Rayuwa da gibi complete na batul mamman - Chapter 22
Rayuwa da gibi complete na batul mamman Chapter 22: Rayuwa da gibi complete na batul mamman Chapter 22. "Mu ne da alhakin sama mata farincikinta. Idan ba…
4,492 words
"Mu ne da alhakin sama mata farincikinta. Idan ba haka ba Allah muna gab da rasata."
"Ni uban mace ki ke so in kira tsohon mijinki in roƙi ya sa ɗansa auren ƴata? Da hankalina fa."
Ɗaure fuska tayi "to sai ka barta ciwon so ya kasheta ai."
"Ki gaggauta kiranta ta dawo gida kafin ranta ya ɓaci wallahi." Har wani haki yake don ɓacin rai. Rainin hankalin Mami ya yi yawa.
Juyawa ya yi zai fita tayi saurin jefa layarta ta biyan buƙata a baki ta tauna. Kamar an tsayar da ƙafafunsa ya tsaya cak.
"Nace ka kira Alh. Hayatu ka san yadda za ka yi dashi ya amince a aurawa ɗansa Taj Salwa." Ta faɗi da izza.
"To. Yanzu ko yaushe?"
"Zauna ka kira yanzu."
Zaman ya yi ya ɗauko waya. Ta miƙa masa wayarta mai ɗauke da numbar Alh. Hayatu ya kwafa ya yi dialing.
"Assalamu alaikum"
Ta jiyo muryar tsohon masoyinta abin begenta har yau. Sake tauna layar tayi ta zarewa Alh. Mukhtar idanu. Jiki na rawa ya amsa sallamar tare da gabatar da kansa. RAYUWA DA GIƁI 24
Batul Mamman💖
Lallai Alh. Mukhtar ɗinnan ya gamu da sharrin Mami shi ne abin da Alhaji ya fara rayawa a ransa bayan sun gama waya. Yadda ya dinga koro bayani akan irin son da ƴarsa take yiwa Taj da fatan amincewar Alhajin don ayi aurensu kai ka san kan ba ƙalau ba. Shi dai yana son ƴaƴansa, amma fa yana ganin babu ƴar da ta isa ta saka shi zubar da mutumci haka a gaban tsohon mijin matarsa. Irin waɗannan abubuwan ya fara gani da burinta na fin kowacce mace matsayi ta kowacce hanya yasa shi sakinta. Yana da labarin yadda matan Alh. Mukhtar biyu su ka fita bayan an aurota. Kuma duk wadda ya ƙaro bata jimawa za ta yi waje ita ma.
Zama ya gyara da ya tuna yadda ya ce masa ya amince kai tsaye. Fakewa zai yi da guzuma ya harbi karsana. Ya san a taurin kai irin na Taj akan ya auri Salwa ya faranta masa gara ya saki Hamdi. Ana yin sakin da kansa zai ce masa ya janye batun auren. Duk da a iya saninsa Salwa yarinya ce mai saukin hali. Babu mamaki sirrin zuciyarta ta sanar da Mamin ita kuma tayi amfani da raunin ƴar ta ɗorata akan hanya mara ɓullewa irin wannan. Tsigar jikinsa har wanu tashi tayi da ya yi addu'ar Allah Ya tsare shi surukuta da Mami da lusarin mijinta kamar yadda ya laƙaba masa suna.
Bai ga alamun Habibu Simagade zai iya wani kataɓus wurin raba yaran ba. Yanzu da ya sami dama shine zai yi amfani da ita. Ɗansa yake muradi ya dawo gida. Amma ba tare da iri ko jinin ɗan daudu a tare dashi ba. Saboda rashin son ganin Hamdi ranar da aka ce za ta zo gidan zamansa ya yi a kasuwa har ƙarfe tara. Shi ba abin ya ce kada ta zo ba matan gidan su soma tijara. Ya fahimci yanzu kamar ma jira suke ya ce kule su ce masa cass.
Ahmad ya nema da yazo gida yana son ganinsa da daddare. Bayan ya taso daga office kai tsaye can ya wuce. Alhaji ya keɓe dashi yana tambayarsa alaƙar Taj da Salwa tunda duka a gidansa su ke.
Tsoro ne ya bayyana a fuskar Ahmad. "Alhaji wata maganar ka ji?"
"Ya zan yi maka tambaya ka amsa min da tambaya?"
Da sauri ya bashi haƙuri tare da amsa tambayar da ya yi masa. "Babu komai a tsakaninsu amma kuma ba faɗa su ke yi ba. Shi Taj ma bai fiye zaman gida ba ai saboda kullum su ke buɗewa."
"Babanta, Alh. Mukhtar sunansa ko?" Alhaji ya faɗi da irin rashin damuwar nan.
Ahmad baya jindaɗin yadda ake magana akan Salwa yanzu. Rannan ƴan uwansa ne su ka yi ana ta dariya. Yau kuma Alhaji ke tambayar sunan babanta kamar wani abin gudu.
"Sunansa kenan."
"Ya kirani yana roƙon na amince Taj ya aureta."
Maganar ta dake shi sosai "Roƙo kuma Alhaji?"
"Roƙo mana. Ya tabbatar min ita take son sa. Kaima yanzu ka ce babu komai tsakaninsu. To me zai sa ita babar taku ta amince harma mijinta ya kirani?"
"Zan yi mata magana Alhaji." Ya girgiza kai "Gobe in sha Allah zan mayar da ita Bauchin. Idan ma mijin ne su sama mata a can." Tashi ya yi zai tafi. Alhaji ya ce ya dawo.
"Babu daɗi mutum ya nemeka akan wata alfarma ka nuna masa baka so. Saboda haka na faɗa masa na amince. Saƙon da nake son baka shi ne ka sanar dasu cewa bana so komai ya wuce wata ɗaya indai da gaske su ke."
Yana magana ne yana kallon yanayin Ahmad. A ransa kuma yana addu'ar Allah Yasa ɗan nasa ya yafe masa. Da gangan yake maganar a haka saboda yana so idan Ahmad ya tashi kai saƙon ya nuna musu shi fa bai ɗauki maganar da mahimmanci ba. Sannan baya ɗokin haɗa zuri'a da ƴarsu. Ya sami wannan canjin ra'ayin ne bayan wani nazari da ya yi. A matsayinsa na uba sai hankalinsa bai kwanta da ya yi amfani da ƴar wani domin biyan buƙatarsa ba. Idan komai ya tafi yadda yake so ya dawo ya ce da Taj kada ya auri Salwa me kenan ya yi? Shi mai ƴaƴa da jikoki mata ya dace ya tozarta ƴar wani haka? Gashi saboda sanin halin babarta ya tabbatar idan ya yi sake ta auri Taj sai sun mayar masa ɗa abin wasan yara.
Ba a raba hanta da jini. Hakan da yake yi ya san duka Ahmad zai faɗawa Mami. Kuma tunda yaro ne hankali zai yi ƙoƙarin nusar da ita illar bari a yiwa ƴarta irin wannan auren. Da bakinsa ne dai akwai nauyi bayan ya aminci ɗazu ya dawo ya ce ya fasa. Abin zai zama cin fuska sosai. Fatansa yanzu dai Allah Yasa iyayen suna da hankalin gane manufarsa.
Da wannan damuwar Anti Zahra ta tarbi Ahmad. Juyin duniya tayi ta tambayarsa amma yaƙi faɗa mata abin da yake faruwa. Abinci ma kasa ci ya yi saboda baƙincikin yadda Salwa take zubar da darajarta ta ƴa mace. Gashi yanzu ta sa iyayenta biye mata. Don ma su Hajiya akwai kawaici. Babu mai zancen Mami a gidan ko a aibata ta. Amma yanzu da sun ji maganar auren nan babu abin da zai hanasu fitowa ƙiriƙiri su ƙi.
Salwan ya kira tana ɗaki tana chatting da Ummi. Cikin sigar wayon da Alh. Usaini ya koya mata take ta jan Salwa tana dukan cikinta. Rai bai so ba ta katse hirar ta fita wajen Ahmad. Ɗakinsa ya kirata ba ma falo ba.
"Kun yi maganar Taj ne da Mami?"
"Eh" ta amsa masa babu wannan girmamawar da ya santa da ita.
Yadda su ka yi da Alhaji ya faɗa mata. Babu kunya ta kama murmushi. Baki har kunne.
"Da ni ne ke Salwa da na haƙura da mutumin da bai damu dani ba. Wane irin aure za ku yi yanzu? Shi baya so kuma na tabbata da wahala ƴan gidanmu su so."
"Ai ba da su zan zauna ba." Ta ce da tsiwar da bai santa da ita ba. Wai duk so ne ya canjata ko kuwa dama can halinta ne da bai sani ba?
"Shikenan. Zan kira Mami na faɗa mata. Duk abin da ya biyo baya kada ki ce ban yi warning ɗin ki ba."
Da ƙunƙuni ta tashi tana cewa "alkhairi zan gani."
Daina bashi mamaki tayi. Ya ce mata ta haɗa kayanta gobe za ta koma gida. Ƙarfe tara za su kama hanya. Tana fita ya kira Mami ta rangaɗa uwar shewa. Mantawa tayi da wa take magana ta ce,
"In ya san wata ai bai san wata ba. Har ni zai wulaƙantawa ƴa saboda yaci sa'a tana son shi?"
"Mami ana dole ne? Aurensa duka-duka sati ne fa da ƴan kwanaki. Ni dai da za ku ɗauki shawarata da kin ce mata ta haƙura."
Da faɗa Mami ta ce "to mai halin ubansa. Wanda baya kishina da na ƴaƴana. Idan ta haƙura kai za ka aureta?"
"Allah Ya baki haƙuri." Kawai ya ce.
"Amin. Kuma ka tanadi abin da za ka bani don a wata guda ko babanta ba zai iya haɗa abin da ya dace ba."
Allah Ya sani bashi da irin kuɗin da ya san idan ya bata ba za ta raina ba a yanzu. Sabon wata ne kuma farkon term an koma makaranta. Ɗa ɗaya amma ɗawainiyar karatu sai dai kawai a dinga yiwa iyaye addu'a. A bisa tsarin gidansu kuma tunda su ka soma kawo ƙarfi sun ɗaukewa Alhaji abubuwa da dama. Ba kuma don bashi da kuɗin ba. Ko a danginsa babu kamar shi har yanzu. Suna yi ne don neman albarka. Kayan abinci, kayan buƙata na gida irin su sabulu da kuɗin kashewa ga iyayensu. Duk masu aiki da masu kasuwanci suna contributing. A matsayinsa na babban namiji duk da cikin matan akwai waɗanda samunsu yafi nashi, amma yana ƙoƙarin ganin ya yi bajinta. A haka kuma yake bawa Mamin dubu talatin duk wata.
"Kai, Ahmad. Baka ce komai ba."
Ya ma manta waya yake. "Allah Ya hore. Sai da safe."
Ko minti goma basu yi da gama wayar ba ta sake kira. Ya san zancen ba zai wuce na kada ya dawo da Salwa ba. Shi yasa yaƙi ɗauka. Zai kaita gida gobe in sha Allahu.
Ƙarfe bakwai da rabi Anti Zahra ta same shi a ɗaki wai Salwa ta fita.
"Bangane ba. Ina ta tafi?"
"Ina ta tambayarta tana kuka. Da alama bata son tafiyar. Da ka ƙyaleta."
A harzuƙe ya tashi yana ta faɗa. Sai a lokacin Anti Zahra taji me yake faruwa. Ta ma kasa comprehending wannan al'amari.
"Don Allah kayi shiru kada Taj ya ji. Kwanansa biyu yana fama da zazzaɓin nan mai zafi. Sannan ko babu komai ka haɗa uwa da ita. Mutumcinta abin karewa ne a wajenka komai rashin daɗin da abin ya yi maka."
"Gidan wa zata da safiyar nan? Idan tana tunanin zan bita ne wallahi tayi kuskure."
"Naji. Ka san ba za ta wuce gidan ƙanwar babanta ba ta Sheka. In ba nan ba kuma ƙila ta wuce Bauchin."
"Ita ta sani."
Sai dare ya ɗauki wayar Mami. Ta ƙare masa tanadi kuwa. Shi kuma ya tsaya akan bakansa na cewa indai Salwa ta dawo gidansa to Bauchi zai maidota. Ba zai zauna da mara kunyar da bai isa ya faɗa mata taji ba. Mami da taga yaƙi tanƙwaruwa ta haƙura.
"Shegen yaro mai halin ubansa."
***
A kwana biyun nan kullum Hamdi sai ta kira Taj. Zazzaɓi ne irin wanda ya kan zo gama gari mai shiga gida gida. Ita kanta tana mamakin yadda ta damu da ciwon nasa da kuma rashin ganinsa. Da Zee ta tsegumtawa Sajida halin da take ciki haɗuwa su ka yi suna tsokanarta.
Zee ta ce "Salman Khan ya sallame zuciyar Hamdi."
Ita kuma Sajida tana dariya ta tuna mata tsohon ƙudurinta.
"Ta dai gama cika bakin bata son namiji mai girki. Yanzu gashi nan mai gidan abinci ya hanata sukuni."
Da yake a wayar Zee ake ta bidirin, gajiya tayi da kare kanta ta tsuke bakin nan. "Aljannar mace dai tana ƙarƙashin ƙafar mijinta. In kuma kuna baƙincikin kada na samu ne sai in ji."
Sajida da Zee me za su yi kuwa banda dariya. Ashe rana irin wannan za ta zo musu a kurkusa haka basu sani ba.
Ƙyalesu tayi ta koma kitchen wajen girkinta. Tana aiki tana tunaninsa. Yau ce rana ta uku tun zuwan da ya yi ta kira masa Kamal. Wayar ma idan sun yi ba wani jimawa su ke ba. Gaisuwa ce da jin yaya jikin nasa. Ɗan wasan nan duk ya daina.
"Ke!"
A firgice ta kalli Yaya. Bata san tun yaushe take tsaye tana yi mata magana ba.
"Jikin nasa ne har yanzu?"
Wayancewa tayi kamar bata gane ba "wa?"
"Garinku in kin san shi. Wa ma za ki ce min?"
Ƙasa ta kalla a kunyace. Fuskarta babu walwala. Yaya ta fahimci har yanzu a kwance yake.
"Jiya dama Abbanku yake zancen zuwa a dubo shi. Zan sake yi masa magana yanzu in sha Allah a waya."
Fuska mai tona asirin zuciya. A take fuskar Hamdi ta washe. Yaya ta kama baki tana salati.
"Anya dama ba shirya maganar auren nan ku ka yi da Taj ba? Cikin ƴan kwanaki kin zurma haka?"
"Ni ban zurma ba Yaya"
"Tsiwar ma ai naga ta ragu. Allah Ya yiwa aure albarka. Amma ki rage murna don ba dake zai je ba. Halifa zai ɗauka."
"Kai Yaya, ni yaushe na ce zan je?"
Dariya tayi "nima wasa nake miki. Ai na san ko tayi aka yi miki za ki ce a'a."
Bata ƙara magana ba tunda ta gane Yayan ma tsokanarta take yi. To ita har me tayi da ake mata wannan fassara?
*
A ɓangaren Taj abin da ya zata zazzaɓin gajiya ne ashe combo ne na typhoid da maleriya. Ciwon da ya manta rabonsa da yi. Shi ne ya yi masa rubdugu irin wannan. Kuma da yake zafi ake yi sai ya haɗu goma da ashirin. Dalilin zazzaɓin ne ma su Mama su ka tsahirta da sanya lokacin biki. Shirye shirye dai sai abin da ba a rasa ba. So su ke amarya ta shiga ɗakinta nan da sati uku ko wata guda. A nasu shirin idan ta tare da wuri za su ɓata shirin Alhaji. A ganinsu dama wata ukun nan da ya bayar ya yi ne saboda sanin cewa da wahala ace Abba Habibu yana da abin da zai yi bikin wata ƴar nan kusa.
Sosai Ahmad yake bashi kulawa. Musamman bayan tafiyar Salwa. Fushin da ya fara akan yadda aka yi mata dole ya kau da ya gaskata ita ce ta janyowa kanta.
Kamal ne dai tun ranar da ya kai shi asibiti ya ƙirƙiri tafiya washegari. Ciwo ke neman kayar dashi kuma baya son kowa ya sani. Haka ya tattara ya tafi asibiti. Mubina ta kwantar dashi. Magunguna tana iya bakin ƙoƙarinta. Bata so su fara dialysis domin ana kaiwa wannan matakin, transplant (dashe) shi ne best option ɗin da zai rage.
Ranar da ta kwantar dashi bayan ya zama stable ta kira Yaya Kubra. Dama kullum jiran wayarta take yi. Tana gani kuwa ta bar ayyukan gabanta ta tafi asibitin.
"Akwai shirin da ki ka fara yi ne Doctor saboda in san next course of action?"
Yaya Kubra ta gyaɗa kai "na fara bincike ta bayan gida. Wata questionnaire na ƙirƙira a google form nace ta research ɗina ce. Ita na tura a groups na family ake ta cike min. Harda families ɗin duka matan gidan mu. Kuma da yake da suna so far na sami mutum huɗu that are rhesus negative."
Idanun Mubina harda ƙwalla ta ce "Masha Allah. Amma dangin kusa ne?"
"Surprisingly daga dangin Hajiya na sami uku. Ɗaya ne a dangin Umma. Ai jinsi baya hana bayarwa ko? Duka huɗun mata ne."
Mubina ta ce gender baya hanawa. "Amma fa Kamal A negative ne. Indai ba irin nasa ba kinsan sai dai O ko AB negative ko?"
"Dukkaninsu O negative ne. Yanzu su Alhaji ya rage su sani sai a tuntuɓe su."
"Muje ki ganshi. Akwai Nephrologist da na fara magana dashi daga Port Harcourt. Idan an sami nasarar samun mai bayarwa sai naji yaushe zai iya zuwa."
Godiya Yaya Kubra tayi mata har ta rasa kalmar faɗa. Mubina ta shige gaba zuwa ɗakin da Kamal yake. A hanya tayi ta nanata mata don Allah ta daure zuciyarta idan ta ganshi. Wannan yasa zuciyar Yaya Kubra ga tsinke tun kafin su shiga.
Mubina ce ta fara shiga da sallama. Yana kwance gaɓoɓi da fuskarsa sun kumburo sosai. Shi kaɗai ya san irin azabar ciwon da yake ji. Amsa sallamar ya fara da muryarsa can ƙasa kawai sai ya yi tozali da Yaya Kubra. Ya yunƙura ya tashi zaune kafin ta ƙaraso.
Hannu ta ɗora akan bakinta don kada tayi kuka mai haɗe da ihu da taga yadda ya koma.
"Kamal?" Ta kira shi da rawar murya.
Ya miƙa mata hannu, kwarmin idanunsa yana ziraro hawaye ta riƙe. A gefen gadon ta zauna su ka rungume juna. For the first time tun bayan ciwon nan ya same shi ya fashe da kuka mai ban tausayi. Duk wani ciwo, ƙunci da damuwa da yake ɓoyewa ya bari ya nuna kansa a wannan lokacin. Shi ɗan dangi yana ta fama da damuwa shi kaɗai. Abin da gidansu basu saba ba.
Yaya Kubra tana kuka tana shafa bayansa da lallashi. Mubina kuwa ficewa tayi don bata son karyar masa da zuciya fiye da halin da yake ciki. Mara lafiya baya son ganin rauni a tattare da likitansa.
Tsahon minti goma zuwa shabiyar kafin yaji sanyi a ransa ya daina kukan.
"Kiranki tayi ko?" Ya tambayeta yana nufin Mubina.
Faɗa ta soma yi masa "Me yasa ka zaɓi wannan rayuwar Kamal? Bamu da mahimmanci a wurinka? Ko kana ganin ba za mu damu da lalurarka ba?"
"Irin wannan kallon kamar kina yi min sallama shi ne bana son gani. Wannan kukan zamu dinga yi kullum har lokaci..."
"In sha Allahu za a dace. Ina nan ina bincike."
"Bata faɗa miki cewa ko dialysis ba zai iya riƙeni na tsayin lokaci ba?"
"Na sani Kamal. You need a new kidney. And we'll find one in sha Allah" ta share masa hawaye da hannunta.
Alƙawarin riƙe masa sirri ya roƙeta har zuwa lokacin da za ayi bikin Taj. Sannan ƙanwarsu mai shirin haihuwa ko yau ko gobe ita ma ta sauke.
"Me yasa? Wallahi ka san ba za ka burge Taj ba. Infact ni ba zan so ganin ranar da zai sani ba. Za ku yi faɗa Kamal. Za ku yi faɗa sosai. Ko jiya da naje duba shi sai da yayi ta zancen wai ina duba maka magungunan allergy kuwa."
Jingina ya yi da pillow don ya gaji da zaman. Ya yi ajiyar zuciya.
"Na sani. Amma Happy zai tsayar da duka uzurin rayuwarsa ne. Zuwa yanzu kin san mutum ne mai sanya abu a rai. Amma kina gani saboda mu ya mayar da komai ba komai ba tsakaninsa da Alhaji. Kuma hakan fa ba ƙaramin ciwo yake yi masa ba."
"Tsakanin uba da ɗa ne wannan. Ina maganar Happy da Happiness. Sai ka shiryawa duk abin da zai biyo baya."
"In ya ganni a haka kina tunanin zai iya yi min mita? Kuka kawai za mu zauna mu sha abinmu."
Yadda yake maganar kai ka san akwai tsantsar tawakkali. Yaya Kubra a nan ta wuni har tara na dare sannan ta tafi. Ta amince za ta yi shiru amma ba don Kamal ba. So take ta samu cikin dangin wanda idan ta bijiro da buƙatar ba zai ƙi ba. Maganar neman donor ta hanyar gwamnati ba zai yiwu ba. Waɗanda su ke kan list sun yi yawa sosai.
Tsakanin Kamal da Taj a waya sai ta whtsapp. Kamal ya cire simcard da sunan baya ƙasar. Wai ya tafi China odar takalma. Taj harda mitar me yasa bai faɗa masa shirin tafiyar ba. Ya ce wanda ya bawa sautu ne ya sami matsala. Gashi kuma komai ya kammala. Ana buƙatar mai kaya. Abinka da rashin sabo da yi. Taj bai kawo komai ba ya yarda. Iyaka dai in suna waya ya dinga kiran wash wash kenan don kawai yaji Kamal yana sannu kamar ya ari baki. Bai san ciwon Kamal ɗin ya ninka nashi ba.
***
Kamar yadda Anti Zahra tayi hasashe, Salwa gidan ƙanwar babanta ta tafi. Gidan da tun farkon karatunta baban ya so taje amma saboda Mami ta raina arziƙinsu ta rufe ido ta ce bata san zance ba. Wannan tafiya da tayi sai ta sami lasisin fita yadda take so tana haɗuwa da Ummi. Gwaggonta kuma bata iya yi mata magana saboda tsoron jarabar Mami.
Bayan bugun cikin da Ummi tayi mata sai ta nuna mata cewa tana jajanta mata rashin samun soyayyar Taj. Ta kuma yi mata alƙawarin za ta taimaka mata ta sami biyan buƙata indai tana so.
"Mamina ma ta gama komai har an fara maganar aurenmu" ta faɗawa Ummi da farinciki.
Taɓe baki Ummin tayi "in an ɗaura muku auren kina tunanin kin yi nasara ko me? Mutumin da baya sonki kuma igiyar auren tana hannunsa."
A tsorace Salwa ta ce "kuma fa haka ne. Amma ba sona bane baya yi. Haɗuwarsa da matar da aka aura masa ƴar ɗan daudu duk shi ya lalata komai. Da muna waya normal."
A zuci Ummi tayi tsaki. Wannan Salwan irin matan nan ne da sakarci ya rinjayi tunaninsu. Gashi dai ta san cewa ta girmeta amma irin shirmen da take yi da sunan soyayya ita ko da wasa ba za ta yi ba.
"Ni naga sharrin ƴar ɗan daudu. Akanta aka koreni daga makaranta sannan aka fasa bikina. Gidanmu kowa ya tsaneni akansu. Wallahi da zan haɗu da Hamdiyya Habib sai na rama abin da tayi min ko yaya ne."
Idanu Salwa ta zaro tana kallonta "Hamdiyya? Ai kuwa ita ma sunanta kenan. Babanta yana aiki a Happy Taj."
"Ni ban san a ina yake ba. Amma dai shi ma sana'ar girki yake yi. Kin ganta. A yadda suke matsiyata bana jin ko iskar da mai Happy Taj yake shaƙa ita ma za ta shaƙa wataran."
Hoton Hamdi ta nuna mata wanda ta samu ta ɗauka daga wayar Siyama na ranar aurensu. Salwa ta dinga sallallami gami da rantsuwar ita ce. Ita ma Ummi ta nuna nata mamakin ƙwarai.
"Indai Hamdi ce nayi miki alƙawarin zan bada nawa taimakon na raba su da masoyinki."
"Nagode. Ni kam alkhairi ne ashe ya kai ni Glory mall rannan."
Ummi sai dariyar yaƙe kawai take yi. Ita kanta duk fitinarta abin da Alh. Usaini ya tanadarwa Taj ya yi mata hatsabibanci da yawa. Ta riga ta nuna masa tana tare dashi bata da hanyar guduwa. Haka kawai take tsoron mutane irinsa waɗanda za su iya yin komai domin biyan buƙatarsu. Rashin kunyarta bata kai nan ba. Domin kuwa duk iya shegenta akwai abubuwan da take tsoron yi don kada su koma kunnen iyayenta. Tunda Allah Ya kawo Salwa sai ta bashi shawarar amfani da ita don ya cimma burinsa.
*** Jinyar sati guda Taj ya yi kafin ya farfaɗo sosai. Har ya faɗa kuwa. Abba yaje duba shi har gidan Ahmad. Kuma ya sami tarba ta mutumci daga gare shi. Wannan ya sake daɗaɗa ransa akan halin ƴaƴan Yaya Hayatu. Da zai tafi ne Taj ya yi masa maganar Hamdi.
"Abba don Allah ina neman alfarma a gareka."
"Indai zan iya in sha Allahu zan maka."
"Maganar rabani da Hamdi. Don Allah ka cire komai a ranka ka bimu da addu'a."
"Innalillahi..." Abba ya riƙe kai "faɗa maka tayi? Ban san Hamdi da surutu ba wallahi."
Taj ya yi murmushi "ba ita ta faɗa min ba." Ya tuna maganar da Salwa tayi ya ce "Yaya Ahmad ne ya faɗa. Amma ya ce kada na damu in sha Allah su Inna ba za su bari ba."
"Lamari na iyaye..."
"Allah bai bawa iyayenmu damar kashe mana aure ba. Musamman idan raba auren cutarwa ne ba hanyar samun maslaha ba."
"Ina jiye maka yawan saɓanin da kuke samu dashi. Hakan ba zai haifar da alkairi ba."
"Abba ina ƙoƙarin tsayuwa akan iyakar addini kan abin da ya shafi Alhaji. Duka abubuwan da yake fushu dani a kai shi yake nuna amincewarsa sannan ya zargeni da rashin kyautawa."
Shi dai Abba gani ya yi zai shiga tsaka mai wuya. Ya yi ta nunawa Taj illar dake tattare da zama cikin fushin iyaye.
"Don Allah ka nemi sulhu dashi kafin lokaci ya ƙure."
Muryar Taj a raunane ya ce "na jima ina wannan amma yaƙi bani dama. Zan cigaba da ƙoƙari amma Abba kada ka kuma sako aurena a ciki don Allah."
Tausayi ya bawa Abban "na daina. Allah Ya kiyaye mana ɓacin rana."
"A sunnar Annabi SAW? Inaaa, Abba ai sai dai lada."
Nauyi Abba ya fara ji tun kafin Taj ɗin ya je inda bai dace ba ya ce "naga ka fara jin sauƙi. Bari na tashi."
Taj ya dinga dariya kamar ba shi ne yake kwance kafin zuwan Abban ba.
***
Inna tana falonta ana yi mata kitso aka yi mata waya. Baƙuwar lamba ta gani. Ta ɗauka da sallama su ka gaisa da matar da ta kira.
"Na san ba ki gane ni ba tunda bamu zauna tare ba. Mahaifiyar Ahmad ce. Ahmad babban ɗa namiji wajen Alh. Hayatu nake nufi."
Murmushi Inna tayi. Wannan ƙalau take kuwa? A take ta cire wayar daga kunnenta ta karanto Ayatul Kursiyyu. Ɗabi'arta ce haka. Duk abin da bata gamsu dashi ba koda bata aka yi sai ta tofe shi da Ayatul Kursiyyu kafin tayi amfani dashi. Yadda Mami ta gabatar da kanta sam bai yi mata ba.
Sai da ta gama sannan su ka gaisa da ita.
"Dama naji shiru ne ina ta sa rai da wayarki amma baki kira ba. Nace bari ni na neme ki naji me ake ciki."
"Wace magana kenan?" Tashi tayi daga wurin kitson ta koma ɗaki.
"Auren Taj da Salwa. Alhaji ya ce baya son a wuce wata guda. Naga har an cinye sati."
Azkar ɗin tunkarar shugaban da kake tsoron cutarwa daga gare shi Inna ta karanto wannan karon kafin tayi magana.
(Allahummak finihin bima shi'ta)
"Wane Taj ɗin wai? Nawa dai sati biyu kenan da aurensa. Bani kuma da labarin zai ƙara wani."
Mami tayi kwafa a hankali tana raya duk za su zo hannu ne. Da ta san haka za ta yi mata tun farko ma da ta karɓo laya.
"To ki tambayi maigidan naki. Sai mu yi magana daga nan."
Inna ce ta fara kashe wayar. Ta dinga karanto addu'o'i. Me yasa duk wata rigimar gidan akan Taj take kunno kai? Istigfari tayi da sauri sannan ta fita ta tafi ɓangaren Alhajin. Dama yana gida. Girkin Umma ne. Inna tayi sallama ta shiga falon bayan Umma ta amsa ta iske shi yana cin abinci.
"Alhaji me nake ji daga bakin tsohuwar matarka?"
Karo na biyu kenan da Inna tayi masa magana babu kyautata kafazi. Yana namiji sai da yaji wanibabu a ransa. Maganar Hajiya na neman tabbata da ta ce masa kada ya ƙure haƙurin Abu don mai haƙuri bai iya fushi ba.
"Wani abin ne ya faru?" Ya tambayeta kamar bai sani ba.
"Ka fini sani Alhaji. To amma ina so ka sani ka gama yi min hawan karkatacciyar kuka. Wannan juya min yaro da kake yi ya isa haka."
"Haba Inna. In ranki ya ɓaci kada ki bari hankalinki ya gushe mana. Da mijinki fa kike magana." Umma ta ankarar da ita don muryarta tashi take sosai.
"Me ya rage min? Yau ko agola ne Tajuddin ai iyakar abin da mijin uwa da baya sonsa zai yi masa kenan. Wai ni matar nan za ta kira ta ce ya maganar auren Taj da Salwa?"
"Me?" Umma ma ta ɗaga murya ba tare da tunani ba.