Taimiyah book complete document by ayshat dansabo lemu txt by hausanovels com - Chapter 40
Taimiyah book complete document by ayshat dansabo lemu txt by hausanovels com Chapter 40: Taimiyah book complete document by ayshat dansabo lemu txt by…
4,449 words
Dukkanin ƴan matan Amaryan sai kabbara suke yi,lokacin da idanunsu ya sauka akan Amarya TAIMIYYAH. Sabida yadda suka ga tayi musu mugun kyau,har suna kasa ɗauke idanunsu daga ƙare mata kallo,Maryam Sunusi ta buɗe baki ta ce, "Fatabarakallahu ahsanulkhaliqin! Allah kai ne abin kambamawa da ka ƙagi wannan kyakykyawar halitta. Allah ka albarkace ta tare da aurenta,ka bata zama lafiya da nutsuwa a cikin gidan aurenta. Ya Ubangiji ka kunyata maƙiyanta ka bata zuriya masu albarka,Congratulation my best friend ever, may urs be among the best In sha Allah TAIMIYYAH."
Su Yasmeen dukansu suka haɗa baki wajen amsa addu'ar da Maryam tayi da cewa, "Ameen ya Hayyu ya Qayyum."
TAIMIYYAH ta ɗaga manyan idanunta ta sauke akan Maryam Sunusi,cike da jin daɗin kyakykyawar addu'ar da Maryam ɗin ta yi mata ta ce, "Ameen Maryama na gode,ku ma Allah ya yi muku zaɓi mafi alkhairy nan kurkusa."
Suka sake amsawa da faɗin, "Ameen." Yasmeen ta matso kusa da TAIMIYYAH ta sake sakin ƙaramin guɗa tana cewa, "Finally yau kin xama Mrs.Maleek Ado."
TAIMIYYAH ta saki ƙayataccen murmushi,sai dai kafin ta yi magana wayarta da ke hannun Anty Laurat,wacce ke faman kashe mata hotuna ya ɗauki ringing. Ta ta so da sauri tana miƙawa TAIMIYYAH wayar ta ce, "Mrs.Maleek ungo Angon ne da kansa ke kira."
TAIMIYYAH ta amsa wayar zuciyarta na bugawa da wani irin yanayi da ba za ta iya fassarawa ba. Ta yi receving call ɗin tare da kai wayar bisa kunni,murya can ƙasa ta yi masa sallama. Maleek Ado daga ɓangarensa ya amsa sallamar sannan ya ce, "Mrs.Maleek Ado!"
TAIMIYYAH ta lumshe idanunta tana jin wani irin abu na malting a cikin zuciyarta,yadda ya furta kalmar ba ƙaramin tasiri ya yi a zuciyarta ba.Ta buɗe idanunta ta sauke akan su Yasmeen da ke faman hiransu babu tsagaitawa,sai ta miƙe a hankali ta dafe guiwar ƙafarta ta fara takawa don barin musu ɗakin. Suka bi ta da ido rii...! Kowacce murmushi na blushing a samar fuskarta,ita ko TAIMIYYAH direct ɗaya bedroom ɗin Ummie ta nufa,in da ta ke zaton ba za ta ga kowa ba don bama kasafai ta ke buɗe ɗakin ba.
Kamar yadda ta zatan kuwa haka ya kasance babu kowa cikin ɗakin,amma a gyare ya ke sai tashin qamshin daddaɗan turaran wuta ke tashi. TAIMIYYAH ta samu bakin gado ta zauna,tana sake dafe wayar akan kunninta ta ce, "Hello!" Maleek da ya yi shiru yana sauraren takun tafiyarta tun fitowarta daga ɗakin da suke,ya saki ƙaramin numfashi ya ce, "Wife ina jin ki,kin gudu ma qawayen na ki ne sabida ke ma kina son ganin fuskar Angon ki ko?"
Bai jiran amsar da TAIMIYYAH za ta bashi ba ya yi cuting call ɗin,ya kirata vid call don dama a ƙagauce ya ke da ya ga kyakykyawar fuskarta. Ya fara kiran voice call ne sabida sanin cewa dole tana cikin mutane,amma yanzu tunda ta kaucewa mutanen dole ya kira vid call don baiwa zuciyarsa abinda ta ke so.
TAIMIYYAH ta kalli kanta kafin ta ɗaga vid call ɗin,cike da jin kunyan yadda karon farko Maleek ɗin zai fara ɗaura idanunsa akanta babu lulluɓi. Sai ta samu kanta da kasa duban fuskarsa lokacin da ta tabbatar nata fuskar, zuwa gangar jikinta ya gama bayyana a allon screen ɗin wayarsa.
Maleek Ado kuwa lokacin da fuskar TAIMIYYAH da kwalliyarta ya bayyana garesa,sai da ya ja wani dogon numfashi ya sauke,zuciyarsa na amsawa da wani baƙon yanayi da ke ratsa har ɓargonsa. Ya sake ware manyan idanunsa akan ƙirjin TAIMIYYAH,yana me saurin rintse idanunsa ya sake buɗe su akan muhallin da ya ɗaurasu akai tun farko. Cikin wata iriyar kasalalliyar murya ya kirayi sunanta 'Zaynabbb!' TAIMIYYAH ta yi saurin ɗago fuskarta jin yadda ya kira yi sunanta very low,idanunta ya sauka akan kyakykyawar fuskarsa zuwa gangar jikinsa,da ke sanye cikin dakakkiyar farar shadda mafi tsada da nauyin kuɗin. Ɗinkin ya yi masa kyau duk da cewa ya cire babbar rigar da hula,sai ƴan cikin ne kawai sanye a jikinsa,a mota ya ke zaune ya kwantar da seat ɗin baya sosai yadda zai ji daɗin yin wayan. TAIMIYYAH ta ɗauke idanunta daga dubansa tana jin wani irin matsanancin ƙaunarsa na sake malting a zuciyarta,don babu ƙarya ya yi mata mugun kyau irin wanda bata taɓa gani ba,sai ta alaƙanta hakan da yadda fuskarsa ta ke a sake ne a yau ɗin.
Cikin muryar shagwaɓa ta ce, "Ina yini ya taro,Allah ya tabbatar mana da alkhairy ya bamu zama lafiya."
Maleek da idanunsa ke kan TAIMIYYAH ya kasa ɗaukewa,ya buɗe baki cikin muryar da ta fi waccar yin sanyi ya ce, "Ameen wife, i luv u so very much don Allah ki riƙeni da amana babe!"
Jikin TAIMIYYAH sai ya yi wani irin sanyi da jin kalaman Maleek Ado,ta sake ɗaura manyan idanunta akan fuskarsa,tana kallon yadda ya ƙurawa waje ɗaya a jikinta ido. Wani haɗaɗɗan kunya ya taso ya lulluɓe zuciyarta,cikin sauri ta furta, "Yah Maleek don Allah minti biyu zan ɗan ɗakko mayafi."
Wani kallo Maleek Ado ya watso mata ta cikin wayar,kafin ya buɗe baki kaman me son yin raɗa ya ce, "No wife! Kar ki fara kashe min waya,yau ba zancen sanya mayafi kin zama mallakina halak malak! Please kar ki ce za ki haramta min kallon halas ɗina."
Ya ƙare maganar yana sake gyara kwanciyar da ya yi a jikin seat ɗin lafiyayyiyar motarsa.TAIMIYYAH da kunya ke ɗawainiya da ita sai ta sake narke murya ta ce, "To mu yi voice call please Yah Maleek,wallahi kunyanka na ke ji."
Maleek Ado ya saki wani ƙayataccen murshi kafin ya ce, "No wife! Ki bani 20 minutes gani nan tafe zuwa gidanku,idan na iso zan kiraki ki fito ki sameni a mota,but u make sure idan za ki fito kin rufe min wannan kwalliyar da Hijab,and bana son ɗaukar wasu hotuna ana yawo da ke a media,shiyasa ni ma bazan shigo ba bare a yi wasu hotuna da aka maida ɗaukarsu fashion,please tell ur friends su taimakeni kar su ba za ki a duniya ana kallemin sirrikana please!"
Yadda Maleek ya kai ƙarshen maganar cike da nuna magiya da zallar kishin da ke cin zuciyarsa, yasa TAIMIYYAH dubansa tana sake jin kunyarsa me tsanani na lulluɓeta.Cikin shagwaɓaɓɓiyar muryarta da ke sake kunna wutar fitina a zuciyar Maleek ta ce, "Zan gaya musu Yah Maleek sai ka iso ɗin." Daga haka ta yi saurin cuting call ɗin tana sauke numfashi,zuciyarta na sake cika da ƙaunarsa me tsanani.
Ɗakin da su Yasmeen suke TAIMIYYAH ta koma,suka ko rufar mata da tsiyar cewa ta gudu sun sha luv da oga Maleek kenan. TAIMIYYAH ta narke musu da shagwaɓa tana kare kanta,ana cikin haka wata Cousine ɗinsu ƴar Rimi ta shigo ɗakin. Ta dubi TAIMIYYAH tana yaba kyawun da tayi ta ce, "Ma sha Allah! Amarya kin sha kyau ki zo Iyah na nemanki yanzu."
TAIMIYYAH ta dubi Nusaiba ta ce, "Okey jira ni mu fita tare don ni kunyar shiga jama'a na ke yi,ina fata dai zuwa yanzu duk mazan da suka dawo ɗaura aure sun watse?"
Nusaiba ta saki murmushi ta ce, "Kai Yah TAIMIYYAH kin cika kunya wallahi,sun watse kam babu wasu maza a wajen tunda Baba Sani ba zama a gidan zai yi ba,ya tafi can hotel da mutanensa don su bar mata su sake a cikin gida."
TAIMIYYAH ta jinjina kai cike da gamsuwa sannan ta dubi Yasmeen ta ce, "Sis zo mu je daga can za ki rakani wani waje."
Yasmeen ta miƙe tana gyara zaman ɗaurinta na ashobin da suka cakare a cikinsa,atamfar kuma ta yi musu mugun kyau dukansu ƙawayen Amaren. Ta bi bayan TAIMIYYAH da suka rigata yin gaba,tana ɗaga murya ta cewa Anty Laurat, "Anty Laurat don Allah ga wayata nan a caji kusa da ke,idan ya cika ki cire min please."
Daga haka ta yi gaba Anty Laurat na amsa mata da cewa, "Tuh shikenan an gama Sis."
Suka cigaba da hiransu da su Zee da su Bushirah,don su kenan ƙawayen na TAIMIYYAH,sabida ita ba mai yawan ƙawaye bace tun farko.
__________
Daga can sasan Baba Sani kuwa shirin tafiya da Amarya Zuhurah Bauchi ake yi,don dama haka aka tsara ana kammala ɗaura aure za a wuce da ita. Ita da Angon da mutane huɗu ne aka biyawa kuɗin jirgi,sai sauran mutane za su bi dogayen motocin da aka zo ɗaura aure da su don kwasan ƴan rakiyar Amaryar.
Amarya Zuhurah da ta sha kyau ita ma cikin kayan da ta sanya,sai faman kuka ta ke yi lokacin da suke sallama da Ummanta. Wacce kallo ɗaya za kai wa Umman kasan cewa akwai manyan damuwoyi kwance a ƙasan zuciyarta. Ta dubi Zuhurah lokacin da wata ƙanwar su Baba Sani da suke ƴaƴa maza da ita,ta kama hannun Zuhuran ta miƙar daga gabanta ta ce, "Zuhurah Allah ya bada sa a,Ubangiji yasa ki shiga gidanki cikin nasara,ki kula da dukkanin huɗubobin da mu kai miki,sannan kar ki yi sake ba ki yi anfani da waɗannan saƙon kamar yadda aka sanar miki ba, Allah ya yi miki albarka ƴata."
Zuhurah dai ba baki sai kuka da ta ke sha kamar za ta shiɗe,bata taɓa tunanin wannan ranar za ta zo ta kasa jin ɗokin barin gida ba,sai gashi tun da aka ce an ɗaura auren hankalinta ya ke a tashe,tana ji a zuciyarta sam bata son barin gidan,wani irin fargaba ke danne zuciyarta wanda ta kasa gane dalilin jin hakan da take yi. Ita ko Amarya Basmah kuwa tunda su sai yamma can za a miƙa su ɗakunansu,sai sabgarta ta ke yi cikin shaƙiƙan ƙawayenta su Amna da Sharifa. Ko kaɗan bata jin fargaban komi a ranta,sai ma ɗokin son a kai ta gidan Nass ɗin su zama abu ɗaya ita da shi,don ita haushin Zuhurah ta dinga ji da ta ke wani faman rusa kuka, kamar wacce za a kai gidan maƙiyinta ba Ameerunta da take ta rawar ƙafa akansa ba.
Aka fito da Zuhurah daga Sasansu aka nufi Sasan Iyah da ita don yin sallama da ita,suna isa Sasan Iyah ne bada jimawa ba TAIMIYYAH suka shigo don amsa kiran Iyah. Ashe dama Iyan ta aika akira TAIMIYYAH ne don ta haɗasu su duka ukun ta yi musu faɗa da nasiha duk gaba ɗaya,don ita ma Basmah an je kiranta ta zo a haɗasu ai musu faɗan tare.
Zuhurah ta zurawa TAIMIYYAH ido lokacin da suka samu waje suka zauna kusa da Iyah,wani irin kyau ta ga TAIMIYYAH ta yi mata irin wanda bata taɓa gani ba.
TAIMIYYAH ko hankalinta na kan Iyah da su Hajiya Rabi aminanta,ta ɗaga ido ta dubi Iyah ta ce, "Iyah gani Nusaiba ta ce in zo kina nema na."
Iyah ta dubi TAIMIYYAH da murmushi a samar fuskarta ta ce, "Eh! Zauna nan ku jira Basmah ta zo,faɗan bankwana za a haɗa ku ai muku. Kin yi kyau Zainabu na Ubangiji ya sanya alkhairy,ya baku zama lafiya a gidajen mazajenku."
Sauran mutanen da ke cikin ɗakin suka amsa da cewa "Ameen." Guggo Bilki da ke zaune daga can ƙarshen gadon Iyah ta ɗago kanta ta dubi TAIMIYYAH ta ce, "Zainab kin ko gaisa da su Yayanki Anas,sun shigo nan suna tambayar ina ki ke na ce su je can Sasan Ummie,sun je ɗin ko wucewarsu su ka yi?"
TAIMIYYAH ta girgiza kai ta ce, "Aiko dai wucewansu suka yi Guggo Bilki,don ko mai kama da su ban gani ba wallahi."
"To ai sun kyauta,sa dawo ganin gida wataran ai." Cewan Guggo Bilki daidai lokacin kuma Basmah suka shigo cikin ɗakin Iyah. Aka haɗu aka fara musu faɗa da nasiha akan muhimmancin haƙury a zaman aure,TAIMIYYAH tuni idanunta suka raina fata,zuciyarta ta karye ta fara kuka me motsa zuciya. Gaba ɗaya ji ta yi tamkar a ɗaga auren a ce anfasa sai zuwa gaba,amma ta san hakan ba mai yiwuwa bane,sosai Iyah da su Guggo Bilki su kai musu nasihu masu ratsa jikin duk wani me hankali da nutsuwa. Basmah kaɗai ce zan iya cewa bata girgiza ba amma hatta Zuhurah sai da jikinta ya sake yin sanyi,zuciyarta ta karye ta cigaba da jin lamari me girma na dabaibaye zuciyarta.
Yasmeen ce ta riƙo TAIMIYYAH zuwa jikinta tana rarrashi,sabida yadda ta ke kuka me asalin motsa zuciya,kwalliyar fuskarta tuni har ya fara ɓaci.
Zuhurah ta isa gaban Iyah bayan an kammala yi musu nasihan,cikin muryar kuka ta ce da Iyah, "Iyah ki yafe min duk laifin da na taɓa yi miki don Allah."
Iyah ta dafe kanta ta ce, "Na yafe miki Zuhurah,Allah ya sanya albarka ya baku zama lafiya,ki kula sosai ki aje duk wasu huɗuba da akai miki na banza,ki kama Allah kaɗai tare da yin biyayyar aure kamar yadda addini ya shinfiɗa,Allah ya kai ku lafiya yasa ki shiga a sa a."
Daga haka aka janye Zuhurah daga gaban Iyah za a fita da ita,amma sai ta zame hannunta ta isa wajen da Yasmeen ke zaune tare da TAIMIYYAH da ke faman kuka har lokacin. Zuhurah ta tsugunna tare da kamo hannun TAIMIYYAH ta riƙe,cikin muryar kuka ta ce, "TAIMIYYAH za a tafi dani,ina roƙon ki yafe min duk wani abu da na taɓa yi miki mara kyau,sannan ina mana fatan alkhairy baki ɗayan mu."
TAIMIYYAH jin muryar Zuhurah daf da ita yasa ta buɗe idanunta da suka fara rinewa ta ɗaura akan fuskar Zuhurah,ganin yadda hawaye ke gudu akan fuskar Zuhurah da yadda ta yi laushi kamar ba ita ba,sai kawai TAIMIYYAH ta rungumeta tana magana cikin muryar kuka ta ce, "Zuhurah in ma kin ɓata min wallahi na yafe miki,ban taɓa riƙe ku a raina ba dama. Allah ya kai ku lafiya ya baki zama lafiya Ameen."
Daga haka suka saki juna kowanne a cikinsu na jin wani irin lamari me girma a cikin zuciyarsa,kowa a ɗakin sai da ya share hawayen tausayinsu.
Guggo Bilki ce ta ce da Yasmeen ta kama hannun TAIMIYYAH su koma Sasan Ummie, a gyara mata kwalliyar da ya ɓaci tunda su sai zuwa yamma za a kai su ɗakunansu ita da Basmah. Yasmeen ta miƙe tana riƙe da hannun TAIMIYYAH na dama,ita kuma TAIMIYYAH na dafe da guiwar ƙafarta da hannun hagu,suka fara takawa suna ratsowa cikin falon Iyah har suka fito daga cikin Sasan baki ɗaya.
Wayar TAIMIYYAH ne ya shiga ringing a hannun a Yasmeen,hakan yasa ta dakata da tafiyar ta dubi fuskar wayar don ganin me kiran. Idanunta ya sauka akan sunan My Maleek kamar yadda TAIMIYYAH ta yi saving.Ta saki murmushi tana maida dubanta kan TAIMIYYAH wacce ke ta faman sauke ajiyar zuciya,ta yi mata signa da ido tana nuna mata fuskar wayar ta ce, "Babyn Maleek don Allah ki bar kukan nan haka,kin ga Angonki ne ke kiran ki ungo wayar ki amsa call ɗin."
Yasmeen ta yi maganar tana miƙawa TAIMIYYAH wayarta da har lokacin ya ke kukan neman ɗauki, TAIMIYYAH ta amsa wayar tana danna receive ta kai kunni. Muryar Maleek ya shiga kunnuwanta lokacin da ya ce, "Wife gani na iso ina waje,za ki ga wata black ɗin mota daga gaban gidan kaɗan."
TAIMIYYAH ta jinjina kai kamar yana gabanta,sannan ta yi magana cikin sanyin murya sosai ta ce, "Okey gani nan zuwa In sha Allah." Daga haka ta yi cuting call ɗin tana maida idanunta akan Yasmeen ta ce, "Yasmeen wai ya zo ne yana waje,mu je a gyara fuskar sai ki rakani don ba zan iya zuwa ni kaɗai ba."
Yasmeen ta saki murmushi cike da tsokana ta ce, "Wow! Ki ce Ango ya zo ganawa da Amaryarsa, amma shi ne ya ƙi yadda ya zo a ɗauki pics bayan ɗaura aure, gaskiya wannan Angon na ki ajinsa har ya ɓaci,oya mu je a gyara wannan fuskar ta ki da kika jiƙe da hawayen gulma."
TAIMIYYAH ta wurgawa Yasmeen harara,hawaye suka sake zubo mata cike da shagwaɓa ta ce, "Yasmeen ni ce ke hawayen gulmar ma? Oya mu je kawai kafin ki sake sani a damuwa."
Daga haka suka jera da juna zuwa Sasan Ummie,bayan an gyarawa TAIMIYYAH fuskarta ne ta samu babban mayafi ta naɗe jikinta da shi. Duk yadda ta motsa wani fitinannan ƙamshine ke ratsa ko'ina a jikinta,ta zurah flat shoe a ƙafarta tana duban Yasmeen da fuskar shagwaɓa ta ce, "Yasmeen mu je please kin ga yana sake kira."
TAIMIYYAH ta yi maganar lokacin da kiran Maleek Ado ke sake shigowa wayarta,hakan yasa Yasmeen ɗaukar wayarta suka fito don yiwa TAIMIYYAH rakiya zuwa wajen Maleek Ado.
Sun fito harabar compound ɗin dai dai lokacin da ake fitowa da Zuhurah daga Sasan su, za a shiga mota don zuwa Kano su hau jirgi su wuce Bauchi,waɗanda za su bi mota irin su Anty Laurat su sun wuce tun ɗaxu.
"Yasmeen shikenan Zuhurah za a wuce,ba ki ji yadda jikina ke sake yin sanyi ba,ina jin tausayinmu mu duka don bamu san wace irin rayuwa za mu je mu taras a gidan auren ba,wallahi ji na ke yi tamkar a fasa auren a bar ni tare da Iyah ta."
Yasmeen ta saki dariya ta ce, "To sannunki sarkin wauta,don Allah ni mu je in kai ki in yi dawowata cikin gida,ni fa wallahi duk wannan kukan da wani roƙon yafiyar da Zuhurah ta dinga yi,sam bata bani tausayi ba don baka saurin sallamawa maƙiyinka,watakili wani salon munafurcin ne kawai aka shirya mata,ita ƙaramar mara kunyar baki ga ko gezau bata yi ba? Wallahi ina tausayin Basmah don rawar kan yarinyar da fitsaranta ya yi yawa,amma In sha Allah xa a gyare mata zama tsaf,ta dai shiga gidan za ta gane Allah ɗaya ne."
Yasmeen tana maganar ne suna takawa a hankali don fita daga gate ɗin gidan,ita dai TAIMIYYAH jin Yasmeen kawai ta ke yi bata iya cewa komi ba,don bata san ma me za ta ce ɗin ba,amma har cikin zuciyarta ta ji tausayin Zuhurah,domin ita tana son su a ranta don gani ta ke yi bata da tamkar su,tunda su ne dai za ta nuna a ko'ina a matsayin ƴan uwanta na jini da iyayensu suka fito ciki guda.
Lokacin da suka ƙarisa fitowa wajen gate ɗin ne, TAIMIYYAH ta shiga wurga ido don gano inda Maleek ya parker motarsa. Idanunta ya hango mata wata danƙareriyar baƙar mota daga gaban gidan kaɗan,kamar yadda ya kwatanta mata,sai ta dubi Yasmeen ta ce, "Yasmeen ina ga waccar motar ce ya ke nufi,don ya ce daga gaban gidannan kaɗan ya yi parking."
Yasmeen ta jinjina kai suna cigaba da takawa zuwa wajen motar. Maleek da tun da suka doso ya ke ƙare musu kallo ta cikin madubin motar,sai ya samu kansa da kasa ɗauke ido akan TAIMIYYAH,wacce tun daga nesa ya ke sake hango irin kyawun da ta yi,sai ya raina mayafin da ta sanyo domin irin Chantly ɗinnan ne me shara-shara. Ya ɗan lumshe idanunsa ya buɗe akansu lokacin da suka ƙariso bakin motar. TAIMIYYAH ta jingina jikinta da jikin motar,ta bar Yasmeen da ƙarisawa bakin driver seat ta yi knocking. Maleek ya sauke tint ɗin glass ɗin motar ya leƙo da kansa yana cewa, "Sis har kun iso? Ce wa wife ta zagayo front seat ta shigo please!"
Yasmeen ta jinjina kai tana komawa wajen da TAIMIYYAH ke tsaye daga baya ta ce, "Amarya Angonki na buƙatar ki ƙarisa daga front seat ki shiga."
TAIMIYYAH ta ɗan shagwaɓe fuska ta ce, "Okey mu je." Yasmeen ta balla mata harara ta ce, "Mu je ko ki je,kin dai ji Yarinya da rainin hankali,in je ina? Ni muna gaisawa yanzu zan juya idan kun gama kya kira ni in fito,idan kuma ya yo miki rakiya har gida kin ga an hutar dani."
Daga haka Yasmeen bata sake cewa komi ba, ta juya zuwa wajen Maleek suka gaisa ta yi masa fatan alkhairy ta juyo don komawa cikin gida, ta bar TAIMIYYAH na zagayawa za ta shiga front seat ɗin,in da har Maleek ya riga ya buɗe mata murfin motar.......✍🏻
#Ɗansabo ce# [12/14, 10:14 PM] +234 703 769 7050: Littafin TAIMIYYAH paid book ne,ga duk wanda ta tsincesa a kowani irin group ne,kiji tsoran Allah karki karanta sai kin biya 500 naira only.
Za ku iya min magana ta wannan number ɗin 08167768704, ko kuma ku turo kuɗin ku kai tsaye ta wannan account ɗin 0504192664 aisha ibrahim dansabo GTbank.*
*Sai ku tura shaidan biyanku ta wannan line ɗin 08167768704.*
Masu turo credit za ku turo katin MTN na 500 ta wannan line ɗin 08167768704.
_Ina ƴan kasuwa masu buƙatar a tallata muku hajar ku? Maza ku garzayo da kuɗi ƙalilan a tallata muku kayan siyarwanku sai dai kawai ku ji ana kiran waya don buƙatan sayan kayan ku,ku tuntuɓeni ta layina kamar haka 08167768704._
*67*
A hankali TAIMIYYAH ta zura jikinta cikin motar tana me barin murfin motar a buɗe,ƙafarta ɗaya me lafiyan na daga waje sai ɗayar kawai ta aje daga cikin motar. Ta ɗaga manyan idanunta ta dubi fuskar Maleek Ado,wanda ke binta da wani irin mayataccen kallo kai ka ce bai taɓa ganinta bane sai a yau ɗin. TAIMIYYAH sai ta sake narke fuska cike da shagwaɓa ta fara gaida shi,memakon ya amsa gaisuwar sai cewa ya yi, "Wife ki shigo sosai ki rufe min murfin motar,magana kawai za mu yi in wuce ba wai cinyeki na zo yi ba."
Yadda ya ke maganar murya can ƙasa da yadda ya miskile fuska,ya sanya TAIMIYYAH bin umurninsa ta maido ƙafarta ɗaya cikin motar tare da rufo ƙofar motar baki ɗaya. Zuciyarta sai faman bugu ta ke yi tana jin ta very uncomfortable ,sabida irin kallon da Maleek ya tsareta da shi.Ta kai dubanta garesa sau ɗaya tana saurin yin ƙasa da kanta,ta fara wasa da yatsun hannunta da suka sha jan lalli da ya yi wani irin maroon. Kamar a mafarki ta ji hannuwan Maleek Ado akan jikinta,hakan yasa ta yi saurin ɗago manyan idanunta ta sauke akan fuskarsa,lokacin da ya ke warware gyalen da ta yane jikinta da shi ya sauke shi zuwa ƙasa.
Jikinta TAIMIYYAH sai ya ɗauki rawa,zuciyarta na wani irin harbawa da matsanancin fargaba,cikin rawar murya cike da shagwaɓa ta ce, "Yah Maleek a waje fa mu ke,don Allah ka bari kada wasu su zo wucewa su gan mu please!"
Yadda TAIMIYYAH ta yi maganar tamkar za ta rushe masa da kuka, ba ƙaramin motsa zuciyar Maleek Ado ya yi ba. Ya sake kafa mata mayun idanunsa yana cewa, "Wife ai babu me ganin mu,dukkanin gilasan motar tint ne ai so u have to be comfortable kina tare da mijinki ne yanxu ba wai saurayi ba okey."
TAIMIYYAH sai ta zura masa ido tana sake ɓata fuska,ƙirjinta har lokacin harbawa ya ke yi da wani irin tsoro me tsanani, ga ƙamshin turarensa da sanyin AC ɗin da ya gama buɗe motar,na sake haifar mata da wani irin yanayi mara misaltuwa. Ba ta iya cewa komi ba illah yin ƙasa da kanta da ta yi,tana ji tamkar ta sakin masa kuka ko zai ɗauke idanunsa daga mayen kallon da ya ke bin jikinta da shi.
"Wife kin yi kyau sosai,irin kyawun da ban taɓa gani akan ko wace mace ba,na gode Allah da ya mallaka min ke amatsayin halalina,ɗago ki kalle ni babe please cox ina son ganin waɗannan idanun cikin nawa."
Maleek Ado ya yi maganar da wani irin salon murya,da ya sanya TAIMIYYAH saurin ɗaga manyan idanunta ta sauke akan fuskarsa,cikin sa a idanunta suka shige cikin na Maleek ɗin. Ta ke sai wani irin maganaɗisu ya yi aikinsa zukatansu suka buga a lokaci guda,kamar yadda kowannensu wani abu ya tsirga masa tun daga yatsun ƙafarsu zuwa zuciya da gangar jikinsu baki ɗaya.
TAIMIYYAH za ta ɗauke fuskarta daga dubansa,amma sai Maleek ya yi saurin miƙa hannu ya riƙo fuskarta a tafukan hannunsa,cikin wani irin kasalalliyar murya ya ce, "No wife please! Ki barni na morewa kallon waɗannan idanun masu tasiri akaina."
Sai TAIMIYYAH ta maida ƙwayar idanun ta lumshe su,wani irin abu na gudu a cikin jini da tsokar jikinta. Zuciyarta ta cigaba da harbawa da gudun gaske,kamar yadda wani abu ke zagaye jikinta tana jin wani yamm...! A ilahirin jikinta. Bata kuma shiga ruɗu ba sai lokacin da ta ji fuskar Maleek Ado akan tata fuskar,yana me haɗe fuskarsu waje guda,tare da ɗaura bakinsa akan nata goshinsu na mannuwa da juna. TAIMIYYAH bata san lokacin da bakinta ya suɓuce ya furta kalmar 'Hasbunallah!' jikinta ya cigaba da ɗaukar wani irin rawa. Shi ko Maleek Ado ko ajikinsa bai ma san tana yi ba,burinsa kawai ya bata kiss ya ji irin ɗanɗanon da ke kan harshenta.
Ya miƙa hannuwansa duka ya riƙo TAIMIYYAH zuwa jikinsa ya rungumeta,ta ke ta sakin masa kuka jikinta na cigaba da ɗaukar rawa,cikin rawar murya ta ce, "Please Yah Maleek don Allah ka yi haƙury!"
Maleek da maganarta ya bashi dariya sai ya sake mannata da jikinsa sosai,yana me raba fuskarsa da tata amma idanunsa na kan yadda TAIMIYYAH ta rintse nata idanun ya ce, "Baki min laifi ba wife, so ki daina bani haƙury kawai ina son jin ɗumin jikin matata ce,ki daina wannan rawar jikin baby babu abinda zan miki da ya wuce inyi kissing ɗinki,just kiss kawai kin ji babe?"
Yana maganar ne yana sake ƙoƙarin haɗe fuskarsu waje guda,TAIMIYYAH ta sakar masa kuka jinkinta na kuma ɗaukar rawa.Wannan shi ne karo na biyu da ta ji ta rungume a jikin namiji,tun bayan karon ta da Yah Deeku a wancan lokacin,amma yadda ta ke ji a yanzu bata ji irinsa a wancan lokacin ba sam. Maleek Ado ya ɗaura bakinsa akan nata yana aika mata da wasu zafafan kiss,so ya ke yi ya zura harshensa cikin bakinta amma ta datse ta hana shi daman hakan.Dukkanin jikinta rawa ya ke yi don lamari ne da bata kawo faruwarsa nan kusa haka ba,ta buɗe baki za ta yi magiya amma sai Maleek ya yi anfani da wannan daman wajen zura harshensa cikin bakinta. Wani abu ya doka a tsakar kan TAIMIYYAH lokacin da ta fara amsan wani irin hot kiss daga Maleek Ado,wanda ke tsotsar harshenta cikin zalama tamkar wanda ya cafki wata alawa me tsananin zaƙi. TAIMIYYAH ta dinga mutsu-mutsun son kwace jikinta amma ta kasa,don wani irin runguma ya yi mata yadda ba za ta iya kwace jikinta ba. Ko kaɗan bai saurara mata ba sai da ya tsotsi bakinta son ransa,sannan ya zare harshensa daga bakinta yana duban yadda hawaye ke gudu akan kyakykyawar fuskar TAIMIYYAH. Wacce ta rintse idanunta tamau ta ƙi buɗewa sabida ba za ta iya kallon idanunsa ba, bayan ya gama mata wannan abun kunyar.
Maleek Ado sai ya saki wani killer smile yana sake jin tamkar ana rura masa wutar fitina akan TAIMIYYAH ne, ya miƙa hannunsa ya fara share mata hawayen da ke sakkowa daga idanunta. Cikin muryarsa da ya sauya sosai ya ce, "Sorry wife na gama,ba zan sake miki komi ba sai zuwa anjima idan an kai min ke ko? So please its okey kukan ya isa haka wife."