Mar'adams book 3 - Chapter 7
Mar'adams book 3 Chapter 7: Mar'adams book 3 Chapter 7. sai da gabansa yayi wani mummunar fad'uwa, zuciyarsa ke qoqarin motsawa amman ya dinga kwantar…
3,347 words
sai da gabansa yayi wani mummunar fad'uwa, zuciyarsa ke qoqarin motsawa amman ya dinga kwantar daita dan idan ya bari maganganunta sukai tasiri zai yi daya sani dan haka yayi shiru kawai ya cigaba da kallonta ba dan ya rasa abun yi ba she's the most beautiful girl I have ever seen in my life ya fad'a acikin zuciyarsa yayinda fuskar maryama ke cikin wani yanayi na fushi sai dai kuma kwayar idanunta na kanshi ta tsura masa idanunta kamar yadda yayi mata muryarta a sanyaye ta cigaba da motsa lip's dinta "kana tunanin dan zanyi aiki daku zan d'auki wannan wulakanci ne ?no I can't take it any more ta fad'a tare da zaro masa fararen idanunta ,da wani irin sauri ya tashi daga kan kujerarsa yana cewa" yana da matukar mahimanci kisan wani abu , yana da kyau kisan cewa kinyi mistake arayuwarki ba wai wulakanci bane kmr yadda kika d'auka, har sau biyu kina samu aiki damu kina rejecting wacece ke da zakiyi rejecting din aiki alokacin da kika só sannan ki so aiki alokacin da kika so "yayi mgnr yana kallon cikin kwayar idanunta ."
Ahankali ta kawar da kanta zuwa gefe tana hura hanci tace "to kuma saboda banyi joining aiki daku ba alokacin da kuka so sai ya zama matsala ? wani irin kallo yayi mata mai tattare da gargadi sannna yasa hannusa d'aya cikin aljihunsa yana kallonta yana jin wani azababben qaunarta na bin jinin jikinsa ahankali ya dinga sauke numfashi kamar wanda yayi gudun tsare sannan yaja tsaki ya kai hannu sumar kanshi ya shiga ya mutsawa yana ciza gefen lips dinsa da d'an karfi "ya Allah karka sa yarinyar nan ta bani matsala "yayi mgnr a kasan ransa still yana cigaba da kallonta ." kusan mintuna goma ya d'auka yana kallonta sannna ya koma ya zauna yana sauke numfashi ya sake d'aukar wani file ya cigaba dubawa sakamakon rashin abunyi "kawai kuce kun nemi na dawo ne saboda kunsan ina da baiwar fikira da zaku amfana dashi well shikenan kawai sai ku rubuta ku ajiye ya zama tarihi ga AGC compaing ,sun ga maryam hussein na da baiwar fikira sun dawo daita aiki byn sun koreta a ranar farko ."yana jinta amman yayi mata banza yayi tamkar bai ji abinda ta fad'a ba haka kuma bai d'ago ya kalleta ba ya cigaba da abinda yake yana satar kallonta ta kasan ido yana danne bugun zuciyarsa dan wani irin sabon yanayi ya dinga jin yana shigarsa."
yayinda maryama tayita fad'ar maganganu son ranta wannan karon kam a matukar zuciye ya ajiye file din da yake rike dashi ya sake tashi ya tsaya cak a gabanta yana sauke numfashi har suna iya shakar numfashi juna da jin bugun zuciyoyinsu "Keep your mouth shut ki kama kanki kisan irin maganar da zakiyi anan dan ba'a kawo min raini , ba'a sakani kuma ba'a hanani and no body question me okay ."ya fad'a a matukar tsawace yana sanya kwayar idanunshi cikin nata, shi aiki da mahimanci ake d'aukarsa kamar yadda shi mai kasuwanci yake d'aukar kasuwancinsa ,ban dawo dake dan kizo kina min haukan banza anan ba, na koreki ne saboda na nuna miki kuskurenki, sannna na dawo dake ne saboda tausayawa domin na fahimci kin shiga tashin hankali mai tsanani a wancan ranar dana koreki idan zaki iya aiki damu kiyi idan kuma bazaki ba "leave!ya nuna mata hanyar waje da d'an yatsansa yana fesar da huci mai zafi daga bakinsa yayinda zuciyarsa ke cike da matsanancin fargaba dan yasan kad'an da aikinta zata iya juyawa ta kama gabanta ."
adduar ya shiga yi domin neman taimakon Allah" ya Allah kada kasa zantuttukana suyi tasiri a zuciyarta Allah kasani ina matukar son yarinyar nan da d'aukacin rayuwata ta shiga zuciyata dayawa ta sace zuciyata,ya Allah kasa na shiga cikin rayuwarta kamar yadda ka shigo daita cikin rayuwata domin ta zamo abokiyar rayuwata ta har abada ina matukar qaunar wannan halitta taka ya Allah ka jarabeta da soyayyata tun kafin na kai ga furta mata soyayyarta dake raina domin na azabtu akanta ,na sha wahala akanta ,ya Allah ka tausaya min ."Ita kuwa maryama shiru tayi na second goma tana dubansa batare da tace masa komai ba har ya gama maganarsa sai dai maganarsa tasa zuciyarta tayi sanyi daga zafin datayi tare da tunani ,duk da ya jefeta da kalmar hauka amman kuma ta wani bangaren sai taji kamar ya fita gsky domin kuwa a wannan zamani aiki wahala yake, idan ba kana da hanyar samunsa ba ko wata baiwa ba sai dai ka mutu haka babu aiki amman da kwalinka da karatunka sai su zama banza bazasu maka amfani ba ."dan haka Ke maryama kiyi maza maza ki shiga taitayinki ki dawo cikin hankalinki karki yarda Kiyi kuskuren da zaki sake rasa aikin nan dan haka muryarta a sanyaye tace "shikenan zanyi aiki da amana da gasky kuma in sha allahu kamfaninku zatai alfahari da ... "da kyau go back to work ." yayi sauri katseta ta hanyar fad'ar hk batare daya kalleta ba duk da kallon nata yake da bukata dan baya gajiya da kallonta amman ya kasa sai ma boyayyayen ajiyar zuciya ya sauke dan maganrta ba qaramin dadi sukai masa ba ."
"Yanzu ko zan iya sanin da me zan fara ?meet sectary "ya fad'a a dake ,ta juya jikin a sanyaye har ta kama handle zata bud'e kofa ya tsaidaita ta hanyar cewa "ke .." ta tsaya cak batare data juyo ba sai dai qirjinta na wani irin bugawa da sauri sauri "idan zaki zo aiki gobe karki kuskure kizo min da wannan package din, kizo cikin tsari shigar aiki Kmr kowani ma'aikaci ."da sauri ta juyo tana masa kallon tsana zuciyarta cike da mamaki to mai ya samu kayanta ?ta jefawa kanta tambaya tana dubansa bai kalleta ba sai dai ta kasan idanunshi yake d'aukar kallonta tana kallonsa ya janyo system gabansa ya cigaba da aiki ta bud'e kofa ta mayar da karfi ji kake kiiiiii har sai daya d'ago yana duban kofar kai kawai ya girgiza tare da furta cray girl kawai ."maryama ta fice tana jan tsaki ranta duk babu dadi "a hankali ta dinga tunanin maganga nunsa gabadaya maganarsa babu dadi sai bugar da zuciya da saka mutun cikin tashin hankali ta sake jan tsaki tana maimaita kalmarsa ta karshe "idan zaki zo aiki gobe karki kuskure kizo min da wannan package din, kizo cikin tsari Kmr kowani ma'aikaci har ta shiga babban office din daaka tanada masu a ranar farko maganarsa bata bar zuciyarta da gangar jikknta sun huta ba ."
anan taga yusura tana ganinta ta qaraso da sauri ta rungume maryama tana cewa "kai naji dadi kawata da kika sake dawowa amman fa Kiyi hattara da mr ATA da mr sultan dan ba kai garesu ba kowa anan tsoronsu yake ji ,suna cikin mgn sultana ta shigo tana cewa "maryam hussein sannu da dawowa compaing mu " wani kallo mryma tayi mata na mamaki fuskarta da alamun tmby "yes ! Ok fa a she bakisani ba ko, to bari na fadi miki wannan kamfanin had'in gwiwar iyayenmu ne ni cousing sister din Mr ATA ce nan maryama ta fahimceta sai dai bata ce mata uhmm bare uhmm uhm .""Kinyi sa'a da kika dawo wannan kamfanin amman kuma Kisani nice nan sanadin dawowarki domin nice na nunawa ya Adam zanenki da kikayi wanda tashin hankali an koreki yasa kika tafi kika barshi "shiru maryama tayi kafin a hankali tace "na gode excuse"ta fad'a sannan ta ra'ba ta gefenta ta wuce ." Gabdaya suka samu guri suka zauna akan makeken table din dake zagaye da office din ."maryama ta bud'e jakar kayan aikinta ta d'auko abun aikinta hanakalinta kwance ta fara gudanar da aikinta "wannna duk wahalar banza kikeyi domin duk kwarewarki bashi zai sa ki burge ya adam ba tana gama fadar haka fita daga office din maryama tabi bayanta da kallon mamaki ."
Aunty hasana ta qaraso ta mikawa hjy granny kofin shayi ta amsa tare da cewa "na gode ta kai cup bakinta sai dai da sauri ta kirata tana cewa " hasana bai kamata ina shan sugar haka ba amman kalli yadda kika zabga min sugar cikin tea ai ko baa fad'a miki ba Kinsan bai dace mai shekaruna haka ta sha sugar ba duk maganar da hjy granny take Aunty hasana bata jinta saboda hankalinta na kan kallon tv "ke hasana bada ke nake magana bane ta juyo a dan firgice tana cewa "na'am hjy kina magana ne ?ya zaki saka min sugar haka acikn shayi ?abun kunya kawai ace kamarki ace shayi ma sai anci gyaranki ba kya ganin yadda maryama take komai nata tana kokarin kula dani fiyye dake sam bata kuskure wajen abinda take min amman ke babu abinda kika iya sai aikin zagin ya'yan mutane da saka ido bazaki tsaya Kiyi koyi da mutanen kirki ba." zaginta tayi sosai ai kuwa haushi ya kamata "hjy ai daman ni na dade dasanin kin tsaneni bakya qaunata komai zaki fad'a ki fad'a ba damuwata bace" idan dai zaki canza ki canza umma ta shigo tana tmbyr lafiya hjy nake jin fad'anki "ina fa Lfy wannan yarinya ce anyi mgn zata fadawa mutane babu dadi me kike son nayi miki hjy ?" bansan me nayi mata ba komai nayi mata sai ta kushe to ki daina sakani aikin ki dinga saka wadan da kike so aranki ta fad'a hawaye na cika idanunta."
umma ta dafata tana cewa "haba hassana ki daina fadawa mahaifiyata magana haka sam bazan ji dadi ba bugu da qari Ke ma uwa ce idan yaranki suka miki bazaki ji dadi ba "to ni yanzu me nayi dag suga yayi yawa a tea sai ta hau min fad'a karbi tea ki sha kiji wallahi ba wani suga na saka ba "ki barta kawai itama ai ta haifa yaya idan ma bata haifa ba akwai na kasa daita zasu mata duk abinda tai min sam bata son gsky tunda take min rashin tarbiya kinji na ta'ba magana akai idan ba yau ba ?dan allah kiyi hakuri hajiya bazata sake ba suna cikin haka maryama ta shigo cike da murna ta tsaya kusa da umma tana cewa "umma ki tayani murna na fara aiki ." umma tai murmushi cike da farinciki Allah yasa kin fara kenan "Ameen ya allah na gode sosai babu wata matsala dai ko ?babu matsalar komai umma duk da dai mr ata ya dan so yayi min hauka amman nayi hakuri .zanyi aiki dashi ne kawai saboda bazan iya bari wani abu ya samu komai naki ba faduwar ki faduwar gabadayanmu ne ."shiru umma tayi kafin tasa hannunta ta kamo maryama karki ce komai umma duk abinda nasan zakiyi farinciki zanyi shi koda kuwa raina ne zan iya mallaka miki shi umma ta lumshe mata ido tana cewa " na gode sosai maryam allah yasa albarka hatta hjy ma taji dadi suka saka a tsakiyarsu suna saka mata albarka ."
*******
Baba qarami yana zaune a cikin wani qaramin office dake cikin falon hjy zulai an tanadi office din ne saboda marigayi alhaji tariq alokacin da yake raye nan ne wurin zamansa ATA ya sauko daga samansa sanye cikin wasu hadaddun kananan kaya marasa nauyi kallo daya yayi masa ya d'auke kansa zai nufi kofar fita yaji sautin muryarsa "Adam zo nan ya tsaya Jim da kamar bazai je din ba sai kuma ya yi wani tunani ya juyo a hankali ya shiga har inda yake zaune fuskarsa a hade kamar ko yaushe "ka zauna saboda me kenan zan zauna? ya tamvayesa atakaice yana hura hanci baba qarami yayi shiru yana dubansa "kana da magana ne ?zan kiraka ne idan bani da abinda zance ? ya fad'a a zafafe shiru ata yayi ."Ka natsu ka shiga hankalinka ba wai ana jin tsoronka bane me ake ciki akan maganar danayi maka akan sultana idan kaki auren hindu ka turata magarkama sultana fa uwarta na bukatar jin raayinka?babu wani abinda ake ciki dan bazan yi abinda Zanzo daga baya ina danasani ba sultuna is not my test ina da raayina haka ma hindu "da alamun zaka dawo da zabin mahaifiyarka ya zama shine raayinka .? a fusace yace "yes !"yana kallonsa "ka koyi respect Adam sam baka da respect bakasan yadda ake magana da babba ba zaka iya fad'awa mahaifinka haka ? Ko da yake wannan uwar..." "enough baba qarami ."! ya fada a tsawace karka sako sweetheart cikin maganarka aure ne ni nake da ikon aure and sultana she's not my tast abawa wani kawai "bari na fad'a maka wani abu komai zakayi wannan karon sai dai kayi amman sai ka auri wata daga cikin family's din nan bare kuma tunda sultana tace tana sonka an gama maga.." kafin ya qarasa mgnrsa tunin ata ya juya ya barshi "kai dawo nan !"ata ya sake dawowa hannuwansa duka cikin aljihu" "wai meye haka ne baba ?nifa nasan abinda zai yi daidai da rayuwata dan allah ka barni na huta bana bukatar wani auren zumunci arayuwata a yanzu shin lallai ne sai ni zaku bawa ya'yanku ."?
Mmn sudais💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 7
Fita ata yayi daga gidan gabad’aya zuwa gidan mb sai dai har yaje gidan abinda baba qaramin yayi masa nata damunsa acikin rai , mb bai fahimci yana cikin ‘bacin rai ba dan yasan halinsa kullum cikin had’e rai da kamewa yake shiyasa ma ya fara da yi masa maganar maryam “adamcy baka ga ya kamata ka waiwayi yarinyar nan maryam da cikin jikinta ba ?shiru ata yayi tare da sake had’e fuska sosai , mb ya dawo kusa dashi tare da tsura masa ido yana dubansa “mai yasa kana girma amman har yanzu baka da wayo ?” yanzu d’an ko ‘yar da zaka fara samu a duniya zaka wulakanta?kallonsa kawai ata yake ko kifta ido ba yayi sai ma wani kalar kallon banza da yake masa .ahankali mb ya sauke numfashi “ka zauna ka natsu adamcy duk ‘yanuwanka sun kawo ido sun zuba maka saboda gudun fushinka “me zanyi mb ?”yayi maganar a zafafe yana jan tsaki “nifa yarinyar nan gabad’aya na manta daita arayuwata idan har ba maganrta akayi ba sam sam bana tunata“.
“ba ace ka dinga tunawa daita ba tunda ansan baka sonta ,abinda take d’auke dashi ake son ka waiwaya kasani ko iya rabonka kenan a duniya ?take ata yaji wani sabon damuwa ya masa mummunar kamu . sosai yaji zuciyarsa na bugawa da sauri sauri “Ka natsu sosai ka duba maganata “.cike da jin haushi ya fesar da iskar bakinsa mai zafi yace “ka daina min mugun baki mana “ba mugun baki bane adamcy misali nayi maka domin kasan kuskure kake yi “to bana son wannan musalin please.”ya fad’a cikin tsnanin fushi “kayi hakuri adamcy ba baki bane bamusan menene a rubuce a cikin kundin littafinmu ba dan haka kayi wani abu ko sau d’aya ne kaje ka ganta “I can’t !”ya fad’a a zafafe .”zaro ido mb yayi “what do you mean adamcy ?kana da hankali kuwa? “ I don’t know ko ina dashi ko bani dashi but I don’t fell to go. “ what’s wrong with you?are you trying to say that you are not going to see her and your baby ?”exactly !”
“Please adamcy don’t do that kaje saboda babynka ba saboda ita ba “I don’t fell like zanje “okay ka kirata ko ta waya ne kaji lafiyarta data baby “dan girman allah mb banason damuwa bana jin zanje koina ,ko nace tayiwa kanta ciki ne ?ko lokacin daakayi cikin nasani bare yanzu kazo ka dameni da banza banzar magana ?ya hau mb da fad’a yana huci yana gama fad’ar haka ya d’aura kansa akan hannun kujerar da yake zaune sake matsowa kusa dashi mb yayi zai masa magan yace “enough !ya fad’a a tsawace tare da d’aga masa hannu alamun ya kyalesa “mb banason sake jin komai akan yarinyar nan .yarinyar data cuceni ta cuci rayuwata bazan ta’ba yafe mata ba tayi adduar ta rigani mutuwa domin idan nine na rigata mutuwa na barta da nauyi domin bazan yafe abinda tayi min ba .”
“zaro ido mb ya sake yi yana cewa”haba haba !!adamcy mai yayi zafi haka ?meye acikin abinda tayi bayan hakinta ne “shine akace tayi min fyade ?”dan allah ka daina fad’ar haka “na gaji mb abar maganar nan hk dan danasan dashi zaka tareni wallahi da bazan zo ba haka mutun yazo da damuwa ka sake qara masa wata damuwa ya fad’a tare da point dinsa da hannunsa “kyalesa mb yayi ba dan yaso ba sai dan sanin halinsa da yayi mutun da idan ya kafe akan abu to zai yi wuya a tankwarasa.” a natse ya mike tsaye yana jan tsaki ya fito zuwa haraban gidan inda motocinsa da masu tsaronsa ke zaman jiran fitowarsa ahankali mb ke take masa baya har suka qaraso inda motar da zai shiga yake aka bud’e masa “adamcy karkace na dameka amamn dan Allah kasamu lokaci ka duba maganata ,ka mika lamarinka zuwa ga allah ka tsarkake zuciyarka dominsa tun kafin haki ya kamaka ka tausayawa yarinyar nan wallahi ina tausayawa yanayin da take ciki ga tarin damuwa ga soyayyarka ga cikin jikinta.”
ata bai ce masa uffan ba sai ma d’aga tsumammun idanunshi yayi ya sauke aka wrist watch din dake d’aure a hannunsa ganin lokaci ya tafi yasashi jan tsaki sannan ya shiga bayan mota ya zauna aka jashi inda zuciyarsa ke wani irin bugawa da qarfin gaske kamar kar mb yayi masa maganarta haka nan kuma sai yaji abun na damunsa har ya dawo gida yana jin maganr na yawo cikin kwakwaluwarsa mai yasa ma naje wajensa?yayiwa kanshi tamabyar yana jan tsaki .” yana hawa sama bedroom dinshi ya nufa ya tsaya a bakin window dakinsa yayi shiru yana tunanin maganar mb gabadaya sai yaji duniya ta tsaya masa waje daya cak bai taba sani dan anyi masa maganar cikin jikinta abun zai tsaya masa arai har ya damesa ba ,wani irin tashin hankalin ya shiga qirjinsa na wani irin bugu “bai sonta amman abinda tayi masa yafi rashin son da baya mata ciwo "ya dauka zafi da ciwon rashin so da baya mata zai tsaya ne iya kanta kawai ashe ba iya kanta kadai zai tsaya ba har da dan cikinta “nonsense girl kawai yadda kikayi cikinki haka zaki raini abunki ki haifa I don’t care .”
Yana tsaye yana tunani mami ta turo kofar bedroom dinsa ta shigo hannunta rike da cup din shayi da d’an qaramin tray yayinda idanunta ke kansa bai san ta shigo ba sakamakon zurfin da yayi cikin tunani “ta qarasa ta ajiye tray din hannunta akan table ta sake dawowa wajensa ta tsaya tana kiran sunansa “adamcy nah ! firgigib ya dawo haiyacinsa yana sauke wani zazzafan numfashi ya tsura mata ido itama idanunta yana kanshi tana nazarinsa “lafiya tunanin me kakeyi haka ?numfashi ya sauke da karfi yana tura hannuwansa duka cikin aljihunsa sannan ya girgiza mata kai yana yamutsa fuska alamun babu komai “okay ga shayi nan na kawo maka ka dauka ka sha “ahankali yaja qafafunsa ya isa inda ta ajiye tray ya d’auki cup din ya rike yana dubanta “sweetheart ina kikaje ne tun safe banji motsinki ba kuma na kira wayoyinki duk suna shiga bakya d’auka ?”yayi maganar kwayar idanunshi na kanta “ naje hospital”da sauri ya motso kuda daita yana kallonta a d’an tsorace “lafiya ina Ke miki ciwo ?mai yasa kike je ke kad’ai baki tasheni ba ?yayi mata tmbyr ajere cike da shiga tashin hankali “lafiya ta lau adamcy naje wajen auta ne ta sauka lafiya ta samu d’a namiji “wani naunayen ajiyar zuciya ya sauke “na tsaya ne sai da’ aka gyara bby da mamansa sannna na dawo .”