Triplets book 2 complete - Chapter 43
Triplets book 2 complete Chapter 43: Triplets book 2 complete Chapter 43. Suna saka number bugu ɗaya ya ɗauka, ba ɓata lokaci suka sanar mashi da abin da…
4,431 words
Suna saka number bugu ɗaya ya ɗauka, ba ɓata lokaci suka sanar mashi da abin da yasa suka kirashi, salati bawan Allah ya fari yi, a wulakance Sani ya ce "Ka ajiye salatin ka a gefe, gaba zai maka amfani, yanzu dai ku kawo kuɗin fansa ku karɓe ta ko kuma mu kashe ta" daga can ɓangaren yayan nata ya tambayi naira nawa ne, nan suka yanka mashi kuɗin da kwakwarsa suka kasa ɗauka mashi, 40 million, daga suka faɗi kuɗin wayar ta yanke dif, da alama ya suma ne, ko kuma dai ya razana ya saki wayar ta faɗi kasa ta tarwatse, ko wani abu makamancin haka.
Tsaki sani ya ja yana faɗin "An jima zan waiwayeka idan ka dawo daidai" ya kai karshen maganar tare da kallon Aafia yana mai bata umarnin akan ta basu number yan gidan su, ai kuwa ta kafe akan lallai ita bata riƙe number kowa a kanta ba, hakan yasa suka tambayi sunan anguwarsu dan su nemo number da kansu, nan fa tsoro ya kara kamata, jikinta ya hau kerma, sosai take ambato sunan Allah a ranta.
Suna a wannan hali Sani ya zuba mata ido suna jiran amsa, ba su ankaraba, kawai sai gani suka yi ɗaya daga cikin bandits ɗin ya kariso wajen, hannunsa ruƙe da zangegen bulala, yana zuwa ya fara zabga mata a jikinta. Irin mutanen nan ne masu gaggawa a kan abu, basu da hakuri, ga saurin hawa, shiyasa ya fara dukanta, wai ta raina masu wayo ne, sai ihu take yi tana juyi a wajen.
Shi kuma buba ɗaga bindigar hannunsa ya yi sama ya fara sakin wuta, Ihu sauran yan bandits dake a wajen suka fara yi suna shewa. Nan take duk sabbin zuwa dake a wajen, wayan da ba su saba ba, suka rungumi juna suna kuka. A zafafe A'afia ma ta rungumi Hanan suna kuka kamar ransu zai fita, duk sun birkita masu kwakwale, shi kuma bandits mai zane Aafia haka ya cigaba da sauƙe masu bulala a jiki, daga Aafia har Hanan ɗin da suka rungumi juna, a tare suke shan bulalar.
Cike da jin haushin abin da suka yi Sani ya dakatar su ta hanyar daka masu tsawa. Ba dan sun so ba, suka dakata, rai a ɓace ya fara magana "Yanzu me amfanin hakan? To da kuka birkita su ai Shikenan, kuna tunanin yanzu za su iya bamu amsa ne, me yasa kukam wata zubin baku abu da ƙwaƙwalwar ku ne? Dan Allah ku wuce ku bani waje a nan hai". Ya kai karshen maganar tare da wucewa ya bar wajen ransa a matukar ɓace, suma wucewa suka yi suka bar wajen, sai wani kumbure-kumbure suke yi, suka nufi in da ya kasance nan ne ɗaku nan su yake. Haka su Aafia suka ci-gaba da zama cikin kunci suna hawaye, duk sun birkice bayin Allah. Sani ya ce zuwa anjima zai dawo dan ya karisa karɓar numbobin yan uwan nasu, kafin nan sun ɗan sami natsuwa....
Ni kuma na tattara kayana zuwa gidan Abbi gobe idan mai dukka ya kai mu, sai mun haɗe gidan Abbi, masoyan yaya Imran, yaya Irfan, yaya Akil, Abba, Abbi, daddyn Jelly, Umaisha, Akila, sai ku saka A'afia a addu'a, domin kuwa wannan bala'in da take ciki, tamkar gaba ɗaya wayan da na kiran nan ne a ciki, yar uwasu ce, kanwarsu, yar cikin su, dole za su shiga matsanancin tashin hankali idan suka sami labari, Allah ka iya mana da iyawarka, Allah ka kawo mana zaman lafiya a kasar mu, Allah ka shiga lamarin mu😭😭, Ma'assalam......✍️ [11/17, 12:27 PM] +234 906 579 6460: 💖💖TRIPLETS💖💖
🔥GIDAN ABBI🔥
*BARI MU FARA DA DADDYN JELLY*
Suna fita da Ayla kai tsaye *ABC SUPERMARKET* suka wuce, yana tuki yana kallonta ta cikin mirror motar, ita kuma ya kwantar da kanta a jikin kujerar tana shakan kamshin perfume nasa, ga kuma kamshi turaren motar abin ba'a magana.
"Babayn daddy tunanin me kike yi?" Ya faɗa yana dawo da kallonsa a kanta, fuska ɗauke da murmushi ta ce "Kawata kuma yar uwata Rimsha nake tunani, ko tana wani hali yanzu? Ina kewarta sosai".
Jinjina kai ya yi cike da kulawa ya ce "Very soon zan kai ki wajenta, ba dai kin ce a Katsina take ba?" Gyaɗa mashi kai ta yi tana mai kai kallonta kan shi, shima ita yake kallo kuma yana tuki.
Murmushi ya sakar mata yana faɗin "Yau kin yi kyau sosai kamar my jelly" "Allah sarki daddy Allah ina son kallon Jellyn nan sosai" mai da lallonsa kan hanya ya yi yana faɗin "Very soon da izinin Allah zata dawo gare mu" ya kai karshen maganar yana dawo da kallonsa kanta.
"Allah yasa, kullun ina mata addu'a" ɗan zaro ido ya yi kafin ya ce "A ina kike yi mata addu'ar?" Ya tambaya yana sake kallon hanya. "A Sallah mana daddy, idan na yi sallah ina yi mata addu'a sosai" "Yaushe kika fara sallah ban sani ba?" Zaro ido ta yi yana kallon shi, dawo da kallon shi ya yi kanta yana faɗin "Amsa me, yaushe kika fara yin Sallah?" Sunnar da kai kasa ta yi tana wasa da yan yatsun hannunta, tana tunanin yaushe daddynta kuma yasan bata Sallah, kwata-kwata yau satin ta ɗaya tare da su, kuma yau take sa ran Jinin zai tafi, dan Aunty ta ce mata sati ɗaya yake yi, wata macen kuma kwana huɗu, to yau ta cika sati da fara yi.
Tana tsaka da tunani kamar ance mata ta ɗago kallonta izuwa kan hanyar, daidai lokacin da shima ya kawar da kallonsa daga kanta izuwa kan hanyar, wani irin mahaukacin burki ya ja lokacin da suka kusa taka wani yaro da ya shigo titin da gudu zai tsallaka.
Tsabar tsorata bata lokaci da ta faɗa jikinsa ba, tana sakin kuka, shi kuma ajiyar zuciya ya sauƙe tare da yi wa Allah godiya da ya sanya ba su buge yaron nan ba, dan ma Allah ya tsare ba wani gudu suke yi a kan hanyar ba, kaɗan-kaɗan suke tafiya saboda yasan suna tafiya suna hira hankalinsa ya rabu gida biyu shiyasa yake tafiya a hankali, da gudun haɗari.
Bayan yan wasu mintuna, a hankali ya dawo da manya-manyan idanuwansa irin na Jellynsan nan a kanta, ta kankameshi sosai ta tura kanta cikin kirjinsa.
"Babayn daddy are you okey?" Ya faɗa a sanyaye, cike da tsoro, da kyar kuma a hankali ta ɗago da idonta tana ayyana yadda zata ga sun taka yaron nan a kan titin, bata ma san yaro kam ya wuce abinsa da Allah ya tsare ba'a taka shi ba.
Kai kallonta ta yi saman titin, sai taga wayam babu yaron, sai motoncin dake kaucewa nasu suna wucewa, dan ma Allah yasa motar tasu bata a kan hanya sosai, suna ɗan gefe.
Dawo da kallonta kan fuskarsa ta yi, ya tsare ta da ido yana kallonta, yunkura wa ta yi zata tashi amma sai ta kasa sakamakon lokacin da ta faɗo jikinsa ta sanya hannunta ɗaya a jikin kujerar da yake zaune, da ya dawo da bayansa wajen sai ya ɗan danne mata hannun nata.
Ko motsi bai yi ba yana ta kallon fuskarta, ita kuma tana son tashi ga shi ba hali, dawo da kallonta kan fuskarsa ta yi, still har lokacin kallonta yake yi.
"Daddy hannuna zan tashi" ta yi maganar a shagwaɓe kamar yadda ya saba yi mata magana kullun, sannan ta yi maganar tana sunnar da kai kasa.
Ya kasa motsa Allah kaɗai yasan me yake tunani a cikin ransa, ya kasa yin wani kataɓus. Ganin haka yasa ta koma ta kwantar da kanta a saman kirjinsa, dan ta gaji tana saman iska, ita bata zauna ba kuma bata karisa tashi ba.
Wani irin yanayi mai wuyar misiltawa ya ji a jikinsa, bai san lokacin da ya kai hannunsa yana shafa kanta zuwa bayanta ba, shiru ita ma ta lafe a jikinsa, domin ya saba rarrashinta idan ta tuna da mamanta tana kuka, shi Aunty take kira ya rarrasheta dan tafi jin maganarsa sama da ko a gidan, shiyasa ta saba da rarrashin nasa, wani sain ma har rungumarta yake yi, idan ta yi shiru sai ya ce ta yi murmushi, idan ta yi ne sai ya rungumeta suna murmushi, shiyasa kwanciya a jikinsa ba bakon abu bane a wajenta ba.
"Daddy hannuna yana yi mani zafi, ka danne sosai" ta faɗa murya can kasa-kasa, hannu yasa ya ɗago da haɓarta fuskokinsu su fuskantar juna. "Babyn daddy kin cika tsoro da yawa fa" murmushi ta sakar mashi tare da yunkurawa zata tashi.
"Ina za ki tashi ki je?" "Wajen zama na mana daddy" ɗan ɗago da bayansa ya yi ta zare hannunta, tana kokarin komawa ta zauna, sai kuma ya jawota jikinsa mai gaba ɗaya, bata wani damu sosai ba, domin tana bala'in kaunar shi kuma ta saba.
"Babyn daddy yau haka kawai nake jin bana son ki raba jikin ki da nawa, ina kewar Jelly da mummy ta sosai, komai ya dawo mani sabo yau" ya kai karshen maganar kamar zai yi kuka. Ɗago da kanta daga saman kirjin nasa ta yi suna kallon juna "Kayi hakuri daddy In Sha Allah za su dawo ka ji" ta faɗa a sanyaye.
Jingina kansa da jikin kujerar motar ya yi yana faɗin "Mummy'n Jelly ta tafi in da ba'a dawowa baby, ba zata dawo ba, sai dai mu mu bita, yau kewarta ya dawo mani sabo, lokacin da ta rasu, nafi shekara uku ina jin tamkar tana a gefena, ba zan ina manta ta ba, a wannan shekara uku kullun na dawo gida ina jin motsinta, ina jin duk wani abin da take yi mani idan na dawo, daga karɓa jata har sauransu, idan na dawo gida sai in ga kamar ta zo karɓar jakata, idan na zauna cin abinci, sai in ji kamar ita take bani a baki, yau komai ya dawo mani sabo". Nan take hawayen da suka cika mashi ido, suka fara gangaro mashi a saman kumatunsa, dama kun san shi da saurin kuka idan baku mance ba.
Jin ruwa ya zuba mata a saman kumatun tane yasa ta ɗago da kallonta izuwa kan fuskarsa, ganin yana hawaye ne yasa ta ɗan tashi daga kwanciyar da ta yi a kirjin nasa, ta ɗan matso ta zauna a saman cinyarsa, ta sanya hannunta tana goge mashi hawaye tana faɗin "Kayi hakuri daddy Allah ya jiƙanta da Rahma, Allah yasa ta huta, ita kuma jelly zata dawo In Sha Allah".
Ji yake yi wani irin yanayi, yau ya tuna da mummy'n Jelly, ga shi sanyin idaninsa ɗaya ɗayar ma bata a yanzu, dama ita yake kallo yana rage kawar mum ɗin ta, abin ya jefa shi cikin damuwa sosai, sosai kuma yake yin wani irin baƙon yanayi lokacin da hannunta ke a saman kumatunsa tana goge mashi hawaye, a hankali ya sauƙo da wayan nan rinannun idanun nasa a kan fuskarta, ɗago kai ya yi suna fuskantar juna sosai, har suna iya jiyo numfashin juna, zubawa fuskarta ido ya yi yana jin kamar ya san mai irin fuakar nan tata, yau da ya kalleta kusa da kusa, sai ji ya yi tamkar ya santa, ko kuma mai kama da ita.
Ganin yadda yake kallonta sosai ne yasa ta yi kakorin barin jikinsa, tun da ta gama goge mashi hawayen nasa, bata kai ga barin jikin nasa ba ya yi maza ya riƙota. "ina zaki ke?" Ya tambaya yana matso da fuskarsa daidai saitin tata, haka kawai ta tsinci kanta da jin tsoron shi lokaci guda ya kamata, muryar ta har sarkewa yake yi wajen furta "Daddy zan koma wajen zama nane sai mu tafi".
Dogon numfashi ya ja tare da sauƙewa a hankali "Baby shekarunki nawa?" Ya tambaya ya kara matso da ita saman kirjinsa. "Nima ban sani ba daddy, amma dai zan kai 15 haka ko 16 years, dan lokacin da muke tare da mamana ta ce shekaruna 12 yanzu kuma kaga rabona da ita shekara na huɗu kenan" ta kai karshen maganar tana zubar da hawaye, ta tuna mamanta.
"Subhanallahi ni fa babay ba wai na tambaye ki bane dan ki yi mani kuka, kin dai kin san bana son kukan ki ko?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e. "To ki yi shiru ko?" Ya kai karshen maganar tare da sanya hannu yana goge mata hawaye. "Ni na tambayi shekarun ki ne domin ina son tantance shi kin kai ki zama haramun zama a jiki na ne ko dai". Shiru ta yi tana ɗan shasshekar kuka.
Jawota ya yi zuwa kirjinsa sosai yana ɗan bubbuga mata bayanta alamar rarrashi. Minti biyar suka ɗauka a haka kafin ta ɗago kai da nufin ta yi mashi magana, tana ɗago kai hancinsu ya gogi na juna, domin ya rankwafo da kansa yana kare mata kallo.
Wani irin shock ya ji lokacin da hakan ta faru, ita dai duk da kananan shekarun ta ta ji wani abu da batasan menene bane a jikinta, ɗan baya ta ɗan ja kaɗan tana faɗin "Daddy mu tafi ko?" Jinjina mata kai ya yi tare da fara ƙoƙarin kunna motar, zata tashi ya riƙeta dan kada ta tashi, yau gaba ɗaya ya rasa me yake damun shi, baya son raba jikinsa da tata.
"Daddy zan koma saman kujera ta ce" girgiza mata kai ya yi a ya yin da yake tayar da motar ya ce "No ki yi zamanki a jikin daddynki" "Daddy to taya ya zaka yi tukin motar?".
Ɗan shafa kumatunta ya yi yana faɗin "Sarkin tambaya ba, to zaki gani ai, kedai yi kwanciyar ki a jikin daddynki" to ta amsa mashi da shi tare da komawa ta kwantar da kanta a saman kirjinsa. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe tare da jan motar suka bar wajen.
Tafiya kaɗan suka yi, suka isa *ABC SUPERMARKET* da ya yi parking a parking space nasu sai ta ɗago kai tana faɗin "Daddy in fita ne?" Tsareta da ido ya yi haka kawai baya gajiya da kallonta, wata sain har mamaki yake yi na rashin son daina kallonta da yake yi.
"Babayn daddy kin ga ji ne da daddyn naki da har kike saurin fita?" Murmushi ta yi tana faɗin "Daddy ban ga ji da kai ba, ai naga mun iso ne kawai shiyasa na ce in fita ne". Shafa kumatunta ya yi kafin ya ce "Duk yadda aka yi mama ko baba ɗaya yaren mu ne, dan ba'a banza zaki yi wannan kyau ɗin haka ba". Yar dariya ta yi har sai da fararen hakwaranta suka bayyana, ta cusa kanta a cikin kirjinsa tana ɓoye fuska.
Rungumeta ya yi yana faɗin "Ai gaskiya na faɗa ko?" Gyaɗa mashi kai ta yi alama e. "To waye daga cikin su ne Yaren namu?" Kasa kasa Muryar ta ke fita saboda ta cusa kanta cikin kirjinsa, tana ta jefa bawan Allah cikin yanayi.
"Mama ta ce" kara ruƙeta da kyau ya yi yana ɗago haɓarta da hannunsa ɗaya, zuba mata ido kawai ya yi yana kallonta, ita kuma ta rufe ido tana murmushi.
A haka kawai ya tsinci kansa da matso da fuskarsa daf da tata, daga karshe ya haɗe fuskokin nasu yana jan dogon numfashi.
Jin fuskarsa a saman tate ne yasa ta buɗe idanuwanta, ai kuwa tana buɗewa sai cikin tasa idanun, da sauri ta mai da nata ta runtse su.
"Babyn daddy kina kunyar daddyn ki ne?" Ya yi magana yana kara riƙota a jikinsa sosai, zuciyarsa na ingiza shi akan ya yi kissing lips nata, idanuwansa na akan lips ɗin tata, ya yin da ita kuma sai murmushi take yi tana faɗin "A'a daddy bana ji" yadda ta motsa lips ɗin nata ta yi magana kusa da shi bakaramar fusgar shi ta yi ba, gaba ɗaya ta sanya ya mance shin wai a ina ma yake? Da waye yake tare? Duk ya mance.
(Sheɗan na daga gefe yana kallonsu😭)
Kara matso da bakinsa ya yi kusa da tata yana ɗan goga lallausar lips ɗin nasa a saman tata, Allah ne kaɗai yasan irin abin da yake ji a cikin zuciyarsa, yau shekararsa 16 ba mace, shakara 16 kenan da rasuwar mummy jelly, lokaci guda ya canza, ya shiga wani irin yanayi mai wuyar misiltawa, riƙota sosai ya yi a jikinsa tare da ɗaura lips nasa saman tata, ya kasa janye wa kuma ya kasa aiwatar da abin da zuciyarsa ke ingiza shi da ya aikata, ita kuma jin ya ɗaura lips nasa a saman tata yasa ta waro idanuwanta, kai tsaye sai cikin nasa da suka yi jawur kamar wuta.
Ba ƙaramin tsorata ta yi ba, nan take jikinta ya fara kerma ta fara ƙoƙarin kwacewa daga jikinsa, duk da cewa ba wani ilimi take da shi ba, ɗan zamanta da Rimsha ta fahimci abubuwa da dama, wadda a ciki kuma harda gudun wani namiji ya taɓa ki, sai kuma ta tuna in da Rimsha ke ce mata mum tasu ta ce mata idan mutun ya fara period namiji ya taɓa shi to zai samu ciki, tuna hakan yasa ta kara tsorata, ta fara yunkurin barin jikinsa.
Riƙeta sosai ya yi, yana jin tamkar ya yi kissing nata, amma ya kasa, saboda ba halinsa bane, ba zai iya yin haka ba, idan ya tuna cewa duk abin da ya yi mata to yana nan a rubuce za'a yi wa Jellynsa hakan yana ɗaya daga cikin abin da yasa ya daure ya jure ya kame kansa bai kai ga yin kissing ɗin nata ba, jin zuciyarsa yake yi tamkar ana hura mashi wuta a cikinta, har wani sara mashi kansa yake yi, da kyar ya iya furta "Babyn daddy please ki zauna shiru kin ji? Babu wani abin da zan yi maki" da kyar ya iya kai karshen maganar yana haɗe words.
Jin yadda ya yi magana kamar mara lafiya ne yasa ta san daddyn nata ba lafiya yake ba, kuma ta kara jin tsoron shi sosai a ranta, shiru ta yi tana tunanin me yake damunsa lokaci guda haka?. Shi kuma cigaba ya yi da goga lips nasa a saman tata, yana jan numfashi da kyar da kyar.
Sun ɗan jima a haka kafin ya manna mata sumbata a saman lips ɗin nata, sannan ya saketa tare da kawar da kallonsa daga kanta, lokaci guda wani irin kunyarta ta kama shi, kasa-kasa ya ce "Babyn daddy je ki kiyi shopping ɗin ki dawo ina nan ina jiranki" tashi daga jikinsa ta yi, ita ma gaba ɗaya ji tayi kunyarsa ta kamata, sai wani sunnar da kai kasa take yi, cikin girmamawa ta ce "To me zan sawo daddy?".
Har lokacin gefe yake kallo, ya ki kallonta ya ce "Jeki fara ɗaukar duk wani abin da ya burgeki, ciki kuma ki haɗa da jakar school irin wadda kike so, sai ki haɗa da kananan kaya zan biyo ki daga baya". To ta amsa mashi da shi, sannan ta buɗe kofar motar ta fita.
Jingina kansa da jikin kujerar motar ya yi yana sauke nauyayyar ajiyar, kasa kasa ya fara magana shikaɗai "Zancen Sadiya ya tabbata, tabbas ina kaunar Ayla, ban san da haka ba sai yanzu, why soyayya zaka yi mani haka? Why?" Ya kai karshen maganar tare da sanya hannu yana shafa lips nasa, a hankali ya lumshe idanuwansa, bayan wasu yan mintoci ya sake warosu, har lokacin suna nan jawur basu koma asalin kalarsu ba.
Ya ɗan jima a haka kafin nan ya fito daga cikin motar ya nufi cikin shopping ɗin.
Can wajen mayukan shafawa ya hangota, zuba mata ido ya yi yana kare mata kallo, a shekaru ba zata wuci Jellynsa ba, amma jelly zata fita tsawo, ita kuma ta ɗan fi Jelly kiɓa, kuma da alama ma tama ji kin yin kiɓa, sai dai ba sosai ba, irin kibar nan mai kyau, idan ta samu natsuwa da hutu zata murmure sosai, wani irin yanayi mai daɗi yake shiga idan yana kallonta, babban kuskuren da ya yi wadda yasa har sonta ya shige shi cikin ƙanƙanin lokaci shine ɗaukarta da ya yi kamar Jelly, ya manta cewa jinin uba da ƴa daban-daban da yar da ba kai ka haifeta ba ka mai da ƴa, komai haɗa jiki da uba da ƴa za su yi ba za su taɓa jin sha'awar juna ba, sai dai idan son zuciya irin ta ɗaya daga cikinsu kuma sheɗan ya buga masu ganga, amma babu wannan a jinin uba da ƴa, ya mance da haka ya rinƙa jawota jikinsa, idan tana kuka haka yake rungumarta yana rarrashinta kamar yadda yake yi wa Jelly, da farko kin yarda take yi, daga baya ta saki jiki da shi, hakan yasa suka yi irin wannan irin sabo, ita ma a daddy take ɗaukarsa kamar yadda yake gaya mata, wannan kuskuren tasa soyayyarta ta yi mashi shigar faraɗ ɗaya.
Ganin ta kasa zaɓar mai ɗin sai rawan ido take yi dan bata saba ba, a gidansu ma bata da mai ɗin bata taɓa shafawa ba. Hakan yasa ya karisa wajen yana faɗin "Babyna baki sami irin wanda kike so bane?"
(Waye ya lura da canjin sunan da aka samu lokaci guda?🤣 Daga babyn daddy zuwa...🤐🤣)
Shiru ta ɗan sunkuyar da kanta kasa, dan yanzu haka kawai take jin kunyarsa.
Hannu ya kai yana duba wadda zai dace da kalar fatar ta, yana yi yana kallonta, sai wani yan kame-kame take yi mashi, shima dai bala'in kunyarta yake ji a yanzu.
Haka ya zaɓa mata mai wadda yake ganin zai dace da skin nata, daga nan ya riƙo hannunta suka wuce wajen kaya da sauran abubuwa, komai shi ya zaɓa mata da kansa, dan tun da ya shigo ta kasa sukuni, taki sakin jiki, shima kuma bai damu da ya sata ta saki jikin nata ba, hakan da tayi ma yafi mashi, dan ya ɗan samu sassaucin abin da yake ji idan tana magana a kusa da shi.
Sosai suka lodi kaya sannan suka wuce wajen biya, katinsa ya bada suka ciri kuɗin, ma'aikatan wajen suka kwasa mashi kayan zuwa cikin motarsa.
Bayan sun shiga cikin motar ne ya kalleta ya ce "Sorry babyna" sai lokacin ta ɗago ta kalleshi, ganin ita yake kallo ne yasa ta mai da lallonta kasa tana wasa da yatsun hannunta, bin hannun nata da kallo ya yi, yatsun nata yan gajeru da su gwanin birgewa. Yar murmushi ya saki tare da kunna motar suka nufi gida.
Suna isa ya fice zuwa part nasu, ya ki tayata kwasan kayan zuwa cikin gida, dan baya son haɗa ido da Aunty, saboda yasan halinta sarai yanzu zata sako shi a gaba da tambayar ya akayi, shiyasa ya gudu abinsa.
Ita kuma haka ta kwashi kaya niki-niki zuwa cikin gida, Aunty bata a Palo, zube kayan ta yi a palon ta zauna saman sofa tana mai da numfashi, a hankali abubuwan da suka faru a mota ya fara dawo mata cikin ƙwaƙwalwarta, haka kawai take jin matuƙar kaunar daddyn nata, shiru ta yi idanuwanta suna gane mata lokacin da suka haɗa ido idanuwansa sun yi ja sosai. Yar firgita ta yi sakamakon taɓa ta da Aunty ta yi tana faɗin "Babyn daddy yaushe kuka dawo?".
Fuska ɗauke da kayatatcen murmushi ta ce "Yanzu muka dawo" zama Aunty ta je ta yi a saman sofa mai zaman mutun 3 tana ɗan kishingiɗa tare da tambayar Ayla ɗin ya tafiyar tasu ta kasance.
Da yake Ayla ba karatun sosai ta yi ba, kuma ba ta da wani sani akan hakan, ba waye wa, dan dai kunga yadda rayuwarya yake, ba da ban Rimsha bama da abin sai ya fi haka taɓarɓare wa, hakan yasa ta gayawa Aunty duk abin da ya faru a tsakaninta da daddy'n Jelly a tafiyarsu har suka dawo.
Sosai Aunty ta ji daɗi tare da ja mata kunne akan kada ta kuskura ta sake gayawa kowa sirrin ta ne, ko ita bata ce ya gaya mata ba, amma dai ta yi mamakin jin cewa daddyn Jelly ne ya aikata hakan, ta wani ɓangaren kuma tausaya mashi take yi matuƙa, ta kuma jinjina mashi sosai, dan ya ma yi namijin ƙoƙari da ya iya tsayawa a iya haka, shekara 16 ba wasa ba, nan fa Aunty ta shiga bata shawari da kuma karin bayani akan abin da daddyn Jelly ke nufi da ita, wato yana son ta ne.
(Kuji Aunty da ƙokari sai kace ya ce mata yana son ta🤔)
Tun da Ayla ta ji haka sai ta ji wani irin kunyarsa ta karu mata, amma kuma ta tsinci kanta cikin matsananciyar farinciki wadda ita kanta bata san daga ina farinciki yake ba.
"To tashi ki ɗauki abincinsa ki kai mashi kin ji? Dan nasan yana jin yunwa" To Ayla ta amsa da shi sannan ta miƙe ta bar niki nikin kayan nata a wajen, ta nufi Kitchen, sai murna Aunty take yi, dan daddyn Jelly yana da kirki sosai yana son ta, tana masa fatan ya yi aure ko zai rage mashi damuwa. Mai aikin su ne ta zo ta kwashe shopping ɗin na Ayla izuwa cikin ɗakinta.
Ita kuma Ayla kamar yadda ta saba haka ta fito da tray mai shake da kayan abincin nasu shi da Irfan, ta ɗaura saman dining table tana kokarin tattare hijabinta ta gyara dan kada ya kayar da ita.
"Ayla ki je ki yi wanka ki cire kayan nan tukunnan sai ki zo ki kai mashi abincin" Cewar Aunty, to ta amsa nata sannan ta bar abincin sama table ɗin ta haura sama
(Aunty!! Aunty!! Akwai iya karawa abu gishiri da sugar 🤣)
A gurguje Ayla ta yi wanka ta shirya cikin doguwar riga mai bala'in kyau launin pink da baki, ta yafa mayafin rigar a kanta, Rimsha ta koya mata sanya turare, hakan yasa take yawan sawa, kuma kullun saboda Rimshan take sakawa, idan ta sanya tana yawan tunata sosai, haka ta fito ta yi kyau sosai. Kai tsaye wajen abincin ta nufa, zata ɗauki abincin Aunty ta dakatar da ita ta hanyar cewa "Ke haka ake zuwa kai wa miji abinci (miji kuma?🤔) Babu kwalliya ba komai, wuce muje na maki kwalliya" to Ayla ta ce tana sunkuyar da kanta kasa, tana jin wani irin yanayi daddynta ya zama miji kuma?.
Haurawa sama suka yi, ɗakin Aunty suka wuce ta fito da kayan make up nata ta fara tsantsara mata simple make up. "Aunty ina Inna ne?" Cewar Ayla.
"Inna ai ta koma, ɗazun bayan tafiyarku yaya Irfan ya mai da ita gida, ta ce na samu lafiya zata koma" "Allah sarki har na fara kewarta" ɗauko lips balm aunty ta yi tana sanya mata a baki tana faɗin "Ke dai bari Ayla kamar zan yi kuka da zata tafi" "Ai dole ne mama fa hmmm" kallonta sosai Aunty ta yi kafin ta ce