Kenza eBookz

Mar'adams book 3 - Chapter 40

Mar'adams book 3 - Chapter 40

Mar'adams book 3 Chapter 40: Mar'adams book 3 Chapter 40. Numfashi ya sauke yana cewa “is okay na fahimceki” na gode sosai Allah ya biya maka bukatunka na…

3,362 words

Numfashi ya sauke yana cewa “is okay na fahimceki” na gode sosai Allah ya biya maka bukatunka na alkhairi a kasan zuciyarsa ya amsa da” ameen!”tana qoqarin fitowa daga cikin motar kira ya shigo wayarta ahankali ta koma ta zauna tare da ciro wayarta sunan umma ta gani yana yawo akan screen din wayar da sauri taja koren maddani tana qoqarin kai wayar kunnenta ya rike tsintsitar hannunta tare da saka wayar a hands free “maryama kina ne ?”kiyi maza ki qaraso gida yau alkubus nayi mana nasan zakiji dadi sosai”kyakkywan murmushi ne ya bayyana akan fuskar maryama sannan tace “sosai kuwa umma nah gani nan yanzu zan shigo ,to shikenan kiyi sauri kinsan idan yayi sanyi bashi da dadin ci” umma ta fad’a cike da kulawa “yanzu nan zaki ganni ummata sai kin shigo umma ta fad’a tana katse kiran inda maryama ta kalli mr ata fuskarta da bayyananne murmushi “tabbas ya yarda matar na tsananin sonta wanda hakan yasa yaji zuciyarsa ta dan bata wani matsugune acikinta har bakin get din gidansu ya rakota sai daya ga shigarta sannan ya juya ya wuce gida .”

Ahankali ya shigo parlour mami ya ajiye yar saman suit dinsa akan hannun kujera idanunshi na kan mami dake tsaye ta d’ago ta kallesa a natse kafin ahankali ta qaraso zuwa inda yake ta tsaya tana tambayarsa”lafiyarka meke faruwa na ganka haka ?”shiru yayi kawai yana hura hanci tasan halinsa a duk sanda yayi haka baya bukatar acigaba da damunsa akan abu “ ka qarasa d’akin ka kayi wanka kazo kaci abinci kanshi kawai ya gyada sannan ahankali ya zagayeta ya haye sama bayan wasu mintuna mami taji shiru bai sauko ba ta nufi dakinsa a zaune ta iskeshi shiru cikin yanayi na tsananin tunani ta zauna kusa dashi “wai meke damunka ne “?ta tamabyesa cike da kulawa “babu abinda ke damuna sweetheart ko kina tunanin akwai abinda zan iya boyewa kyakkywar mahaifiyata ?”harara shi tayi tana cewa ”akwai mana sau nawa ina tambayarka abu kace min babu komai alhalin kuma ni nasan da komai din .”shiru yayi batare da yace uffan ba “nifa nasan halin d’ana,nasan yanayinsa kuma nasan yanayin damuwarsa kawai dai ka fad’a min “ya kamo yatsun hannunta cikin nashi yana cewa “babu komai sweetheart just believe me, I can’t believe you adamcy amman dai me kake son kaci muna da rice and stew da farfesun kan rago muna da tuwon semoveter da miyar danyar kubewa da cat fish, muna da light soup daakayi mix dinsa da kan rago da kayan ciki da busashen kifi muna da ..” sweetheart alkubus zanci .”

“ alkubus zaka ci bayan shekaru masu yawa rabon daka ci “?“yes shi zanci sweetheart ya fad’a yana lunshe mata tsumammun idanunshi shiru tayi kawai tana kallonsa ,kin bude idanunshi yayi saboda gabadaya jinsa yake acikin wani iri yanayin kamar ya yi kuka ko ya samu salama a zuciyarsa da Kyar ya bude idanunshi sakamakon jin shirun mami “kiyi hakuri sweetheart nasan bazan samu ba “babu wannan ranar da d’ana zai ce ga abinda zai ci ni kuma na kasa masa tayi maganar kamar zatai kuka “na dade ina expecting haka kullum burina naji kace zakaci abinci da mahaifinka yafi so shiyasa naji maganar wani iri”bari naje nayi maka just ka bani lokaci kad’an yanzu zanje nayi maka alkubus “ ta mike ta fita da sauri tana goge gutun hawayen daya cika gefen idanunta.”

“Kai umma qamshi allubus din ya cika koina agidan nan ,da gaske maryma?allah kuwa barin ma qamshin miyar maza maza kije kiyi fresh up kizo kici tun kafin yayi sanyi “okay umma ta fad’a tare da nufar hanyar dakinta da sauri .” bangaren mr ata zaune suke shi da mami akan gado tana bashi alkubus abaki “sweetheart !”bata amsa ba ta tsaya tana kallonsa me kike tunani haka ?”ina tunanin wasu abubuwa da suka gabata ne sannna kuma ina kallon kyakkywan d’ana .”sweetheart ki daina dogon tunani haka kinji kin rasa abba amman kuma kina damu biyar ina son ganinki cikin farinciki’ “uhm ta furta a kasan ranta sannan ta soma mgn “kana son ganina cikin farinciki amman zuciyarka ta kasa amsar zabina kuma farin cikina ?”tayi maganar cike da rauni ina tsananin jin tausayin maryam” yanzu haka nata rayuwar zai kare cikin rashin jin dadin rayuwa?mai yasa adam?ni abinda nake so kuma yafi komai mahimanci arayuwata shine ka yarda ka kuma amince da cewar cikin jikinta naka ne kuma zaka so shi kamar yadda naka uban ya soka ya kuma nuna maka gata ,ina son naga murmu shi akan fuskar maryam I just want to see the smile on her face .”shiru yayi yana kallonta kafin ahankali ya motsa lips dinsa “sweetheart kin kasa fahimtar zuciyar adamcy dinki abinda bazai ta’ba yuwa bane is not possible na amince …”

Cak zuciyar mami ta tsaya ta daina bugawa yadda ya kamata tare da zuba masa idanunta” ki rabu da damuwar yarinyar nan kawai ta girbi abinda ta shuka dan Allah sweetheart ki bar min maganarta ,ki barni a yadda na tsaida zuciyata shiru ne ya biyo baya kafin ahankali ta cigaba da motsa labbanta “batun wacan yarinyar fa ?”yayi shiru kawai yana dubanta fuskarsa da alamun tambaya “wacan yarinyar data shigo rayuwarka nake nufi ko ..”ko itama bazaka ce wani abu akanta ba ka kawo min ita ni zan fad’a mata cewar kana sonta kuma nasan zata fahimceni ina son naga ka zama cikakken mutun adamcy duk da kai baka bin umarnina ni zan maka komai amatsayina na uwa zan baka farinciki daka qasa bani saboda tsnanin son da nake maka ta qarasa maganar kamar zatai kuka “tunda naji zuciyata tana son ganin yarinyar tabbas rayuwar adamcy nace .”shiru yayi kawai tare da zuba mata idanunshi yana shafa fuskashi da tafin hannunsa yana tunain maganganun maryama wanda har lokacin zuciyarta tana ga wani ,gabansa ne ya dinga bugawa da qarfi “sweetheart karki damu maryama zatazo ta ganki “

Mmn Sudais💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

38

A kaikaice mami ta kallesa sannan tace “maganata ta tabbata kenan ?ATA ya bala’in tsurawa mami Ido yana kallonta fuskarsa d’auke da mamakinta yayinda kwakwaluwar sa ta shiga maimaita masa abinda ta fad’a yanzu “maganata ta tabbata kenan “.to me hakan yake nufi?” “adamcy!“ ta kira sunansa tare da riko tafin hannunsa cikin wani irin yanayi mai cike da tashin hankali da jin tsoron abinda take son fad’a ,shi kam kallonta ya cigaba dayi cike da rauni tare da yin kasa da murya yace “sweetheart ina jinki “da gaske adamcy son yarinyar nan kake tunda gashi kace zata zo? numfashi ya sauke yana cigaba da kallonta “itace fa ta matsa masa da batun tana son ganin maryama yanzu kuma ga abinda take fad’a “wai meyasa sweetheart take masa haka ne ?numfashi ya janyo da kyar ya fesar sannan ya motsa lip’s dinsa yana cewa “sweetheart nifa ban fahimceki ba?” ya qarasa maganar yana mai kawar da kanshi daga kallonta “adamcy nasan ka fahimceni sosai ba iya zargina ba ,hatta zuciyata ta aminta da son da kake ma yarinyar nan abida naso ya faru akan mar…” .“sweetheart abar maganar nan .”ta sake bud’e baki har ta soma magana ya juyo da sauri yace “dan Allah sweetheart karki sake cewa komai akan yarinyar nan ,itama maryama baza tazo ba shikenan “ya qarashe maganar cikin ‘bacin rai da rauni a fuskarshi ,ya rasa dalilin da yasa take masa haka idan ma son yarinyar yake me ye laifi aciki tunda shi ba yaro ne da zaa dinga masa irin haka?.”tace tana son gani yariya yace yaji sannan kuma ta shigo masa da batun wata maryam abinda ta rigada tasani ne ko maganarta baya son ana masa,wannan matsalar na cikin abinda yasa yake son ya auri maryama a boye sai bayan sun haihu sannan ya fad’a mata dan yasan kota amince ya auri maryama to fa kullum sai tayita masa mitar rashin kasancewarsu da wannan banzar maryam din ”.

“Me yasa?kuma saboda me za’a bari “?me yasa zaka d’auki zafi daga ‘yar wannan maganar har kace baza tazo ba ?”tayi masa tambayar ajere tana dubansa cikin tsananin tashin hankali duk da dai tafi son shi da maryam dinta amman kuma hakan bazai sa taki son abinda yake so ba dan arincikinsa shine nata “kayi shiru kana jina kayi magana mana,sarkin zuciya. “Kai dai ba’a ta’ba yin hirar arziki da kai batare da ka shigo da zafin zuciya ba ,kanshi ya juya tare da zare hannunsa cikin nata ya had’e waje d’aya ya fuskanci mahaifiyar tashi cikin sanyi yace “ba maganar zuciya bane kawai dai gani nayi rashin zuwan nata zai fi zuwanta samun kwanciyar hankali”amman dai kasan kana son yarinyar nan “inna lillahi ya furta yana runts ido “babu wani batun inna lillah gskyr dake cikin zuciyarka nake son nasani “dan girman Allah sweetheart ki bar maganar nan kuma maryama bazata zo ba dan nasan zuwanta ba zai kwantar miki da hankali ? ”girgiza masa kai tayi alamun a’a.”karka damu ka kawo min ita Ina son naga ka sake ajiye iyali a karo na biyu, zaka auri yariyar nan kuma anan kusa idan ma bazaka iya sheida mata kana sonta bane ni zan sheida mata da kaina karyata taki amincewa ,dan banga macen duniya da zaace mata ga miji kamar d’ana tayi rejecting ba gara ma ka natsu ka kawo min ita ni na sheida mata d’ana yana sonta tunda kai girman kan tsiya bazai barka ka iya sheida mata ba.”numfashi da ajiyar zuciya ya sauke atare still idanunshi na kallonta .mami ta jima zaune suna hira irinta d’a da mahaifiya sannan tai masa sallama ta sauko qasa ta shige bangarenta .”

Bayan fitar mami tashi yayi ya shiga bedroom dinsa ya qarasa inda system dinsa yake ya d’auka ya dawo kan bed dinshi ya kishingid’a akan gadonsa had’e da tokare hannunsa d’aya a gefen kungunsa sannan a hakan ya kunna system ya soma daddana keyboard din system dinsa yana amsa sakonin abokan kasuwancinsa yayinda bangaren maryama itama zaune take a tsakiyar gadonta ta rungume pillow a qirjinta tana tunanin abinda ya faru yau atsakaninsu sosai take tunanin abinda mr ATA yayi mata a yau din nan ,ahankali komai daya faru tsakaninsu yake zuwan mata daki daki har zuwa sanda ya kamo hannunta yace“tayi jump !”jump maryma” ya fad'a hankalinsa a matukar tashe yana sake hura hanci “wannan shine best solution agareki ,shine kawai abinda zai kawo miki qarshen kuncin da kike ciki ,kuma shi zai kawo qarshen rayuwarki .” ”kina zubar da hawayenki a banza bayan Kinsan mutumin nan ya mutu baya raye "wani irin tsoro da matsanancin firgice taga ya bayyana akan fuskarsa alokacin "oya jump!”har sanda ta soma kuka mai tsanani wanda ya zamo sanadiyyar kawar da tarin damuwarta wani irin naunayen ajiyar zuciya ta sauke mai qarfi tana cewa “duk rashin kirkinka da nake gani still kai din mutu min kirki ne ,ban ta’ba tunanin zaka zamo silar yayewar damuwata ba sai gashi acikin awanni ka zamo silar kawar da tarin damuwar da nayi shekara da shekaru ina dawainiya dasu.” “hakika kai din mai kyakkywar zuciya ne ,kawai da nice da wasu daga cikin mutane muke maka wani irin kallo ,duk da kana da wasu dabi’u marasa kyau amman dai kana da kyakkyawar zuciya .”ta furta a fili fuskarta bayyane da murmushin farinciki ta matse pillow dake makale a qirjinta tana cewa .”maryama tana godiya bisa qoqarin da kayi mata na gode sosai daka canza min rayuwa .”

ahankali mr ata ya d’auke kwayar idanunshi akan system zuwa wani bangare dabam tare da rufe system din gaba daya“ya d’aga kanshi sama kallon saman d’anki tunanin maryama yake yana jin kamar ya kirata “idan ka kirata kace mata me?”ai ita ya kamata ta kiraka no kai ya kamata call her and tell her how much you loves her dan idan ka bari wani ya sake sace zuciyar yarinyar nan zaka iya mutuwa for real you’re so much in love with her .”ya fad’a yana runts tsumammun idanunshi .a natse maryama ta sauko daga kan gado ta soma tafiya tana magana a fili muryarta cike da matsanancin farinciki “na gode sosai mr ata Allah saka maka da mafificin alkhairi.” shima bangarensa mikewa yayi tsaye tare da yin shiru ya saka hannunwansa duka cikin aljihunsa wondonsa yana magana a fili “lallai soyayya ya zautar da kamilar yarinya mai tsananin baseera da sanin kan aikinta yana matukar son furta mata cewar yana sonta amman soyayyar wannan mataccen da yake hangowa har yanzu acikin kwayar idanunta shine dalilin da yasa ya kasa fad’a mata ,hakazalika itama karon kanta shine dalilin da yasa ta kasa fahimtar inda ya dosa ina ma zata bashi damar daya d’an d’ana mata gard’in soyayyarsa.”amman zan yaki zuciyarta. “ zan yi duk yadda zanyi na raba zuciyarta da tunanin kowa sai nawa ,zan dasa mata qaunata ta yadda zata kasa samun kwanciyar hankali sai tana tare dani.”cire hannuwansa yayi duka yaje ya bud’e wordrobe dinsa ya d’auko wani takarda ya rufe wordrobe din ya tsaya sosai rike da takardan yana kallo yana cigaba da tunanin maryama sosai yake jin tsananin soyayyarta na sake ratsa dukkanin sansar jikinsa kai kawo ya shiga yi acikin d’akin shi kad’ai yasan irin azabar da yake ji ajikinsa .”

Hotonsu maryama aunty abida ta tsaya tana kallo jikinta na wani irin rawa tmkr mazari “meye haka sultana? meke faruwa haka ?”mafarki nake ko kuwa gaske ne abinda nake gani adam ne rungume da wannan yarinyar ?shine aunty ai ba wannan bane karo na farko da suke lalatarsu a office sai dai wannan shine karo na farko da nayi qoqarin d’aukarsu batare saninsu ba bama fa AGC wannan abu ya faru ba d’aukar ta yayi taka nas suka bar kamfani zuwa ATA company .” “aikinsu fa kenan sai dai idan basu had’u da juna ba.” nan take gaban aunty abida yayi wani irin bugawa da qarfi tamkar wata matarsa “aunty da alamun yaya adam yana tsananin qaunar yarinyar nan “ai wannan ma ba abu ne mai yuwu ba sultana kinji yadda nake ji kuwa “ta mika mata wayar tana cewa” ai kallon wadan nan hotunan zai iya sa mutun yayi loosing temper dinsa .”wallahi aunty haka nake fama da wannan bakinciki kullum zuciyata kamar ta fashe ni nasan bazan ta’ba samun auren yaya adam ba kinsa zuciyata ta kamu da tsananin soyayyarsa .”ta qarasa mgnr tana dafe goshinta

“aunty kece kika dasa min soyayyarsa a zuciyata gashi nazo ina masa wani irin mahaukaci so da bazan iya rayuwa babu shi ba “sultana ta qarasa maganar cikin zafin rai “ki natsu sultana duk runtse duk wuya ina tare dake kuma zaki auresa sannan soyayyarsa da wannan yarinyar ba abu ne mai yuwuwa ba kamar ma ya lalace ya gama “me zaki iya yi aunty akai ?zanyi komai akai sultana “sultana ta matso kusa da auntynta tana cewa “aunty kibi komai a hankali karki yi bakin jini ki barni dashi “no no sultana gara ni nayi saboda kinsan halinsa bazai ta’ba d’aga miki qafa ba “yadda bazai ta’ba d’aga min qafa ba haka kema bazai d’aga miki ba amman da sannu ni zanyi maganinsa sai na watsa hotunan nan zuwa social media kowa ya san halin da yake ciki sai dai kafin nayi haka sai muyi da wajewa dashi zai aureni ko kuwa na yad’a idan ya amince fine idan kuma yayi taurin kai nima zan nuna masa kalar nawa taurin kai ta fad’a idanuwanta na kawo ruwan hawaye “.

“mai na rasa aunty da yaya adam bazai soni ba ?wallahi aunty ina tsananin son yaya adam yana da matukar mahimanci arayuwata ina mutuwar son shi amman shi ko kad’an baya qaunar sanyani acikin kwayar idanunshi .”mai yasa ya bawa maryama mahimanci haka arayuwarsa in takaita miki aunty a irin soyayyar da yakewa yarinyar nan baya iya juyata a office komai taga dama shi take yi kuma yana kallonta bai isa yayi magana ba amman kuma nasan duk yana yin haka ne saboda yana samun wani abu agurinta ka rasa ma sonta yake ko kuwa saduwa yake daita .?”ni babu ruwana sultana da ma koma menene a tsakaninsu ni dai ya barta kawai ya fuskanceki kema Kinsan dole kema kiyi closing dashi idan ya kama ki mallaka masa kanki ne duk kiyi domin dole ki zama suruka acikin gidansu dan bazan bari wata mace ta sake shigowa cikin rayuwar adam ba never .”sultana tayi shiru kawai tana duban yayarta dake tsaye cikin tsananin tashin hankali anya kuwa zata iya wannan kasadar mallaka masa kanta fa ta ina ma haka zata kasance a tsakaninsu mutunin da ko second biyar baya bata za dai ta tuntubesa akan aure idan yaki kuwa zata bashi mamaki .”

*****

Washegari

Ahankali maryama ta shigo cikin ma’akatan sanye cikin doguwar riga baka mai ratsin ash colour ajiki tayi rolling din kanta da mayafi ash yayinda qafafuwanta ke sanye da bakaken flat shoe haka jikinta wani irin sihirtaccen qamshi mai sanyi ne yake fitarwa,jikinta a sanyaye take tafiya makale da jakar aikinta sai dai kallo d’aya zaka mata ka fahimci yau din tana cikin farinciki .”a natse ta shiga lifter zuciyarta da kwayar idanunta cike da tsananin farinciki son d’aura kwayar idanunta akan mr ata kofar lifter na gama bud’ewa ta fito tare da mutane dayawa kowannensu ya d’auki hanyar office din da zashi .”kai tsaye hanyar office dinsu ta nufa a natse ta shiga fuskarta d’auke da murmushi ta gaishe da abokan aikinta sannan ta cire jakarta ta ajiye akan table daidai saitin kujerarta sannan ahankali ta kai kwayar idanunta zuwa ga office din mr ATA ta hango kujerarsa empty da alamun bai zo ba tai shiru kawai tana cigaba da kallon office din kuma tana tunanin kalmomin da zatai amfanin dasu wajen gode masa domin ya cancaci tai masa godiya na mussaman amman gashi bai zo ba har yanzu babu mamaki yazo ya fita ne ? zuciyarta ta fad’a mata haka .”

ahankali ta tsuke qaramin bakinta kafin ahankali ta fito zuwa inda ta hango madam some zaune ta qaraso tana gaisheta “good morning ma ?” ”mornig maryama !”ta amsa mata tana dubanta da kulawa “amm ko mr ata yazo kuwa ?”no !bai zo ba amman dai zai zo yana kan hanya “okay maryama ta fad’a tare da juyawa ta koma office dinsu ta zauna zuciyarta na cigaba da tunaninsa haka fuskarta na cigaba da bayyana farincikinta.” Ko cikakken minti shabiyar batai da zama ba qamshin daddaden turarensa ya soma karasowa inda suke ta juyo zuwa bayanta nan take kwayar idanunta suka sauka akanshi yana taku ahankali cike da izza da isa yayinda duk taku d’aya idan yayi sai zuciyar maryama ya buga da qarfin gaske sakamakon qamshin turarensa dake kusantota .” ahankali ya shigo office dinsa na farko inda madam some take zaune hannunsa d’aya cikin aljihunsa ,yayinda jikinsa ke sanye da wani had’ad’den suit brown colour ,suma kanshi dana fuskarshi na kwance luf luf kamar ta yan india madam some na ganinsa ta mike tsaye da sauri cike da girmamawa tace “good morning sir ?.” ”morning ! ya amsa mata atakaice sannan ya nufi kofar shiga cikin office dinsa ya zauna yana juyi akan kujera .”

ahankali maryama ta mike ta nufi kofar office dinsa ta turo kofar ta shigo ta tsaya a gabansa tana gaishesa “good morning sir ?” a natse ya d’ago tsumammun idanunshi wad’an da suka wadatu da gashin ido dana gira ya zuba mata tare da yin shiru yana sauraronta itama shiru tai tana kallonsa tana wasa da yatsun hannunta ganin irin kallon da yake mata yasa babu shiri ta sunkuyar da kanta qasa ta cigaba da murza yatsun hannunta dake tsarke cikin juna ta sake d’agowa ahankali fuskarta d’auke da murmushi amman nan take murmushi ya d’auke a fuskarta sakamakon ganin fuskarsa a had’e tamkar yadda ya shigo ,kwatakwata fuskar nan babu alamun fara’a bare annuri akan fuskarsa ,dole tasa ta shanye dukkanin wani farinciki da take tattare dashi .”

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull