
Post
Lu'u Lu'u Book 3 page 1
.....really...they are rotating between the people who are kneeling on their knees in front of him. The people he never thought he would find inside the house, even though he knew... and he felt in his body that they were probably THOUSANDS of things that could be a burden that not every heart could take... and he believed that again... he believed again when he entered the house and wanted to be a threat to them. From the wide parlor, it becomes the HEART of the house, and the link is really dangerous data about every hidden area of the house.....the hidden corners that an ordinary person can't see or understand. With a kind of calmness, he lowered his eyes on the man whose appearance and manner of entering his life was different from every person kneeling in the parlor. "TAMIM" The name hit him again with a kind of surprise and once again I was amazed at the size of the thread that is tied to all the tangles. Three TAMIM names were born and created and confirmed in Agadez Emirate. Not for anything, but to mislead the minds of the intelligent, to change the analysis and vision of everyone who thinks that the name of TAMIM will be pronounced in the emirate of Agadez, where all th
Bismillahir rahmanir raheem
💎 L U'U L U'U
(The diamond)💎
haisam&akhnan tales
H U G U M A
BOOK 03///PAGE 01
AGADEZ
VILLA STREET
Wani irin ginin gida ne wanda yasha banban da dukkanin gidajen dake jerarru kuma tsararrun layukan da anguwar ke dasu.
Daga waje ba zaka bashi wannan martabar da kwarjinin ba,kamar yadda koda wasa ba zaka taba kawowa zaka samu cikin anihin gidan dauke da wani irin gini da tarin tsaron daya daukesu lokaci me dan tsaho kafin su cimma cikin gidan dama target dinsu ba.
A hankali ya sauke babbar takardar daga idanunsa......takardar data kasance launin ruwan bawon lemo wadda ke dauke da wasu irin tarin rubuce rubuce da suka qunshi bayanai masu muhimmancin gaske.
Sanye da wasu irin baqaqen kaya da suka sake bayyanat da ainihin zatinsa......kamalarsa suka kuma cikashi da wani irin kwarjini. Duk da cewa bai bada dama ga duk wanda ke tsaye a gurin ba da zaiga fuskarsa kai tsaye ba.......amma wadannan idanun......wadannan idanun dake jiqe da tarin abubuwa masu yawa da nauyin gaske........suna juyawa ne tsakanin mutanen dake durqushe saman gwiwoyinsu a gabansa. Mutanen da bai taba tunanin sune zai samu cikin gidan ba,duk da ya sani......yana kuma ji a jikinsa tabbas BINNANNUN ABUBUWA ne da zasu iya zama da nauyin da ba kowacce zuciya ce zata iya dauka ba......ya kuma sake gasgata hakan........ya sake amanna lokacin da shiga cikin gidan yake neman zame musu barazana.
Daga faffadan parlor din daya zama ZUCIYAR GIDAN,kuma mahada me hatsarin gaske data game kowacce boyayyar shiyya ta gidan.....boyayyun sasannin da ba lallai ordinary mutum ya iya gani ko ya iya fahimtarsu ba.
Da wata irin nutsuwa ya sauke idanunsa akan mutumin da qirarsa halittarsa da kuma salon shigarsa yasha banban data kowanne mutum dake durqushe a parlor din.
"TAMIM" Sunan ya sake harbawa a kansa da wani irin tarin mamaki da kuma sake jinjina girman zaren dake daure da dukkan wata sarqaqiya. An haifa an kuma qirqirar tare da tabbatar da sunayen TAMIM har uku cikin masarautar agadez. Ba don komai ba,sai don a batar da hankalin masu hankali,a sauya nazari da hangen nesan dukkan wani me tunani a duk sanda za'a furta sunan TAMIM a masarautar agadez,ta inda dukka hankali bazai kai ba.
Da wani irin sanyi ya sake zare idanunsa daga kan mutumin.......mutumin daya dauki shekaru yana wahalar da K'ASARSA......mutumin daya sanya shugabanni masu yawan adadi da suka jagoranci Security Agency dinsu suka kammala wa'adinsu.....suka kuma sauka da tarin burin shigarsa hannunsu.....mutumin daya zama silar jefa tsoro cikin masarautar OROMO.....mutumin daya yanke nutsuwa da dukkan farinciki daga ahalin AJANI AHMED. Kallonsa kawai yana rura wata irin wuta daga zuciyarsa......kallonsa kad'ai yana sanyashi yaji kamar ya yanke dukkan hukuncin daya kamata ace ya fuskanta a lokacin.....saidai kuma akwai saura......akwai kuma lokaci.....ba kuma yanzu ba.....ba'a daidai nan ba.
Yanaso ya zama AIKE ga dukkan wani sassa da rassa sa sukayi tarayya wajen ginashi.....wajen gina laifukansa......wajen tabbatar da wanzuwarsa. Sau biyu yana bude baki da zummar masa magana sai ya maida bakinsa ya rufe. Baya da tabbacin komai da zaice masa.......saidai yayi imanin duk da girman jikinsa.....wannan gangar jikin da yake alfahari yake kuma taqama da ita tayi laushin da har tsakiyar zuciyarsa yasan yana ji. Artabu ne suka fara dasu beeno......daga qarshe dole muhammad haisam yayi taking over......yayi masa wata irin qofar rago ya sanyashi a corner ya shigo hannunsu.
Takun tafiyar dake kusanto gurin ya sakashi maida idanunsa hanyar da sautin yake fitowa. Omar salawii da abeer ne......sai idanunsa suka sauka kan matashin saurayin dake tafe a tsakiyar su.
Dukkan idanuwa haisam ya zuba masa.....kamar yadda shima matashin nasa idanun ke cikin na haisam tamkar yana neman wani abu daban.....wani abu daya banbantashi da sauran halittun dake gurin.
Wannan zuciyar dake kwance cikin qirjij haisam ce ta motsa.......yana jin wani rauni yana tsarga masa. MATASHIN AMSAR TAMBAYARSA NE......fuskarsa kawai AMSA ce ga tarin tambayoyin da basu qarasa warwarewa cikin kansa game da gidan ba.
AJANI qarami yake gani yana takawa da qafafunsa.......ta wani motsin nasa kuma SAFEENA ce. Shine wannan jinjirin......wannan jaririn da aka dauke tun daga ranar haihuwarsa......shine wannan yaron jini na farko.....kuma iri na farko daga jikin safeena.......
Ci gaba da kallonsa haisam yakeyi,sanda suke sake kusanto inda haisam din ke tsaye. Sai yaji kaman qafafunsa sunayin sanyi a sanda yake karantar sigar yaron,don haka ya dunqule dukkanin hannuwansa yana cusasu a aljihun wandonsa yana ci gaba da qarewa matashin kallo.
Idan dai har nazarinsa yana tafiya a yau a daidai......idan dai har abinda idanunsa suna iya gane masa daidai......nutsuwa da wani irin kamewa yake gani qarara tattare da matashin,abinda yasha banban sosai da AHMAD ALMAZ.
Kallon kallon dake Tsakaninsu bai yanke ba,har sai da suka iso dab dasu. Da idanu ya yiwa omar magana,sannan ya maida dubansa akan sauran dukkaninsu. Su dinma da ido kawai ya musu magana suka fahimci me yake nufi,ya juya a hankali ya fara takawa,saidai maganan da tamim babba yayi da yaren oromo ya sanyashi d'an dakatawa kadan.
"Ina kyautata zaton kai din jinin ABA JIFAR NE......IBRAHEEM din da qaddarar salwantar SALEEM magajinsa tazo a hannuna" Yayi maganar da qeqasashen lafazi,da kuma wannan qeqasashiyar zuciyar da a iya lafazinsa kawai ta nuna hakan.
Yaji saukar maganarsa har cikin ransa......yaji saukar dukka lafuzansa gaba daya.......saidai juyawa ya kalleshi a irin wannan yanayin zai iya haifar da komai,don haka sai ya zabi ci gaba da takawa a nutse,muryarsa da wannan haibar ya furta.
"Beeno.......inason a batar da gidan". Gajeriyar maganar data qunshi tarin ma'anonin da baida buqatar tsaiwa fassarawa su abdii din.
A K H N A N
Ba zata ce ga wani abu dake riqe da zuciyarta ba.......amma tabbas akwai wani baqon abu dake ragaita tsakanin zuciyartata zuwa qirjinta.
Wani fayau takeji tsakanin zuciyartata zuwa qirjin nata lokacin data tsinci kanta da sanya karatun qur'ani bayan shuru da kad'aicin da ita ta zabeshi ya mamayi dakin......zuciyarta tana mata tuni da kalamansa na qarshe
"yawan saurare da karanta alqur'ani yana sanya zuciya ta samu nutsuwa"
A hankali haqiqanin yarda da maganarsa yake ratsata,wani irin yanayi me cike da nutsuwar da bata zaton akwai yiwuwar samuwarta ba ga ruhi da gangar jiki bayan fuskantar wata mummunar baraza daga rayuwar dan adam ba itace take ratsata. Sassanyan sautin nan nasa daya samu nasarar shiga kamfanonin dake sarrafa na'urar MP3 na zamani masu zuwa da fitilar gado. Wannan kwantacciyar qira'ar......wannan muryar dake nuna zallar nutsuwar da mamallakinta ya mallaka tun kafinma kakai ga ganin anihin fuskar me muryar.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Kamar ita dai......a yanzun da sautin karatun ke shiga kunnenta da wani irin nutsuwa da sanyi,sai fuskarsa take dawo mata......sai fuskarsa take gilma mata da dukkan wannan motsin nasa dake nuna irin izza da qasaitarsa......tun daga ranar farko a hippodrome.......a hankali har zuwa awanni da lokutan da suka samar da kusanci me girma tsakaninsu....wato festival d'lAîr......ranar da taso zame mata wata mummunar rana da zata shafe tarihinta raga SARAUNIYAR QASAR AGADEZ zuwa wata halitta mafi qasqanci. Saidai taimakon Allah,da kuma wanzuwarsa.......jarumtarsa dama wata irin zarra daya mallaka ya sanya ta kubuta daga wannan mummunan harin.
A hankali ta bude idanunta da zuwansa qarshen suratul baqara wanda yayi daidai da tambayar data harba cikin kwanyarta.
"Akwai wani abu da wani zai sake bata a duniya da yakai darajar abinda yayi mata?" Tambayar ta sauko mata a hankali tana hadewa da wata tambayar data sake zuwa mata.
"Inda ace tamim ya samu nasarar abinda ya qudirta......inda ace abinda ya tsara ya tabbata......inda ace haisam baya tare dasu a wannan lokacin fa?.....me zai faru?. Tambayar data sake buga wani abu me girma a qirjinta,abinda ya tilasta mata lumshe idanunta a karo na biyu,saita samu labbanta ta furta.
"Astagfirullahal azeem" Da wani irin yanayi da ya bayyana cikin kunnuwanta......da wannan muryar tasa......da wannan taushin a sautinsa wanda ya zama tamkar dan jagora a gareta,har zuwa sanda taji yanayinta ya daidaita......yanayin kuma da yazo daidai da fara kiran salla cikin wayarta dake ajiye a gefanta.
Idanu ta zubawa wayar tana kallonts kamar me sauraren jiran wani abu,kiran sallar yana fita a nutse......irin kiran sallar da masjid haramain sukeyi kowanne lokaci na salloli guda biyar din,bata kuma dauke idanunta ba har sai da wayar ta gama kiran sallar.
A hankali ta miqa hannunta ta dauki wayar tana latsawa. Shine ya sanya mata kiran sallar tun a wancan ranar daya kaita wancan gidan......wancan gida dai da batasan har yanzu ina bane?,gidan waye kuma cikin agadez. Kiran sallan da a wancan lokacin takejin ya takura mata.......saboda duk wata sa'ar da lokacin sallah ya shiga zai dameta da bugawa har sai tabar komai taje tayi sallar. Tayi dukka shige shigenta cikin wayar amma kuma ta gaza ganin ta inda ya sauke manhajar,ta kasa gane komai......ta gaza fahimtar komai. A dole ta haqura,har kuma zuwa yanzu data fara sabawa da abin.
"Manzan Allah yayi jan kunne sosai game da sallah......ya gargademu mu kiyaye lokutanta,wata abace da duk kyan ayyukanka idan ka samu naqasu a kanta to bata yadda zaka wuce a gurin Allah.....komai naka.....dukkan ayyukanka sun baci......sallah kadai magani ce......tana gyaran zuciyar dan adam dama ayyukansa,idan ka kyautata sallarka to hatta da zunubai zasuyi qaura daga gareka.....amma idan har kana sallah.....kuma baka daina aikata munana ayyukan da Allah ya hana ba.....ta iya yuwuwa sallarka aslan bata karbuwa........ko batayi yadda Allah yake sonta ba,shi yasa bata tasirantu a kanka gurin hanaka miyagun laifuka ba". Ta tuna d'aya daga cikin maganganunsa da taji a wata rana da suke karatu dasu falaak.
Kafin tayi kowanne motsi birra ta nemi izinin shigowa,kamar kowanne lokaci cikin girmamawa da suka saba bata ta sadda kai.
"Lokacin sallah yayi ranki ya dade" Tayi maganan tana sunkuyar da kanta qasa. Idanu akhnan tadan zuba mata kadan. Karan farko da birra ta soma shigowa don tunasar da ita lokacin sallah?.......to me ya faru?......me ya kawo wannan sauyin?.
Bata tsananta wannan tunanin ba,saboda jikinta dake bata daga inda canjin yazo,sai kawai ta yunqura ta miqe sosai tana zama saman lallausan qaramin gadon hutawar.
"Tanti Aisa ta bayar da saqo......tace a shaida miki ta wuce......tace mu barki basai mun mata iso ba.....mu barki ki huta......amma zata dawo nan da kwanakin tafiyarku taga tashinku in sha Allah" . Ta danji mamaki kadan na tafiyar aisa din a wannan lokacin. Ba lokaci bane daya kamata ace ta tafi din ba,saboda ko kwanakik festival din basu kammala ba bare ayi shirin komawa......
"Akwai wani abun da kike buqata?" Birra ta sake fada a ladabce. Maganan yadan bawa akhnan din mamaki,har sai data waiwaya ta dubi birran. Ta sani......wani sabon abune yin kalar wannan tambayar ga akhnan din.
"Afwan........umarni ne daga abdii wanda ya sameshi daga sheikh muhammad........komai qanqantar buqatarki a sanar a kuma yi abinda ya dace". Ta dauki wasu lokuta kadan tana kallon birra,maganan kuma yana samun wani mazauni na daban yana zama cikin kanta.
Ba yau ne karo na farko da ake kula da buqatunta ba.....ba yau ne lokaci na farko da buqatunta suka zama abun riritawa da kulawa ba......amma a yau dinne takejin komai kaman yasha banban da yadda aka saba mata.
Batace da birra komai ba ta miqe a nutse.
"Ina buqatar zuwa dakin karatu na mai martaba" Ta fadi haka kurum. Haka kawai takejin tana buqatar duba wani littafi daya shafi tarihin manzan Allah. Tanason ta samu haske kan abinda ya shafi ma'aikin da yake yawan cewa yace ko yayi. A yau karo na farko a rayuwarta tana sha'awar duba tarihin rayuwar fiyayyen halitta da yadda yayi rayuwar tasa.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽