙungiya garesu”. Kujera ta jawo ta zauna saɓanin da da take tsaye ta ranƙwafo jikin tebirina, tace, “Miyasa kikai wannan tunanin bily?”. Kallonta naɗanyi na ɗauke kaina ina cigaba da aikin gabana, nace, “Saboda Amina mana, kinga su su Nazifa a gida ɗaya akai musu ita da marigayiyya, sai kuma na yarinyar jiya, amma ita Amina ai a gidanmu akai mata, yanda ake salon fyaɗen duk iri ɗayane, sai an bugar dasu ake cutar dasu, sannan babu wandda ta taɓa ɗaukar ciki a cikinsu, zuwa yanzu ina buƙatar mu haɗu waje ɗaya mu duka biyar ɗin, dan yadace mushiga binciken neman sauran waɗanda hakan ta faru garesu, inaji a jikina Ummie basu kaɗai bane akwai wasu”. Na ƙare maganar da kallonta idanuna cike da ƙwalla. Kanta ta girgizamin a hankali alamar karnai kuka, na ɗauke kaina ina haɗiye abinda ya tokaremin maƙoshi mai nauyi d
a ƙyar. Nuna mata Computer ɗin nayi ina zooming ɗin wani waje cikin video ɗin da faɗin, “Ummie kalla dan ALLAH mikika fahimta a wajen nan?”. Matsowa tayi sosai tana kallon wajen cike da nazari, kafin ta amshi mouse ɗin hannuna ta maida video'n slowly, “Kai bily kilura da ƙyau wani kasuwancin kurame akeyi a wajen nan fa, ki kalli zuwan yarinyarnan wajen da ƙyau, kafin ta ƙarasa wajen shi wannan mai kifin saida suka kalli juna da mai raken can sukaima juna wata inkiya da idonu, sannan bakin mai kifin ya motsa alamar magana yayi”. Kaina na shiga jinjina mata, nace, “Haka nima duk na fahimta Ummie, to amma sam na kasa fahimtar mi mai kifin ya faɗa, na maimaita wajen yafi sau goma wlhy, amma kuma abin lura anan shi wacan mai facin minene ya ɗauka cikin tayoyi ya bama gurgun yaron can almajiri?”. Baya ummie ta dawo da video dai-dai wajen, da alama mai ɗaukar video bai saka da mai facinba a ɗaukar, dan acan gefe yake yana harkokinsa shi kaɗai, hakan yasa ba komai ake iya fahimta dangane da shiba. “Bily kinsan mizakiyi?” nace, “A'a saikin faɗa”. kije office ɗin boss kimasa bayani, inba hakaba zamu iya rikita komai anan”. Gabana ne ya faɗi jin ta ambaci boss, abinda ya faru jiya ya shiga mani kaikawo, gashi yau yanda na lura baije duba aunty Shahudah bama tun jiya da safe kamar yanda naji iyayenmu na tsogumi a asibitin, ALLAH dai yasa ba maganata bace ta jawo hakan, dan yakamata ace ya cika alƙawarin daya ɗaukama Dad na zuwa gidanmu a daren jiya......... “Lafiya kuwa? Ina magana kin tafi tunani”. Numfashi na kawo ina dafe kai, nace, “Babu komai, bara nakai masan”. Nasan yanda nai maganarne a sanyaye ya sakata bina da kallo, ban yarda mun haɗa idoba na cire flash ɗin daga Computer'n na ɗauki takardun danake rubuta bayanan na tattare cikin file ɗin daya bani jiya na fita. Maimakon na nufi office ɗin nashi saina tafi office ɗin Oga Aliyu. knocking nai aka bani izinin shiga, su biyu na iske a ciki, hakan yasani gaishesu na tsaya gefe su kammala, dan naga magana suke. Basu wani ɗauki lokaciba wancan ya miƙe ya fita, oga Aliyu ya nunamin kujera alamar na zauna, sake gaidashi nayi sannan na zauna ina ɗora takardun hannuna a tebirin gabansa. “Mami ta samune?” yay maganar cikin zolaya. Murmushi nayi nima na bashi amsa da “Sosai ma”. Yay ƙaramar dariya yana amsar takardun, “To ALLAH yasa mai washa-washa ne da zamuci mu more”. Yanzunkam saida naɗan dara kaɗan, dan bansan yana magana mai tsaho hakaba, yaɗan duba takardun sannan ya kalleni, “Mami ban fahimci komaiba anan, na minene?”. Hannuna naɗan matsa kaɗan sukai ƙara, na muskuta zamana, “Oga Aliyu bayanan daga wani video suke” nai maganar ina miƙa masa flash ɗin hannuna da cigaba da faɗin, “Nice na haɗasu anan, to kuma na cije a wani waje shine nazo neman haske”. shiru yay na sakanni batare daya amshi abin hannunaba, kafin yace, “Okey, wanene ya baki aikin a cikinmu?”. Nace, “Boss ne”. Takardun ya miƙomin, “Kinga to kije wajensa, dan bansan case ɗin miye ba, nasan zai miki bayanin duk da zaki fahimta”. Shiru nayi na kasa amsar takardun. Aliyu dake kallonta yace, “Da matsalane?”. Kaina na ɗago na kallesa, sai kuma na sauke idanuna ƙasa, “ALLAH oga shi ya cika faɗan tsiya, yaytama mutane mazurai”. Dariya sosai Aliyu yayi da wannan magana tawa, saida ya gaji dan kansa yay shiru, sake miƙomin takardun yayi har yanzu fuskarsa da murmushi, “Ai sai an masa ba daidaiba yake mazurai, tunda akan aikine zai fahimceki bazaiyi faɗaba kinji”. Kaina na jinjina masa, badan nasoba na amshi takardun na fita. Jinake kamar karnaje, amma wani sashe na zuciyata na bani shawarar naje dan akan aikine, bai kamata kuma na sanya wasa akan aikinaba, nidai na kiyaye duk wata hanya da zata sake haɗani dashi harnaga fushinsa kamar na jiya kawai. Da wannan ƙwarin gwiwar na nufi office ɗin, knocking nai aka bani izinin shiga, gabana sai faman faɗuwa yake na tura ƙofar da sallama a ƙasan maƙoshi na shiga. Tarin aikine jibge a gaban Jawaad, ko buƙatar shigowar wanima babayi office ɗin, hakan yasa koda Bily ta shigo sallamarta kawai ya amsa amma bai ɗagoba, ƙarasowarta gabansa ƙamshinta
ya tabbatar masa itace, sake ɗaure fuska yay sosai fiye da yanda ta shigo ta sameshi. Kallo ɗaya naima fuskarsa na ɗauke kaina, a ɗaure take fiye da kullum ma dana sani, gaba ɗaya ƴar jarumtar dana shigo da ita saita gudu itama, gashi yaƙi kallon ko inda nakema dukda inada tabbacin yasan nice na shigo. Da ƙyar na iya daurewa nace, “Ina kwana Sir”. Batare daya kalleniba yanzunma yace, “Lafiya”. Shiru nai nakasa cigaba da magana, dan yanda ya amsa gaisuwar tawa a daƙile ya sake sanyayamin jiki sosai, ganin tsayuwar tawa bata da amfani na daure nace, “Sir dama akan aikin daka bani ranar monday ne”. Harna fidda rai da samun amsa sai naga ya nunamin kujera batare daya ɗagoba. Ɓoyayyen nunfashi na sauke ina ƙara ƙoƙarin ƙarfafa kaina. Na ajiye takardun hannuna a gabansa kafin naje na zauna a kujerar, shiru muka sakeyi na mintuna, saida ya tattare wasu takardun gabansa waje guda ya ajiyesu gefe kafin ya kalleni. Saurin nuna masa takardun dana ajiye nayi. Janye idanunsa yay daga tsatstsarenin da yay dasu ya ɗauki takardun, shiru tsawon wasu mintuna yana dubasu kafin ya ɗago, yace, “Kin gama ne?”. Sau ɗaya na kallesa na ɗauke idanuna ganin ni yake kallo, na girgiza kaina, “A'a ban gamaba, akwai wani wajene a video'n to sai nakeson ka gani kafin na shigar da bayanansa” na ƙare maganar da miƙa masa flash drive ɗin, bai amsaba ya ɗauke kansa daga gareni ya maida ga Computer ɗin gabansa, “Taso kisa”. kamar nai kuka haka naji, sai dai bani da wata mafitar daya wuce bin umarninsa, inda yake naje, a mamakina sai naga ya tashi daga kujerar tasa ya nunamin alamar na zauna, batare da yace uffanba............✍
Yau shafin nakune ƴan telegram, kuma ku warwasa da wannan, alkairin ALLAH yakai gareku aduk inda kuke, ammafa babu canji mun ƴan hud-jay team ne😜😂😂😂😍😍😘😘😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu🙏🏻😭. Bilyn Abdull 📚: Page 21
...............Kallonsa nai ya zubamin harara, babu shiri na ɗauke idanuna na zauna kamar yanda ya buƙata a lallausar kujerar tasa dariya nazomin a cikin rai, danni mamakin yanda ya iya harara wa mutane nake, sai kace wani mace. Da ƙyar na iya riƙe dariyar daketa son fallasa na saka flash ɗin a jiki, duk abinda nake yana tsayene a kaina harna kunna video ɗin. Har ya kai karshe ya sake komawa baya baice komaiba, ganin mun maimaitashi sau uku yaƙi magana saina juyo dan inga koma dai nikaɗai nake kallon. Mamaki ya kamani ganinsa tsaye a bayana hannayensa duka biyu cikin aljihun wandonsa, idanunsa akan Computer alamar duk yana kallona. “Idan kin gama kallon nawa saiki nuna inda baki ganeba”. Ya faɗa ƙasa-ƙasa, kamar wani mai tsoron a jisa. Fuska na kumbura tare da ɗauke kaina, a raina nace, ‘Kai wama ya kaika iya kallon mutane’. hannuna na ɗaura saman mouse ɗin nai zumin dai-dai wajen mai faci ina faɗin, “Akan mai facin nan ne dama, kamar akwai alamar tambaya dangane da shi, dan......” kasa ƙarasa maganar nai saboda kusancin da muka samu, a dalilin ranƙwafowar da yay har munajin saukar numfashin junanmu, ya ɗaura hannun hanggunsa saman table ɗin, na damar kuwa saman nawa dake kan mouse. Da sauri na rumtse idanuna, tare dayin azamar janye hannuna dake ƙasan nasa, saboda wani mugun harbawa da zuciyata tai. Baice komaiba, shikam ko a jikinsa, saima ƙoƙarin maida video slowly da yay. Nayi matuƙar takura da tsorata da wannan kusancin namu da yay matuƙar yawa, har takai jikina ya fara rawa, idanuna suka ciko da ƙwalla, sam bana fahimtar bayanin da yakemin ma, dan sama-sama nake jin sautin muryarsa. Jawaad da duk abinda yake akan sani yayisa ya juyo yana kallonta, ta rumtse idanu zufa dukta tsatstsafo mata a goshi tamkar babu ac a office ɗin. “Hummm” ya faɗa acan ƙasan maƙoshi ya janye jikinsa. A mamakinsa sai yaji ta sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi, hawaye sun silalo saman kumatunta, saurin ɗauke kansa yay tamkar bai ganiba. Har bigewa nake da shi wajen rawar jikin miƙewa daga kujerar jin ya matsa, na goge hawayen dake bin kumatuna batare da na bari ya ganiba, gefen tebirin na koma na tsaya kaina a ƙasa nace, “Sir, bara kawai naje can dashi saina ƙarasa tattara bayanan”. Jawaad da har yanzu yake binta da kallo yaɗan lumshe idanu ya buɗe yana ƙoƙarin danne dariyar dake son kufce masa, murya a daƙile yace, “Barshi zan ƙarasa, ɗauka waɗanan files ɗin ki kaima Hafiz, zuwa anjima ki dawo zamu fita”. Bawani fahimtarsa nakeba, kai kawai na ɗaga masa na ɗiba files ɗin na fice cikin sassarfa. A raina banda takaici babu abinda nakeji, miyasa halin mazan wannan zamanin kusan duk ɗayane? Burinsu kawai su taɓa macen da ba muharramarsu ba a matsayin wayewa, ashe shima mutumin nan haka yake ban saniba?, “Aikam na daina sakar masa fuska wlhy” na faɗa a fili cike da takaici.
★★★★
Ƙarfe biyu muka fita cin abinci ni da Ummie, sai da muka gama nai ƙoƙarin biya sai nagama kuɗin dake jikkar tawa bazasu isaba, kusan koda yaushe Ummie ke biya mana inhar bada Yah Qaseem mukazo ba, sai naga da kunya hakan tacigaba da faruwa ai, ATM ɗina na shiga lalube dan na basu su cire, amma sai shima ɗin dai ban gansaba, gabanane ya shiga faɗuwa, dan bama shi kaɗaiba duk cards ɗina basa ciki kenan tunda a tare nake ajiyesu waje guda, kuma inada tabbacin itace jikkar danasan na fita da ita daga gida last. “Wai mikiketa lalube hakane kamar wata makauniya?” Ummie dake shan ruwa ta faɗa bayan ta ajiye kofin. Guntun tsaki naja ina mai bata amsa da, “Ai namafi makauniya yau Ummie, wlhy banga duk Cards ɗinaba, kuma inada tabbacin anan ciki suke”. Tasowa tai tana tayani, sai dai kumafa da gaske babu ɗin, hankalina yayi matuƙar tashi, “Ummie na shiga uku, a ina na jefar nikam?”. “Bily bazan saniba, amma nasan baki da mantuwa, yaushene rabonki dasu?”. “Ummie A ranar lahadi fa da hannuna na sakasu cikin nan dazan fita”. Tace, “Ai da sauƙima, ki tuna ranar ina da ina kikaje tunda kin tabbatar a ciki suke?”. Zama nai idona cike da kwalla ina tunano dukkan abinda ya wakana a wannan yinin, da sauri na kalli Ummie, “Ummie idanma har yardawa nai to
bazai wuce wajaje biyu ba wlhy”. Ummie tace, “Ina da ina ne?”. “Saloon da wani garden, amma bara na bincika a saloon ɗin dan inada Number ma'aikaciyarsu ɗaya”. Ummie ta biya kuɗin muka fito a wajen, sai da muka koma office sannan nai kiran Number danai saving da Ladies mirror, bugu biyu kuwa aka ɗaga, bayan mun gaisa nace, “Dan ALLAH kiyi haƙuri, na kiraki maybe ba'a lokacin daya daceba”. Daga can tai dariya da faɗin, “lah babu komai”. Nace, “Okey ngd, ranar danazo wajen nan naku ina tunanin na yarda wallet ɗina, sam hankalina bai kaiba sai yanzu, ina fatan anan na yardar ɗin?”. tai ɗan jimm na wasu sakanni kafin tace, “Eh tabbas anan kika yarda, amma bata wajenmu, tana masarauta wajen su aunty Amaturrahman, dama sunbar saƙo akan idan kinzo nema a baki card ɗinsu, yanzu yaya za'ai kenan?”. Wani sanyi naji ya ratsani, na sauke numfashi da cewa, “Babu damuwa, idan na tashi aiki zan biyo na amsa, nagode sosai”. ta amsa da “Babu damuwa, sai kinzo”. Bayan mun kashe wayarne na faɗama Ummie duk yanda mukai, daga ni har ita mamaki muketayi na cewar wallet ɗin na masarauta. Ban samu kiran boss ba kamar yanda yace zamu fita har lokacin tashi yayi, zuwa nai na sanarma yah Qaseem ya wuce gida ni zamuje nida Ummie wajen wanke kai, yanzunma da damuwa na iskesa, dan haka bai wani jamin zanceba yace mu haɗu a gida. Nidai al'amarin nasa sake ɗauremin kai yay yanzunma, har muka isa Ladies mirror banbar mamakin wannan canjin nasaba. Sosai Ummie ta rikice da haɗuwar wajen, harda ma kanta alƙawarin zuwa wannan weekend ɗin su mata aiki, bamusha wata wahalaba muka samu wadda na kira ɗin, ta bani card ɗin da suka bari. bamu daɗeba muka fito dan magriba ta gabato. Ummie ta ajiyeni a gida ta wuce, koda na shiga saina iske an sallamo auntu Shahudah, falon cike da dangin Momy, da sukazo dubata, nidai na gaishesu itama nai mata yaya jiki na wuce, saboda a rayuwata na tsani kallon wilaƙanci, sukuma naga alamar indai ba nasuba to kowa banzane. Wanka na farayi harda wankan tsarki saboda baƙona ya gudu, na fito na gabatar da sallar magriba nai azkar, ina zaune a wajen har aka kira isha'i, har lokacin inajiyo hayaniyar ƴan gidansu Momy, dukda yunwar da nakeji saina zaɓi haƙura na kwanta a haka, ɗan kayan maƙulashen da yah Qaseem ke yawan siyamin nakan ajiye a ɗaki su nai zamanci, gefe guda kuma ina ƙoƙarin kiran Number jikin card ɗin da aka bani, saida ta kusa tsinkewa aka ɗaga, munyi gaisuwa da wadda ta ɗagaɗin a mutunce dukda bansan wacece ba, kafin na mata bayanin kaina. Nayi mamakin yanda tai saurin ganewa, kai tsaye tace na tura mata address ɗin inda nake kawai, zasuzo su kawomin har gida. Sosai na ƙara mamaki da jinjina ƙyaƙyƙyawar tarbiyyarsu gaskiya, sam basuda girman kai tamkar ba waɗanda suka fito daga babban gidaba. Godiya nai mata mukai sallama, ban zauna ɓata lokaciba na tura mata number dan inada buƙatar cards ɗina su dawo hannuna da gaggawa. Jin gidan yayi shiru yasa na miƙe, dan fitar motoci da naji ya bani tabbacin duk sun wuce, ƙaramin hijjab na saka saman wando da rigar kayan barcina kalar ruwan hoda na fito, wata irin muguwar yunwa nakeji wlhy, rabona da abinci tun wanda mukaci da Ummie da rana. Babu kowa a falon duk sun tafi, na wuce kicin hankalina kwance, plates kawai nagani zube wanda sukaci abinci, sai dai babu komai a kulolin duk an cinye, cike da haushi na fara ƙoƙarin ɗora noodles dan bazan iya haƙurin kwanciya banci komai ba, dan danan na kammala dafawa na fito, mamaki ya kamani jin ƙamshin turaren da banyi zatoba, zuciyata sai harbawa take da sauri-sauri, waige-waige na shigayi a falon, saiko idona ya sauka akan wanda zuciyar tawa ke rayamin, tsaye yake dafe da ƙarfen benen dake falon waya a kan kunnensa, kamar koda yaushe ƙananun kayane a jikinsa, ido cikin ido muka kalli juna, nai azamar janye nawa ina damƙe plate ɗin indomie ɗina daketa tururi, inaji a jikina har yanzu kallona yake, hakan saiya haifarmin da tafiya a hankali kamar wata hawainiya harna shige lungun ɗakinmu ni da aunty Aamilah. Jawaad daya kasa ɗauke idanunsa a kanta har saida ta shige sannan ya sauke ajiyar zu
ciya yana lumshe ido da cije lip ɗinsa na ƙasa, sannan ya cigaba da wayarsa, bai wani jimaba sukai sallama ya maida wayar aljihu idanunsa akan lungun da bily ta shiga, cike da kasalar data saukar masa yanzun ya haye saman ya koma wajensu Dad da Alhaji baba da Uncle Nasir da sukazo tare suke tattaunawa.
Ban kawo komai a rainaba dangane da ganin boss gidanmu, tunda ai dama yayma Dad alƙawarin zuwa, sannan kuma ga aunty Shahudah ta dawo gida itama, abincina naci hankali kwance nai brush na kwanta domin na hutama raina.
ALLAH YAY DARE.
Washe gari safiyar alhamis, koda na tashi sai naci karo da abubuwa uku na farin ciki sun samemu, na farko samun sauƙin aunty Shahudah da har aka sallamo daga asibiti a daren jiya, na biyu maganar aurenta da Boss bayan ansha gumurzu ya amince da ƙyar saboda saka baki da kakansa yay a maganar, na uku tsaida maganar aurena da Yah Qaseem bayan Dad yaje wajen dangin mahaifina ya samesu ashe a jiya da rana, an tsaida aurenmu rana ɗaya dasu aunty Shahudah bayan salla ƙarama da sati biyu. Koba komai na samu kwanciyar hankali da nutsuwar zuciya, dan nikam abubuwan dake faruwa na wannan lokacin suna matuƙar tsoratar dani da sakani firgici. Ban ƙara tabbatar da ina son Yah Qaseem ba sai da aka tsaida ranar auren nan namu, shi kansa wani sake lallaɓani yake da ji dani a yau, dukkan abinda zai saka a gidansa kuma sanda muke tafiya wajen aiki ya nema shawarata, hakama kayan lefe saida yace na faɗi duk abinda nake buƙata, nidai kunyace ta kamani nace kawai na bashi zaɓi. Sai dai abu mafi bani mamaki sune jama'ar gidanmu, musamman ma Momy, koda wasa ban taɓa tunanin zata goyi bayan aurena da Yah Qaseem ba, amma sai gashi koda a fuska bata nuna komaiba, saima shirye-shiryen gagarumin biki take na nunama sa'a akan babban ɗanta namiji da zata fara aurarwa. Yah Salman ne kawai da aunty Aamilah sun shafema idanunsu toka suna ƙara faɗaɗa hantarata da muguwar tsana akan ban cancanci zama matar ɗan uwansuba, ƙiri-ƙiri suke nuna hakan babu ko kara a wannan safiya, su Dad dai basu tsawatar musu ba, sannan basu goya musu bayansu ba, Yah Qaseem ne daifa da yay kansu da masifa har saida na roƙesa yayi haƙuri kafin yay shiru muka fito. Tom nidai lamarinsu bai ɓatan rai, Alhmdllh tunda wanda zan zauna dashi yana sona, sannan iyayensama suna sona, dansu ƙannensa sunce basayi miye a ciki. A dangima dai akwai ƴan adawa, dan harda inna zainabu faɗa taitama Dad akan haɗani aure da ɗansa da yay kamar yanda Aunty Aamilah take faɗamin cikin gori da tsana, wai acewar inna Zainabu duk ƴaƴan manyan mutane masu kuɗi abokan Dad Qaseem ya rasa wadda zaiso saini? Haka taita jaraba tamkar itace ta haifi Dad ko yah Qaseem ɗin.