Kenza eBookz

Noor al hayat complete by khaleesat - Chapter 36

Noor al hayat complete by khaleesat - Chapter 36

Noor al hayat complete by khaleesat Chapter 36: Noor al hayat complete by khaleesat Chapter 36. Direct office din Dr Abdul khaleel ya wuce, ya samesa xaune…

4,677 words

Direct office din Dr Abdul khaleel ya wuce, ya samesa xaune yana aiki, ganin khaleel ya bar abinda yake yi yace "He is improving ko Dr" khaleel bai tanka sa ba isa gabansa ya dafa table yana kallonsa bbu yabo bbu fallasa yace "Dr Aliyu.... Where is his home?" Dr Abdul yace "Aliyu? Ba yana office ba?" Khaleel yace "Baya nan" da mamaki Abdul yace "Hope babu matsala dai?" A takaice Khaleel yace "Babu, ina gidansu yake" Abdul yace "Toh, he is not the type that mingle gaskiya I dont knw his home" juyawa Khaleel yyi ya fice office din, direct parking space ya nufa ya hau motarsa ya wuce gidan Farouq. Umma ta dinga kwantar ma khadijah hankali duk da taki saurarenta, daga karshe Umma ta fita ta biya bill dinsu don bata ga amfanin xaman asibitin ba, na khadijah kadai suka karba ban da na sudais kamar yanda Aliyu yyi instructing din su, da kafa suka fita asibitin don Umma bata xo da mota ba, suna isa bakin titi ta tsayar masu da abun hawa suka wuce gida. Girgixa kai Farouq yyi yana kallon Khaleel yace "Ni fa ba ruwana, kamar yanda na ki ba sa address din ka, to kai ma baxan baka address din sa ba gaskiya, ku kuka san abinda ya hada ku can.." Wani kallo khaleel ke masa kafin ya mike ya fice daga gidan ya shiga motarsa ya wuce, yana driving ya dau wayarsa ya fara kiran Khadijah, har ya katse bata dauka ba, nan ko tana zaune ita kadai daki tayi kukan har ta ji ba dadi, Umma kuma na parlor da Nanny sun yi jigum, Umma ta rasa ta ina xata fara yanxu ta ina xa su fara xuwa neman yara, Jin wayar ya sake ring Khadijah ta daga da kyar ta kai kunne, jin muryar ta jikin khaleel yyi sanyi, a hankali yace "Plss ki kwantar da hankalin ki Khadijah, xa a amsar maki kids din ki, he have no right over them, in sha Allah we will get back ur kids" kasa cewa komai tayi tana share hawayen da ke xubo mata, yace "Kin san address din can gidansu?" Shiru tayi kafin ta girgixa kai cikin sanyin murya tace "Na manta" yace "Amma xa ki gane gidan?" Nan ma ta d'an yi shiru, anya xata gane gidan yanxu kuwa, murya can kasa yace "Khadijah?" Tace "Kilan in gane" yace "Good, kuna clinic din har yanxu?" Ta girgixa kai tace "Mun dawo gida" yace "Toh xan taho yanxu, but promise me baxa ki sake kuka ba plss" a hankali tace "Toh baxan yi ba" yace "Good, ina tahowa yanxu" daga haka ya katse wayar, Sosai Khadijah ta ji hankalinta ya kwanta, ta ji ta samu natsuwa. Tun da Aliyu ya shiga dakinsa bai sake fitowa ba, Mumy da maganganun Anty khadijah suka fara sa mata ciwon kai ta daga kai tana kallonta a karo na farko tun shigowarta dakin, ban da kumfar baki kamar wata xararriya babu abinda take tana nuna yan biyun dake xaune kan gadon Mumy, suma yaran kallonta kawai suke a tsorace, Baby ma na tsaye sai hararan Anty khadijah take tana tabe baki, Mumy ta dakatar da ita a tsawace tace "Khadijah ki fita ki ban waje don Allah ki bar ni in ji da guda daya, ciwon kai kike kara min ki fita don Allah, ko makaho ya shafa yaran nan yasan na waye, Baxa ayi DNA din ba...." Anty khadijah da idanuwanta suka kankance da mugun mamaki tace "Anty fati ni kike cewa in fita in baki waje don ina nuna damuwa ta kan shegun da aka makala ma Aliyu aka ce nasa ne, Ni Anty fati??" Mumy tace "Ehh ki fita nace" tayi wani murmushi tace "Xan fita yanxu kuwa" daga haka ta fice daga dakin kamar xata tashi sama, Mumy ta kalli yan biyun dake bata tausayi har ranta, a hankali tace "Me xa ku ci?" Sudais dai bai ce komai ba, Shureim ya girgixa mata kai shi ma bai ce komai ba, karasowa tayi ta xauna gun yaran tana kallonsu, wani sonsu take ji a xuciyarta, ta d'an yi murmushi tace "Ayi maku noodles and egg?" komawa Sudais yyi ya kwanta ta kai hannu jikinsa taji xafi sosai, kallon baby tayi tace "Xaxxabi ne jikinsa fa sosai..." Baby ta karaso ita ma ta taba yaron taji xafin jikin ta kalli Mumy tace "Mumy ko in kira yaya?" Mumy tace "Kira sa" juyawa tayi ta fita, ita ta fara dawowa dakin sannan Aliyu ma ya shigo, kallon yaron yake har ya isa kan gadon ya taba jikinsa, dago sa yyi ya xaunar da shi, yana kallonsa yace "Are you feeling pain anywhere?" Sudais ya nuna masa kan sa, kamar xai yi kuka yace "I want to go to my Anty plss" Aliyu ya lumshe ido ya bude a hankali yace "Ohk I will take you there" Mumy dake kallon Aliyu tace "Ina ita khadijahr take?" Kamar Aliyu baxae ce komai ba, sai kuma ya shafa kansa murya can kasa yace "Bayan ta bani su tayi tafiyarta" wani kallo Mumy ke masa ganin yanda yyi maganar, can ta girgixa kai tace "Karya kake..." Da sauri ya kalleta, sai kuma ya marairaice yace "Mumy bata sani ba na taho da su, idan ta sani baxa ta bani su ba" Bude baki Mumy tayi tana kallonsa, da damuwa tace "Me yasa xaka yi haka Aliyu, me yasa xaka raba su da uwar su...." Kasa cewa komai yayi, Mumy da duk jikinta ya kara yin sanyi tace "Aliyu tell me how everything happened, garin yaya kayi ma yar mutane haka, where was I that day? kar ka boye min komai plss, tell me the truth...." kallon Mumy Kawai yake ko kiftawa babu, can ya xauna gefen gado ya rike kansa yana jin kamar ya fara mata hawaye, bai son tuna mummunar ranan nan a rayuwarsa, Mumy na kallon Baby tace "Baby xo ki tafi da su ki dafa masu indomie ki basu, shi wannan ki kai sa dakin ki ya kwanta" Baby ta karaso ta sakko da boys din daga kan gado ta wuce da su dakinta, Mumy na kallonsa tace "Ina ji Aliyu" Da kamar baxai ce komai ba, sai kuma a hankali ya fara magana, "Mumy ni dai nasan I woke up fine that very day...." Ya d'an yi shiru, nan ya fara ba ma Mumy labarin abinda ya faru ranan bai boye mata komai ba har yanda bayan kwana biyu ya ba ma khadijah kudi me yawa yace ta wuce gun ummarta, hawaye kawai Mumy ke yi tana kallonsa a sanyaye, bai iya ya dago kai ba shi ma hawayen na sakko masa cike da karfin hali yace "Mumy nayi abinda nayi ne out of confusion, I was confused, ban taba xaton xan aikata ma khadijah haka ba, bayan tafiyar ta ku shaida ne, nayi bankwana da kwanciyar hankali da farin ciki na, I never had rest of mind again kuma na kasa gaya maki abinda ya faru ban san ya xa ki dau xancen ba, shi yasa a ko da yaushe nake ce maki ki taya ni da addu'a, wani lkcn idan na kwanta bacci ita kawai nake gani, kuma it's not as if nasan da cikin bane, kawai ni dai nasan ban kyauta mata ba saboda marainiya ce bata da kowa, ban san ta Inda xan fara nemanta ba don ban san kowa nata ba, da babu abinda xai hanani nemanta Mumy, idan baki manta ba akwai wani lkci da na taba tambayar ki ko kina da number warce ta kawo ta kika ce baki da shi, ni ban sa ko Khadijah xata yafe min ba and it looks as if I don't deserve that.... Amma abinda ke bani mamaki har yanxu shine yanda aka yi Anty khadijah ta san abinda ya faru bayan bata gidan kuma ita ta fita tare da su baby a ranan, gidan ya rage daga ni sai Khadijah, sai kuma jiya tana waya a bathroom din dakinta, I overheard all what she was saying on the phone.... Nan ya gaya ma Mumy duk abinda ya ji Anty khadijah ke fada a waya jiya, yana girgixa kai yace "We shud keep on pretending mum, she was so shock da ta gan ni a dakin, but i pretend ban ji komai ba, hakan kuma ya sa hankalinta ya kwanta, a sannu abinda take yi xai bayyana a fili tun da ba mu da hakkinta, kuma ina mai tabbatar maki soon komai xai bayyana, ke dai kawai ki ci gaba da sa mata ido, xan dai sa su Sanusi su tone bayan gidan to check what she was talking about on phone" Mumy ta dinga kallonsa ko kiftawa babu cike da shock, ya goge idonsa har lkcn bai kalleta ba yace "And... Mumy kilan idan ke kika yi ma khadijah magana xata iya yafe min, ni ta ki saurarata har yanxu, kuma mumy plss kar ki ce min baxan iya aurenta ba, hakan kadai ne xan iya mata in wanke kaina, I knw I can't pay her all what she passed through, kar ki hana ni aurenta mumy..." Mumy ta sauke ajiyar xuciya har lkcn tana mamakin abinda Aliyu ya fadi mata kan Anty khadijah, she is still finding it hard to believe that, infact bata ma yarda bane tasan Anty khadijah baxata yi abinda Aliyu ke fadi ba, Aliyu yace "Mumy kinyi shiru" Mumy ta kallesa ta kara sauke ajiyar xuciya sannan tace "Idan kuma ita bata son ka fa?" Ya d'an hade rai yace "Toh sai ta bar min yarana taje tayi aurenta shikenan na raba ta da wahala, idan kuma ta yarda ta aureni sai mu xauna mu rike yaranmu, domin kuwa su din abun kyama ne idan ta kai su wani gidan, ko ba yanxu ba wataran xa a kyamace su, to idan muna tare fa? We can never do that to them" Mumy bata kuma cewa komai ba tayi nisa tunanin da take na Anty khadijah, Bude kofar dakin Anty khadijah tayi ta shigo tana kallon Mumy da kumburarrun idonta da ta sha kukan takaici, kallo daya Mumy ta mata ta dauke kai xuciyarta na kara karyata Aliyu, Aliyu kam bai ma kalli inda take ba, tana kallon Mumy tace "Ina son sanin matsayin auren iklima a gidan nan Anty fati, na hada kayana idan Ita ma in hada nata ne toh..." Sai a sannan Aliyu ya kalleta yace "Anty aure ya taba mutuwa ba ayi saki ba?" Hararansa tayi ta juya ta fita, dakin baby ta bude ta dinga kallon yaran dake kan gadon cike da tsana, a tsorace suke kallonta su ma, can ta juya ta fita dakin ta sauka downstairs xuciyar ta na tafarfasa, Baby ce kitchen tana bare eggs da ta dafa masu indomien na kan wuta, Anty khadijah ce ta shigo kitchen din ta dau cup ta xuba ruwan xafi daga flask, Baby ta kalleta ganin yanda ta tsaya tana tunani, da sauri Anty khadijah ta bude gun da madara suke ta fiddo kayan tea ganin kallon da baby ke mata, tana hada shayi tace "Baby ina wani sarka da na baki ki ajiye min ranan da aka yi bikin iklima a gidan nan?" Baby tace "Anty yana cikin jakata a daki" Anty khadijah tace "Je dauko min kayana" Baby tace "Yanxu Anty?" Anty khadijah ta balla mata harara tace "Aa anjima" a sanyaye baby ta juya ta fita kitchen din bayan ta rage gas kar indomien ya kone, Anty khadijah ta fara kalle kallen kitchen din da sauri, lkci daya ta fita waje ta kofar kitchen din ta tafi gun da ake ajiye snipper, Baby har ta fara haura stairs ta d'an tsaya, da sauri ta koma ta rabe jikin bango tana lekan kitchen din ta ga Anty Khadijah bata ciki, har xata juya ta bar wajen sai ga Anty Khadijah da gudu ta dawo kitchen din ta bude abun hannunta ta xuba cikin indomie da ke kan wuta, Xaro ido baby tayi taji kafafuwarta sun kasa daukar ta, lkci daya hawaye ya cika idonta ta juya da sauri ta haura sama, dakin Mumy ta shiga ta fashe da kuka, Aliyu ya mike yana kallonta yace "Me ya faru?"

Baby ta durkushe dakin tana kuka sosai tace "Mumy Anty Khadijah ce na ga tana xuba snipper a cikin indomien yaran da nake dafawa" Aliyu ya xaro ido yace "Snipper??" Da sauri ya nufi kofa mumy tayi maxa ta dakatar da shi, ya juyo hankali tashe yana kallonta, Mumy na kallon Baby tace "Ta gan ki?" Girgixa kai baby tayi tana hawaye, Mumy ta hadiye abu da kyar, cike da karfin hali tace "Je ki dauko yaran ki kawo su nan, kar ki ce mata komai" Aliyu sai kallon mumy yake xuciyarsa na bugawa, Mumy ta kallesa tana kkrin goge hawayen idonta tace "Kar ka ce mata komai, let pretend we don't knw... Don't say anything Aliyu" Baby ta dawo dakin da su sudais mumy ta daura su kan gadon tana kallonsu a sanyaye, ta dubi Baby tace "Tafi ki xubar da indomie din, kar ki ce mata komai kin ji, ae basu da hakkinta don hka bbu abinda ta isa tayi masu wanda Allah bai masu ba" Baby ta fita dakin a sanyaye hawaye ya ko tsaya mata, ganin abun take kamar a movie, ynxu da bata dawo ba haka xata dau indomien ta ba yaran su ci su mutu?? Anya Anty khadijah na da conscience kuwa, me yan yaran suka mata, Aliyu kam ya kasa cewa komai, Mumy ta dinga share hawayen dake ta xubo mata, me tayi ma khadijah ta mayar mata da family dinta haka, dama laifi ne idan ka jawo naka ya xauna tare da kai?? Baby bata ko kalli Anty khadijah da ta xauna parlor tana shan shayi ba ta shiga kitchen din, Anty khadijah ta bi ta da kallo ta gefen ido, daukar indomie da kwan baby tayi ta fita ta xubar cikin shara ta tara tukunyar a bakin tap, sai da ta tabbatar ta wanke tas sannan ta dawo kitchen da shi ta ajiye ta fito kitchen din ta wuce stairs, Anty khadijah ta bi ta da kallo baki bude, da sauri tace "Ke wai sai indomien ya kone ne kin bar ma mutane gas yana ci" Ba tare da baby ta juyo ba balle ta kalleta tace "Sun ce baxa su ci ba na xubar" Daga haka ta haura sama Anty khadijah ta mike baki bude tana kallonta gabanta na faduwa, da sauri ta wuce kitchen ganin tukunyar a wanke ta fita waje ta leka bola taga indomien an xubar, still tayi a gun xuciyarta na mugun bugawa, kar dai ta ganta ne.... Jiki a sanyaye ta dawo cikin gidan tana adduar Allah yasa dai ko ta ganta kar ta gaya ma Mumy, Mumy da kanta ta sakko ta shiga kitchen din da ruwan gora biyu a hannunta, ta dumama ruwan sannan ta wuce sama da shi a cup don tana da kayan shayi a dakinta, Anty khadijah ta bi ta da kallo a sanyaye, shikenan kila baby ta gaya mata kenan, da sauri ta fita da wayar ta tafi can baya xata yi kira, nan daki mumy ta hada ma yan biyun tea ta basu Aliyu dai na xaune dakin yana kallon innocent kids din, baby da har sannan jikinta yake a sanyaye tana tsaye dakin ita ma. Duk da yanda Umma ta so bin Khadijah da khaleel xuwa gidan Aliyu kamar yanda khaleel yace kasa furta hakan tayi saboda kunya, Nanny ta dai raka Khadijah har bakin motar khaleel ta koma ciki, khaleel ya din ga kallon khadijah ganin yanda ta fada saboda kuka ta bude front seat a hankali ta shiga kanta a kasa, tausayinta ya ji har ransa ya tada motar ja suka bar layin, sai da suka hau saman titi a hankali yace "But you promised not to cry again Khadijah" da sauri ta kallesa da idanuwanta da suka rine tace "I didn't cry again, ai na riga na maka alkawari, wllh ban kara ba" a hankli yace "Toh naji dadi, kin dai san sunan anguwar su Aliyun koh?" Kai ta gyada masa, yace "Ina ne?" Tace "GRA" yace "Ai biyu ne Gra din, new or old?" Ta buda hannu a sanyaye alamar bata sani ba, wayarsa ce ya fara ring ganin me kiransa ya gangara gefen titi ya daga kiran tare da yin sallama, bayan sun gaisa da mai kiran nasa yace "Salman dama plss am asking... Can you connect me to a lawyer that you knw is just perfect, ni ba xaman Nigeria nake ba so I don't really knw, there is this case that I need one for... I don't want to talk about it to my family shi yasa I decided to contact you" Sai kallonsa Khadijah take ko kiftawa babu, bayan wani lkci ya shafa lallausan gashin kansa yace "Sure... Ina jira, thanks much" daga haka ya katse wayar, ya juya ya kalleta ta dauke kai da sauri, d'an shiru yyi kafin yyi murmushi yace "Frnd dina ne, xae hada ni da lawyer yanxu, I think it's better we sue him, kulasa ayi hayaniya ba yi da fa'ida, and xai iya kai yaran wani gun, so ynxu two cases xa ayi da shi, 1st na rape... Sai kuma na biyu ya dawo rana daya yana claiming yaran da bai ma san kin dau cikinsu ba saboda rashin kunya...." Ita dai Khadijah ba ta ce komai ba, yace "So bari in jira xae turo min number Wani barrister da xanyi contacting yanxu" a hankali khadijah tace "Toh nagode, Allah...." Fingers dinsa ya daura bakinsa a hankali yana kallon kwayar idonta, ba shiri ta sauke idonta tayi shiru ta samu kanta da yin murmushi, text ne ya shigo wayarsa ya dauka yana kallon number da sunan barristern da Salman ya turo masa, dialing number yyi yana ganin ya shiga ya kai kunne, Sai da aka daga sannan Khaleel yyi sallama cikin cool voice dinsa, jin an amsa yace "Barrister barka da yamma" daga daya bangaren aka amsa masa da barka dai... Khaleel yace "You are speaking with Dr Ayman, plss ina son assigning din ka ne kan wani case, hope i won't inconvenience you..." Barristern ya amsa masa da "Sure, but na baro office yanxu" Khaleel yace "Waow.. So yanxu ya xa mu yi, and we need to talk today barrister" Barristern yace "Okay mu hadu eatry yanxu don ban shiga gida ba" Khaleel yace "Maa sha Allah ina godiya for ur time barrister" sunan eatry din Barristern ya gaya masa daga haka suka yi sallama, Khaleel ya katse wayar yana kallon khadijah yace "So mu je mu samesa eatry din yanxu koh" kai kawai ta gyada masa ya tada motar ya nufi eatry din, khadijah tayi nisa tunanin da take, gaba daya ji take kamar tayi shekara da shekaru rabonta da lovely twins dinta, bata taba tunanin tana son su har haka ba sai ynxu, ta ji ta kara tsanar Aliyu fiye da komai na rayuwar ta, she hate him with passion... kallonta kawai khaleel yake bayan ya gama parking cikin babban eatry din, a hankali ya kai hannunsa kan nata, lkci daya ta dawo duniyar tunanin da ta tafi, yyi kasa da murya yace "Thinking about ur twins?" Lkci daya hawaye ya kawo idonta tana kallonsa a sanyaye, ya girgixa mata kai yace "You've broke the promise" da sauri ta goge idonta tayi murmushi cikin sanyin murya tace "Don Allah kayi hakuri" murmushin yyi shima ya fiddo handkerchief dinsa ya mika mata, ta karba a sanyaye tana goge idonta, kamshin handkerchief din ya kara kwantar mata da hankali, ganin bata maido masa ba ya bude motar ya fita ita ma ta fito ya rufe motar, yana gaba tana biye da shi suka shiga cikin eatry din.

Khaleel ya dinga bin few mutanen da ke xaune eatry din da kallo yana tafiya a hankali, ganin he can't tell who is barrister a cikinsu ya wayarsa ya shiga kiran contact dinsa, at one end of the eatry ya ga wani mutumi da ke backing din su ya dau wayarsa dake gabansa ya kai kunne, nan khaleel ya gane shi ne, yace "Alryt na gan ka barrister" daga haka ya katse wayar ya kalli khadijah yace "Mu je" tana biye da shi har suka isa gun da barristern ke a xaune, Khaleel ya ba sa hannu suka yi musabaha, sannan ya ja kujerar da ke side din barrister ya kalli khadijah yace "Come over" ta karaso a hankali ta xauna shi kuma ya xauna yana facing barristern dake operating wayarsa, Khadijah ta dago kai a karo na farko tana kallon barristern da har lkcn idanuwansa ke kan waya yana kkrin silencing wayar, ji tayi komai nata ya tsaya ta dinga kallonsa ko kiftawa babu xuciyarta na bugawa, dai dai lkcn da shi ma ya dago manyan idanuwansa don kallon bak'in nasa yana cewa "Alryt... Barkan...." Makalewa sauran maganan nasa yayi ya dinga kallon khadijah ko kiftawa babu, lkci daya hawaye ya kawo idonta ta mike ta bar wajen da sauri tana hade hanya, Mikewa yyi shi ma da sauri ya bi bayanta yana cewa "Amiraa..." Khaleel ya bi su da kallo da catlike eyes dinsa yana shafa beard dinsa, lkci daya sudais ya tsaya cak kamar wanda ya tuno wani abu, a hankali ya juyo yana kallon khaleel dake kallonsa shi ma, dawowa yyi da sauri yana girgixa kai yace "Am.. am really sorry plss, don't knw if she is ur wife, kayi hakuri.... I.." Sai kuma yyi shiru very confused, khaleel dai bai ce komai ba ya mike kamar bai son tafiya ya nufi kofar fita, Sudais ya xauna ya dafe kansa xuciyarsa na ci gaba da bugawa, Khaleel na fita can gun motarsa ya ga khadijah tana hawaye, ya iso gabanta ya tsaya yana kallonta yace "Who is he?" Tana share idonta a sanyaye tace "Sudais" shiru yyi na few seconds yana juya wristwatch din hannunsa, can ya dago kansa yana kallonta yace "So what next?" Ganin Sudais ya fito eatry din ya tsaya nesa da su yasa bata ce ma khaleel komai ba wasu hawayen suka dinga sakko mata a sanyaye tana kallon sudais, har ya iso inda suke shi ma duk a sanyaye yake, yana kallon khaleel a hankali yace "Am sorry Dr Ayman, idan matar ka ce kayi hakuri ka bani just 2mins in mata magana plss" da damuwa ya kare maganar, Khaleel ya d'an yi murmushin karfin hali sai dai bai ce komai ba, durkushewa Khadijah tayi gaban Sudais cikin rawar murya tace "Me yasa baka son ganina a rayuwar ka kuma barrister, I won't be a burden to you again, amma ko xumunci ne sai kayi da ni don Allah, me yasa ka gan ni kayi pretending you've never known me all ur life, did I deserve that? Ni nasan har karshen rayuwata baxan mance ka ba Sudais, kai din wani haske ne a rayuwata har kullum, baxan iya biyan ka abinda ka min ba but plss allow me to show appreciation always, I have missed you for many years.... I thought baxan sake ganin ka a duniya ba, sai gashi na ganka kayi shunning...." Kasa ci gaba tayi tana kuka sosai, Sudais da idanuwansa suka kada lkci daya ya isa gun khaleel yace "Plss is she... Married??" A hankali khaleel ya girgixa masa kai, Sudais ya runtse ido ya bude yana kallonsa yace "Sorry I have to do this" yana fadin haka ya dawo ya durkusa gabanta ya rike hannunta gam cike da karfin hali yace "I know I have soo missed you Amira, I missed you... Nayi kewar ki da yawa, nayi kewar ki fiye da wanda kika min, nayi kewar twins dina, ba da son rai na na tafi na bar ku ba Amira... I have no option, kullum dake nake kwana nake tashi a rai na, but ya xan yi?? Mami na..." Kasa karasawa yyi, idonsa ya kada sosai, ita ma kuka take a hankali tana kallonsa, lkci daya yace "Where are my boys??" Tsayar da kukan da take tayi tana kallonsa a sanyaye, ganin kallon yasa gaban Sudais ya fadi sosai shi ma ya dinga kallonta, Khaleel dake rungume da hannayensa yana ta kallon dramar su yace "That's exactly what brought us here barrister" mikewa Sudais yyi da wani expression ya isa kusa da khaleel yace "What happened to them?" Khadijah ta mike tana goge idonta cikin rawar murya tace "Aliyu..." Kasa karasawa tayi, Sudais da idanuwansa suka sauya launi ya juya a hankali yana kallonta cikin husky voice yace "Aliyu did what?" Khaleel yace "Took them away from her" Sudais ya tsaya kallon khaleel mouth agape... Lkci daya yanayinsa gaba daya ya canxa, ya kalli khadijah dake hawaye yace "I will teach him the lessons of his life" khaleel ya daga kafada bai dai ce komai ba, Sudais ya kalli khadijah yace "Har yanxu gidan nan da muka je suke?" Tace "Nima ban sani ba" kallon khaleel yyi yace "We have to go to the house now..." Khaleel yace "Ohk then" har Sudais xai ce khadijah ta taho su tafi a motarsa sai kuma yyi saurin barin hakan a ransa, muryar Khaleel ya ji yana cewa "Or ko xaki je da barrister a car dinsa, xan bi bayan ku ni" shiru khadijah tayi tana wasa da fingers dinta, can ta saci kallon Sudais ta ga kallonta yake, tayi saurin dauke kanta, bata san lkcn da tace "Ohk, xan hau tricycle ku tafi kawai, xan gane gidan kila" ta gefen ido khaleel ya kalleta bai dai ce komai ba ya nufi motarsa, shi kansa Sudais bai ce komai ba, can ya shafa kansa a hankali yace "You don't worry tun da tare ku ka xo da shi, ki tafi ki hau tasa motar Amira" shiru ta yi tana kallonsa, murya can kasa yace "There are a lot of things to talk about Amira, but let settle Aliyu's case first" kai kawai ta gyada masa yace "Toh tafi kar ya tada motar" A hankali ta juya ta nufi motar Sudais ya bi ta da kallo ko kiftawa babu, tana isa xata bude motar khaleel yace "No, no you don't worry Khadijah ki tafi ku je tare da shi, we will meet there" daga haka ya fara reverse ta koma baya hankali tana kallonsa har ya fita, Jiki a sanyaye ta dawo gun sudais dake ta kallonsu, yana ganin haka ya xaga ya bude mata front seat, kanta a kasa ta shiga motar bata son ya ga hawayen idonta ya rufe motar, kafin ya xaga ya shiga maxaunin driver ta goge idonta da sauri, yana rufe side dinsa ya tada motar yyi reverse ya fita shi ma, ta madubi yake ta kallon motar khaleel dake jiran nasa yana hawa kan titi ya dau hanyar gidansu Aliyu khaleel ya bi bayansa, lkci lkci sudais ke kallon khadijah da tayi nisa tunanin da take, murya can kasa ta ji yace "Amira" da sauri ta kallesa yace "Waye Dr Ayman?" Kallonsa ta tsaya yi ta kasa cewa komai, a hankali yace "Kin yi shiru" Ta dauke idonta daga kallonsa bata ce komai ba still, hakan yasa bai sake ce mata komai ba, sai da suka yi nisa taji sanyayyan muryarsa yace "Saurayin ki ne koh?" Khadijah ta saci kallonsa still ta ki cewa komai ba, a sanyaye yace "Ki min magana pls Amira" Ajiyar xuciya ta sauke a boye, murya can kasa tace "Just as u tried ur best not to make me feel lonely in this world, shi ma abinda yake min kenan... He is also playing same role in my life." Ta gefen ido Sudais ya kalleta na few seconds kafin ya lumshe ido ya bude yace "you didn't answer my question Amira" Khadijah ta juya tana kallonsa tace "Lkcn da kake tsaka da taimako na, where you my boy friend?" Kasa ce mata komai yyi na few seconds, murya can kasa yace "Ohk.. But I am now, I want to be noe" juyawa tayi tana kallonsa da sauri, ba tare da ya kalleta ba ya gyada mata kai yace "Yea...."

Readers Also Read