Kenza eBookz

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 24

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 24

L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 24: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 24. Wazeer ne ya gyara zamansa sosai yana dora idanunsa a…

3,365 words

Wazeer ne ya gyara zamansa sosai yana dora idanunsa a kanta.

"Mun gode sosai sheikh haisam.......shawararka ta karbu,kuma in sha Allah bazamu kunyata sultane ba,Ahmad ya dawo a daidai,zamu dafa masa har sai ya cimma gaci,saboda dukkaninmu ya fimu cancanta,alamun nutsuwarsa kawai tana bamu tabbacin zai iya"

"Na gode sosai.....na gode da fahimtata da akayi" Haisam.ya fada a girmame yana kashe kira.

Wani ajiyar zuciya morsa safiyya ta sauke hawaye yana sauko mata sanda kowa ke rattaba hannu gurin yarda da amincewar cancantar ahmad akan mulkin AGADEZ. Ta sake girmama hukuncin Allah me juya al'amura a yadda yaga dama. Wa ya taba tunanin sake samun ahmad a raye?,har wannan rana tazo da zai hau sarautar mahaifinsa koda kuwa riqon qwarya ne.

"Zakaran da Allah ya nufa da cara" Ta furta a hankali,saqon kuma yakai kunnen mammina,saqon da ta fadeshi ne kawai saboda lamarin ya mata kama da hakan,maganan kuma ya dauki hankalin mammina daga mummunan kallon da take saukewa wazeer. Yadda ya bata amsa a dazun kamar akwai wani qulli a ransa shima game da ita,me yasa bata tana sakashi cikin target dinta ba?.

"Yanzu ma bata baci ba,ban makara ba" Ta bawa kanta da kanta amsa,sai murmushi ya biyo baya ta jinjina kai.

"Kun sake sakashi a qabarinsa a karo na biyu.....qabari kuma duk wanda ya shigeshi sai ranar tashin qiyama shida fitowa" Ta fada can qasan ranta.

*ETHIOPIA*

*_ABA JIFAR INTERNATIONAL AIRPORT (JIMMA AIRPORT)_*

Cikin shigar da tayi daidai data 'yan uwanta,cikin yanayin da bai banbance matsayinta dana su Aanani ba take zaune cikinsu,cikin ayari ne musamman dake dakon isowar prince sheikh muhammad haisam aba jifar.

Tun daga ranar da labarin YAYI AURE ya shiga kunnenta,idan tace tayi cikakkiyar lafiya ta zuci data gangar jiki to tabbas tayi qarya. Daga wannan rana BACCI ya zame mata wani abu me wahalar samuwa ga idanuwanta.....daga wannan rana suka qulla abota da kukan zuci....daga wannan rana ya zamana ba wata rana da zata fito ta fadi bata tsaya gaban madubi ba.....bata kalli kanta ta tambayi kanta da kanta.

"ME KIKA RASA SAAMEE?.....MEYE BAKI DASHI DA KIKA GAZA FARAUTO SOYAYYAR CAPTAIN SHEIKH?" Wata tambaya guda daya data gagara samun amsarta.....sai kuma wani rashin tabbaci na

"Kin haqura?.....zaki yarda makamanki?,zaki tabbata mara nasara ta hanyar barwa wata shi?" Wannan tuhume tuhume ne da zuciyarta ke yawan yi mata su amma ta gaza bawa kanta da kanta amsa.

A daidai wannan lokacin sai takejin wani ciwo yana qulle mata a qirji. A duk inda ta ajiye idanunta zallar farinciki take gani a fuskar kowa na dawowarshi.....zumudi da walwala da fatan isowarshi cikin ahalin aba jifar da matar da zata yita amsa sunanta da nashi a maqale

"Matar shiekh muhammad haisam... Yarima me jiran gado" Ta lumshe idanunta muryarsu Aanani na mata amsa kuwwa. Ta kasa bude idanunta saboda ba abinda take kalla sai walwalar dake saman fuskokinsu.

Sanda qugun jirgin da yake bata tabbacin jirgin da suke dako ne ya iso.....a sannan ta bawa kanta da kanta amsar tambayarta..... Ba zata iya jurewa ba.....ba zata sallama haka da sauqi ba......ba kuma zata yarda tayi asarar abinda ta rayu shekaru kusan uku tana burin mallaka ba.

Saita samu kanta da miqewa tsam.....a sannu a sannu ta soma ja da gaya tana bacewa idanun duk wanda zai iya ganinta,tana barin dakin jira na musamman din da aka bawa iyalin me martaba ibraheem aba jifar don jiran isowar SHALELEN QASAR HABASHA......wanda airport din ta cika da manyan mutanen dake dakon isowar haziqin ma'akacinsu......sannan masarauta ke dakon isowar magajinta.

Ko ba'a gaya maka ba,koda kuma baqo ne kai cikin garin jimma idan ka kalli aba jifar international airport din zakasan cewa akwai babba kuma muhimmin abu da yake faruwa cikin airport din,saboda wasu irin lafiyayyun motoci dake jere bisa tsari masu kama d'aya dukkaninsu suna jiran isowar private jet din dake dauke da prince sheikh muhammad haisam aba jifar da matarsa.

Dukkanin mutanen dake airport din suna jiran isowarsun suma cikin tsari suke,fuskokinsu cike da walwala annashuwa da hira kadan kadan me nuna nutsuwar kowannensu.

HUSSAM kyakkyawan matashin mallakin qabilar oromo,kuma jini ga sheikh haisam din,kusan shine jagora kuma shugaba na tafiyar gaba daya. Kai kawo yake yana duba lokacin da yake a rubuce na saukar jirgin. Kamar ya matsu yaga isowar captain obbo......ya matsu idanunsa su sauka akan d'an uwan nasa da macen da tayi nasarar wuf dashi.

Cikin nutsuwa private jet din ke sauka da wani irin yanayi daya sauka saman zuciyar akhnan wadda ke zaune cikin kujerun alfarma da jirgin ya mallaka. Iya kujerun da su kadai sun isa su gaya maka luxury din dake cikin jirgin koda baka taka qafarka zuwa ko ina ba.

Yau jikinta yafi yin sanyi sama da ko yaushe....a yau da jirgin ke daukosu daga jidda zuwa jimma sai takejin komai yana kwance mata fiye da ko yaushe.

Wani irin royalty take gani.......wani irin yanayi na zallar girmamawa da wani irin respect. High luxury na rayuwa daya sake damalmala mata lissafin data fara qullawa kan WANENE HAISAM DIN.

Tafiyar awa shida ce.....amma banda sallah da yace tayi ta shiga toilet ta fito tazo tayi sallar bata sake motsawa ko ina ba. Hasalima yau da suke zaune guri daya na awanni masu yawa ya zame mata kamar wani surukinta. Tun shekaran jiyan da wannan abun ya gilma.....tun ranar bata sake bari idanunta sun shiga cikin nasa ba. Haka kuma takejin nauyin yana sake daduwa a kowacce rana,da mamakin yadda yake komai kanshi tsaye ba wan kwana kwana kamar komai ma bai taba faruwa ba.

Lumsassun idanunta ya soma budewa a hankali bayan ta tabbatar jirgin ya isa ga qasa......qasar da takeji a ranta a nan zata rayu?......na tsahon wanne lokaci ne?,wacce kalar rayuwa zatayi?,dawa dawa kuma zata rayu din?. Tambayoyin da suke sanyayar mata da dukka gabbanta.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Falaak take tunawa taji sanyi da nauyin dake qirjinta ya ragu,saidai sam ba zatace taga falaak sau biyar cikakke ba tun daga barinsu agadez zuwa yanzun da suke sauka a jimma cikin jirgin da iya ita dashi ya dauko kamar dai wadancan jiragen. Akwai banbanci me yawan gaske na zahiri tsakanin wadancan jiragen da wannan.....nisan tazarar daya sake luluqa tunaninta a kanshi.

Idanunta duka ta qarasa warewa jin jirgin ya tsaya. Bata tsammaceshi a kusa da ita haka ba,don haka kanta tsaye ta ware idanun nata fes sukayi kyakkyawan matsugunni cikin nasa kuwa.

Zaune yake sosai a kujerar da take facing tata kujerar.......da wannan kayan da tunda ya fito daga dakin hotel dinsu na raffles makkah ya dauki idanunta da hankalinta,saidai a yanzun takatsantsan take da komai daya shafeshi a yanzun,bata yarda wani dogon kallo ya hadasu ballantana ya kama idanunta.

Ya zuwa yanzu ta gama sallama.....idanunsa ba.....burgeta suke,wani irin burgeta sukeyi,tana jin kamar a duniya sune idanu mafiya kyawu na farko data taba gani. Bata yarda ta kalleshi kai tsaye ba,saita sauke idanunta akan dogayen yatsunta farare tas da har yanzu sauran lallen jiki bai fita ba.

Shuru ya ratsa tsakaninsu,wani irin shuru da batasan me hakan yake nufi ba.

"A jirginma.....a qasarsa ma sai ya nuna izzar?" Ta fada can qasan ranta tana jin alamun idanunshi a kanta.

Da gaske ita yake kalla,zara zaran yatsunta da take murzawa a hankali. A duk sanda zai kalli hannuwanta sai tuna yadda yatsunsa suke narkewa cikin nata duk sanda zai kamasu. A duk sanda ya kallesun sai yaji kaman ya kamasu ya maqalesu cikin nasa. Taushi da dumin da yakeji a jikinsu na dabanne. Rigar jikinta wata irin luxury abaya ne da aka sanya dollars masu nauyi aka siyeta cikin haramin makka. Sun mata wani irin kyau.....wani irin black color me daukan idanu. Yana jin bazai iya barinta ta fita a haka ba......yana jin kamar duk mutanen jimma suna bakin qofar jirginne suna son ganin fuskarta.

Idanunshi ya zare yana jin wani numfashi me nauyi yana subuce masa. Ya saka hannunsa yana yaye labulen window din jirgin don ganin yanayin da farfajiyar ajiyar jiragen take ciki.

A kanta idanunsa suka sauka......Khansaa Moti ibraheem aba jifar. Jinin sheikh muhammad haisam,kyakkyawa macace 'yar qabilar oromo na asali,diya ta farko daga tsatson ibraheem aba jifar da khadeeja yunnus jallata.

Sanye take da wata tattausar lafaya wine color,wadda aka yiwa ado da olive green me wani irin nau'i me daukan hankali. Kyakkyawa ce ta gaske......wadda jinin moti aba jifar ke gwada kansa sosai a jikinta. Da kallo daya kawai idan kayi mata zaka tabbatar da cewa basarakiya ce.....akwai sarauta da mulki dake zagayawa cikin jininta.

Ita kadai yake hangowa tana takowa da kan matattakalar jirgin. Kallo daya ya yiwa fuskar 'yar uwartasa ya hangi wani irin murmushi kwance saman fuskarta dake kama data moti sak da sak.

Daga matakalar qarshe ta dakata,cikin izzar nan data zame musu natural a halittarsu,ta miqa dogon hannunta dake shirye da wasu irin awarware na iko tana karbar kyakkyawan qaraman luggage din dake hannun hadimarta,wadda ke ajiye qafarta duk inda khansaaa ta ajiye.

"Ki koma qasa,zamu fito yanzu" Tayi maganan da iko sosai cikin muryarta. Rusunawa tayi ta miqa mata akwatin,sannan ta soma sauka da stairs na jirgin tana komawa inda sauran mutanen ke tsaye jikin matakalar cikin jerin sahu guda biyu hagu da dama.

Murmushi ta sake saki sanda crew din ke bude mata qofar tana mata nuni da inda su haisam din suke cikin girmamawa,ta jinjina kai kadan sannan ta fara takawa a nutse fuskarta shimfide da wata tattausar fara'a tana nufar gurin.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 44*

Sakin labulen yayi,a jikinsa yaji alamun shigowarta jirgin,sai ya miqe a nutse yana gyara thobe dinsa,sannan ya fara takawa zuwa dan qaramin kyakkyawan curtain din da shine kawai zai haba khansaaa ganinsu.

A tare suka daga labulen shi da ita,dukkaninsu fara'ar fuskarsu ta kasa boyuwa,musamman khansaaa da sai da jerarrun fararen haqoranta suka bayyana.

"Captain obbo" Ta fada tana kallonshi cikin dariyar dake nuna zallar qaunar juna dake tsakaninsu irin na 'yan uwantakar data samu kulawa daga iyaye,da soyayyar dake nuna zallar hadin kai.

"Malka khansaa(prince khansaaa)" Ya amsa mata cikin yanayi na sakewa da juna da kuma tsokana. Murmushi sosai tayi me hade da sauti

"Xiqqaa koo(my little one)" Ta amsa masa tana dubansa kai tsaye. Ya sani,tanason tsokana ne kawai,don tana cikin wadanda mamakinsu bai buya ba sanda akace musu yayi aure tun daga agadez.

"Na sameku lafiya?" Ya sake tambayarta yana dubanta.

"Alhamdulillah.....amma dai da farko duk ba wannan ba.....kasancewar munyi kewarka irin wadda bamu taba yi ba,amma zan gaya maka gaskiya a wannan karon.....bata taka muke ba.....baquwarmu muke marabta ba kai ba.....ko zaka iya dan yimin haquri na qarasa naga wannan kyakkyawan ruhin da yayi nasarar sace wannan zuciyar da aka gaza budawa kowacce mace ita?". Murmushi dole ya subuce masa,tun a nan?,a haka ma khansaaa mutuniyarsa ce sosai.....abokiyarsa....kuma ta wani fuskan yadda take treating nasa yasa yake mata kallon nanay ta biyu? Tun a nan ta gaza boye tsokanarta?,ina ga tarin cousins dinsa da suke jiransa da sauran abokai?.

Baice mata komai ba,yayi taku biyu baya ya matsa yana bata hanya.

Da murmushinta ta rabashi tana wucewa,dukkanin idanuwanta suna kan akhnan. Kanta yana qasa daga sanda taji baquwar muryar mace suna magana dashi da wani yare da bata ganewa. Ta lumshe idanunta,wannan yaren kawai ya isa ya bata tabbacin zuwanta wata duniya ta daban. Ya isa ya gaya mata a yanzun ita ba wancan akhnan din bace.....ba a agadez take ba....ba'a Niamey take ba,ta shigo wata duniya ne ta daban.

Mamakin saurin amintar da sultane da yayi,da har ya aminta ya dauketa ya damqa masa ita ba tare da sanin ainihin tartibin ina zaikaita ba?,wayeshi?,ina zai ajiyeta a rayuwarta ta gaba?.

"Keessummaa keenya” abinda khansaaa ta fada kenan da wannan 'yar gayun muryartata me dadin sauraro. Sautin kadai shine ya fusgi hankalin akhnan ta daga kanta bawai donta gane me take fadi ba.

A take idanunta ya sauka kan fuskar khansaaa.

" Subhanallah" Ta fada can qasan maqoshinta tana hadiye wani abu. Shige idanun nan nasa ne take dashi,banbancinsu nasa yana da wani irin shape da bata ganshi tattare da wannan ba,hakanan wadannan nata idanun an zizara musu kwalli daya sake qawata idanun.

Jar lafayar jikinta na nuna zallar iko,don duwatsun da aka shiryawa lafayan kadai magana suke da madaukakin sauti zuwa nuna ainihin tsada da darajar suturar jikinta.

Hannun khansaaa data miqo mata tana sake mata wani amintaccen murmushi tabi da kallo,wani tattausan hannu da aka zanawa kyakkyawan zanen jan lalle wanda adon flowers din sukasha banban dana yankin agadez nesa ba kusa ba.

"Afaan Ingiliffaan ishee waliin dubbadhu(ki gwada yi mata magana da English)" Yace da khansaaa data rusuna a gaban akhnan. Kai ta daga ta kalli haisam,ta saki murmushi tana maida dubanta ga fuskar akhnan,wadda sai yanzu taga fuskarta sosai saboda ta tsugunna ne ta gabanta.

"Maaaa shaaaaa Allahhhhhh......subhanallah.....captain?" Khansaaa ta fadi sanda idanunta ke saman fuskar akhnan idanunta suna nuna zallar daukan hankalinta da akhnan din tayi.

Basarwa yayi,don kafin tace komai yasan akan me zatayi magana,yanayinta ya karanta masa,sai ya fara takawa kawai yana ficewa daga gurin,abinda ya sanya khansaaa sakin dariya tana maido dubanta ga akhnan.

"Mijinki miskili ne.....yana da wahalan sha'ani wani lokacin,ina fata kin fahimci hakan?" Ta fada da harshen turanci tana kallon akhnan. Sai a sannan taji kaman an sassauta mata d'aurin da akayi mata,ta fahimci abinda Khansaaa tace,saidai kuma nauyin da takeji nata haka kawai ya sanya ta kasa maidawa,sai wani qaramin murmushi data saki tana sake karantar Khansaaa a fakaice. A jikinta takeji kamar JININ SARAUTA ce ita....wasu motsi nata yana mata kama da mutumin daya fito daga royal family.

"Ina miki jinjina......ina kuma sake sallama miki da yadda kika bude wannan zuciyar me tsananin kafiya....zuciyar data shekara talatin da biyar ba macen data dauko maqullinta daidai ballantana ta samu daman budeta" Ta sake fadi da wani yanayi na raha cikin muryarta. Murmushi akhnan tayi qoqarin maida matan,amma maganganunta suna sauka saman zuciyarta a hankali.

"Kowa so yake yaga wacce me sa'ar ce tayi wannan gagarumin aikin?" Khansaaa dake riqe da hannun akhnan tana jin kamar hannun rumaisa ko na Aanani ko noorah ne ta riqe ta fada tana qaramar dariya. Dariyar data sa ya akhnan sakin murmushi a nutse tana sake sadda kanta qasa,haka kawai takejin wani irin nauyin matar da ta kasa riqe sunanta da taji ya kira.

"Bazai taba bari ki fita a haka ba,koda al'ada batazo mana a haka ba,idan ban takuraki ba,ko zaki shiga dakincan ki canza kayan jikinki?,saboda zamu wuce palace learning residence kaman yadda yazo a al'ada" Yadda take maganan cikin kulawa da taushi ya sanya akhnan binta da kallo. Akwai sarauta sosai a yanayinta,amma akwai wani sauqin kai da martaba me yawa a kallonta da maganganunta,bata gane me take nufi ba illa dai batun canza kayan kawai.

"Akwai wanda za'a kira miki don ta taimaka?" Shuru ta danyi,kafin ta lumshe idanunta ta budesu a hankali sannan tace.

"Birra" Murmushi Khansaaa ta saki,karon farko da taji muryar data matuqar burgeta ba. Ta murmusa a nutse tana dannan wani madanni jikin wani lafiyayyen agogo dake daure a hannunta,sautin muryar akhnan na ratsata,laushi da wani irin aji dake tattare da ita.

"Birra" Kawai akhnan taji Khansaaa din ta fadi,cikin qasa da minti daya qofa ta bude birra ta shigo.

"Ki tayata ta shirya" Khansaaa ta fadi cikin yaren oromo. Ga mamakin akhnan sai taga birra ta gyada kai,a maimakon taga ta rude tana neman ma'anar abinda akace mata,sai taga ta dauki luggage din ta taka zuwa dakin

"A fito lafiya" Khansaaa ta fada cikin girmamawa da harshen English. Bata da wani zabi saita juya tana bin bayan birran.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Tunda taga dakin yanzunne shigarta ta farko. Tsoro takeji ta shiga bacci ya kamata ko wani abu makamancin haka wani abun ya faru da ita,shi yasa ta shanye dukka awannin a zaune cikin luxury sofas din.

Tasha mamakin irin suturar da taga birran na fitowa da ita daga cikin luggage din. Harkar sutura ce sana'arta....bangarenta ne. Duk wani fabric da zare yarn da dutse me tsada ta sanshi. Ta sake qarewa rigar kallo da kyau,sai taga tayi mata kama sak da sabuwar rigar da companyn Elie Saab sample din da ake saka ran zasu fiddashi shekarar 2030.

Batace komai ba,tana tsaye kawai birran ta shiryata tsaf,sannan ta nadeta cikin ni'imtaccen yadi na alfarma,wanda ya qarawa rigar kyau a jikinta.

Mirror ta ajiye mata yadda suka saba a kowacce shiga da zatayi a agadez,ta taka a hankali ta matsa gaban mirror din. Wata akhnan daban take gani ba irin wadda ta sani ba,wata akhnan ta daban ba princess of agadez ba. Wata akhnan daga wata qabila daban take gani,wata akhnan da kayan da take sanye dashi ya zame mata wani irin abu na daban daya fidda wata irin sigar kyau tata,duk kuwa da cewa ta lullube kowanne abu nata da zai iya zama al'aura. Haka kawai taji jikinta yana yin sanyi,hakan kenan yana nufin ta sauya qabila?,ta sauya qasa da al'umma gaba daya?.

"Zan iya shigowa?" Taji muryar Khansaaa daga bayan qofa.

"Eh" Ta amsa mata a sanyaye tana waiwayowa gaba daya.

"Fatabarakallahu ahsanul khaaliqeen" Ta fada murmushinta yana sake qaruwa. Hannunta ta miqawa akhnan tana fadin

"Duk kowa yana waje yana jiranki,lallai dole captain obbo ya buqaci a boye wannan kyan,mu kanmu kishinmu yake ballantana halal dinsa?" Ta fadi tana murmushi sosai. Murmusawa kadan tayi don kada tabar Khansaaa da fara'arta ita kadai,saidai can qasan ranta,can qasan zuciyarta tana jin wani shafi yana budewa na sanin sabbin halaye da dabi'unsa da bata sani ba a baya.

"Sunana Khansaa ko hasnaa.....duk wanda kikeso zaki iya kirana dashi.....nice yaya ta biyu ga captain sheikh,kuma aminiyarsa".

"Captain.....sheikh....obbo" Duka sunayensa ne?.

Zata iya cewa sunan sheikh dinne kawai ba baqon suna ba a wajenta,amma gaba daya sauran baqi ne a gurinta.

Ta daga kanta a hankali sanda suke dab da bakin qofa,sai idanunta suka sauka a kanshi. Yana tsaye fuskarsa na fidda wannan hasken,wannan kwarjinin da haibar shimfide saman fuskar tasa,saidai kuma mayen waya....mayen waya ne kaman yadda ta soma laqaba masa. Idanunsa suna kan wayar yana danne danne.

"Bismillah captain" Hasnaa'u ta fada tana miqawa haisam hannun akhnan. Sai a sannan ya daga fararen idanunsa ya saukesu a kanta.

"Ya hayyu ya qayyum.....ya zaljalalu wal ikram" Ya fada can qasan maqoshinsa adams apple dinsa yana motsawa sama da qasa.

Wata mace daban yake gani.....haihuwar qabilar oromo.. Wata matashiya yake gani daban ba khadeeja muhammad hammud ba cikin tufafin al'ada na sarautar jimma oromo. Sai yaji wani sanyi yana ratsa sannan jikinsa.....wani abu yana mamaye ilahirin jikinsa,ya dauke idanunsa a hankali yana duban gaban jirgin da mutanen da suke jiran saukowarsu.

"Su waye da waye a waje?" Ya tambayi Khansaaa da yaren oromo,da wani irin yanayi da kasala ke bibiye da sautinsa,kasalar da yanzu yanzu ta saukar masa.

"Daga nan yan uwa ne na kusa,daga can farfajiyar airport din kuma bazance ga adadi ba". Idanunsa ya lumshe a hankali saman fuskar Khansaaa sannan ya budesu. Da iya hakan kawai da yayi ta iya karantar yanayinsa,ta kuma iya gane me yake kaikawo cikin zuciyarsa.

"Kayi haquri captain.....iya na yau ne kawai,dukka masoyane dake daukin dawowarka" Ta amsa masa tana qunshe dariyarta. Shuru ya sakeyi baice komai ba,still cikin kwantar da kai tace.

"Ba wani abu daya bayyana,nayi amfani da sutura mafi suturcewa cikin kayan mu na al'ada" Ta fadi tana karyar da wuya. Tasan halinsa.....wani irin farin sani datayi imanin idan bata zama ta uku bayan moti da nanay ba bazata zama ta hudu ba.

Bai amsa ba still,saidai ya miqawa akhnan hannunsa,hannun da tabi da kallo a hankali ta aza nata cikin nasa.

Dukkaninsu kusan a tare kuma lokaci daya suka sauke wata boyayar ajiyar zuciya. Ba wanda yasan dan uwansa yayi amma Khansaaa ta lura hakan,ta saki siririn murmushi ta koma bayansu ta tsaya.

Readers Also Read

More by Huguma