Kenza eBookz

Triplets book 2 complete - Chapter 25

Triplets book 2 complete - Chapter 25

Triplets book 2 complete Chapter 25: Triplets book 2 complete Chapter 25. Bayin Allah har suna haɗa baki wajen cewa "Yau muke son komawa, kuma ko da me aka…

4,476 words

Bayin Allah har suna haɗa baki wajen cewa "Yau muke son komawa, kuma ko da me aka mai damu mun gode". Murmushi ya yi yana kallon yadda Rimsha ta yi maganar cike da zumuɗi har kamar zata tashi daga mazauninta dan murna.

"Queen of beauty ai yanzu yamma ta yi, sai dai zuwa gobe da safe, zan yi waya da daddyna ya nema muku alfarma ku samu jirgin safe".

Kamar abin haɗin baki, a tare suka zamo kasa daga mazaunin su, suka zube gwiwowinsu a kasa, suna hawaye suka fara zuba masa godiya. Fuskarsa ɗauke da murmushin tsantsan farinciki ya ce "Ya isa haka kukan, ina jin ku tamkar yan uwana ne ku, musamman Ayla yadda ta yi kama da daddyna ji nake yi kamar kanwata Anisa, ba dan na san cewa Anisa na wajen mum ɗin ta ba wlh da na riƙe Ayla nace Anisa ce, dan sun yi kama sosai, ita ma Anisa da daddy take kama, bari ma ku ga hotonta, amma dai Anisa zata fiki shekaru dan yanzu haka tana 200 level a school, kin ga kuwa zata girme miƙi" ya kai karshen maganar tare da fito da hoton Anisa a wayar hannunsa, sannan ya miƙa musu wayar.

Karɓar wayar suka yi suna kallon matashiyar budurwa dake jikin hoton, tabbas kamaninta ɗaya da Ayla, ba abin da ya raba su, sai dai ita cikakkiyar budurwa ce ba yarinya kamar Ayla ba ce, zata iya kai 21 years.

Rimsha ce ta ɗago kai tana faɗin "Allah ta yi kama da Ayla sosai" "Ni kuma fa Queen of beauty? ban yi kama da ita ba ne" ya yi maganar yana tsare ta da ido. Kawar da kallonta daga kanshi ta yi tare da sunkuyar da kai kasa ta ce "Gaskiya muryan kane ya yi iri ɗaya dana Ayla, amma baku kama Sosai, ta fi kama da Aunty Anisa" murmushi ya yi, a zuciyarsa yana faɗin "tabbas Rimsha ta yi gaskiya shi kan shi lokacin da ya fara jin muryar Ayla da tasa muryar ta masa kama, sai daga baya daya saurara sosai sai ya ji tafi kama dana daddynsu.

Miƙa masa wayarsa Ayla ta yi, karɓa ya yi ya ajiye a gefensa yana faɗin "To yanzu idan kuka koma gida, idan na dawo Abuja ina son ganin ku a ina kenan zan ganku?" Cikin sauri Rimsha ta ce masa "Ni ai Katsina nake ba Abuja ba, ita kuma Ayla Kaduna take"

Zaro ido ya yi kafin ya ce "Kai to kenan ku da kanku ma idan kuka rabu baku da tabbacin zaku sake haɗu ko ba zaku sake haɗuwa ba, tun da baku san in da gidan juna yake ba, kuma bama gari ɗaya kuke ba".

Jin wannan magana tasa ta sanya gaba ɗayan su idanuwansu suka cika da ruwan hawaye, jikinsu ya yi muguwar sanyi, ɗagowa Rimsha ta yi tana kallon Ayla, a yayin da ita ma Ayla kallonta take yi, abin gwanin ban tausayi, kenan yanzu idan suka bar nan sun rabu kenan? A tare suka gefawa kansu wannan tambayar.

Ganin haka yasa Ahmad ya yi murmushi sannan ya ce "Ai ko dan ma wannan zumunci naku ya ɗore dole na saya muku waya, domin ku rinƙa kiran juna kuna gaisawa, sannan nima idan zan zo wajen ku na kira ku a waya ku bani address, kuma idan ɗaya na son zuwa wajen ɗaya kunga zaku yi ta waya kuna yiwa juna kwatance har ku samu ganawa".

Tsabar murna ji suka yi kamar su miƙe su rungume shi saboda daɗi, shi kuma abu uku ne yasa ya yi musu wannan babbar taimako, na farko saboda Allah, na biyu saboda ya kamu da matsanancin son Rimsha lokaci guda, na uku kuma yana jin Ayla tamkar kanwarsa, tamkar yar uwarsa ta jini, wannan dalili ya sa ya tsaya musu.

After some hours👌

Bayan sun yi sallar mangariba. Da sallama Ahmad ya shigo cikin ɗakin, ya dawo daga masallaci. Cike da kulawa ya ce "Ku shirya muje cikin gari mu sayi abinci daga nan sai na saya muku waya, sannan kuma daddy ya gaya mini jirgin Kaduna zaku hau, Queen of beauty, idan kin sauƙa a Kaduna zaki iya zuwa park ki shiga motar Katsina?" Shiru ta yi tana tunani ita da bata san ko ina ba, shima Katsinar tun da suka koma sau ɗaya ta fita, sai kuma ranar da aka sace ta shine rana ta biyu.

Ganin ta yi shiru yasa ya ce "To idan kuka sauƙa a airport zamu yi magana, zan kira ki a waya sai na gaya miki in da zaki je, sai ki tari mashin zuwa wajen, idan kin je wajen sai mu sake yin waya, daga nan zan gaya miki in da motocin Katsina suke, idan kin je wajen sai ki haɗa ni da driver a waya zamu yi magana da shi, dan nasan wannan shirun da kika yi ya tabbatar baki san ko'ina ba a Kaduna, bayan haka kuma dama nasan da wuya ki san wani wajen tun da ba garin ku bane".

Sunkuyar da kai kasa kawai ta yi ba tare da ta yi magana ba.

"Queen of beauty kuma Queen of kunya, to dai yanzu ku shirya mu je mu dawo da wuri dan kuzo ku yi barci da wuri, saboda jirgin karfe 7 zaku hau". Yana kai karshen maganar ya juya ya fice daga ɗakin, dan ya basu damar shiryawa a nutse.

Hijabi kawai suka ɗaura saman Abayar jikin su, sannan suka sanya takalmar Kausar da suka zo da shi, domin a kayan da ya sayo musu babu takalmi. Har sun kai bakin kofar ɗakin zasu fita, sai Rimsha ta dawo da sauri ta ɗauki perfume na shi dake saman drawer mirror ta fesa, dariya Ayla ta yi, kasa kasa ta ce "Ɓarauniya, to dai shi turare ba'a satarsa". Wucewa wajen switch na ɗakin ta yi, ta kashe wutar tana faɗin "Anyi ɗin idan mutun shima yana da ra'ayi ba sai ya yi satar ba". Sai faman guntse dariya Ayla take yi ta ce "Allah yasa ma turaren makale mata ne, ki makale masa ki ce ba zaki koma ba".

A kule Rimsha ta ce "Bakar muguwa, to dai nariga ki na ce Allah, kuma ta Allah ba ta mutun ba!" tuntsurewa da dariya Ayla ta yi, daman dariyar ya ciwota sosai, wato ita dai Rimsha duk wani zance da zai kawo mata zancen kada ta koma gida bata son shi ko da wasa.

Haka suka fito waje sai faman guntse dariya Ayla ke yi, ita kuma Rimsha ta sha kunu ta murtuke kamar hadari fuskar nan ta zama, dama Rimsha ba baya ba wajen iya tsare gida, idan aka ɓata mata rai.

Tsaye suka same shi yana kallon gari ya juya musu baya. Sallama suka mashi, juyowa ya yi yana kallonsu da yake hotel ɗin akwai wuta, an tada gen, hakan ya bashi damar kallonsu sosai, Rimsha Queen of beauty tamkar ka sace ta ka gudu da ita saboda kyau, hijabin ya mata kyau sai dai bai karisa kai har kasa ba.

Sai murmushi yake yi ya ce "Muje ko?" Ya yi maganar yana nuna musu hanya, gaba suka yi ya bi bayan su, yana kallon yadda suke tafiya a nutse ɗaiɗai abin su, ba hayaniya ba hargaga kamar yan matan kauye, a nutse suke. Wani azababben son Rimsha ne ke kara ninkuwa masa a zuciyarsa, sai wani murmushi yake yi shi kaɗai, kamar ba lafiya ba.

Ya kasa daina kallon su har suka isa wajen mota, abin mamaki sai yaga dukkansu sun shiga gidan baya, ɗan ɗaure fuska ya yi kafin ya ce "Ni driver ku ne? Ku fito ku dawo gaba". Ba dan sun so ba suka fito suka dawo gidan gaba, sannan shima ya shiga ya tada motar suka bar wajen.

Challenge suka fara nufa, wato kasuwar wayoyi. Wayoyine iri daban-daban a wajen, gasu nan a zube kamar kyauta ake rabawa.

Wani katafaren shago suka shiga, kun san yarabawa da son kyawawan mata, duk in da Rimsha ta wuce sai sun kalleta sun sake kallonta, da yake ko ina a wajen akwai hasken wuta sosai, saboda business ɗin su.

Wani irin bakin ciki Ahmad ya ji, haushi ya kama shi yadda suke ta kallon Rimsha, ji ya yi dama bai zo da su ba, kuma yanzu in da suka yi parking na motar su akwai ɗan nisa, ga shi yana son su yi sauri dan su koma su yi sallar isha, haka ya hakura ya danne suka shiga cikin shagon.

Wayoyi yasa aka kawo musu kala, huɗu ya ce su saɓi dai ɗaya, duk ka kuma Samsung ne masu tsada, A72 ne da A 12 sai A10 guda biyu.

Kallon su ya yi ya ce "Ku zaɓi wanda kuke so a ciki" Mai shagon duk da baya jin Hausa ya fahinci zaɓi Ahmad ya basu ai kuwa ya yi maza ta cap ke da cewa "Wannan kyakkyawar yarinyar da A72 ta dace" ya yi maganar cikin harshen turanci ba yarabanci ba, ai kuwa Ahmad ya zo har wuya, cikin ɓacin rai ya ce ba za su sayi wayar a nan shagon ba sun fasa, sosai mai shagon ya rinƙa ba shi hakuri, amma ina ya murje idanuwansa ya ce ba za su saya ba.

Haka suka wuce zuwa wani shagon, a nan ya sai musu A12 guda biyu iri ɗaya har color ma ɗaya, sannan suka fito, ya saya musu sim card, sai ya wuce da su wani katon super market dake gaba da challenge ɗin kaɗan.

Ko da suka je wannan super market ɗin kuwa, saboda karfin hali irin na Ahmad har da cewa su zauna a mota su jira shi, dan tsabar kishi, haka suka zauna ya rufe su tare da kunna musu Ac, ya wuce ya je ya yi sayayyar da zai yi ya dawo suka wuce Item 7, a nan suka sayi abinci suka dawo gida.

Lokacin da suka dawo karfe 9:10. A hanzarce Rimsha ta yi alwala ta gaba tar da sallar isha, shi kuma Ahmad suna dawowa da ya rako su ɗaki ya juya ya fice, ita kuma Ayla saman drawer ta zauna tana kallon Rimsha.

Bayan ta idar da sallah ne, suka jawo ledar abin cin da ya basu kafin ya fita da nashi, sosai suka ci abincin, sannan suka haɗa da fruits da ya sawo ɗazun kafin su fita, dama kafin ya fita ɗakin sai da ya ce musu su sha fruits ɗin su ya sayawa.

Bayan sun gama, sun tattare komai tsab, sai suka yi kwanciyar su a kasa wajen da suka kwanta ɗazun.

Can kuma kamar wayan da a ka tsikara, haka suka ta shi suka kunna kallon a Tv dake ɗakin, suka kama tashar zee wold.

Sai karfe 10 daidai Ahmad ya dawo hannunsa ɗauke da kananan trolley guda biyu, kusa da nashi trolley ya ajiye sannan ya zauna saman dadduma suka ɗan yi hira kaɗan, zuwa karfe 10:30 ya ta shi ya sanya musu wayoyin su a charji bayan ya sanya musu sim card da ya sai musu, saboda suna sauri gobe zasu tafi hakan yasa ya saya musu sim mai register amma ya ce musu idan suka koma su yi register wani sim ɗin da kan su. To suka amsa mashi da shi, sannan ya musu sallama ya ce su rufe kofar da key ta ciki su kwanta su yi barci da asuba zai zo ya tashe su.

Ba karamin daɗi suka ji ba, dama suna ta tunanin ya za su yi su kwana da shi ɗaki ɗaya, ashe dai yana da hankali sosai. Yana fita Ayla ta haye gado ta baje kafafu tana faɗin ",Yau dai ba gadon Kausar zamu kwana ba". Ita kuma Rismha wuce wa ta yi ta rufe musu kofar ɗakin da key sannan ta shiga toilet dan yin wanka.

Bayan ta yi wanka ta fito ta shirya cikin ɗayar abayar da ta rage a ledar da ya kawo musu ɗazun, bayan ta gama ta haye gado tana faɗin "Ayla ki je ki yi wanka mana". Ina Ayla barcin gajiya ya ɗauke ta baiwar Allah, yau dai sun kwana cikin farinciki, ita ma Rismha tana kwanciya ba jimawa barci ya yi awon gaba da ita. Amma kafin ta yi barci sai da ta ɗan yi tunani a kan ya za'ayi su hau jirgi ba passport ba komai, ko dai private jet ne, ko kuma sai da safe idan sun je zai musu passport ɗin. Da wannan tunani a ranta ta yi barci.

(Uh su Rimsha yau ana busy kuma ana murnan komawa gida, ba'ayi tunanin masoyi GAR ba🤣 an samu freedom)

Asuba ta gari

Nima kuma na haɗa kayana zuwa gidan Abba, sai mun haɗu gobe dan jin yadda zata kaya a gidan Abba. Na barku lafiya da yar dan mai duka. [11/17, 12:27 PM] +234 906 579 6460: 💖💖TRIPLET'S💖💖

💖💖GIDAN ABBA💖💖

Yau ma kamar jiya Umaisha ta yi wuni mai cike da annashuwa da farinciki, sakamakon Rufee ta sake dawowa, tun karfe 7 na safe ta dawowa gidan, yau ko shara Umaisha ba ta yi bare kuma a kai ga su gyaran ɗakin Abba da Ammie.

Ita kuwa Ammie kwata-kwata bata shiga harkar Umaisha ba, kamar bata nan a gidan ita ma, ta yi shiru a ɗakin ta, saboda tana tsoron bala'i Rufee.

(Toh fa wannan shine gaba ma da gaban ta)

Su Imran kuwa, wannan zuwa Kano da suka yi, sun sallami su Zuwaira masu aikin gidan su Jelly, Imran ya ce musu idan komai ya daidai ta zai zo har kauye da kansa ya ɗauko su, sannan ya ɗauki dollyn Jelly dan su dawo da ita Kaduna, da suka ta shi tafiya, sun rufe ko'ina na gidan, duk wani kayan wuta dake jone a sucket sun cire shi, daga karshema Akil ya kashe wutar gidan gaba ɗaya suka wuce suka kama hanyar Kaduna rai a ɓace domin har wa yau ba su yi nasara ba, amma sun bar baba mai gadi a gidan basu sallame shi ba, sun ce ya cigaba da kula da gidan.

Shi kuma baban Muneer yana yawan zuwa neman daddyn Jelly sai dai Allah bai taɓa haɗa shi da su Imran ba, ba'a kwana biyu bai zo gidan ba, sai dai su Zuwaira su ce mashi daddyn Jelly ya yi tafiya, ya ci alwashin nan da wata ɗaya in har daddyn jelly bai bayyana ba, to zai saki wannan video wa duniya, a cewar sa daddyn Jelly ai ɓuya ya yi, domin Company sa na aiki, bai san cewa Imran da Irfar ke tafiyar da company yanzu ba, kuma yana zuwa har company ya tambayi Engineer Muhammad Imam shin ko Maik ya dawo, kullum amsa ɗaya yake ba shi shine a'a bai dawo ba, duk kuma mafiyawancin lokutan da baban Muneer ke zuwa, su Irfan sun bar company, kuma a zahirin gaskiya daddy'n Jelly bai gayawa kowa abin da ke tsakanin shi da baban Muneer ba, a cewar sa idan ya yi hakan ya tonawa kan shi da kan shi asiri ne, shiyasa ya rufe maganar kawai, ya yi wa su Imran karya.

Sai Misalin karfe 6 na yamma su Akil suka shigo gida, gaba ɗaya a gajiye suke, sai wani ɗaure fuska Akil yake yi, to da yake shi Akil part na shi a cikin nasu Ammie yake, shi kuma Imran daga waje harabar gidar part nasa yake ta gefe, bai haɗu da nasu ba, hakan yasa suka rabu da Imran a harabar gidan, Imran ya wuce part nasa hannunsa riƙe da dollyn Jelly, duk ta rame, saboda bata cin abinci sai su Zuwaira sun mata ɗure.

Shi kuma Akil ya nufi cikin gida. Yana shigowa babban palon su, ita kuma Ammie tana saukowa daga sama. Sauri sauri ya yi mata sannu da gida zai wuce part nasa, dan a gajiye yake sosai.

"Ina kuke yawan zuwa ne Akil?" Ammie ce ta jefa masa wannan tambayar, wadda ya ji ta tamkar saukar aradu, domin kuwa idan har ya gaya mata cewa gidan bappansu suke zuwa neman yar uwarsu ta gefen Abba, to ba makawa tsine masa zata yi, ga shi shi kuma bai iya karya ba, shiya lokacin da ya auri Umaisha ya fito karara ya gaya musu gaskiya, bai ma san ta ina zai fara yin karyar ba, to idan ma zai yi karyan me zai faɗa mata.

Ganin ya yi shiru ne yasa ta ce "Akil lafiya kake kuwa?" Yar firgita ya yi ya ɗago yana kallonta "Ammie na ga ji sosai ne, daga Kano fa nake, dan Allah ki bari naje na huta kin ji? Idan ba haka ba zan iya faɗuwa". Jin haka yasa ta ce to ya wuce part na sa da wuri ya je ya huta, kuma a gaskiya ita bata ma san asalin garin da yan uwan Abba suke ba, bata san suna Kano ba, a iya nan Kaduna ta sani, shiyasa bata yi wani tunani ba ta ce ya wuce part na shi, da ta sani ko tana zargin yan uwan Abba na Kano to ba faɗuwa Akil zai yi ba ko mutuwa zai yi sai ya gaya mata gidan uban da ya je, idan kuma ya gaya mata, ta ji cewa wajen yan uwan Abba ya je, to ba makawa tsine mashi zata yi, kamar yadda ya faɗa.

Da sallama ɗauke a bakinsa ya shigo part ɗin, gaba ɗayan su suna palonsa, Akila, Rufee, Aafia, Umaisha, kasan cewar 24 hours akwai wuta a gidan su, hakan yasa gaba ɗaya ko'ina haske ya gauraye cikin palon.

Akila da Umaisha ne suka ta shi a tare suka nufe shi suna faɗin "sannu da dawowa yaya Akila". Wani haɗiyar yawu Rufee ta yi, a ranta ta furta "dama nan ne gidan gayen nan? Sorry Umaisha dole na ari mijinki na yan kwanaki"

(Tofa rashin sani ya fi dare duhu, in dai Akil ne bismillahi)

Cikin rawar kafa ta miƙe tsaye tana faɗin "Sannunka da dawowa mijinmu" galala Aafia ta saki baki tana kallonta. Da yake shima Akil ɗan air ne ko kallon in da take bai yi ba, ya rungumo Akila ta gefe Umaisha ta gefe yana faɗin "Na yi missed na ku my pleasures".

Lafewa suka yi a gefe da gefen kirjinsa suna fuskantar juna, sai murmushi suke yi kamar dukkan su matan sane.

Cike da zolaya ya ce "Heartbeat ke daga nan na sallame ki, ki zauna a nan da su Aafia, ke kuma my baby mu je ki yi mini wanka ki mini tausa dan na gaji sosai". Turo baki Akila ta yi, ta turɓune fuska a shagwaɓe ta ce "Wlh yaya Akil kana cimin fuska, kana saka Aunty Umaisha tana rena ni, kuma na fita shekaru, haka ranar ma har da ce mini ta yi wai mijinta ya kusa dawowa na wuce ɗaki na, wannan cin fuska Allah ya yi mini yawa" ta kai karshen maganar tana raba jikinta da na shi, ita a dole ta yi fushi.

Cikin sauri ya jawota ta dawo jikin nasa, cikin sigar rarrashi ya ce "Haba my heartbeat wasa nake yi miki ai, ke ai kin san tawa ce, ban isa ba, amma yanzu dai ki zauna a nan ina zuwa" ya kai karshen maganar yana jan hancinta,

Turo baki ta kuma yi kamar zata saki kuka, ita dai Aafia bin su kawai take yi da ido, abin gwanin ban sha'awa, sai fatan Alkhari da fatan kasancewa cikin farinciki na har abada take yi musu, saɓanin Rufee da take kallon su take ayyana wa a zuciyar ta, wannan farinciki da ita ya kamata Akil ya rinƙa yi, duk wannan tarairaya da soyayya ita ya kamata ya yi wa ba Umaisha ba.

Umaisha kuwa tana lafe a kirjin mijinta ta fito da ɗan harshenta waje tana yiwa Akila gwalo, a kule Akila ta ɗaga hannu zata make bakin nata, cikin sauri Akil ya tare hannun nata yana faɗin "So kike yi ki fasa mini baki na ko? To baki isa ba, ai gara ki buge nawa ba nata ba, dan idan kika buge nata sai na fita jin zafi da ɓacin rai"

(Akwai wanda ya gane zancen Akil kuwa?🤔)

"Kai yaya Akil yanzu wlh ka dawo mai son kai sosai" "Wai ku ba zaku kyaleni naje nayi wanka na huta ba, sai na faɗin muku a nan ne? Ku dama idan kuka haɗu kuka sani a tsakiya Allah ne kawai ke kwatata".

Raba jikinsu Umaisha ta yi tare da riƙo hannunsa tana faɗin "Muje hai yaya Akil, muje na maka wanka bar heartbeat ɗin nan bata da aikin yi sai dai ta zo ta dame mu" ta kai karshen maganar tana yi wa Akila gwalo, kwafa Akila ta yi tana faɗin "Wlh ba zan bari ki ba, kin ɗauki bashi, kuma sai na rama, nice ma bani da aiki ya ba? Ba komai".

Shi dai murmushi kawai yake yi, yana matukar kaunar Akila dan tana son duk wani abin da yake so, kuma tana goya masa baya sannan ta taya shi kula da wannan abin, idan baya nan sosai take kula da Umaisha, ko motsi Umaisha ta yi sai ta tambaye ta me take so, sai dai idan ta tafi school ne, sannan suna sharing secret tare da Umaisha, suna kuma rufawa juna asiri, yanzu ma duk abin da Ammie ke yi wa Umaisha Akila tana sane, sai dai abin da yasa bata gayawa Akil ba, tana tsoron idan ta faɗa Ammie zata iya saka shi ya saki Umaisha, shiyasa ta yi shiru, amma fa tana nan tana kulla ta yadda za'a yi Akil ya canzawa Umaisha gida, dan kullun sai ta yi mata kukan abin da Ammie ke yi mata, sannan kuma in dai tana nan Ammie tasa Umaisha aiki to tare suke yin wannan aikin, shiyasa yanzu ta iya wanke-wanke da ɗan aikace-aikace gida.

Wucewa cikin ɗaki Akil da Umaisha suka yi, ita kuma Akila ta dubi su Aafia ta ce "Kuzo mu je ɗaki na mu zauna, idan yaya Akil ya fito zai mayar da ku gida..." A hanzarce Rufee ta tari numfashi ta da cewa "A'a ki dai bari mu zauna a nan ɗin tun da mu bakin Umaisha ne" da yake Akila bata kawo komai a ranta ba, sai ta biye musu kawai suka zauna a wajen.

Shi kuma Akil su na shiga ɗaki ya jawo matarsa ya runguma yana faɗin "Nayi kewar ki my baby", ya kai karshen maganar yana sumbatar goshinta. Hannayenta ta kai saman botir na rigarsa ta wuya ta fara ɓalle wa tana faɗin "Ai nima na yi kewar ka yaya Akil". Cire hannayen nata ya yi ya kankame ta a jikinsa sosai, a nitse ya haɗe bakin su ya fara bata hot kiss, ba ɓata lokaci ita ma ta fara mayar masa da martani, nan take suka birkicewa juna, hannun sa ya zura cikin rigarta ya fara bata sako na musamman.

Sun jima a haka har sai da karfin su ya kare, Umaisha na kokarin faɗuwa mashi kasa, sannan ya yi saurin sakin ta, idanuwansa duk sun sauya launi, har wani duhu-duhu yake gani. Da kyar ya iya sai ta nitsuwarsa ya wuce toilet dan yin wanka.

Ita kuma ta kasa binshi ta cire masa kayan, a bakin gado ta zauna tana sauƙe ajiyar zuciya dan dama in da sabo ta zaba Akil ya kware wajen iya soyayya, yanzu zai sata ta mance duk wani damuwa da take ciki komai girmar damuwar, hakan yasa da ya dawo gida duk wata matsalar ta, ta kau kenan, sai zallar farinciki.

Tana zaune a wajen ta kasa motsawa har ya fito wanka ɗaure da towel a kugunsa.

"My baby this time fa kin yi kewata sosai kema na ga alama" ɓoye fuska ta yi tana murmushi, domin kuwa ya faɗi gaskiya ta yi kewar shi sosai da sosai.

Yau dai komai shi ya yi wa kansa, har kayan sawa shiya ciro wa kansa dan ya lura babyn tasa ta karɓi wuta sosai har lokacin bata dawo normal ba.

Jallabiya ya sanya a jikinsa sai tashin kamshi yake yi, ya shinfiɗa dadduma ya gabatar da sallar mangariba, ita kuma Umaisha miƙewa ta yi da kyar ta fito wajen su Aafia, ta ce suje ɗakin Akila su yi sallah a tare, ko kuma su shiga ɗayar ɗakin kusa da nasu, Rufee ce ta ce lallai su shiga ɗakin kusa da nasu, a nan za su yi sallah, A'afia ta lura Rufee bata son barin part ɗin ne tun da ta kalli Akil ya dawo, Allah dai yasa ba wani abin take shiryawa ba.

A ɗayar ɗakin suka yi sallah a tare gaba ɗayan su har Umaishan, sai dai ita Rufee bata yi sallar ba, ta ce musu wai tana period, Aafia tasan karya Rufee keyi domin kuwa kullun haka take ce musu a school wai tana period, har suka gane karya take yi, a zahirin gaskiya kuma wani lokaci bokanta ke hanata yin sallar gaba ɗaya, wani zubin ya ce mata iya sallar mangariba kawai ya halakta mata da tayi, wani lokaci kuma sai ya ce kwata-kwata ma kada tayi.

Bayan sun idar da sallah ne suka fito palo suka zauna suna hira.

Cikin dabara Umaisha ta zame jikinta ta gudu wajen mijinta abinta, dan tana kewar shi sosai, ashe Rufee na ankare da ita, tana ganin tafiyarta, sai wani ciza laɓɓa take yi alamar tana kishi da Umaisha, kuma tana jin haushi.

Umaisha kuwa tana shiga cikin ɗakin ta isko shi yana miƙe a saman bed nasu.

Cikin sauri ta tafi ta faɗa jikinsa tana murmushi, shiru ya yi mata kamar bai san da zuwanta ba. A shagwaɓe ta ce "Yaya Akil meyafaru?" Shiru ya yi kamar ba shi a wajen, ganin haka yasa ta kama lips nasa na kasa ta fara tsotsa kamar sweet.

Kwace lips nasa ya yi yana lumshe idanunsa alamar ya ji daɗin hakan, sai dai kuma fushi yake yi da ita, kasa ta yi da murya cikin girmamawa ta ce "Kayi hakuri" a kule ya ce "Ba zan yi ba, ai baki damu da ni bane, har da zaki tafi ki barni a ɗakin nan tun jiya fa rabon mu da juna..." Bata bari ya karisa maganar ba ta yi maza ta cabke lips nasa tana mashi wasa da hannun ta a saman babban sashe.

Jin wannan salon yasa ya mance da fushi ya kara jawota jikinsa suka lula duniyar sama jannati.

Su Aafia kuwa sai hira suke yi a palo, amma ita Rufee kunnanta da hankalinta duk yana jikin kofar bedroom ɗin su Akil, tana mutuwar son taga meke faruwa a cikin ɗakin, burinta kawai ta ga me suke yi a cikin.

Kiraye kirayen sallar isha ne ya dawo dasu daga duniyar sama jannati da suka lula, da kyar ya iya saita kan shi tare da kamewa, sannan ya miƙe zaune duk idanuwansa sun rine tamkar ba shi ba, ita ma Umaisha duk ta birkice masa, sai wani lumshe idanu take yi.

"Ta shi kiyi wanka kizo ki yi sallar isha sai ki shiya ki saka nikaf zamu fita restaurant" ya yi maganar da murya kamar mai raɗa.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull