Kenza eBookz

Triplets book 2 complete - Chapter 32

Triplets book 2 complete - Chapter 32

Triplets book 2 complete Chapter 32: Triplets book 2 complete Chapter 32. Gefenta ya zo ya zauna daidai lokacin da Ummi ta fito daga cikin ɗakinta, tana…

4,449 words

Gefenta ya zo ya zauna daidai lokacin da Ummi ta fito daga cikin ɗakinta, tana faɗin "Baby kizo ki shirya mu tafi, ko kuma in tafi in barki". Ganin Nawid a wajen yasa ta ce "Yaushe ka dawo Nawid?" Ajiyar zuciya ya sauƙe kafin ya ce "Yanzun nan na dawo, dan Allah Ummi ina Abbo? Ina son yin magana da shi" "Abbonka yana nan, yana part ɗin su Afnan sai ka bari sai ya fito ko kuma ka kirashi a waya, bana son ka je can, dan dai kasan sauran, idan kaje ba zaku wanye lafiya da su ba".

Guntun tsaki ya ja irin yana cike da haushin su Afnan ɗin, a yatse ne ya ce "No zan jira shi sai ya dawo part ɗin nan, amma ina zaku je na ji kina cewa baby ta zo ku tafi". Murmushin ne ya bayyana a kan fuskarta ta ce "Wajen Aunty Hajizatu zan je mana" ɗan kishingiɗa ya yi yana faɗin "Yaushe Aunty Khadija kuma ta dawo?" "Kwana uku da suka wuce ta shigo kasar, tun da ta shigo take kirana wai nazo muje gidan mijinta, to ban samu zuwa ba sai yanzu nake son in je in ji me kuma zata je yi a gidan tsohon mijin nata". Jinjina kai ya yi yana faɗin "Hmm adawo lafiya, amma dai Ummi dan Allah kada ki biyewa Aunty Khadija duk da take yarki ki" Harara ta wurga mashi kafin ta sa kai ta wuce wajen Jelly take ta zuba kallonta kamar bata a cikin palon.

Hannunta ta kama ta mikar da ita tana faɗin "Wuce mu je ko na tafi na barki". Ba dan ta so ba ta miƙe suka wuce cikin ɗaki. Shima Nawid ya miƙe ya wuce bedroom nasa.

A ɓangaren Imran kuwa, kai tsaye gidan su ya nufa. Ya na yin parking ya fito ya buɗe kofar gefen da Rimsha take a ciki, cikin natsuwa ya sanya hannu ya ɗauke ta cak, domin shi har yanzu kallon yarinya karama yake yi mata, jin an ɗauketa yasa ta farka a razane, ganin ta buɗe idanunta ya sa ya ce "Kin tashi lafiya?" Ya yi maganar ba tare da ya sauƙeta ba, kuma bai daina tafiya ba, kokarin zamewa daga jikin nasa ta yi ba tare da ta yi mashi magana ba, ganin haka yasa ya sauƙeta yana faɗin "Sorry bana son tashin kine shiyasa" shiru bata yi masa magana ba, domin kanta wani mugun ciwo yake yi mata, har wani jiri take gani saboda barci bai ishe ta ba.

Da hannu ya yi mata nuni da kofar palon, kusan a tare suka shiga, zaune suka isko Ammie saman sofa, bakinsu ɗauke da sallama suka shigo ciki. Juyo da kallonta Ammie ta yi izuwa kansu, a zabure ta miƙe tsaye tana kallon Rimsha, gaba ɗaya tsikar jikinta sai ta shi yake yi, kamar wadda taga wani mugun abin tsoro, jikinta har kerma yake yi, tana haɗe words cikin tsawa ta ce "Wace ce ke?!"

Zaro ido Imran ya yi yana mamakin yadda Ammie ta ɗaga murya haka. "Koma wace ce ke ki fita daga cikin palon nan yanzun nan, bana son ganinki" sosai Rimsha ta tsorata, shi kanshi Imran ya tsorata juyowa ya yi yana kallon Rimsha ko zai ga wani abin a tattare da ita wadda ya sanya Ammie ta ce bata son ganin ta, amma ina bai ga komai ba sai ma kyakkyawar, ga kyawawan dara-daran sleeping eyes nata masu ɗauke da barci.

Tsawa Ammie ta kuma daka musu "Imran idan baka fitar da yarinyarnan daga palon nan ba, wlh zan tsine maka albarka, nace maka bana son ganin fuskarta ko?!!" Tashin hankali juyawa ya yi ya riƙo hannun ta suka fice daga palon. Suna fita Ammie ta zube saman sofa tama mai da numfashi sama sama, alamar fuskar Rimsha ya tsorata kuma ya ɗaga mata hankali sosai.

Shi kuma Imran yana fita palon kai tsaye part nasa ya wuce hannunsa riƙe da nata, wasu siraran hawayene suka fara bin kuncinta, ba tare da Imran ya lura da hakan ba.

Suna shiga part nasa ya ce "Kada ki damu a nan zaki zauna, kada ki je cikin gida, kada ki fita ko kofar palon nan, kiyi zaman ki a nan, heartbeat ɗin mu Akila zata rinƙa zuwa kuna hira, wancan ɗakin shine naki, ni kuma ga nawa ɗayar, kada ki sa komai a ranki, duk abin da kike so ki tambaye ni kai tsaye kin ji ko?" Ya kai karshen maganar yana dawo da kallonsa kan fuskarta.

"Subhanallah Rimsha kukan me kuma kike yi haka?" Ya yi maganar yana goge mata hawayen nata, kasa magana ta yi sai ajiyar zuciya kawai da take sauƙewa, sai rarrashinta yake yi har ta yi shiru, sannan ya kai ta har ɗakin nata ya fito domin ya ɗauko mata trolley ta.

Ɗaki ne mai bala'in kyau kamar dai ɗakin ta time da daddynta yake raye, ɗakin ya yi kyau sosai, ga katafaren bed 6 by 7 an shinfiɗa masa bed sheet na alfarma mai kyau launin pink da white color, abin ba'a magana, sai kamshi ke ta shi a ɗakin. Kai tsaye toilet ta nufa dan yin wanka ta ɗauro alwaya ta gabatar da sallar azahar.

Lokacin da Imra y kawo mata trolleynta tana cikin toilet ajiye mata kawai ya yi, sannan ya wuce nashi ɗakin dan ya je ya yi wanka shima ya yi sallah.

Bayan yan wasu awanni.

Shirye take tsab cikin doguwar riga ɗaya daga cikin wanda Ahmad ya saya mata, ta yafa mayafin rigar a kanta, tayi kyau sosai kamar ka sace ta ka je ka ajiye ta kayi ta kallonta dan kyau, sai dai kallo ɗaya zaka yi mata kasan bata cikin walwala da farinciki. Palon ta fito ta ɗan kara gyara shi fes, sannan ta nufi wani wajen da take zaton shine Kitchen na part ɗin.

Ai kuwa Kitchen ne, ko ina a gyare tsab, sai dai da alama ba'a amfani da Kitchen ɗin sosai, ana kwana biyu ba'ayi amfani da shi ba, ciki ta shiga ta fara yan dube-duben ta, akwai komai da mace zata buƙata a cikin Kitchen ɗin, irin su pot, spoon, plate, cup, da kuma ingredient na miya, da sauransu, sai dai babu kayan abinciki a cikin kitchen ɗin, hakan yasa ta nufi wani ɗan karamin kofa dake cikin Kitchen ɗin wadda take zaton store ne.

Tana shiga ciki ta yi arba da kayan abinci kala-kala, wani daɗi ta ji, cikin sauri ta fito ta ɗauki pot mai kyau daga cikin sets da suke jere cikin drawer kitchen ɗin, a wanke yake tsab, amma sai da ta sake wankewa, sannan ta ɗaura ruwa a saman gas, farar shinkafa ta dafa, sai kuma ta rasa da me zata yi miya, domin bata ga kayan miya irin su Tomatoes a cikin Kitchen ɗin ba, yan dube-dube ta fata yi ko zata ga kayan miyar, can ta hango wani katon freezer daga gefe, cikin sauri ta karisa wajen ta buɗe, ai kuwa shake yake da kayan miya nama kifi da sauran su, shiru ta yi tana tunanin kenan yaya Imran yana yin girki da kanshi ne? Ko kuma dai yana da mata ta yi tafiya ne?.

Ganin babu wani abin da tunani zai tsinana mata, sai ta ɗebi iya adadin kayan miyar da take buƙata, tazo ta wanke su tas ta ajiye a gefe, sai ta koma ta ɗebo nama kamar an sata, haka tazo ta wanke namar ta gyara shi fes tare da yi mashi haɗi da kayan kanshi da sauransu ta ɗaura saman wuta, bayan ta ɗaura sai ta ɗauki kayan miya ta zuba a blender ta fata markaɗe.

Bayan ta gama nama ya dahu ta soya shi ta kwashe, sai ta zuba kayan miya ta fara soyashi shima. Haka ta haɗa miyar nan ya ji kayan kamshi da nama, sai tashin kamshi yake yi, ta gama komai ta wanke duk wani abin da ta ɓata sannan ta zuba abincin a cikin kuloli masu kyau, ta jera a saman tray ta ɗauka da niyar fitarwa palo, juyawar da zata yi suka yi ido huɗu da shi, yana tsaye ya goya hannu a kirji, yana sanye da jallabi ash color, ya zuba mata ido kallonta kawai yake yi.

Wani irin tsorata ta yi saura kaɗan ta saki tray ɗin abincin ya faɗi kasa. "Asarar abincin zaki yi mini ko? Baki son yau naci girkin first lady kenan?" Ya kai karshen maganar tare da karisowa cikin Kitchen ɗin ya karɓa mata abincin yana faɗin "Waye ya koya miki girki haka? Nafi 30mins ina tsaye ina kallonki, karar blender da kika kunna ta fito da ni". Ya yi maganar yana fita Palo.

Bayansa ta bi tana faɗin "A gidan su Kausar na koyi girki, sannan kuma ina da takardar girkin ina koya".

Saman table ya ɗaura tray sannan ya ce "Gaskiya ne ga shi kamshin abincin duk ya addabawa cikina yasa sai yunwa nake ji, amma fa wannan shine first and kuma last kada ki sake yin girki, domin ba yar aiki na ɗauko ki ba, ki bari zamu rinƙa fita mu sawo, wannan kayan da kika gani a kitchen ɗin ma ina ajiyewa ne saboda abokaina, akwai wasu daga cikinsu basu cin abincin restaurant sai dai su girka da kansu, to saboda su nake ajiyewa". Turo ɗan bakin nan nata ta yi tana faɗin "To nima ai ina daga cikin mutanen da basu cin abincin restaurant, ni ba zan iya ba gaskiya, dan Allah ka bari zan rinƙa yin girkin da kai na". Baya son ɓata mata rai dan haka sai ya amsa mata da to Shikenan, daman kun san ta da son iya girki, sai murna take yi, shi kuma ya ce zai ɗauketa su je shopping anjuma da daddare ya saya mata kayan sawa da su man shafawa da duk wani abin bukata sannan ya saya mata littatafan koyan girki masu kyau.

Saboda tsabar murna ji tayi tamkar ta ringume shi, sai zuba mashi godiya take yi. Yau dai Imran zai ci abincin da ba na restaurant ba, ɗaukar plate ta yi ta fara serving nasa.

Zuba nata ido ya yi yana kallon ta, sai da ta shake masa plate ɗin tap da abinci, yana ta ce mata ya isa amma taki bari sai da ta cika plate ɗin, sannan ta tura mashi gabansa tare da miƙo mashi spoon, karɓa ya yi yana zuba mata Albarka, ba ɓata lokaci ya fara cin abinci dan dama yunwa yake ji, wani irin daɗi ya ji lokacin da ya kai abin cin bakin sa, ɗanɗano na musamman ya ji, nan take ya fara santi, ɗaukar wani plate ta yi ta zuba nata abincin ɗan kaɗan tana ƙoƙarin zuba miya, nan fa ya ce bata isa ba, karɓar serving spoon ɗin ya yi ya cika mata plate ɗin shima kamar yadda ta mashi, sannan ya bata dama ta zuba miya ta ɗauka ta wuce bedroom nata.

Subhanallah wani shegen daɗi ya ji lokacin da ya kai tsokar namar cikin miyar bakinsa, wow ya furta afili Rimsha ta iya girki, ga hannunta da zaƙi, haka ya buɗe cikinsa ya fara ci, yau ba abincin restaurant bane, bai san lokacin da ya cinye abincin nan tas ba, cikinsa kamar zai fashe saboda koshi, bai taɓa yin lodin abinci irin na yau ba.

A wannan hali Akila ta shigo ta same shi, dawowarta daga school kenan, tasha ruwan mamaki ganin yadda yake ta santin abincin, ta kasa hakuri har sai da ta tambaye shi.

Daɗi ya hana shi yin magana, da hannu kawai ya nuna mata kular abincin, buɗe kular ta yi, wani daddaɗar kamshin steew ɗin ne ya daki hancinta, cikin sauri ta ɗago ta ce "Yaya Imran wannan abincin wani restaurant ne?" Girgiza mata mai ya yi sannan ya shiga bata labari.

Ai kuwa da murnarta ta miƙe tana faɗin "Kai yaya kace na samu kanwa kuma mai koya mini girki, bari naje wajen ta" bata jira amsar shi ba ta wuce zuwa ɗakin da Rimsha take a ciki, . Akila baiwar Allah bata da matsalar komai, tana bala'i son mutane sosai. Da fara'a sosai ɗauke a kan fuskarta ta shiga cikin ɗakin.

Rimsha na cin abinci, domin lokacin da ta shigo ɗakin ajiye abincin ta yi sai da ta yi wanka ta shirya cikin wata doguwar rigar sannan ta ɗauki abincin ta fara ci, shiyasa Akila ta iskota bata kammala cin abincin ba.

Murmushi ɗauke a kan fuskarta ta ce "Sannunki da zuwa" ɗago kai Rimsha ta yi tana kallonta, lokacin guda ta sakar mata cool murmushi har sai da hakwaranta suka bayyana, a ruɗe Akila ta ce "Wow dimple, open teeth, dogon hanci, karamin baki, kyakkyawar gashin gerar, sleeping eyes da nake mutuwar so, kyau iya kyau duk sun haɗu waje guda, ya ilahi ya lillihi ka bani yarinya mai kama da wannan baiwar taka, kyau iya kyau". Dariya abinma ya bawa Rismha, zuba mata ido Akila ta yi tana kallon yadda take dariyar abin ba'a magana gwanin birgewa.

"Gaskiya kina da kyau sosai" Akila ta sake faɗa tana karisowa wajen da take zaune, saman mirror chair, miƙewa Rimsha ta yi dan ta bata wajen zama tana faɗin "Kece Akila ko?" Da sauri Akila ta gyaɗa mata kai ala'mar sannan ta ce "Yaya Imran ya baki Labarina ko?" "E ya bani labarinki ai ya ce mini ke ce bugun Zuciyar su gaba ɗaya gidan" kara faɗaɗa murmushinta Akila ta yi sannan ta karɓi plate ɗin abincin ta ce "Mu koma tsakiyar ɗakin saman carpet muci abincin a tare" to Rimsha ta amsa mata da shi, sannan suka koma saman carpet ɗin suka fara cin abincin a tare da spoon ɗaya, wannan ta ci ta bawa wannan kamar sun jima a tare haka suka yi sabon lokaci guda.

A ɓangaren Aafia kuwa, tun da ta suma a wajen bata farka ba sai washe gari da safe da Umaisha ta zo ta tashe ta, lokacin already ta mance komai kuma lokacin da dodannin suka ɓace ta farfaɗo daga sumar sai dai kuma barci ya ɗauke ta shiyasa bata tashi ba. Wanka ta je ta yi ta shirya zuwa school, bata zo da motar ta ba kuma Akil baya nan hakan yasa ta hau abin hawa zuwa school ko breakfast bata tsaya ta yi ba domin burinta kawai su haɗu da Rufee.

Karfe 8 daidai ta shiga cikin school, kai tsaye wajen da suka saba zama ta nufa, ai kuwa a nan ta isko Rufee tana zaune ta dukar da kanta kasa. Kusa da ita ta je ta zauna tana faɗin "Good morning Rufee, where is Anisa?" Ɗago kai ta yi bakinta a kunbure saboda dukan da Akil ya yi mata jiya, ganin bakin nata a kunbure yasa Aafia ta fara bata hakuri domin ta san menene sila. B komai Rufee ta ce mata sannan ta ɗaura da cewa "Aafia ina son ki rakani wani wajen idan ba damuwa" to Aafia ta amsa mata da shi sannan suka miƙe a tare suka nufi motar Rufee ɗin.

Rufeen ta ja su suka bar school ɗin. "Ina zamu je Rufee?" Aafia ta tambaya tana ƙoƙarin sanya wayarta a silent. "Wani waje zaki raka ni, ke dai ki zuba ido ba zamu jima ba" "A'a Rufee bana son yin nisa da school dan kin ga yaya Akil ya ce zai yi bincike kuma ga yaya Irfar yana gari, ina tsoron su zo school ba su same ni ba" ta yi maganar cikin raunanniyar murya.

"Kai A'afia kin cika tsoro wlh, to ba wani jimawa za mu yi ba, minti 40 ya yi zamu dawo" Allah ya dawo da mu lafiya shine abin da Aafia ta faɗa kawai, daga nan bata sake yin magana ba.

Sun yi tafiya mai nisa ya yin da suka sauƙa daga kan titi suka keta ta cikin daji, Aafia ta fara tsorata domin bata taɓa wuce school, shopping, kasuwa, sai kuma gidan su Imran, iya in da take zuwa kenan, amma yau ga shi har cikin daji suka shiga, hakuri ta yi ta jure ta zuba ido tana kallon yadda Rufee ke keta cikin dajin da motarta.

Wajen wasu guntayen bishiyoyi masu cikar ganye ta tsaida motar, sannan ta ce Aafia ya jirata tana zuwa, to A'afia ta ce mata amma zuciyarta tsorone a cike a cikin shi fal, kijinta har kerma yake yi, dan bata taɓa zuwa makamancin waje irin wannan ba, ita kuma Rufee fita ta yi daga motar ta kama hanya.

Cikin dajin ta kuma ketawa da kafarta, tun A'afia na iya ganinta, har ta kurewa ganinta. Wajen malaminta ta je, nan ta sanar mashi da cewa tana son ya kwance aikin da ya yi wa Abbi ya mai da shi kan daddyn Jelly, sannan ta bashi hoton Akil ta ce tana son a haukata mata shi, ya shiga duniya kowa ya huta, to bokan nata ya ce sannan ya karɓi hoton ya gaya mata kuɗin da zata biya, buɗe jakarta ta yi ta zube mashi kuɗin sannan ta masa sallama ta dawo wajen A'afia.

"Rufee me kika yi a cikin wannan daji haka?" A'afia ta tambaya fuskarta ɗauke da mamaki ga tsoro kamar zata yi fitsari a wando, shiru Rufee ta yi mata bata tanka ta ba ta kunna mota suka kama hanya.

Suna tsaka da sharara gudu suka ga an tare hanyar da wasu duwatsu, wani irin mahaukacin burki Rufee ta ja, domin basu san da wayan nan duwatsu ba, dan a lokacin da suke zuwa babu su a hanyar, kuma yanzu ma basu lura da su ba har sai da suka iso wajen, saura kaɗan ma su bi ta kai, Allah dai ya tsare suka gani.

Suna taka birki Rufee ta buɗe kofar motar zata fito kenan, wasu mutane suka fito daga cikin dajin hannayensu ruƙe da bindigu, ihu Rufee ta fara kurmawa ita kuma A'afia ta fara salatin annabi kawai. Cikin tsawa ɗaya daga cikin mutanen ya ce su fito daga cikin motar. Gaba ɗaya mutanen sun rufe fuskokinsu da irin rawanin buzayen nan, baka iya ganin fuskokinsu sai dai idanuwansu da hujin hanci da baki.

Ba musu suka fito jikinsu sai kerma yake yi, Rufee kuwa wage baki ta yi tana kurma ihu ko wani zai kawo musu ɗauki, ba imani bare tausayi ɗaya daga cikin bandit ɗin nan ya sanya bindiga ya harbeta a tafin kafarta suna faɗin "Idan baki yi mana shiru ba, sai mun harɓe ki a in da zaki mutu" Wani irin azaba take ji amma haka ta sanya hannu ta toshe bakinta tana hawaye.

Tasasu a gaba suka yi suka shige cikin daji da su, wani irin bakin azaba Rufee take ji, ga shi kuma sun ce sai dai ta taka kafar nata idan ba haka ba su fasata da bindiga, haka ba yadda ta iya ta fara taka kafarta suka bar wajen, suka bar motar a buɗe wayoyinsu da komai yana a ciki.

Cikin wannan azabar suka rinƙa taka kafafunsu a cikin wannan ƙungurmin dajin, banda sunan Allah ba abin da A'afia take kira, ita kuma Rufee kuka kawai take yi, azaba ya yi mata yawa, ga wahalar tafiya ga azabar sun fasa mata kafa ɗaya, sai jini yake zuna kamar me.

Sun yi tafiya mai nisan gaske, har suka wuce wani katon dutse kafin su iso wani waje kamar cam haka wajen yake, an yi ɗakuna da irin manya-manyan tampol ɗin nan.

Gaba ɗaya wajen kewaye yake da manya-manyan maza madaka kanti suna riƙe da bindiga suna tsaitsaye, da alama gadin wajen suke yi.

Suna isa wajen ɗaya daga cikin bandit da suka taho da su Rufeen ya ce "Kai Habu ku shigar da wayan nan ciki zuwa anjima idan su garba sun dawo, sai mu haɗa su mu ga yau mutane nawa muka kama" Wadda aka kira da Habun ne ya kariso wajen hannunsa riƙe da bindiga ya sanya irin rawanin buzayen nan shi ma ya rufe kai zuwa fiskarsa, baka iya ganin komai na daga fuskarsa sai ido, jikinsa na sanye da kaki na sojoji, a shekaru ba zai wuci 22 years ba.

Tasa su ya yi agaba zuwa cikin ɗaya daga cikin ɗakunan tampol dake wajen. Rufee dai ya sha azaba iya azaba, ga shi ba halin ta yi wata magana za su harbeta suka ce, ita kuma A'afia tunanin ta ɗaya shine idan su yaya Irfan suka je school ba su same ta ba me zata ce musu, ba ta yi tunanin cewa matsalar da take a ciki yanzu ya ci uban wanda take hangowa ba, a'a ita tunanin hukuncin yaya Irfan take yi, domin ita bata san kidnaping ba, labari kawai take ji, bata san yadda ake yi ba.

Habu na kai su bakin kofar ɗakin ya ce su shiga sannan ya juya ya bar wajen, jikin su a mace suka ja kafafunsu zuwa cikin ɗakin. Mata ne za su kai mata 30 a cikin wannan ɗan ɗakin, gaba ɗaya matan dake a wajen suna ƙoɗe alamar sunci bakar wahala, duk sun yi futu-futu da su, mafiyawancinsu akwai busasshen hawaye a kan fuskarsu alamar sun sha kuka, wasu kuma iyayene da yaransu kanana, wasu yan mata wasu kuma sun manyanta, abin gwanin ban tausayi, duk wata zuciya mai imani idan taga wayan mata sai ta zubar mu su da kwalla, saboda yana yin da ke a kan fuskokinsu ma kawai ya isa ya karyarwa da ɗan adam zuciyarsa, ya sanya shi kuka, ko makiyinka ba zaka yi mashi fatar kasancewa a waje irin wannan ba.

Babu wadda ta kula su kowacce daga cikin matan nan tana fama da kanta, tsuru-tsuru su A'afia suka tsaya sun kasa gaba sun kasa baya, ga kuma Rufee kafarta na mata ruwan bala'in azaba. Wata wace ce wadda take zaune daga ta bakin kofa ta miƙe kafafu yarta wadda ba zata fi shekara 14 ba ta tada kai da cinyoyinta ita kaɗai ta iya ce da su A'afia su shigo su zauna, ba musu suka je kusa da ita suka zauna a takure, dan dama sun ga ji, A'afia da ta zo zama sai da ta kakkaɓe wajen tas sannan ta zauna, ita kam Rufee zaman yan bori ta yi tare da ciki hannunta daga bakinta ta fara kuka kasa-kasa dan kada su ji.

"Sannunku da zuwa" matar ta sake yi masu magana, Aafia ce ta iya amsa mata ita kam Rufee ba'a magana da kyar ma take iya fidda numfashi.

"Da kin dai na wahalar da kanki kina zubar da hawayen ki a banza ma da ya fi maki, idan baki daina ba hawayen ne za su kare a banza" Cewar matar ta kuma yi maganar tana kallon Rufee.

A'afia ce ta yi karfin halin cewa "To saboda me zata daina kuka? Baki son su ji kukan nata har a sami wani mai tausayi ya tausaya ya taimaka matane?" "Taimako a lallai ke yarinya ce sosai" matar ta bata amsa ta kuma ci-gaba da cewa "Ai tun da ba su ji tausayinku wajen ɗauko ku su kawo ku nan ba, to fa duk abin da za su yi muku ba za su taɓa jin tausayin ku ko kaɗan ba, babu zancen imani a nan wajen, kawai ku yi addu'ar Allah ya kuɓutar da ku, amma a halin da muke a ciki yanzu ma ko an kawo kuɗin fansa suna karɓa sai su ki sakin mutun ya koma gida, mafiyawanci haka suke yi, mu samman idan suna son mace, wlh aurenta suke yi wata zubin suce da yan uwanta yaransu sun kasheta da basa nan wata zubin kuma idan suna son mace taki yarda tofa suna kashetan da gaske kuma su karɓi kuɗin fansa ba yadda aka iya da su, ba mai iya tinkararsu, sun fi karfin kowa ne nake ga a kasar nan, ku dai tun da kuka shigo nan sai ku kama addu'a a cikin zuciyoyin ku domin ko sallah ma basa bari bawa ya yi bare kuma har ya samu damar kai kukan sa ga Ubangiji, amma duk da haka ku dage da addu'a cikin zuciyoyinku dan Allah ya kuɓutar da ku, a yanzu kuɗi baya kuɓutar da mutun daga hannunsu".

"Amma su ɗin su waye ne a kasar nan har da suke aikata hakan ba mai kama su ayi musu hukunci?" A'afia ta tambaya tana kallon yarinyar dake kwance kan cinyar matar "Ya naga yarinyar nan kamar bata da lafiya?" Ta sake cefawa matar tambaya. Nisawa matar ta yi kafin ta ce "Su ake cewa masu garkuwa da mutane wato kidnapas, yarinya kuma e bata da lafiya, zazzaɓi take yi, amma sun bamu magani ai ta ji sauki".

Shiru A'afia ta ɗan yi tana jujjuya kalaman matar, sun bata magani kenan suna da asibiti ne a nan wajen? Ta tambayi kan ta a cikin zuciyarta, kidnapas dama haka suke? Ta sake tambayar kanta.

Sake ɗagowa ta yi ta kalli matar sanna ta ce.......... Dole na dasa aya a nan na don na so ba sai dan page ɗin ya cika da yawa, mu haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu [11/17, 12:27 PM] +234 906 579 6460: 💖💖TRIPLET'S💖💖

💖After 2days👌💖

(Bari mu fara da restaurant kafin mu yi wani wajen kuma)

Acikin yan kwanaki biyun nan Rimsha ta saba sosai da aikin restaurant ɗin, dama kun san ta da son koyar girki, dan haka sai ta tare wajen girkin hotel ɗin, saɓanin Jehan da ko leƙa wajen bata yi, sai dai idan ta zo ɗaban abinci zata kai wa masu saya.

A yanzu Rimsha fa ta iya abinci sosai, kuma akalla zai kala girki kala 15 ta iya, bata da kiwuyar aiki, haka zalika bata jin nauyin jikinta, sake jiki take yi ta murji aikin ta, idan ta koma gida ta yi wanka ta yi ta barcin ga ji ya, sannan a yan kwana biyun nan kafin ta tafi restaurant ɗin sai ta yi wa maman Sadiq shara da wanke-wanke sannan ta tafi.

Yau ma kamar kullun da sassafe ta tashi ta yi wanke-wanke da shara, sannan ta yi wanka, ta shirya, ta ɗauko wayarta, tun da ta zo sai yau ta ɗauki wayar, kokarin kunnawa ta yi amma ina battery ya kare wayar ta mutu ba charji, turo ɗan bakin nan nata tayi sannan ta yi wa mamam Sadiq sallama ta wuce sauri sauri domin Sadiq yana tsaye a waje yana jiranta.

Tare suka jera zuwa bakin titi, a yanzu saura mata 4k a cikin 20k da Ahmad ya bata, gaba ɗaya ta kashe kuɗin a sayawa maman Sadiq irin su omon wanke-wanke da sabulun wanki da wanka, bata damuwa idan ta zo zata yi abu idan taga babu sai ta ciro kuɗi ta saya, harta tsintsiya ita ta saya musu guda uku, Yusuf mai rakata sayowa, dan shine babban abokinta.

Karfe 8 daidai ta shiga restaurant ɗin nasu, kai tsaye wajen girki ta nufa, masu shara har sun yi sun goge koina, wajen ya yi fes,

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull