Kenza eBookz

The sexxxy boss complete by maman teddy - Chapter 4

The sexxxy boss complete by maman teddy - Chapter 4

The sexxxy boss complete by maman teddy Chapter 4: The sexxxy boss complete by maman teddy Chapter 4. _Don Allah idan kin san You Are under 18 Kar ki…

3,167 words

_Don Allah idan kin san You Are under 18 Kar ki karanta mun wannan labarin na the sexy boss , but if you're above 18+ ba damuwa , sai dai muce asha karatu lafiya...💃💃_ _________________________

To ke Umaima yanzu ya kike ganin zamu hukunta Auwalu ,kin san fa shima tantiri ne ,kuma koma yaya dai wanda ya girme maka ya fika dabara . Murmushi Umaima tayi tana duban Fatima da ita ta gama tsorata da Auwalu ,don sarai tasan waye shi a iskanci da sanin duniya . Ke kin san yanda zamuyi ne? Ki ƙwantar da hankalin ki , ba kina da Waya ba? Nima Ina dashi ? Gyaɗa kai Fati tayi tana duban wayar su wanda duka babu ɗaya ƙwaƙƙwara . A gobe zamu tafi da Auwalu , muna tafiya zan kiraki in sanar dake , da ganan zan kashe wayata yanda babu wanda zai kuma samuna ,ke kuma aikin da zakiyi shine matso kiji . Saurin matsawa Fatima tayi kusa da Umaima tana raɗa mata magana ,kamin Fatima ta saki wani irin dariya tana cewa " Tabbas Auwalu ya shiga Uku ,bamu zamu yi masa hukunci ba ,mutanen Unguwa . Dari ya Umaima keyi kana tace ki shiga gida nima Bara na shiga , sai da safe don bana tsammanin ko sallama zamuyi ,don da asuba zan fice ,daga ɗebo ma Umma na ruwan safe sai dai suji labari .

Eh Haka za'a yi Umaima ,amma Ni dai Allah yasa idan kin samu wannan kuɗin kar ki manta dani . Murmushi Umaima tayi tana dafata tare da cewa " Haba ƙawata ya za'a yi na manta dake ?. Ina dawo wa zamu shiga makarantar gaba ,daganan shekaru kaɗan zamu zama manyan masu kuɗi , mu sauya masu Umma gidan nan , jiba fa lokacin damuna kullum da gudu muke shigewa saboda ji muke tamkar garun zai faɗo mana aka . Dariya suka kuma kechewa dashi kana Fatima tayi soron gidan su , Umaima na nufar tasu gidan .

*** Ru'aifa ne tayi duba ga Hajiya Turai kana tace " Yanzu Hajiya me kike so ayi kenan? Me yasa kuke shakkar Wannan yaron ne Umair ? Nifa ba yarinya bace , i age him , na girme mawa Umair A shekaru wanda kin san cewa wanda ya girme ka yafika dabara, abu ne mai sauƙi nasa Umair ya faɗa komata , bashi ga Ɗan iskan Ƙwarto ba ,kuma marar mutunci , to wallahi yana kuskuren yayi wani mu'amala dani to daganan zan fara juya sai yanda nayi da shi... Dafe kai Hajiya Turai tayi kana tace " Wannan wani irin shashanci ne? .

Ke kin san waye Umair kuwa? Ban taba ganin tantirin yaro kaman sa ba . Mata nawa na tura masa suka sheƙe ayan su , amma daga zarar ya ƙwanta da mace sau ɗaya ya barta kenan ,baya kuma ƙara jin sha'awar ki . Ya barki kenan ,ɗan duniyan yaro ne idon sa a yage yake , ko da yake ba mmki wayakai Turawa iskanci ?.

Dariya Ru'aifa tayi tana cewa " Hajiya wai shin kin san Ni Karuwanci na mai lasisi nakeyi , nice Ru'aifa Wanda duk ƙwartancin ɗa namiji yayi Sex dani ,wallahi duk inda nake sai ya nemo Ni ,Ni ke gajiya da namiji na koresa da kaina badai shi yace ya gaji dani ba. Kin san meye dalilin ? Girgiza kai Hajiya Turai tayi kamun tace " ki kula Umair yaro ne tantiri sosai ,ganin kowa yake a tafin hannun sa bare kuma mace da bai ɗaukarta da muhimmanci . Murmushi Ru'aifa tayi tana cewa " Magana ce fa ta kuɗi Hajiya kuma nace zan maki wannan aikin . Nisawa Hajiya Turai tayi tana ƙara fankankan a kujerar da take zaune ta cike shi dam , tana malolo da naman wuya tace " Indai kikayi wannan nasarar Ni kuma nayi maki Alƙawarin Duk yanda zanyi sai nayi ganin Umair ya Aure ki , ai har yanxu bashi ke da kan shi ba , mahaifin sa nada cikakken iko akan sa , wanda duk abun da ya fadi masa sai yabi ko baya so.! Kinga wannan hanya ce mafi sauƙi ma , a wannan satin zan shirya zuwa Lagos . Cewan Ru'aifa tana sakin wani irin makirin murmushi .

***

Da gudu ta nufi gidan Su Umaima tana ƙwala kirar sunan Umma ,wanda ta fito da sauri ita da Yayar Umaima wato Hannatu da take Aure a dogarawa nan Zaria . Cikin haki da kuka wanda Fatima batasan zata iya ba take faɗin " Ina Baba?. Hankalin Umma Ramatu a tashe ta riƙo Fatima tana cewa " meke faruwa Fatima? Ina Ƙawar taki Umaimatu?. Cikin matsanancin kuka Fatima tace "Umma ya tafi da Umaima ,Auwalu ya tafi da Umaima a idona ya rufe mata baki yasa ta a moton shi yanxu da safiyar nan , babu kowa ya gudu da ita , sai ihu take tana kirar sunan ki ,Wayyo Umma Umaima..! Innalilahi wa'inna ilaihir rajiun ,Shine Kalmar da Yaya Hannatu da Umma Ramatu ke faɗi kenan , kamin Cikin tashin hankali Yaya Hannatu ta saka mayafi tana fitowa daga gidan bangan bangan . Kowa ta gani a hanya sai tace " ina Auwalu ?? ,Sai ace mata ba'a san inda yake ba , bata wucewa sai tace " Ya gudu da Umaima wai ya rufe mata baki yasata a moto . Nan zakaji an hau salati masu nufar gidan su Auwalu da ban ,masu neman sa daban , nan take mutanen Unguwa aka buraɗa har tasha neman Auwalu da Umaima , wasu na cewa" Tabbas ya shaƙa mata wani Abun ne don an san Auwalu dama bugagge ne mashayi kuma manemun mata mazinaci. Yara kuwa ƴan yungu yungu ana cewa ba'a ga Umaima bace cewa suke " Wayyo shikenan Malama Umaima ta ɓata mai ilimin layin nan ,babu wanda yakaita ,kullum ita take koya mana karatu , shikenan Auwalu ina zai kaita.?? . Kowa da irin maganan da yake yi akan ɓatar ta , yayin da wasu da dama suka lashi takobin idan Auwalu ya dawo sai sun bar shi babu rai .

Yaya tsohuwa ce ta fito tana kuka irin ta tsofaffi ko hawaye baya fita daga idanun ta . Kallon su mai Wada tayi da Nadabo da ya zauna a bakin shagon shi yana kallon sunan da Umaima tasa ma Shagon nan ,kuma ya samu kasuwa sosai wato Sofar barbar salun shop . Allah sarki wannan yarinya dama nasan ƙwazon ta baza'a barta ba , Allah yasa ba rayuwar ta zai salwantar ba , irin yaran nan masu ƙwazo da hazaƙa ba'a barin su haka...cewan Yaya tsohuwa tana daɗa matso ƙwalla tare da kallon nadabo da ya rafka ta gumi .miƙewa yayi a fusace yana cewa " Ina wallahi yaya idan ya salwantar da UMAIMA shima sai mun kashe shi. Yaya ne ta amshe da cewa " Idan kuma Lalata yayi da ita , kar mu jura hukuncin Gomnati Shari'a ,a kama sa a datse gindin yin zinan ,shi kenan a huta da yaɗuwar iskanci da Ƙwartonci . Yaya tsohuwa ta ƙare maganan a fusace . Samarin layin ne kusan su baƙwai suka yanke shawarar nufan Lagos don dawo da Umaima daga hannun Auwalu shima su kamoshi su taho dashi Zaria ,daganan sai ayi masa hukunci dai dai da yanda Yaya tsohuwa ta faɗi.

Ɓangaren Umaima kuwa tun da ta sanar mawa Fatima ta kashe wayar ta kaman yanda tace , a haka moto cike da pasinger ƙwana sukayi a hanya kana su isa Lagos , suna isa Lagos bayan ya isa moto park yayin da passengers ke sauka itama ta sulale ta nitsa cikin su ta gudu Auwalu bai sani ba. Gudu take sosai kaman wanda tayi babban zunubi , abun ka ga can ba ruwan wani da wani babu wanda ya tambaye ta ko lafiya . Abu ɗaya tasan tana dashi ,shine naira ɗari huɗu da hamsin gaban ta da bayan ta . Sai da tayi nisa kana ta tare adaidaita sahu tana shigewa tare da cewa " Mu tafi malam". Juyowa yayi yana kallon ta kaman mabaraciya a wulaƙance yace " kin ɗauki duka adaidaita kenan . Eh malam muje. Tayi maganan kan ta tsaye ba tare da taji nawa ne kuɗin sa ba ,haka kuma batasan inda zata ce yakaita ba.

Fara jan adaidaita yayi yana ɗaukar hanya tare da cewa " To ina za'a kai ki? . Hannun ta tasa a jakar ledar dake ɗauke da hoton Umair Ahmad moddibo ,sai kuma tayi saurin mai dawa cikin nuna confidence tace " Layin Umairu Ahmad moddibo zaka kaini.

Ƙiiiiiii taji yaja kambun Adaidaita ya tsaya. Juyowa yayi cikin sauri yana cewa " Ke Sir Umair kike nufi? Sir Umair dai Ahmad moddibo ?. Eh bawan Allah nan dai zaka kaini. Ke kin san haɗarin wurin kuwa ,masu abun hawa basa zuwa layin ,domin girman ta yafi wata Unguwan anan Lagos,kuma nashi ne shi kaɗai . Gaba da baya sojoji ke fadin wurin , kuma camera ne ta ko ina ma ɗaukar sa .

Huuuuu nisawa tayi kana tace " Eh na sani , ai Ni aiki nake a gidan , ka kaini in yaso ko daga nesa layin ka aje Ni. Jin tace haka yasa shi fara jan adaidaita yana ɗaukar hanya. Tun Umaima nasa ran zuwa har tafara jin jina ashe nisa ne dasu da gidan . Tafiya sukayi kusan na a Wanni biyu ,kana ta ganta a wani layi mai kama da G.R.A . ja yayi ya tsaya yana cewa " Kinga kina miƙe can layin zaki fara haɗuwa da sojoji ki mike zai mai ki har gida... Ihu aikin mace ke aiki kikeyi a gidan.

Murmushi tayi tana cewa " Yes. Hannu tasa tana miƙa masa ɗari huɗu tana cire hamsin ɗin. To. Na gode ta juya zata tafiyar ta. Wani irin kallo Mai adaidaita yayi mata kana yace " Amma ke ƴar rainn hankali ce. Wannan tafiyar da mukayi yini zungur ne zaki bani ɗari huɗu?. Shiru Umaima tayi kana ta kuma miƙa masa Hamsin ɗin. Ke alƙu'an baki isa ba , wallahi sai kin bani ɗari takwas Sannan zan barki. Juyowa Umaima tayi tana cewa " Kai da Allah ka Sanni kuwa? Kasan wacece Umaima? To ka kiyaye Ni, ka nemi rainamun hankali yanzu zan saka wannan basawan sojojin suyi maka dukan tsiya. Tana gama maganan bata jira mai zaice ba ,ta juya tare da nufar hanyar da ya faɗa mata. Duk tijarar sa ya kasa nufar ta , cikin ɗaga murya yace " kije Allah ya isa .!

***

A falon sa yake gyefe guda irin hajiyoyin nan ne wanda su burin su kawai su ga suna lalata da samari ƙanana , su ƙwashe masa ƙuruciya , wanda suke ganin zasu iya biyan ko nawa indai zasu samu yaro matashi ya ci su . Ƴar siyasa ce babba ,kuma ta tara dukiyar , daga zuwa asibiti ta haɗu da Umair ya bata card ɗin shi , a yau suka haɗu ta iso gidan shi . Tun da ta shigo tsoron sa ya kamata ,yanda ake maganan sa yafi haka ,idan dukiyar ne yafi yanda ake expecting ɗin sa ,Haka idan ƙwartancin ne ya wuce tunanin mai tunani . Kallon shi tayi don duk jarabar Hjy Baraka ji tayi ta gaji don sosai ya buɗa ta , duk wasu matse matse nata Duk ya wargaza ta a 1st round . Zaune take tana maida numfashi tana jin hannun sa a bayan ta yana shafa tun daga bayan ta har zuwa ƙasan ta , don irin manyan matan nan ne , masu jiki da ƙiba da haka suke jefa rayuwar su ga halaka . Kin san me nafi so.? Yayi maganan fuskar sa babu wasa ,kaman yanayi da ƴar cikin sa . Cikin sauri Hajiya baraka tace " A'a sai ka faɗa my alawan. Goho..!

Yayi maganan yana jefan ta da wani irin kallo , duk da taji maza ta jigata ,amma saurin juyawa tayi tana dafa one seater ɗin dake gyefen sa . Tashi yayi daga zaunen da yake yana fiddo da Buran sa daga short nicker ɗin sa... Wani gurrr yaji na ƙarar wayar sa , can tahau ruri , kaman ba zai ɗauka ba don kan sa ya ɗau chaji , sai kuma yasa hannun sa yana ɗaukar wayar . Sunan Ammie ya gani , wannan yasa shi cikin sauri ɗaga kirar hannun sa na akan dama daman mazaunan Baraka yana shafa su yanda ta juya masa su baiƙi ya ƙwana yana kallon su ba . Cikin wani irin miskilalliyar Murya yace " Ammie". Umair gani a ƙasa yanzu zan yayi Meta na shigo . Saurin datse kirar yayi a gigice yana cewa " Ke tashi Ammie na tazo.! Ɗagowa tayi daga gohon da take kana tace ' Wannan gumin da yake karyo maka ga ,ko da muke sex idan xakayi release ban ganin irin wannan gumin. Ke Ammie fa nace? Ammie na..! Y kuma maimaita maganan cikin tashin hankali , kana yayi saurin maida joy Stick ɗin nasa yana cewa " Maza haye sama ki kulle kan ki. Bai tsaya bi ta kanta ba ya nufi window da sauri yana leƙawa .

Ƙyaff ³ ya kuma yi da ido hango Ammien sa cikin shiga ta alfarma gyefe guda wata gaja ya gani , da leda aka bakin ta motsi yake alamu tana ta zubo mawa Ammie zance. ,WHO is she? Yayi maganan yana faɗawa Duniyar tunani kamin ya juya cikin sauri yana nufar ƙasa ,don yaga sun nufo ciki ......

_Kar ku manta free page zai ƙare a page na gaba wato PAGE 5 maza hanzarta wajen mallakar taki_ _Regular group₦300_ _Vip group₦500_ _Special ₦1000 via 6037312299 Mohammed Aisha keystone bank ko ki Turo da katin MTN ta wannan number 08081202932_

*ANTY AISHA MMN TEDDY* _🕊️THE SEXY BOSS🕊️_ _(Romantic and comedian story)_

_Written by: Maman teddy_

_Last free page 5_

_Daga wannan page ɗin free page ya ƙare , ga masu buƙatar cigaban wannan littafi na the sexy boss zaku biyo wannan process ɗin_ _Regular group ₦300_ _Vip group₦500_ _Special payment₦1000_ _Zaku iya turo da kuɗin ku ta wannan account 6037312299 Mohammed A'isha keystone bank ,ko ku tura katin MTN ta wannan number 08081202932...Idan vtu ne sai kuyi ta wannan Numbobi 09061466409_

_________________________

Nufar down stairs yayi don tarbar Ammie da baƙuwar ta ,wacce tafi kama masa da irin ƙwasassun mahaukatan nan . Ɓangaren Umaima kuwa kallon Ammie take tana daɗa washe baki tare da cigaba da kora mata bayani , wanda a lokaci guda Hajiya Maryam taji ta natsu da Yarinyar ,kuma ta yanke hukuncin zaman ta a cikin wannan gida na Sir Umair . Sai suka hanaki shigowa baki faɗa masu cewa kin taho neman aiki ne ba..? . Nisawa Umaima tayi tamkar wacce tayi dogon tafiya kana tace " Ai Hajiya wa'annan mutane ina ka ga fuskar tun karar su da irin wannan magana? Jubi fa kalla kiga dukan su fuskokin su baƙaƙe ne , irin su su kashe ka su kashe banza ko labari ma baxa'a ji ba. A'a babu abun da zasu yi ai ,iya kan su gadi ne , sai masu kula da sauran hidimomin cikin gidan Ɗan nawa. Oho to Amma Hajiya wai dama ɗan ki ne? Ai baki mun bayani ba . Murmushi Hajiya Maryam tayi tana faɗin Umaima kina da Abun dariya sosai . Kamin Umaima ta ƙara wani magana ne nan taga Maryam ta sa yatsar ta ɗaya ta danna wani abu , nan take taga ƙofa ya buɗe , ƙafarta tasa tana shiga wannan wuri , kana tace ma Umaima itama ta maza ta shigo . Cikin kuwa sauri Umaima ta shige tana kallon Yanda Hajiya Maryam ta saki da ita . Shiru tayi tana faɗawa Duniyar tunani tare da cewa " Mace mai kirki , Allah kasa ɗan nata shima haka yake , kai ina jifa irin yanda ya haɗa gira a hoton sa na jarida , wannan bai kama da normal mutane ba , sai dai BOSS. Ji tayi wani abu kaman machine yayi sama dasu ba ƙara kawai dai taji suna sama ne... La'ila ha'ilallahu wayyo Umma na...Meye wannan Hajiya ?. Saurin dafata Ammie Maryam tayi kana tace " Ki ƙwantar da hankalin ki ki natsu lifta ne . Lifta?? Cewan Umaima tana daɗa rarraba ido kaman wacce tayi ƙarya. Ganin yanda jikin ta ke kar³ yasa Ammie saurin kai hannun ta tana riƙeta , gani tayi abun ya tsaya ashe sama yayi dasu . Ganin wani wuri tayi da ta kasa fassara ina ne nan ?. Juyawa tayi tana ƙara bin wurin da kallo , ɗakuna ne ta gani a zagaye a wannan wuri da yafi kama mata da falo . Saurin nufar window ɗin falon tayi tana kai fuskar ta tare da leƙawa babu tsoro , hango sojojin nan tayi ta can baya , a hankali ta furta " Ƙwarai kuwa Sama muka hayo.

Wani irin dadɗan sihirtacciyar ƙamshi taji ya mamaye wurin a lokaci daya ,wanda yasa ta saurin juyawa tare da kallon ɓarayin da take jiyo ƙamshin . Haaaaaa ta wangale baki tana bin sa da Wani irin kallo , wannan daga ina? Badai shine ɗan nata ba. Lumshe idanun ta tayi tana ƙara buɗe su tare da ƙare masa kallo . Amma wannan ɗan dambe ne ko? Badai likita ba gaskiya , kalli yanda yake jiki a murmurɗe , wannan ai firgita mai naƙuda za tayi tana ganin irin wannan surar tashi , wallahi haihuwa zatayi nan take koda haihuwar bata zoba saboda tsoro . An ya shine Umair Ahmad moddibo kuwa? Duk maganan take a zuciyar ta , naga baiyi kama da yanda ake ce masa bane , Ance SEXY GUY . wannan ne Sexyn?. Mutun ga tsawo ga murɗewar jiki , wannan ɗan iskan sajen da ya aje na meye?? Kai gaskiya nifa tsoro ya fara bani ,dole ƴan jarida sukasa sanin komai akan sa .

Ke Umaima million ɗari biyu da hamsin fa? Ko zaki ne sai na tun karesa wallahi , bare ma kawai sirrin sa zan naɗo . Juyawa tayi tana kallon yanda har a wannan lokacin yana rungume da Ammien tasa,itama tana rungume da ɗan nata . Wannan iskanci da mai yayi kama? Aa..! Topa yanxu wannan safcecen na mijin da rungume?? , Janye jikin ta tayi daga nasa tana murmushi tare da sa hannun ta tana shafa gyefen fuskar sa , kana lafiya ko? . Murmushi ya sakar mata wanda hushiryar sa suka bayyana ,hannun Ammie Maryam ya riƙe yana zaunar da ita a ɗaya daga cikin kewayayyun kujerun falon . Ammie ina lafiya ya su Fareesa Surayya?. Sauke ajiyar zuciya Ammie tayi kana tace " Duk kowa lafiya , fitowar safiya nayi , don na ganka don ko farkawa daga barci basu yi ba na fito, kasan da sun san zan zo ai sai sun saka rigima . Murmushi yayi yana tuno da Attabon su da ɗaya daga cikin tagwayen nata . Kamin yayi magana ne tayi saurin juyawa tare da kallon side ɗin Umaima ke tsaye riƙe da ƴar ledar ta . Matso ɗiyata kinga yaron nawa.!

Readers Also Read