Kenza eBookz

Nayi nadama book 1 complete - Chapter 3

Nayi nadama book 1 complete - Chapter 3

Nayi nadama book 1 complete Chapter 3: Nayi nadama book 1 complete Chapter 3. ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Da garfi ta saki qara gami da fizge hannunta dan azabar da ya…

3,262 words

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Da garfi ta saki qara gami da fizge hannunta dan azabar da ya ratsata jini kuma a take ya rinqa tsirtowa abinka da farar fata gata da laushi kamar auduga kuka take sosai tana yarfa hannun tana bubbuga qafafunta a qasa Ahmad kam tuni ya kamo ta ya riqo hannu yana matse kan dan yatsar da niyar tsaida jinin amman abin yaqi Adam ya jawo handkerchief en Yusuf dake kan cinyarsa da sauri ya yagi gefen handk en ya kamo hannu ya daure kan dan yatsar Amman ina jinin zuba yake Abubakar kam da Ahmad tamkar a jikinsu jinin ke zuba kuka take sosai jin kukan yasa Ummi da Nenne suka shigo a tare da sauri sukayi gunta tana lafe jikin Ahmad cikin mmki Nenne tace kai Ahmad meya yankata haka shiru yayi yana girgiza kai yana damqe da hannun ba abinda yake furtawa sai sorry Aysha cikin jin takaici da tausayinta a hatsele Ummi ta buga musu tsawa kai ana muku mgn duk kunyi shiru ke Aysha waya miki muguntarnan dan ita tuni tasan mai aikata aikin dan duk suna zagaye da ita suna ta tausarta shiko oga ko a jikinshi ko inda suke bai kai idonsaba kamar baya gun kanshi a sunkuye yana ta danne danne a phone enshi ga cup en coffee a gabanshi yana dan Sha Ummi ta sake daka musu tsawa tace wai kuna jinmu kunyi shiru Rabi,u ya dan kalleshi yaga a sunkuye yake ya maida dubanshi gun su Ummi gamida gyaran murya ya dan dunqule hannushi ya miqar da dan babban yatsarshi ya nuna Yusuf in gamida dan musu alama shine yana gedawa Ummi kai da dan furta haaa Nenne tace toh Koma waye yanzu dai kai Yusuf zoka San yadda zakayi ka tsaida jinin kanshi a qasa yace Nenne ni kuma ? Ummi ta jinjina kai tace a a ba kaiba wani mugun da ban da ya yanketa wlh ka kiyayeni ka fita harka yarinyar nan dan banga me ta tsare maka ba tunda kai zuciyar dutse Allah ya maka baka da qaunar yar uwarka bare tausayi kullum sai mugunta fada sosai takeyi Shiru yayi zuciyarshi najin zafin yarinyar da tsananta a ranshi shi kullum a kanta sai ranshi ya baci cikin jin takaici ya shiga dakin innayi ya fito rike da kwalbar turare da qarfi ya fizqo hannu ya matse ya danna bakin kwalbar fesss ya fesa cikin yankan Da qarfi ta saki qara dan jin yadda azabar zafin ke ratsa jikinta har cikin zuciyarta sosai ta qanqame ya Abubakar tana wayyo Ummi ya qasheni ya Ahmad zafi nakeji gaba daya hannu sai bari yake Ahmad ya zagaya ya kamo hannun yana huramata iskar bakinshi mai sanyi yana dan shafa kanta Abubakar kuma yana dan buga bayanta a haka dai jinnin kam ya tsaya sai ajiyar zuciya take ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

Gaba daya porlon sunyi shiru suna sauraron Bappa Yaya A hankali yayi gyaran murya ya dan jinjina kanshi irin Na manyan mutane ya kalli yayan nashi daya bayan daya cikin muryar gsky da gsky ya kalli baba bello yace bello mgnarmu akan yarannan lokaci yayi da ya kamata ace duk mai shirin aure ai masa Sam banji dadin ganinsu a haka kun xuba musu ido suna abinda sukaga dama ya dan yi shiru sannan ya kalli Aliyu yace Aliyu inason mako mai zuwa Umar yazo da qanwarku Aysha dan insha Allah zamu San matakin da zamu dauka akan abin cikin girmamawa yace to Bappa insha Allah zan kirashi Juyawa yayi gunsu Ahmad cikin yanayin tabbaya yace kai Adamu kai ka fidda matar aureko ? Ehh ya bashi amsa yana mai nuna Amira yana ko dai baza ka ban ita bane a a Na isa nine mai badasu oho nasani ko zaka gwada ikonka.. Dudabe ya kira Yusuf ya dago cikin jin haushi yace meye kuma ? Ehh akwai batun aure fatan ka shirya dan bazaka bar qasannanba saida matar aurenka uhum kawai yace dan yasan tsohonnan da iya kalen fitina shi kuma Bappa Yaya cewa yake wlh kunji kunya kune manya kan Abubakar Amman gashi dayin aurensa shekata 2 kenan da da saurin rabo da har an samu qaruwa Ahmad ya danyi murmushi yace toh ai shikenan muma zamuyi yanzu kam cikin kallon Ahmad din yace shiyasa Na yarda da kai Ahmad kai mutum ne sosai Na tabbata bazamu samu matsala da kaiba shisa matarka ta musammance Adam ya dan kalleshi yace mukuma ba mutane bane ko eh ai Ku kam gwara ma kai akan sarkin fadannan kam ya nuna Yusuf haka dai yaitawa zuriyarsa addu,a da fatan Allah ya maidasu lfy har bakin gate ya rekasu ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

Tun daga bakin qofa yakejiyo hayaniyarsu duk sun cika gidan da sowa a hankali yayi slm ya shiga pictures suke ta dauka dasu Ahmad da Adam Abubakar kam duk ya gama biye musu sosai suke ta dauka harda kaka da ta zo yanxu Usman shike daukarsu harda nunamusu yadda zasuyi cikin mmki yake klnon yadda yake tawani lonqwosa kamar mace Aysha fake tsaye tsakanin Ahmad da Abbakar duk sun dan sunkuyo Suna kallonta suna murmusawa itako ta dan dago kanta tayi kalan shogoba da sakalci Ahmad yasa hannushi ya dan tallabo fuskarta good Usman yace kunyi kyau ya daukesu ahankali ya karisa tsakiyar palon duk da baya ta bashi qamshi turarenshi ya sheda mata ya shigo dan haka ba tare da sun juyaba sukayi cikin wani parlon da sauri Kaka ta kalleshi cikin tsokana tace toh fa watsa taro duk ka watsasu ya dayamutsa fuska lokacin da yauzauna gefenta Ahmad da Adam suka sashi tsakiya Usman ya kallesu sunyi ras dasu gwanin Sha,awa ya dan kalli Yusuf a marairaice yace plss Hamma Yusuf bari Na daukeku daya wlh kunyi kyau harara ya watsa masa kaka tace Abubakar maza karbi ka daukesu ai shi photo tarihine wataran zaka tuna da dan uwanka Camera ya karba ya rinqa daukarsu duk motsin da sukayi sosai sukayi kyau kamarsu ta fito Sak da Sak suyi tamkar taurari kaka ta kallesu tace toh ko kufa ya dan yamutsa fuska yace kai nifa banson fitina da surutu ke Sam bakya iya shiru eh din nayi surutun bakinka ko nawa haka dai suka wini hira su Nenne Na musu dry Sam shi Yusuf da kaka in sun hadu sai fada

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Yau asabar tun da safe suke ta shirin tafiya mambila su Goggo Aysha kam da su hydar da Maryam da maigidanta baba umar tun jiya jumma'a suka wuce mambila

By garkuwan Fulani [4/9, 1:48 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 MI,WASMITI.....page 7⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Gaba dayansu kusan a porlon suka wuni sunata hirar zumunci sukuma su bappa Yaya da 'yayashi da surkinshi suna can parlonshi Na mu samman suna ta tattauna mgnarsu ta mu samman Tafe suke bayan sun fito masallaci yin sallan la.asar har sun danyi cikin gida Adam ya kallesu cikin raha yace biyaye muje cikin rafi mana mu dan Duba yanayin wajan Ahmad ya dan kalli Yusuf yce biyaye zamuje ? Kai ya dan gyada mai alamar bazashiba wlh sai kaje mutum kamar mai iska in kai kadaine ai kullum sai kaje amman dayake kaga su Rabi,u ma zasu sai ka wani ce bazaka ba cewar Adam kenan usman ya dan kallisu cikin salonsa Na dan rigima yace toh fili da fadi ai ba saimun zo gunkuba.. Haka dai suka jashi suka tfi ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Rafine babba mai dubbin sirrai da qworamai ga duhuwa da qamshin furanni ga wani sanyi mai sanyaya zuciyar dan Adam ga yanayin shauqi da tsuma zuqatan masoya wurine mai dubbin tarihi tun na iyaye da kakanni suna kiran wurin da funa rafi

Suna shiga duk suka watse cikin rafin kowa da abinda yake buqata Yusuf mutum ne mai son yananin sanyi da qamshi wurin Na tsuma zuciyarsa gaban wani qwarama mai ruwan garai garai qarqashin sirran bishiyiyin ayaba ga qatuwar bishiyar bangoro da wata bishiyar kashu da jijiyoyintama cikin tabkin suke ninqaya ga kukan tsuntsaye masu kama da sautin sarewa a hankali ya taka ya qarisa kan daya daga cikin kuyerun da aka jera a wurin masu dan tsawo Wanda sunfi kama Dana kwanciya 🌳 A hankili ya kwanta tare da yin wata sassanyar ajiyar zuciya gamida lumshe idanshi duk Wanda ya ganshi yasan yana cikin nishadi Cikin yanayin tsokana Adam ya dan yafito Ahmad ya nunashi da ido yace shi dai har abada haka yake son kasan cewa ba kowa kusa dashi ya lumshe ido kome yake gani ranine.? sai Allah Ahmad ya bashi amsa yana dan murmusawa cikin shauqi ya fara zagaya wurin yana dan ciren yayan itatuwan cikin zuciyarshi Aysha ce ke yawo phone📱enshi ya zaro gami da kiranta bugu daya ta daga Cikin muryar tsantsar qaunar Ya Ahmad dinta take mgn jin muryarta da shauqi ya jingina jikin bishiyar 🌳 hadi da lumshe ido cikin sanyin murya yace Aysha kina ina ? . Ta dan qara magalewa jikin innayi ta danyi ajiyar zuciya tace Ya Ahmad gani a kan gadon innayi Cikin sanyi ya fesa munfashi yace toh kizo lambu gani ina jiranki Toh tace gamida da cewa ya Ahmad ta wanne gefen kake ? Bakin gwaramannan ya bata amsa Aiko cikin zumudi ta figi mayafinta ko Amira da Maryam bata nemaba ta fita da Sauri sauri ta nufi rafin Ahmad ya nufi gun kenan yaci karo da hydar da sauri ya miqa mai phone enshi yana ya Ahmad Abba Na nemanka tun dazu yake kiranka layinka bai Shiga shine yace Na kawo ma Da sauri ya kara phone en a kunne 📱👂🏻cikin biyeyya ya ke mgn toh Abba ganinan zuwa ehh yanzu zanzo cikin sauri ya katse kiran ya miqawa hydar phone en ya nufi gun su Yusuf fuskarsa dauke da murmushi yace biyaye ni Abba Na kirana ZAmu tf bakin kogi gun dabbabi 🐄🐪 da sauri Adam ya miqe yana muje Nima xani har sundayi nisa Ahmad ya dawo ya dan kalli Yusuf yace biyaye kai bazaka jebane ? Kai ya gyada mai alamar bazashi ba Adam yace kai da Allah zo mu tf ai kasanshi ba zuwa zaiyiba ya fada yana hararanshi shi ko sarkin hali ko idanshi bai budeba da sauri suka tf abinsu ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Tunda ta shigo cikin rafin sanyin iskar da qamshin furannin suke ratsata ta lumshe idanta hadi da ware hannayenta tana tfy cikin rausaya tana shaqar qamshi kai tsaye gun da ya Ahmad dinta ya gayamata ta nufa tana dan ratsewa shuke shuken har ta qarisa wajen duk idanta a rufe cikin nitsuwa take dan tsallaka kujerun a nufinta zataje bakin ruwan ta zauna aiko a hankali qafarta ta dan zame zata antaya cikin ruwan da sauri ta ja qafar baya tana shirin juyowa taji ta afka kan kujerun Yusuf dake kwance a rigingine idanshi a rufe ba abinda yaji sai fadawar mutum a kan faffadan girjinshi cikin mmk da sauri ya ware idanshi gami da dan yunqurawa zai tashi Ita kam tun da ta fadi cikin razana ta yunqura sai tajita jikin mutum da sauri cikin fara.a tace ya Ahmad yau kam Dana karye ta dan saki murmushi gami da dan manna fuskarta kan girjinshi ta zagaya hannuta ta bayanshi duk abinnan da take idanta a rude Shiko cikin takaici da jin haushinta ya ware manyan idanunshi kan fuskarta cikin fushi da takaici ya danna mata tsawa keeee Baki da hankali ko jin muryar dodonta cikin tsoro ta bude idanta dan tsawace mai rikita mutum ya sakarmata har sai da cikin rafin ya dauki sautishin da sauri ta yunqura dan ta tashi bata gama firgicin tsawarba taji wani irin axabebben mari daya yarfa mata cikin jin zafi tasaki qara aiko ya miqe cikin zafin nama ya rinqa zuba mata Maruka tun tana tsaye har ta fadi qasa nanko yasa qafarsa ya rinqa bol da ita tana kuka tana wayyo Hamma Yusuf dan Allah kayi haqri wlh ban saniba ne plss Na tuba su hydar dake can gefen bishiyoyin goiba da sauri suka nufi gun amman suna zuwa ganin Hamma Yusuf ne ke tabkarta yasa gaba daya suka tsaya hydar ya kallesu cikn jin takaicin Yusuf yace wai me ya tsaiya daku ? Rabi,u yace tab wazai qarisa wannan mugun yahada dashi shi dama in dai baiyi dukaba baya jin dadi cikin jin tausayin ta ya Shiga tsakaninsu ya sunkuya ya dagota ya dan juyo badan ya soba sai dan kar Yusuf yace ya rainashi yace dan Allah kayi haquri Hamma Yusuf Cikin fushi da murtuqe fuska yace maza Ku bacemin da ganan aiko da sauri ya jata suka tf

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Abinka da farar fata tuni fuskarta ta kumbura tayi jawur ga wani azabebben zazzabi daya rufeta tun kafinnsu isa gida jikinta sai bari yake tab aiko Ummi kam ta hatsala fada take tamkar zata aro baki har zuwa bayan maggariba fada take sosai Nenne sai bata haquri take amma ina fada take har su Abba da Ahmad suka shigo gida yayinda bba bello da Yusuf ke binsu a baya .

Yan uwana musulmai ina barar addu,arku ga dan uwana ya Abubakar Wanda Allah ya mai rasuwa ya Allah ya jiqanshi da rahama 👏🏻😭😭😭

By garkuwan Fulani 090,,,,,, [4/9, 1:48 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 MI,WASMITI.....page 9⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 🙏🏻Bayan ya bude taron da addu,a ya dan yi gyaran murya ya jinjina kanshi jikin kushin ya dan kalli illahirin Family enshi din haqiqa shi da kanshi yanajin nauyin furicin da zaiyi zuciyarshi Na samun rauni idan ya kalli idanu jikokin nashi yana samun fargaba sosai yanajin tsoron kar yau ta kasance ranar nadama ko ranar baqin ciki ko ranar daukewar farin cikin wani sashi daga cikin sashikan zuriyar tasa jikin jinjina kai ya dan dago kanshi Ya dan zuba musu ido gaba daya a hankali ya danyi gyaran murya ya bude baki cikin sanyin lafazi da taushin baki yace

Bello da kai da sauran qannan ka da matanku da qanwarku da maigidanta da dan uwana da iyayenku mata Yau gashi mu dukkanmu Allah ya kawomu wannan rana da muke fatan isar da wani alqawari da muka dauka idan Allah ya nufa yai shiru ya dan zuba musu ido sukuma yara daga kan Adam har xuwa kan Aysha ido suka zuba musu cikin yanayi tabbayar wanne alqawarine wannan Ahmad tun wayewar garin bugun zuciyarsa ta zarce tunaninshi sai yanxu yaji abin Na sauqa shiko Adam kallon kakan nasu yayi cikin dan zaquwa yace gsky mu bama son Jan rai kana mgn kana jinkirtawa da sauri baba Umar ya daga mai hannu alamar ba batun wasa ganin haka yasa gaba daya sukayi shiru sai yusuf shi dama baiyi mgn ba asalima kanshi a sunkuye yake Aysha da ke dan manne jikin innayi ta maida kanta tai lamo yayinda Amira ke gefen Adam maryam kuma Na jikin Nenne duk suka maida hankalinsu kan Bappa yayan a hankali yaci gaba da cewa Ahmad Bai Amsaba sai ido daya zuba mai bugun zuciyarsa Na tsananta 💗Ahmad ya kuma kiransa da gyar ya iya amsawa Na,am jin yadda sautin muryar Ahmad din ta fito yasa Yusuf da Aysha dagowa a tare suna klonshi sai yanxu su duka sukaji wani baqon yanayi ya darsu kan zuqatansu sautin muryar kakan Nasu ya katse musu Al,amarin yana mai cewa Ahmad A kullum duk zuriyarmu tana alfahari da kai haqiqa Na tabbata kai mutum ne mai cikir haiba da nazartan hilin da ake ciki Ahmad ina alfahari da kai a zuriya ta Na tabbata kai dayane mai fahimtar kalemen mutum duk kaushinsu da dacinsu Tun kana yaro baka taba kaucewa Umurnin iyayenka ba ko yaushe kai mai biyeyyane a garemu Baki daya shiru ya dan kumayi yayinda duk parlon sukayi sit Yanayin Ahmad kuma yafi kama da wanda tsoro ya cika zuciyarsa sukuma iyayensu gaba daya sada kansu qasa sukayi Cikin qarfin hali yaci gaba da cewa Ahmad a yau Alfarmanka nake nema kuma da yafiyarka dani da iyayenku baki daya Ahmad muna masu tausar zuciyarka muna kuma buqatar haquri daga gareka Cikin rashin fahimta yace bappa yaya ni kuma muryarsa har rawa take yaci gaba da cewa ya isa tunda tun forko kace iyayena toh mgna ta kare ba wani neman alfarma tsakaninmu a hankili ya daga kanshi ya kalli qanin mahaifinshi yace Abba ni dai ni din Abba me kuke buqata a gareni da har kuke ban haquri ni Ahmad danku meye rage da baku minba a duniyarnan 🌍 ya maida dubanshi gun mahaifinshi da mahaifi yarshi yace baba da Nenne kun gama min komai Nenne am Na Dade ina Neman abin da kike buqata in miki a duniyar nan da kema zakiji bakiyi asarar yaranki da suka rasuba cikin 'yaya 12 da kika aifa sai mu 3 Allah ya bar miki Nenne ni Ahmad ki gayamin meye buqatarku yaku iyayena ya qarishe mgnar Yana mai zubda qwallah😭 ya dan kalli kakanshi yace bappa Yaya gayamin meye buqatarku ko zanji sauqin abinda ka dauramin haqiqa zuciyata ta soku 💘in dai bazaku sani Abu kai tsayeba sai kunce kuna Neman alfarma Ahankili Abba ya daura hannushi kan tsakiyar kanshi cikin wata iriyar murya yace Ahmad Allah yamaka albarka ubangiji ya jibanci Al,amuranka Cikin muryar kuka nenne tace Amin yusuf kam tuni zuciyarsa ta fara tafasa ganin hawayen biyayenshi Aysha ko kuka takeyi sosai innayi Na tausarta Gyaran murya yayi yace Ahmad alfarman da muke nema a gareka batun Aurenka da Aysha sai kuna ya sunkuyar da kanshi ganin yadda gaba dayansu jikokin nasa suka zuba mai ido Haqiqa yusuf yasan wannan zaman kalen fitinane shiyasa ya dago kai fuska a murtuqe yace dan Allah kai mgn kana gasamin zuciya da maganganunka da suke Sa dan uwana zubda qwallah

Ayijar zuciya ya danyi Yace Ahmad batun aurenka da Aysha babushi dan ita Aysha tana da mijin 😳😳😳 Cikin razana da fargaba da bugawar zuciya ya katse shi da meyasa ? Waye mijin tadin ? A ina yake ? Hannunshi Na dafe da qirjinshi yake wadannan tabbayoyin a take sukar zuciyarsa ta tsananta wani nauyi ya danni maqoshinsa Zufa ta fara ketomai tsoro mai tsanani ya rufeshi har cikin hanjinshi yake jin sanyi Na ratsashi Itako Aysha tunda taja wani numfashi sai ta zama mutum mutumi a zaune sai barin da jikinta keyi cikin mmk abin yusuf yace ai wannan mgnar hogice wayeshi da za,a hana dan uwana farin cikinshi akan wani can banxa tun tana qarama yake wahala da ita wlh ni dinnan a matsayina Na yayanta ni zan aurar da ita ga dan uwana Adam ya dan kalli Bappa Yaya a fakaice yace cikin yanayin kaji tsohonnan da zance shirme ai wanan ba huruminka bane sai ka bari iayenmu suyi ikonsu a kanmu Allah sarki Ahmad duk sun rikice sabida bidar farin cikinsa dama Ku hausawa kunce nagari Na kowa Su Usman ma duk sunyi zurui Abdul mai saurin kuka shikam da Sadiq kuka suke sosai Rabi,u kuma sai kada kanshi yake a hankali yace (nayeku Na ko jibare ) tsufa ko rikicewa ne Baba bello ne ya dan rinqa musu fada cikin qarfin hali yana sabida me zaku samu a gaba kuna kuka ko ance muku mutuwa akayi da gyar dai suka dan tsaqaita sai yanxu Bappa Yaya yaci gaba yace Ahmad tabbayoyinka harsunmin yawa duk da dai zan amsa ma ka su yanxu wasu kuma sai wataran zakuji amsar sai batun aurenka da Aysha babu shi domin kuwa ita tana da miji Amman duk da haka ba hanaka sure za,ayiba tunda an dakatar dakai kan Aysha haka nan kuma an mayarma ka da yar uwarka Maryam a madadinta Sai yaxu Usman yace toh wai waye ne wannan da za,abashi Aysha a hana ya Ahmad ita ? Yusuf ne shine mijinta shine Abokin rayuwarta shine tsohon alqawarin zuriyar nan ya basu amsa

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull