Taimiyah book complete document by ayshat dansabo lemu txt by hausanovels com - Chapter 9
Taimiyah book complete document by ayshat dansabo lemu txt by hausanovels com Chapter 9: Taimiyah book complete document by ayshat dansabo lemu txt by…
4,253 words
_______Da sallama Anty Laurat ta shiga Sasan Iya,wacce suke zaune daga waje saman lallausan Carpet da takan shinfiɗa ta zauna tana bitan karatun Qur'ani duk kusan yamma,daga gefen Iyan Ladi ce zaune itama tana gyaran farce daga gefe guda,Iya da Ladin kusan a tare suka amsa sallaman Laurat ɗin,wacce ta ƙariso ta zube gaban Iya tana kwasan gaisuwa,Iya ta amsa da fara'a tana faɗin "Maraba da Lauratu saukan yaushe,ya mutanan can Yoben ina fata duk iyayen na ku nanan lafiya ko?"
Laurat tayi murmushi tana faɗin "Lafiya Iya duk sunce a gaida ku,wallahi jiya na zo naso shigowa sai dare yayi ga gajiyan zaman mota,shine sai yanzu nace bari in shigo in miƙo gaisuwa,ya TAIMIYYAH hala bata nan ne ?" Laurat ta ƙare maganan da tambayan Iya,Iya ta murmusa tana gyara zaman glass ɗin da take anfani dashi idan zatai karatu sabida ƙara ƙarfin gani,ta amsa da faɗin "Tana nan ta ƙule a ɗaki tana karatu hala ko ana faman danne-dannen waya da bakwa gajiya ku yara." Laurat ta saki murmushi tana faɗin "Allah sarki to bari in shiga daga ciki mu gaisa ankwana biyu ba'a haɗu ba."
"Hakane kam ƴarnan shiga ku gaisa ai kin kyauta da kika taho zumunci."
Cewan Iya tana bin bayan Laurat ɗin da kallo,wacce ta nufi ƙofan shiga falo,Iya na yaba nutsuwan Laurat ɗin da hankalinta,wacce har Iyan ke ji Laurat ɗin tafi kwanta mata arai ma akan Surukan nata Umma,da sallama Laurat ta shigo falon Iya tana sake ɗaga murya da kiran sunan TAIMIYYAH,ita ko TAIMIYYAH na can daga cikin ɗakinta tayi ɗai-ɗai suna kwasan Vid call da qanninta su Nahar,tana ta biye musu suna bata labarin Lagos da irin wajajen da ake kaisu na shaƙatawa duk Weekend,can sama-sama take ji kaman ana kiran sunanta hakan yasa tai sallama da su Nahar tana cewa zata kira su later,ta aje wayan tana miƙewa ta sauko daga Bed ɗin,tana sanye ne da wani gown me kyau na Material da akaima ɗinkin da ya amshi jikinta sosai,ta dafa ƙafanta tana takowa zuwa falo,idanunta ya sauka akan Laurat da ke zaune daga hannun kujera,ai da hanzari TAIMIYYAH ta ƙariso cikin falon,tana faɗin "Laaah! Anty Laurat ce yau a gari,sannu da zuwa saukan yaushe Anty?"
Laurat ta saki murmushi ta kasa ɗauke idanunta daga kan TAIMIYYAH,tana ganin yadda TAIMIYYAN tai wani girma kyawunta ya ninka na da,domin a ƙallah zai kai shekaru uku rabonta da ganinta,har TAIMIYYAH ta ƙariso kusa da ita idanunta na kanta,tana jinjina baiwa da ƙudiran ubangiji wanda ya ƙagi wannan kyakykyawan halitta,hannu ta miƙawa TAIMIYYAN suka cafke Laurat ɗin na faɗin "Wow! TAIMIYYAH haka kika koma wata Big Gal,kinga yadda kika sake zama wata haɗaɗɗiya ta musamman gaskiya ke ɗin matan manyace,Allah kaɗai yasan meyasa ya ɗan tauyeki kaɗan."
TAIMIYYAH ta saki murmushi tana faɗin "Anty kenan ina yini kin zo lafiya?"
Laurat ta amsa da "Lafiya lau Zaynab ya bayan rabuwa."
"Alhamdulillah! Anty sannu da zuwa,bari a kawo miki ruwa ko."
Cewan TAIMIYYAH tana yinƙurin miƙewa tsaye,Laurat tayi saurin dakatar da ita da faɗin "Wallahi zauna abinki bana jin ƙishi,tun jiya fa na shigo garin nanne bansamu shigowa ba sai yanzu,ya karatu ana ta strike kuma Allah dai ya kawo ƙarshensa,ko da yike Zuhurah tace duk kun gama sai jiran a koma ku ɗaura daga inda kuka tsaya,tuh Allah ya taimaka in kuma Allah ya kawo miji sai mu sha biki kawai ba."
Yadda Laurat ɗin ta kai ƙarshen maganan yasa TAIMIYYAH sakin dariya kawai,ba tare da tace komi ba Laurat ɗin da yake gwanar iya hirace,ita ke ta janyo zance har TAIMIYYAH ta sake suna ta hira,sai kusan biyar ta bar Sasan Iyan tana cewa TAIMIYYAH zuwa anjima don Allah ta shiga can Sasan ayi hira,domin ita har ga Allah ƙaunar TAIMIYYAN take ji da zuciya ɗaya,dariya kawai TAIMIYYAH tayi don tasan Iya ma bazata bari ba,uwa uba ita kanta ma bazata shigan ba,don tasan ƙarshenta da ɓacin rai zata fito Sasan,ita ko a yanzu babu abinda take tattali irin farin cikinta,shiyasa gaba ɗaya ta ɗauki duk wata soyayya da takewa su Zuhuran da qawazucin su ta adana shi can ƙasan zuciyanta,babu abinda take so da ƙauna da bashi muhimmanci a yanzu irin karatu,ga kuma wayanta da ke ɗebe mata kewa tana karance-karancenta masu muhimmanci da take ƙaruwa dasu,ga groups na karatuttukan manyan malamai da ake turowa suna sake wayar da kanta da samun tarin ilimi,shiyasa ko kaɗan yanzu zaman kaɗaici baya damunta,ko da Anty Laurat ɗin ta tafi ma ɗaki ta koma ta kunna karatun Qur'ani cikin suran da zata kai hadda sati me zuwa,tana saurara har akai kiran sallan magriba,sannan ta kashe karatun da yike tana period ba sallan zatai ba kawai sai ta fito zuwa Kitchen,tana jin sha'awan cin wainan fulawa ko Pancakes,don ita idan tana al'adah komawa take kaman wata me yaron ciki,bata iya cin abinci sosai sai kwaɗayi kala-kala, buɗe can rufe can tana tunanin me xata ƙaƙala tayi,har dai zuciyanta ya tsayu akan yin wainan fulawan,hakan yasa ta ɗebo fulawan ta tankaɗe ta jajjaga tarugu da albasa kaɗan,haɗi da yanka albasa me dama ta zuba a kwaɓin,ta fasa egg guda biyu ta zuba spices da maggi ta motsa sosai,sannan ta ɗaura nonstick pan ɗinta a wuta,manja ta zuba me bala'in kyau irin wanda ake kawowa Iya daga Lagos,nan da nan qamshi ya fara tashi na suyan wainan fulawan,already tana da dakakken yajin da take dakawa da kanta tana ajewa,don ita Iya bata cin yaji sam TAIMIYYAN ma da take so kullum cikin yi mata faɗa Iya take,qamshi ne ya ishi Iya da ke zaune a falo ta ɗaga murya tana faɗin "Wai ni kam me kike soyawa ne haka TAIMIYYAH?"
TAIMIYYAH da ta gama arranging wainan fulawan cikin plate ta wani zubo yaji daga gefe,sai qamshi ke tashi ta fito hannunta riƙe da plate ɗin,ɗaya hannun na dafe da ƙafatan tana takowa har zuwa cikin falon,sai lokacin ta saki murmushi tana duban Iya take faɗin "Iya wainar fulawa ce fa kawai na ɗan soya,in matso mu ci ne tare na ga cewa kike ke bata dame ki."
TAIMIYYAH tayi maganan tana sakin dariya,ganin irin hararan da Iya ke aiko mata,kafin Iyan ta furta "To sai dai naci wannan irin qamshi haka,wallahi raina ya biya maza matso da shi ince ko ɗaya ne,ai da ne dai nake cewa bata dameni ba,amma banda yanzu da kika ɗanɗana min irin wannan haɗin daɗin da kike masa." TAIMIYYAH tana dariya ta ƙarisa gaban Iya suka fara ci tare,Iya me cewa zata ci ɗaya sai ga shi ta tada guda uku tana faman santi,me TAIMIYYAH xatayi inba dariya ba,Ladi aka rage ma guda biyu TAIMIYYAN ta fita kai mata ɗakin ta,ita kuma Iya ta shige ɗaki don gabatar da Sallan isha'i,TAIMIYYAH ɗaki itama ta shige bayan ta dawo kaima Ladi wainan fulawan,ta ɗauki wayanta tana turawa Abie saƙon Text Message akan tana son ya siya mata sabuwan Laptop,amma samfurin Apple take so,can zuwa anjima kaɗan kawai taji alert ya shigo wayanta na kuɗi masu kauri,sai kawai ta shiga kiran line ɗinsa,buga biyu ya ɗaga da yake vedio call ta kira,yana ɗagawa idanunsa suka sauka akan ƴar nasa da yake matuƙar jinta cikin zuciyansa,domin duk idan ya ɗaura idanunsa akanta Zaynab ɗinsa yake gani,wata ƙwayan mace guda ɗaya da bazai taɓa iya haɗa soyayyanta dana kowace ɗiya mace ba "I miss u Abie ka rabu da shigowa Zaria." Muryan TAIMIYYAH ya shiga kunnuwansa,ya sauke numfashi me sanyi yana duban ɗan ƙaramin bakinta da ya iya shagwaɓa,ya saki murmushi sosai yana faɗin "Miss u too Zayab,na ga saƙon ki ina fata kinji alert?"
Yayi maganan idanunsa akanta,ta sake narke masa da shagwaɓa tana faɗin "Eh Abie naji nagode,Allah ƙara buɗi yasa kafi haka, idan Yah Sadeeq ya dawo shi kawai zan baiwa kuɗin ya siyo min."
"Hakan yayi Daughter ina Iyan taki take,hope duk kuna lafiya zan shigo garin zuwa next week insha Allah,har kin fara zuwa Cimputer skull ɗin kenan?"
TAIMIYYAH da ke sauraran Abie ɗin amma bata kalli face ɗinsa ba ta furta "Lafiya lau Abie Iya tana sallah ne,skull kuma sai monday xa'a fara ina so ne kafin afara na mallaki Computern yadda duk abinda aka koya mana zan zo in sake gwadawa a nawa."
"Gud gal! to Allah ya taimaka ki gaida Iya ai munyi waya ɗazu bye zan amsa wani call."
Daga haka yai cuting call ɗin,TAIMIYYAH ta sauke ajiyan zuciya tana jin ƙaunar Abie ɗin me girma a cikin xuciyanta,duk da basu da shaƙuwa me zurfi tsakaninta da shi,amma ita da kanta ta san yana son ta sosai domin idanunsa basa iya ɓoye hakan,wanda Iya tasha gaya mata cewa Soyayyar da yakewa Mamanta dole ya shafeta don yayi mata wani irin so me wuyan misaltawa,ashe rayuwansu bazai yi tsayi tare da juna ba,ta lumshe idanunta tana jin inama ta taso tare da wannan uwa nata,sai dai ko kaɗan bata maraici don bata ma san daɗinta ba tunda bata rayu da ita ba,Iya itace ta taso ta gani a matsayin uwarta,sai dai har kullum Iya ta kwaso pic ɗin Maman nata tana jimawa riƙe da shi,tana kallon tsantsan kaman da suke da juna,hatta a wayanta tayi snaping copys ɗin hotunan marigayiyan da yawa,ta adana lokaci zuwa lokaci takan shiga folder ɗin tai ta kallon kyakykyawan fuskan mahaifiyan nata,to a yanzu ma da son ganin pic ɗin ya motsa take ta shiga ta danno pics ɗin tana gani ɗaya bayan ɗaya. _________
*9:40pm*
A.Maleek Ado ne zaune daga cikin falon da ke upstairs,yayi zaman dirshan don cin tuwan Semo da ya sanar da Suhailah yana so,daga gefensa Suhailan ce zaune sanye da wani pencil skat da Riga me siririn hannu,sosai kayan sukai mata kyau ƙirjinta ya fito sosai ta saman rigan,idanunta har lokacin basu gama wartsakewa daga uban kukan da ta sha a yau ɗin ba,loman farko da ya kai bakinsa ya tauna ya haɗiye,ya aje spoon ɗin manyan idanunsa ya sauke akan Suhailah,yana faɗin "Ɗauke min wannan abincin daga gabana please!"
Yadda yai maganan muryansa na bayyana ɓacin ransa a fili,yasa Suhailah dubansa a razane,ya cigaba da furta "Mena faɗi Suhailah tun a gidan Hajjah game da yin wannan abincin? Amma sabida ban isa ba sai da kika baiwa bayinki suka yi sabida ki nuna min iyakata ko?"
Yayi maganan a mugun fusace yana miƙewa ya nufi ɗakinsa,ya bar Suhailah da baki sake gaba ɗaya ta rasama abin cewa,bata san meyasa yake iya bambamce girkin da tayi dana masu aiki ba,duk da cewa Ameena da take gani ƙwararriyace ita ta saka tayi masa,amma gashi sai da ya gane ɗin,ta lumshe idanunta tana jin babu daɗi,dama ya lafiyan giwa ita me laifi ce gashi ta sake ɗaura wani laifin,jikinta a sanyaye ta miƙe ta nufi ɗakinsa,sai dai tana shirin shiga shi kuma ya fito,hannunsa riƙe da mukullin mota ya sauya kaya zuwa wasu Riga da Wando na Gucci,saura kaɗan su gwabza karo Suhailah tayi saurin ja baya tana duban fuskansa da babu annuri take faɗin "Don Allah kayi haƙury Sweet wallahi kaina ne ya dinga ciwo dana dawo,shiyasa na kasa yi da kaina gudun karka dawo kuma ka tadda ba'a yi ba yasa nace Ameena tayi,don Al......"
"Alright! yayi kyau."
A.Maleek ɗin da ya katseta ya furta,yana raɓata zai wucewansa tayi saurin shan gabansa tare da riƙo rigansa,wani mugun kallo yai mata yana zare hannunta daga jikinsa,ya wuce da sauri zuwa Stairs da bibbiyu ya dinga haɗa steps ɗin benan har ya sauka ƙasa,da kansa yake driving ya bar gidan megadi na ɗaga masa hannu da fatan dawowa lafiya,Apple white ya nufa yayi Ordern wani irin Tea nasu me daɗi haɗi da Snacks,bai tsaya ci anan ba akai masa take away ya fito zuwa mota,ya sake isa wani wajen sai da ƙoda ya siya sannan ya wuto gida lokacin da agogo ke buga sha ɗaya har da mintuna biyu,nan falon ƙasa ya zauna yaci komi iya yadda xai iya ci,yana cikin ƙarisa shanye tea ɗinsa Suhailah ta sakko,tana sanye cikin kayan bacci Riga da wando da suka fidda suranta,gaba ɗaya qamshinta ya cika wajen lokacin da ta iso,amma kallo ɗaya yai mata ya ɗauke kai ita kuma ta zauna idanunta na kansa bayan ta gama kallon yadda ya barbaje packs ɗin da aka zuba masa komi ciki,cikin wani irin salo na bada haƙury ta buɗe baki zatai magana,yayi saurin ɗaga mata hannu,yana tashi tsam ya bar mata falon gaba ɗaya ya haura zuwa sama,murzawa ɗakinsa key yayi don bayama buƙatan damu bare ya saurari ban haƙurinta,sabida tana sake fusata zuciyansa ne sosai,ya daɗe yana gayawa kansa abubuwa da yawa da yake shayewa daga gareta tana cin albarkacin Hajjah ne,da kuma ƙarfin zumuncin da ke tsakaninsa da ita,uwa uba Soyayyan da Inna Kareeman ta gwada masa,wato mahaifiyan Suhailan yana sake taka rawa wajen danne zafin zuciyansa akan Suhailah,amma baya ji idan aka cigaba da tafiya a yadda Suhailah take masa yanzu baza'a samu matsalaba,don sosai take son ƙure duk wani haƙurinsa da kauda kan da yake yi a wasu lamuran,yana ji tana faman nocking yai biris da ita,sai ma wayoyinsa da ya janyo ya kashe su baki ɗaya,dama baya kwana da waya a kunne sam,har bacci ya ɗauke sa bayan ya kwanta baisan yadda ta ƙare tsaye abakin ƙofar ɗakin nasa ba.........✍🏻
Littafin TAIMIYYAH paid book ne da zai zo akan 500 naira only,ga masu buƙatan yin payment zakui min magana ta wannan number ɗin 08167768704, ko kuma ku turo kuɗin ku kai tsaye ta wannan account ɗin 0504192664 aisha ibrahim dansabo GTbank.*
*Sai ku tura shaidan biyanku ta wannan line ɗin 08167768704.*
_Masu account da Arewa books,zaku dinga siyan sabbin shafuka dalla-dalla akan farashi me sauƙi,ga yadda zaku siya pages a arewa books kamar haka_ 👇🏻
https://arewabooks.com/chapter?id=62d29e11aa5f8f19bc9621cb
*DANNA LINK DIN NAN KASHA KARATU👆🏽👆🏽👆🏽*
*_YADDA ZAKA SIYA LITTAFI A AREWABOOKS_*👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾
*Recharge* - inda ake shiga domin saka kudi cikin account.
*Balance* - Zai nuna kudin account dinku da zaku iya sayayyan littafai cikin kasuwar ArewaBooks.
*Credit/Debit Card* - Hanyar farko kuma mai dadi wajan Recharge din account dinku.
A inda (Enter your amount) za'a saka kudin da akeson Recharge din sai a taba "Proceed". Zaibude muku inda zaku saka bayanan katin banki, kuna gamawa kudinku zaishiga account dinku kaitsaye (instant).
--------
Akwai wasu hanyoyin saka kudi a ArewaBooks account kamar:
*Bank Transfer* *Airtime Transfer*
Saidai su ba kaitsaye bane (instantly) sai ArewaBooks ta tabbatar da Transfer din, amman bayakai 1hour za'a gansa a Balance.
#Ɗansabo ce# [12/14, 10:04 PM] +234 703 769 7050: *TAIMIYYAH*❤️
©️Ayshat Ɗansabo Lemu ✍🏻
*Page 20 to21*
*END OF THE FREE PAGES*
*To masu karatu a wannan page ɗin Free pages ya zo ƙarshe.Don haka sai ku hanzarta biyan 500 ɗinku don jin cigaban labarin,domin duk yadda zan gutsira muku ya labarin TAIMIYYAH yake ba za ku gane inda aka dosa ba har sai kun shiga cikin labarin tsindim sannan za ku gane inda tafiyan ya dosa.Don haka kar ku bari a barku a baya ku bi sahun masu rubdugun shiga Payment Group don jin ya labarin TAIMIYYAH zai kasance? Yah Maleek da Suhailah za su kwashe a gaba,shin da gaske zai iya sake auren wata mace don samun haihuwa,ko bazarana ce kawai yake? Duk za a warware muku zaren labarin a gaba.Ku dai kawai ku biya ku shige cikin group don kwasan karatu.Saina ga ruwan ƙauna daga Fans ɗina* 😍
_______Washegary Suhailah da kanta ta tashi ta shiryawa A.Maleek Breakfast,sai dai cikin rashin sa'a A.Maleek ɗin tun ƙarfe takwas ya bar gidan ba tare da sanin Suhailan ba,sai da ta gama tsara kwalliya ta nufi ɗakinsa ta tadda babu kowa ciki,sai ɗakin da ya bari a hargitse duk kayan da yai anfani da su gasu nan zube bisa Bed ɗin,waya ta ɗauka ta kira shi zuciyanta na bugawa da ƙarin takaicin kanta da kanta,yana ɗaga wayan sai ta nemi sanya masa kuka yayi saurin dakatar da ita,yana sanar da ita ya wuce Kaduna daga can kuma zai bi jirgi ya wuce Lagos,sai next week zai dawo bayan an rantsar da shi akan sabon muƙamin da aka bashi,wanda za'a rantsar dasu a Abuja sati me zuwa, don haka ya bar mata garin tayi yadda take so,ai Suhailah bata san lokacin da ta rushe da kuka ba shi kuma yai cuting call ɗin yana jan ƙaramin tsaki,zama tayi a ɗakin taci kukanta ta more kafin ta fice ta koma zuwa nata ɗakin,ta cigaba da neman layin Zuby cikin sa'a bugu biyu Zubaidan ta ɗauka,sai Suhailah ta sanya mata kuka,cikin nuna kiɗemewa Zubyn ke tambayan Suhailah abinda ke faruwa amma sai Suhailah ta shaida mata cewa zancen bana waya bane,don haka idan ta samu lokaci kawai ta zo gidan nata akwai maganganu,daga haka sukai sallama Suhailah ta aje wayan,zuciyanta sam babu daɗi tana tsoran ace Maleek ya juya mata baya a dai-dai wannan lokacin,takaicin kanta na yadda take kasa binsa a yadda yake so na sake lulluɓe zuciyanta.
________
*Monday,10:10am.*
TAIMIYYAH ce tsaye daga bakin titin kwaltan shiga layinsu,sanye take da dogon Hijab kalan sararin samaniya,kaman yadda kalan Material ɗin jikinta yake,Napep take jira don zuwa wajen Computer Training ɗin da zasu fara a yau ɗin,sai dai da alama yau ɗin za'ai wahalan abin hawa,ta sake kallan agogon da ke ɗaure a tsintsiyar hannunta,ta ga lokaci na sake tafiya sai takaicin rashin barin Sani Drivern Iya ya kaita ya kamata,don ba yadda Iya ba tayi akan ta kira Sanin ba amma ta nuna tafi so ta dinga zuwa da kanta,tsayuwan mintuna kusan goma ta ƙara bata samu abin hawanba gashi ita ba gwanar jurewa tsayuwa bace sabida laluran ƙafanta,wayanta take shirin cirowa a jaka ta kira Sanin ta ji idan yana kusa kawai yazo su wuce,sai dai tsayuwan wani me Napep a gabanta yana faɗin "Hajiya tafiya ne?" Shi ya katsewa TAIMIYYAH hanzari ta ciro hannunta daga cikin jakan tana gyaɗa masa kanta,kafin ta furta "Eh tafiya ce,can gaban Congo kaɗan zaka kaini."
Ta ƙare maganan tana shiga cikin Napep ɗin ta zauna,shi kuma ya ja sukai gaba ko da suka isa sauka tayi ta nufi cikin wajen bayan ta biya shi kuɗinsa,shi kuma yaja mashin ɗinsa yai gaba,Ƙarfe ɗaya dai-dai suka tashi kaman yadda aka sanar dasu tsarin karatun,su shiga ten afito one ga mamakin TAIMIYYAH kuma suna da yawa sosai wanda suke karatun tare maza da mata,cikin wanda suka fito kusan a tare wata budurwace me yawan fara'a,baƙace sosai sai dai tana da kyau dai-dai misali,ta dubi TAIMIYYAH lokacin da suka gama fitowa daga cikin ajin ɗaukan karatun,ta miƙa mata hannu tana faɗin "Salamu alaikum,sunana Zaynab Haroun." TAIMIYYAH itama sai ta miƙa mata nata hannun sukai musabaha,da murmushi a saman fuskarta take faɗin "Sunana Zaynab Sameer."
"Wow! nice name Namcy,ina farin cikin haɗuwa da takwarata." Cewan budurwan itama murmushi kwance saman fuskanta,suka jero a tare da TAIMIYYAH har zuwa bakin titi,budurwan na ta ɗan jan TAIMIYYAH da magana akan Programme ɗin da zasuyi na Computer Training ɗin,zuciyanta cike da tausayin yadda TAIMIYYAN ke tafiya,a zuciyanta take ayyana mace har mace kyakykyawa da ita ga dirin jiki amma Allah ya jarbceta da nakasan ƙafa ɗaya,ita dai TAIMIYYAH tana amsa mata jefi-jefi,suna tsaye tare har suka samu abin hawa,TAIMIYYAH ta shaida masa gyallesu zata nufa,yayin da itama Zaynab tace Gaskia ita ta nufa,hakan yasa sukai sallama da juna TAIMIYYAH ta shiga ya wuce da ita.
Ta iso gida a gajiye sosai burinta bai wuce ta ganta a Sasan Iya ba,tayi wanka ta sawa cikin ta abinci don yinwu take ji sosai,a hankali take shigowa cikin Compound ɗin gidan,bayan ta tsaya sun gaisa da sabon megadin da Baba Sani ya kawo a shekaran jiya me suna Tukur,matashi ne kuma bamai nisan shekaru sosai ba don bazai wuce shekaru arba'in ba,tana cikin tafiya sai ji tayi ana kiran sunanta,sai ta dakata da tafiyan hannunta dai dafe da ƙafanta me laluran,ta waiwaya baya idanunta na sauka akan Anty Laurat da ke tahowa daga Sasan su Zuhurah,sai TAIMIYYAH ta saki murmushi tana cigaba da tsayuwa har Anty Laurat ɗin ta ƙariso wajen,tana furta "Daga ina ƴan mata da uwar ranannan?"
TAIMIYYAH ta sake faɗaɗa murmushinta tana sanar da Laurat ɗin daga inda take,Laurat ta furta "Ayyah! Sannu da dowawa tuh,ya karatun hope ya fara daɗi?" Yadda tai maganan da zolaya yasa TAIMIYYAH sakin murmushi tana faɗin "Anty Laurat kenan sai mu ce Alhamdulillah!"
Laurat itama ta saki dariya kaɗan tana faɗin "Bari na barki ki ƙarisa daga ciki,nima wai na fito zan ɗan je kasuwa ne akwai abinda zan nemo,zuwa anjima zan shigo ai yau ina so ki ɗan gwada yin Doughnut irin wanda ki kai shekaranjiya ɗinnan,yayi daɗi ina so na ga yadda kikai kwaɓin."
"Ok ba matsala Anty Laurat,sai kin shigo ɗin bari in ƙarisa na gaji sosai." Cewan TAIMIYYAH daga haka kuma ta cigaba da takawa zuwa Sasan su inda tafi wayo,a falo ta tadda Iya tayi baƙuwa qawanta Hajiya Sahura ne ta zo,da alama tazo garin kenan sabida ta bar Zaria da daɗewa,ta koma can Bauchi wajen Yayanta namiji da ya ɗauke ta tun bayan rasuwan mijinta,TAIMIYYAH ta durƙusa har ƙasa ta gaida Hajiya Sahuran da ke mata sannu da zuwa,ta amsa da fara'a tana faɗin "Sannu TAIMIYYAU ai ina zuwa na tambayeki Iya tace kina wani makaranta na koyan na'urannan me ƙwalƙwala,to Allah ya bada sa'a." TAIMIYYAH ta amsa da "Ameen,amma Hajjaju ki dinga faɗin sunan dai-dai TAIMIYYAH ne fa ba TAIMIYYAU ba."
Yadda TAIMIYYAH tai maganan a shagwaɓe yasa Iya da Hajiya Sahuran yin dariya,Iya na faɗin "Ja'irah to ya karatun na ga kin jima nema baki dawo ba."
"Lafiya lau Iya,rashin abin hawa ne wallahi ya tsaidani,don da zani ma da ƙyar na samu,ina ga dai naki zanbi Sanin kawai ya dinga zuwa ya kaini idan zan dawo na dinga dawowa ni kaɗai ɗin."
Cewan TAIMIYYAH tana tashi don shigewa ɗaki,Iya tabi bayanta da kallo tana faɗin "A tuh! Da dai yafi miki kam."
Bayan shigan TAIMIYYAH ɗaki ne Hajiya Sahurah ta dubi Iya tana faɗin"Kinga yarinya yadda ta zama ƙatuwar budurwa kyau kaman ita tai kanta,lallai na jima rabo na da Zaria Iya wallahi kamanninta da marigayiya uwarta har ya ɓaci,inama ina da ɗa namiji da anyi haɗin zumunci don ni dai ina ƙaunar wannan ɗiya ina kuma tausayinta matuƙa,Allah yai mata zaɓi ya kareta daga sharrin samarin zamanin nan." Iya tayi caraf tana amsawa da "Ameen,ke dai bari kawai Hajjaju kullum addu'an da nake kenan Allah fito mata da nagari,ya kaita inda bazata cutu ba ko dan laluran ƙafannan nata,kinsan halin mutanan mu koya suka ga mutum da nakasa sai ya zama abin rainawa,bayan basu san irin baiwan da ubangiji ya aje a garesa ba,Allah dai ya shige mana gaba yai mata kyakykyawan zaɓi Ameen." Daga haka suka cigaba da hiransu Iya na ba qawan nata labarin yadda Umma ta ɗauki karan tsana ta ɗaurawa TAIMIYYAN,Hajiya Sahuwa abinka da mace me saurin ɗaukan zafi,nan take ta dinga la'antan baƙin halin Umma,har tana mata fatan Allah ya gwada mata samun nakasasshen cikin jikokinta in tana ganin ta gama haihuwa ne a yanzu da har take nunawa TAIMIYYAH baƙin tsana irin haka,ita dai TAIMIYYAH da ta fito daga wanka tana jiyo tashin zancen su Iyan sama-sama daga ɗakinta,har ta gama shiri ta fito kai tsaye ta nufi wajen cin abinci,ta zuba wanda zataci ta fara ci bayan ta kammala ɗaki ta shiga,tana ɗakko sabuwar Laptop ɗinta da Yah Sadeeq ya taho mata dashi daga Kd,randa yazo Weekend domin tunda Abie ya turo mata kuɗin sayan sai taiwa Yah Deekun magana ta waya akan tana so ya siyo mata yazo mata dashi,tayi-tayi ya turo mata details ɗinsa ta saka masa kuɗin,amma sai yai mata wayau yace ta bari idan ya shigo Weekend zasuyi magana,sai kawai ganinsa dashi tayi randa ya diro garin ya kawo mata Sasan Iya,yana mata dariya wai Suprising ɗinta yayi,aiko murna a gun TAIMIYYAH kaman ta rungumeshi haka taji,musamman da ta duba taga Exactly irin wanda ta tura masa hotonsa ta chart ne tace irin shi take so,hatta Iya tayi murna da wannan kyauta da yaiwa TAIMIYYAN,tai ta masa godia yana hararanta a lokacin yana faɗin shi baiga abin godia ba don ya saiwa TAIMIYYAN Laptop kawai.ta saki murmushi lokacin da take buɗe Laptop ɗin ta kunna,cikin sauƙi ta fara operating ɗin abinta cike da farin ciki,tayi abu me yawa a ciki duk cikin karatun su na yau ɗin,kafin ta rufe ta mayar ta aje tana komawa gado don ta samu ta ɗanyi bacci kafin akira sallan La'asar.
Kamar yadda suka rabu da Anty Laurat zata shigo koyan Doughnut,aiko ana idar da sallan la'asar ta shigo Sasan Iya,bayan sun gaisa da Iya a falo ne ta wuto ɗakin TAIMIYYAH,wacce ke amsa call ɗin Maryam Salis da ke sanar da ita rashin lafiyan mamansu da aka kwantar a asibiti,TAIMIYYAH ta bata tabbacin zata sanar da Iya su je su dubo Mum ɗin a asibitin kafin a sallamesu,ta sauke wayan daga kunni bayan sunyi sallama da Maryam ɗin,manyan idanunta ta ɗaura akan Anty Laurat da ke bin TAIMIYYAN da kallo,ganin yadda Rigan jikinta yai mata kyau,tare da fito da kyawun halittan TAIMIYYAN a sarari "Anty Laurat har kin shigo?" Cewan TAIMIYYAH da murmushi saman face ɗinta,Laurat ɗin itama murmushi tayi tana faɗin "Eh! Wallahi TAIMIYYAH gani na shigo,gara afara yanzu kada muyi dare ko?"
Daga haka suka fito zuwa kitchen ɗin Iya,da yake babba ne sosai sam babu wani takura,Ladi na ta hidiman ɗaura abincin dare su kuma suna aikin kwaɓa Doughnut ɗin,wanda TAIMIYYAH tace a kwaɓa na mudu ɗaya kawai,aci har ayi sadaka da sauran wa maƙwafta,hakan ko akayi ta fiffito da kayayyakin yin,fulawa mudu ɗaya (8 cups) ta baiwa Anty Laurat ɗin tace ta tankaɗe cikin wani bowl,ita kuma ta fito da 2 eggs, sai Sugar 1 and half cup, sai 2tbsp na Yeast ,sai 1tsp Salt,sai Half Simas,sai 2 cups liquid milk(warm),sai 1tsp Vanillah powder.