Labarina complete - Chapter 1
Labarina complete Chapter 1: Labarina complete Chapter 1. Copied By HAYATU BABA ZUBAIRU (admin Arewa hausa novels Novels villa Duniyan novels Hayat hausa…
4,483 words
Copied By HAYATU BABA ZUBAIRU (admin Arewa hausa novels Novels villa Duniyan novels Hayat hausa novels Hausa novels and fashion And Cool novel, makeup and cooking)
WHATSAPP NO: +2347039625239
[2/15, 7:20 PM] +234 703 962 5239: 💕💕💕 *LABARI NA*💕💕💕
*Written by*✍✍✍ *Salmah Ali wada* ~*(Aunty)*~
Page 1-5
Umma na tafi makaranta,wai Ke saurin me kike haka da baza ki tsaya yan uwan naki ba ko karyawa ma baki yi ba, Haba umma kalli fa lokacin 7:30 kuma kin san yanxu wahalar mota ake sai kafi minti nawa kana jiran adaidaita baka samu ba kuma sai kaje duk saurin da kai prefects su raina ma hankali ni dai gaskiya kuyi sauri......
Ke kinga in baza ki tsaya mu ba ki tafi prefects din banza, to ya isa haka ku shige ku tafi Allah ya kiyaye hanya to umma sai mun dawo.....
zainab ni gaskiya bazan hau hayis ba duk kan kaje skul uniform dinka yayi squeezing nima wllh, daman Aisha mayyar hayis...
bana son wannan malamain ya shigo duk ya dami mutane,Ke mufeeda surutun me kike in kika kuma magana zaki fita.....
Ke yi sauri kizo muje mu siyo sbd kar a fara cika,ke ban baki lbr b jiya banyan na koma gida na hau fbuk na hadu da wani guy amma fa ya hadu kut😳 kice kin kamu mtsw Ke kinji matsalar ki d anfara magana sai ki fara zance soyayya kin san ni nace miki ba yanxu zan fara ba.to naji
ah ah me ake tattaunawa haka to uwar gulma, kin san ban so lbr ya wuce ni bakomai,in tai wari maji,maryam Ke nan har kin fusata wai yau me zamu cine ko awara ma ae tayi Ke ni nagaji da awara,kin ga maryam in bazaki ci ba ni sai mu siya to naji........
Ina zaune ina assignment waya ta tafara ringi dauka ne tare da dubawa wata special number ce dauka nayi tare da sallama,yar uwata naji an fada nasan baki gane me magana ba dan uwanki ne Ahmad Lah ya kake lpy lau kinyi mamakin kiran da nai miki ne a'a ae na baka number dn naji shiru ban gan ki online ba shine na dau number da kika bani jiya,aiki ne yamin yawa shiyasa,lallai ga dan uwanki me yasa baki kirani nazo na taya ki ba, uhmmm sis daman hk kike da sweet voice I lyk it. Uhm ae kaima hk naka yake to ya samari kai samari rufan asiri😳😳
Me yasa kika ce hk ah haba am too young na kula samari yawwa sis na gwanda Karki kulasu....
Hka muka Kasan ce kullum sai ya Ahmad ya kirani,gashi ya iya bani lbr in be kira ni ba sam bana jin dadi.har wata shakuwa ta kullo a tsakanin mu..... Sis zainab sun yi candy dn hk ynx ni kadai Ke tafi skul...
Mufeeda maihaifin su yarasu shekara daya da ta huce yana da 'ya'ya ashirin maza da mata.....
Shirye shiryen fara waec muke karatu nake sosai narage wasa sbd ina son in ga nasami gud result, Zaune suke suna hira maryam tace Ke ni har na tsaugu muyi candy aemin 😜😜😜da gaske kike nagode fa,mufeeda sai naga kamar akwai soyayya a tsakanin ku,da wa😳 ba wani kawai muna mutunci fatima kyaleta kawai maji nan gaba hmmm kwaji da shi, yace ma yana gaishe ku......
Yau alhamis ta kasance ranar candy mufeeda,maryam da Fatima da ka kalle su Kasan suna cikin farin ciki sbd an kamalla neco raba calendar da sukayi suke yi cikin farin ciki da annashuwa, kowa da burin sa a ransa haka suka rabu ba dadi duk da sunyi alkawarin zasu dinga ziyarta junan su.....
Satin mu biyu da candy tayi jugum tana tunani gashi munyi alkawari da yayana Ahmad da mungama exam zai zo ni inna tuna gabana har fadawa yake karan wayana me ya katse mun tuna ni na in dubawa na ga shine cikin sanyi murya na dauka yace sis kina lpy,yana Ji murya ki hk dg bacci na tashi amsar dana bashi Ke nan sweet sis kina sane da alkawarin mu..... [2/15, 7:20 PM] +234 703 962 5239: 💕💕💕 *LABARI NA*💕💕💕
*written by*✍✍✍ *Salmah Ali wada* ~*(Aunty)*~
Page 10-15
_*wannan shafin naki ne*_ _*F.A YA'U*_
Eh ina sane,to yaushe zan zo kabari na fara fadama umma sai na fadama sanda zaka zo tom shikke na asa da wuri kar aja lokaci dan na tsagu naga kyakkyawar fuskar ki me ciki da murshin da Ke sani fari ciki..hmm tom zan fada mata in ta dawo dg wajen aiki sai ki turo min da address din kamin lkcn tom, mukai sallama tare da daukin ganin junanan mu,umma na ma aiki ciyar gwamnati ce,kamar yanda abbana yake tsohon director a bangare ma'aikatar ilimi dake kano.
Umma yau fa Ahmad zai zo,to mufeeda kinsan dai dokar gidan nan,bnda kwashe kwashe kisan irin samarin da zaki dinga kulawa,samarin yanxu sai addu'a sabida ba kowanne ne na Allah ba to umma.
Salamu alaikum wai ana sallama da mufeeda kinji a kace gata nan,fadilah kai shi dakin baki kamin na karasa,ta fito dg daki sanye take da wata hadaddiyar atmafa pink dinki ya amshi jikin dan dama mufeeda ba daga nan ba wajen iya kwalliya ga sarrafa dan kwali ta yafa orange din mayafi da plate shoe ma orange Wanda ya dai dai da ratsin dake jikin atamfar kai masha Allah, ta feshe kanta da turaruka masu dadi kamshi ta karewa kanta kallo a mirror din dakin ita. Kanta Tasan tai kyau. Umma bari naje tom ki kiyaye kan ki tom dai dai bakin kofar baki ta tsaya can sakamakon daddadan kamshin turaren sa Wanda yasa gabanta yafara faduwa kamar ta koma,ki shigo mana ko baki farin ciki.
Zaunawa tai cike da kunya ta shiga kanta a kasa tare da sallama,cikin muryar sa me dadi ya amsa,zama tai cikin sanyi jiki kamar wadda kwai ya fashe wa a ciki,sweet sis yau dai na ganki duk da nasha ganin k a pics amma kin fi kyau a zahiri,tana dago kanta suka hada ido dashi cikin kunya ta maida kanta kasa haba sis yau nazo muyi magana mai muhimmanci amma kin ki ki magana.
Uhmmm ina jinka a gaskiya mufeeda tun sanda na ganki naji kin kwanta min a raina kuma tun lkc nake son ki na bar maganar ne sbd na bari sai kin karasa skul dam gaban ta ya fadi ciki razani tadago kanta da sauri tana kallon sa maimaita maganar ta kana sona yes mufeeda ko baza ki soni ba,ko ban can canci hakan ba pls mufeeda wllh ina sonki ki taimakan dasauri ta tashi ta bar dakin dan gaba daya ita tsoron soyayya take dn gani take kamar wahalace kiranta yake amma har tashige cikin gida ya zauna yana tunani har yaga dai ba zata dawo ba ya tashi ya fita yana fita yaci karo da fadila kanwata ga wannan ki kaiwa auntyn taki tom,da sauri ta shige daki sharaf ta fada gado hade da rintse idanuwa maganganun sa suna dada yimata yawo a kanta mufeeda ina sonki tun ran da muka hadu nake son ki ki taimakn.
Aunty wai gashi inji bakon da ya tafi ajiye a nan,waya na nai saurin dauka na kashe dan gaba daya tsoron sa ma nake.
Gaba daya taka sa sukuni haka ta zauna a daki kamar mara lpy, juyi take a gado dan ta kasa bacci zuciyar ta da tunani kala kala Ahmad daie kyau ne,yana da kyau da duk wata mace zata so sukance tare,kuma yana da nutsuwa wannan tunanin bacci yai awon gaba da ita.
Shi kuwa Ahmad ya kasa samun nutsuwa sai kai komo ya Ke shi kadai yasan abinda yake Ji game da son yarinyar gaba daya ta sanja mai tunani saima da ya ganta a zahiri kuma trying number dinta yai still akashe tun da ya dawo yake kira amma a kashe,shi kan sa be san iya adadin messages din da ya tura mata ba. Alwala yayi tare da sallah yana rokon Allah yasa mufeedan sa ta so shi.
Yana zaune dan yanda yaga rna haka yaga dare,har akai sallar asuba yana abu daya.
Tana idar da sallan asuba ta kunna wayar,messages ne suka fara shigowa,daukan wayar sa yai ya dannan kiran ta da tunanin Allah yasa ta kunna cikin sa'a wayar ya shiga be san sanda ya saki wata nannuyar ajiyar xuciya game da sallam... [2/15, 7:20 PM] +234 703 962 5239: 💕💕💕 *LABARI NA*💕💕💕
*written by*✍✍✍ *Salmah Ali wada* ~*(Aunty)*~
Page 20-25
Cikin sanyi murya da faduwar gaba ta amsa sallamar,haba mufeeda me yasa zaki kashe waya kin tafi bamu karasa magana,kuma kin kashen waya ko bakya sona ya kamata ki tsaya ki saurare ni,tunda ya fara maganar batai magana b sai yanxu kayi haquri tace masa,tom shikke nan yanxu ki bani amsa ko na sami nutsu mufeeada kina sona ko kina da wanda kike so?
Shiru tai ba amsa,kina da wanda kike so ya jefo mata tmbyr a'a ta bashi amsa to kina so na nan ma shiru tai pls Kice wani abu mana ko sai nazo zaki fadan da sauri tace a'a to ya kina sona uhmmm kabari sai nayi tunani ah sweetie ba wani tunani ki fadan,ah ni gaskiya sai anjima zan fada ma,to ina neman alfarma dn Allah kar ki kuma kashen waya kina sani a cikin damu tom shikke nan sai anjima,kashe wayar ye cikin farin ciki da karfin gwuiwa. Sai a lokacin ta tuba da gift wrap din da ya bata ta daukko ta bude wasu hadaddun turaruka ta gani cike da jin dadi ta dauka tana kallo zuciyar ta aminta da Ahmad din ta, sai dai tana tsoron kar sai ta fara son sa ya yaudare ta,ko da yamma da ya kira ta sai da ya tabbatar da tana son shi sannan ya barta,amma ina tsoron kar wata rana ka yaudaren bayan na fara sonka haba dan Allah ki daina wannan zance in Allah ya yrd baza'a sami wata matsalaba. to tun daga wannan lkcn soyayyar me karfi ta kullo a tsakanin su ko da yaushe suna manne a waya. ****
Sweetie kina gida ne eh to zamu shige ta bakin layin ku nida su Muhd da Abdul shine nace bari mu kara so,to sai kun kara so tashi tai ta kara powder ta lipstick a fuskarta ta fito tace umma ga su Ahmad sun zo mu gaisa shida abokan sa to,Karki dade anyya kuwa yaron nan zai barki ki I Ishashen karatu kuwa uhmmm,waya yai mata yace sun iso.plate ne wanda aka zuba lemukan kwali da ruwa ta dauka tai sitting room. Ah gimbiya sannu. Da zuwa ah ku zan ma sannu da zuwa ya kuke ya hanya, lpy tunda ta shigo ya Ke kallon ta,ah gaskiya dole ki fari d hnklin abokin mu,hk kike da kyau uhmmm tace cike da kunya,Abdul ya kalli Muhd ko nima a nan gidan zan zo nasami mata,kai ya isa hk kun sata a gaba kun cika t d surutu ko ta so mu tafi,sai munyi waya,tom nagode ku gaida gida...
Bayan wasu lokuta tana zaune ta da daddare a dakin tana yin game wayan ta ya dau kara ta dauka bakuwar number ce,ko sallamar da tai ba'a amsa ba kece mufeeda race eh wake magana sunana hafsa kuma nice buduwar Ahmad tun yanxu ina jamiki kunne ki rabu da shi kan ranki ya baci banza kawai aka ja dogon tsaki aka kashe wayan.....
Tooo😳 wace kuma wannan ciki bacin rai xuciyata kamar ta fashe na kira Ahmad,daman yana da wata budurwar amma yake kulani,hello sweetie kin kira inata magana kinyi shiru wace hafsa na tambaye a fusace hafsa kuma ko zakace ba ka Santa ba,to budurwar ka da ka bata number ta,ta kira ni kuma ta fadan ita kake so dn hk kafita harka,kit nai sauri na kashe wayar kuka na sa ki na bacin rai ga wani kishi da yake ta so min kira ya Ke amma naki picking......
Message ya turo mata kiyi haquri ki dauka muyi magana,sai da wayan ya kusa katsewa sannan na dakau pls mufeeda ki saurare ni wllh ni wannan ba budurwa ta bace kawai ita take shirmen ta,yar yayana ce ta karbi wayar tana game shine tai dabarar daukan number ki,kiyi haquri ni Ke nake so,km duk abnd zatai miki Karki saurare ta,kinti shiru ko baki haquri ba? Bakomai ya huce tnx sweetie.
Wai me wannan jakar take nufi dani kullum sai ta kira ni ta zage ni,akan Ahmad gashi zuciyata tai nisa da son sa ya Allah,hk abu yai ta faru wa,ga zuciyata ta ki ta bani hadin kai na cire dg raina, yanxu in dai ban kira shi to ba zai kira na ba kuma ko na masa text ba reply.
Hk aka fara shirye shiryen bikin maryam sam banda walwala,wai me Ke damun mufeeda tunda tazo ta kasa sakewa hmm ku tambaye ta ko zata fada muku nayi nayi ta fadan ta ki,kai na ne yake mun ciwo ga kuma tunanin zamu rabu d aminiya na Wayan ce da hk,ko da aka gama biki bata san ja zani Ahmad ya fita harka t baya kira na in nakira baya picking,
Hello abdul, ah'ah yau kece a gari hmmm wllh,daman kiran ka nai naji Ahmad lpy Kwana biyu inna kira baya dauka tooo😳 kodai ya koma wajen hafsa ne,gaskiya in hk ne da matsala amma zanje muyi maganr tom nagode, da daddare na kuma kiran Ahmad amma shiru be dauka ba wasu siraran hawaye ne Ke xubo min,Alama message ya shigo wayata naji da sauri na dauka ganin number Ahmad ce tashin hnlki na shiga ganin irin abinda yake cikin sakon........... [2/15, 7:20 PM] +234 703 962 5239: 💕💕💕 *LABARI NA* 💕💕💕
*written by*✍✍✍ *Salmah Ali Wada* ~*(Aunty)*~
Page 30-35
Mufeeda ina so ki yanke alaka dani dg yau ki cire ni dg zuciyar ki,ki manta kin taba sani wani Ahmad, inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un nake ambata gaba daya hankli na ya bar jiki na,jefar da wayar nai tare da sakin kuka me karfi,da sauri umma ta shigo dakin lapiya mufeeda mai ya samaki nuna mata wayar nai bata re da na bata amsoshin ba,innalillah ta ambata kuma shi Ahmad din ne ya rubuto kuwa,haba umma kalli da kyau number din sa ne,umma me yasa zai min hk,me yasa zai rabu dani a lkcn da zuciyata ta Ke tsaka da son sa,kiyi haquri mufeeda duk tsanani yana tare da sauki kiyi addu'a Allah ya sassauta miki,ta cigaba da min na sihohin da bakomai nake ganewa b,har ta gama ta fita,
Kullum sai nakira wayar Ahmad ba adadi,bawa kaina shawara nai, *in dai so cuta ne haquri magani ne* na dage da addu'a Allah ya yaye min cikin hikimar ubangiji nafara jin sauki a raina gashi.naje jigawa nayi jarrabawar jamb fatan Allah ya bamu sa'a.lokacin da aka fara sakin result ko da aka dubomin ban samu nasara ba duk naji ba dadi barwa Allah komai.
Muhd abokin Ahmad ne ya kira ni,yau a gari hmmm kin manta da mu a'a ba hk bane nan na warware masa ko na fada masa,Ayya me yasa baki fadan ba to ae komai ya huce to kiyi haquri Allah yasa hkn shi yafi alkhaeri nace Ameen,daman kiran ki nai na fada miki next week za'ae biki na to Allah ya sanya alkhaeri Ameen sai anjima nagode.
Yau kimanin wata shida da rabuwar mu da Ahmad samarin sun sha zuwa gidan mu kuma dk wanda ya aiko bana fita ko fita unguwa nai bana sauraran su,a hk har aka shiga hidimar bikin sisters dina zainab, Aisha da Farida mun sha hidima a wajen bikin na hadu da samari iri iri sai duk cikin su ba wanda na sakarwa fuska har aka gama biki.
Wai mufeeda ana sallama da mufeeda kaje kace bata nan haba mufeeda kace gata nan,ya za ae duk wanda yazo Kice baza ki fita ba, cikin kuka nace haba umma ki kalli abinda Ahmad yai min, to kiyi haquri ynx ki tashi Kije kinsa ba duka suka zama daya ba,raina bace na fita,barka da fitowa saurauniya kallon wane kai na sakar mai tare d harara,hb mufeeda wannan ce gaisuwar eh itace ban iya ba bazan ba,Kaga malam ba dogon zance na fito ba me yakawo ka,eh nidai sunan anwar kuma gaskiya tunda na ganki naji ina sonki,koh lallai yayi kyau kace kaima kazu ka yaudare ni kawai aa wllh ba hk bane,tun kwanaki na karbi number ki a wajen wata sister dn ki sai dai tace kr na fada miki sunan ta,to shine naga maganar nan bata waya bace zuwan sai ya fi,ina Fatan zaki karbi soyyaya ta,hmmm in ka gama ni Kaga tafiya ta,
Tun daga ranar kullum sai anwar ya kira tn bana dauka har nake dauka amma fa baya jin magana mai dadi amma hk yake kirana.kitchen na shiga bayan na gama girki ina yanka salak waya ta da Ke gefe ta fara ringi,dogon tsaki nai na ajiye wayar a karo na biyu kira ya kuma shigowa haba malam wai baka san aiki nake ba kit na kashe, Da yamma ina daki ina gyara gashi na ya kira dauka nai kina lpy,lpy lau na kira ki muyi hira ban da wanan lkcn pls mufeeda ki sassauta ranki be kamata laifin wani ya shafi wani ba, hmmm ae halin naku abn tsoro ne ki yarda dani tom shikke nan.in tambaye ka mana ina Jin ki my star kana da aure,aure kuma, me kika gani bakomak kawai tambayarka ni a'a bani da shi,cikin salon iya soyayya d Jan hankalin mace anwar ya ci galaba akaina amma ban zake ba kamar ynd nai wa Ahmad...
Aikace aikiacen gida nake waya ta na daki, wash! na fada Tare da fada wa gado dn nagaji waya ta na janyo domin kiran Fatima akan zance ankon bikin ta missed calls Nagani cikin tsananin mamaki nake kuma kallo wani kiran ne ya kuma shigowa Ahmad ne,tab ko me zai ce min oho,hello mufeeda ina ta kiran ki baki dau ka ba,bana kusa pls mufeeda dan Allah kiyi haquri wllh.....cikin sauri na katse shi ba sai ka rantsan ba komai ya huce,to mufeeda yanxu ma kiran ki nai dan mama ta matsan na fidda matar aure,hhhhhhhhh...lallai me kace? matar aure tab duka mahaukaci sai sarki kai ynxu baka ji kunyar fadan wannan maganar ba,ba hk bane wllh duk sharrin hafsa ne,to Kaga kayi haquri kaje kasami wata amma ba mufeeda ba ki tsaya mana, nai maka mai jin wannan yaudararrun kalaman naka bada ni,kum dis should b d first and last kar ka kuma kira na sai anjima........
For comments or corrections 08062077070
Love you all my fans😘😘😘 [2/15, 7:20 PM] +234 703 962 5239: 💕💕💕 *LABARI NA* 💕💕💕
*written by*✍✍✍ *Salmah Ali Wada* ~*(Aunty)*~
Page 40-45
Lallai ma wannan be da kunya tab ae ko maza sun kare bazan kuma sauraran sa ba yanda ya gasan aya a hannu,tab dakiki ne Ke maimaita aji.
Gaskiya anwar ka fada mata gaskiya lamari,eh zan fada mata amma ba yanxu ba to menene amfanin boyewar da matsala fa in ta
fuskanta,uhmmm nima ina wannan tunanin kabeer Kasan halin mufeeda,tana da kisha amma ae fada mata xakai, kar azo garin tushe baraka a bullo da wata to zan gwada,ta so muje gidan su al'amen gaida shi Kasan an sallamo shi kar lkc ya kure,
Na gama breakfast wajen 11 ina kokarin jona wayana a charge kiran sa ya shigo, aslm barka da hantsi barka kadai mufee ina son miyi wata magana da Ke amma dan Allah in kinji Karki guje ni,kai😳 kamar ya? Eh kamar yanda na fada miki to kai maye ne, a'a barowa ko kuwa me bin mata a'a duk ba daya,to menene?
Ina da *mata* mata kamar ya eh ina nufin ina da aure innalillahi.....basan lokacin da na tashi tsaye ba,kana da mata fa kace eh to mutuwa tai ko kun rabu a'a Muna tare tab din Jan shekaran ku nawa da aure 2 'ya'yan ka nawa bani da da amma ta kusa haihuwa,
Lallai anwar ka cika cikkaken mayaudari maci amana makarya ci da ka san kana da aure ka buye min mene amfanin karya sbd gudun hk n tambaye kamin karya,ba hka bane ina tsoron karna fada miki ki ki yarda dani,na fada ma ko ynx da ka fadan ba zai hana rabuwa ta da kai ba,macuci makarya ci ynx Inbanda tsabar yaudara aure 2years amma kana harin wani, Daga yau Karka kuma kula ni tunda kai makarya ci ne bazan yi rayuwa da makaryaci ba,ni ae sai shekara daya na fari anyi biyu ina ga kari aikin banza ka canja hali.
Fatima wai yaushe zaki kawo min ankon ne,zuwa nan da jibi tom ina son ganin ki dan da labari Allah, ban in sha a'a ki bari sai dai kin zo,ah to na fasa zuwa jibi gobe zan zo,au da iskanci ne yasa baza ki zo goben ba sai da kika Ji gulma tom sai dai kin zo,
Amma kayan yayi kyau a satin nan zan je wajen me dinki,zanyi wanka fa da bikin nan Allah ko sosai ma,Ke ban lbr hm Ashe anwar makaryaci ne,yana da aure be fadan ba ya rufen,da gaske wllh,ni kuma wllh tunda ya rufen na gama da harkar sa,sbd Karyar da yaimin wllh fatima ni har nagaji ni banyi sa'a ba kudai kun huta,kidaina fadar haka kin san kowa da irin kaddarar sa,ki ci gaba da addu'a tom.yanxu wane hukunci zaki yanke masa hmmm rabuwa kawai zamuyi to Allah ya sawwake bari naima Jameel waya yace in zan tafi nai masa waya mu tafi daga nan sai ku gaisa. anyi bikin Fatima gwanin sha'awa komai anyi shi ynd ya kamata ga samarin biri akwai su.hmmmmm
Shirye shiryen fara skul nake,zan fara zuwa school of technology,yanxu sam na naida kulawa samari duk nacin su sunyi sun gama..... [2/15, 7:20 PM] +234 703 962 5239: 💕💕💕 *LABARI NA* 💕💕💕
*written by*✍✍✍ *Salmah Ali Wada* ~*(Aunty)*~
Page 50-55
Umma yau ina so zani gidan maryam, tun bayan sati biyu da bikin ta rabona da gidan tom ki shirya kije da wuri kar yamma tayi tom,
doguwar riga nasa baka ammata ado da pink din duwatsu, mopling nai da pink din maya fi nadau pink din jaka da takalmi na pink amma plate ne, na fisa plate shoe sbd ina da tsawo kare ma kaina kallo nai a mirror na sa kamar kaina murmushi,
mufeeda duguwa ce siririya bata da kiba sannan ba fara ce can ba tafi karkata ga bakeke kalar en mexico city ne da ita ga ido tubarkalla gashin idon ta sai kazata eyelashes ta saka, tana da dogon hanci dai dai matsakai ciyar fuskar ta, dan karamin bakin wanda pink ne sai kai tsammani janbaki take sawa, turare ta dauka Arabian perform ta fesha ta fito cikin ta kun ta me Jan hankali,,,
Umma na tafi to ki gaishe ta Lah Muhd da ka shirya da ka rakani kanin ta ne, tab ni ba inda zan raka ki bayan in kina tafiya baki iya sauri ba, tunda baza ka ba shikke nan, umma sai na dawo Allah ya kiyaye Ameen, Wai Ke har yanxu baki taho bane ina hanya yanxu na fito dg gida Kice ba zuwa zaki muyi hira ba,
To gani a baki kofa fito ki buden yar rainin wayo
Ashe ma kin kara so kika tsaya jama mutane aji Ke har yanxu ki nan da halin ki na Jan aji uhmm ni dai matsa na shige kin tsayar da ni a hanya kina ta magana kamar me shirin fara aiki a gidan radio,
Maryam Ashe da ban zo ba sai dai naji kin haihu wllh kam ae baki da m.tunda ake bikina baki dawo ba Ke mutuncin ne dake kin taba zuwa namu gidan tun bayan bikin ki,ayi haquri ba tunene za ae ba tashi mu karasa dining area ga abinci can,
Suna cin abin suna hirar yaushe gamo,ajiye cokali maryam tai ta tsaya ta karewa mufeeda kallo, Ke lapia irin wannan kallo hk kar ki sa na kware, hmm wai Ke dan Allah bazaki fiddo da miji ki aure ba kin tsaya ruwan ido hmm maryam Ke nan Ke kike ganin hk kin san aure lokaci ne,
to yanxu wane akan network bakowa, ban yarda ba bakowa kika ce eh, ah haba keda nasani da samari to duk na dakatar da su dan duk suna da matsala to Allah ya kyauta.
Ke dai ki tsaya ki zabo nagari wai Ke maryam girma kika ki sani a gaba kina nasiha yaushe kika fara wa'azine ni bari na tafi sai anjima ki tsaya Bashir ya dawo sai mu rakaki tab a hakan da kike zama da kyar ta shi da kyar nagode basai ki. Wahalar da kanki ba,
maryam ta shiga daki ta hado mata kayan cosmetics ,gashi akuma yakar samarin birini Ke kika damu dasu ni ynxu karatuna ne agaba na, in bash din ya dawo a gashi shi ze Ji.....
Karatu nake sosai ba tare da wasa ko shiriritar biyewa samarin skul ba ko cos mate sai dai gaisuwa Ke hadani da su , kawayena na biyu shukrah da na'ima kullum muna tare.......
Karatun mu yayi nisa gashi muna shekare karshe yan gidan mu sun gaji da korar samarin da nake tun suna magana har sun dai na, na'ima na tsagu mugama skul ma huta kullum kana tafe a hanya kamar ruwa duk kabi kayi baki ga muni ah Karki fa ki zage ni a hakan kikai muni Ke kin fiye abu,ni ban wannan maganar ba sai Ke lallai nima wllh na gaji. Kinga ni'ima ko har yanxu jikin shukrah ne bata warke ba,Ke kin san shukra da lalaci keda ita in kuna cuta kamar akan ku aka fara,ba wannan zance ba yakamata a weekend mu samu muje mu duba ta gaskiya kam,ranar Sunday yayi a'a abarshi Saturday tom Allah ya kai mu ameen,
To sai ki biyo ta gidan mu mu karasa,Ke kin fiye wayo duk inda za'a sai anje ta gidan ku ah to ae mune a tsakiya ke kina godon kaya ni a cikin gari wajen gidan sarki Ke ita kuma shukrah a nassarawa.
To kinga tunda malamin bazai shigo ba taso mu tafi ki bari mu kuma huta wa,wane Hutu kuma a cikin makaranta tab ni dai taso mu tafi in ma aka fara fitowa kin san zamu dade kamin mu sami abin hawa tom...... [2/15, 7:20 PM] +234 703 962 5239: 💕💕💕 *LABARI NA* 💕💕💕
*written by*✍✍✍ *Salmah Ali Wada* ~*(Aunty)*~
Page 60-65
_wannan page din naku ne masoya masu bibiyar wannan littafin nagode da nuna soyayyar ku Allah ya bar zumunci_
Ke kullum likaf ni bazan jera da Ke ba a skul likaf in za'a fita unguwa ma haka ni gaskiya ki cire aikuwa bazan cire ba sai dai mu raba tafiya, kina da matsala matsalar me dan nasa likaf sai ya zama matsala ni muje Karki bata mana lokaci umma mun tafi a gaishe ta to.
Ashe ma kin warke kika ki zuwa skul uhmm wllh hutawa nake nasan yanxu anyi covering shiyasa ya jikin da sauki,