Kenza eBookz

Triplets book 2 complete - Chapter 45

Triplets book 2 complete - Chapter 45

Triplets book 2 complete Chapter 45: Triplets book 2 complete Chapter 45. (To fa Maryam Allah ya kuɓutar da ku dukkanku na haɗa kaya na zuwa wajen mai…

4,483 words

(To fa Maryam Allah ya kuɓutar da ku dukkanku na haɗa kaya na zuwa wajen mai Rimsha, sai na dawo dan ganin ya ake ciki)

🔥🔥GIDAN ABBA🔥🔥

Kamar yadda Dr Nawid ya faɗa kuwa bayan sallar isha sai ga shi nan ya zo, ya ci wanka ya sha dakakkiyar shadda blue color, ya yi kyau ba karya, amma fa ko kallo da ido bai samu daga wajen gimbiyar tasa ba, sai tashin kamshi yake yi yana ta zuba murmushi, ita kuma tana zaune saman sofa ta tsare gida ta haɗe rai, bai damu sosai ba, saboda yasan bata da lafiya...gaisuwa suka yi, daga nan suka zauna shiru, Rimsha ta yi kasa da kai shi kuma ya zuba mata idanu yana lallonta.

A haka Akila ta shigo ta same su, wani irin haushin Dr Nawid ne ya kamata, dan bata son abin da zai ɓatawa Rimsha rai kwata-kwata, kusa da ita ta zo ta zauna tana ɗagawa Dr gaisuwa, da fara'a ya amsa tare da tambayarta ya school, lfylou Alhadulillah ta amsa mashi da shi, daga nan ta dawo da kallonta kan Rimsha, ganin yadda ta yi kasa da kai kamar zata yi kuka ne yasa ta ce mata

"Meesha mu je ki nuna Mani in da kika ajiye kayan mun can" to ta amsa a tare suka miƙe Akila tana faɗin "Yaya Nawid ina nan dawo maka da ita" bai kawo komai a ransa ba, sai murmushi ma yake yi ya amsa mata da tayi sauri fa.

Suna shiga ɗaki Akila ta ja ta rungume ta, kasa-kasa ta fara magana "Rimsha ki dai'na ɓata rai kin ji? Ba ke kaɗai ce baki son shi ba har da ni, dan Allah ki saki ranki, idan kun ɗan yi hira na 30mins sai ki ce mashi kanki na ɗan maki ciwo zaki kwanta, kinga a haka za ku rabu lafiya, amma a duniyar yanzun nan baa fitowa mutun filli anuna ba'a son shi, wlh zaki ga uwa ɗaya uba ɗaya kuka fito da mutun ma a zamanin yanzu yana iya kashe ki akan abin duniya, dan haka ki sani ba'a shedan ɗan adam, ki san taya zaki zauna da kowa, kada ki damu In Sha Allah idan Lion ya fara son mu ba sai ma kin yi masu magana ba, ina da tabbacin sunan shi ma kawai idan suka ji daga ranar wlh ko millon nawa za'a basu, babu mai kara zuwa wajen ki ko ya kira ki a waya, so dan haka ki kwantar da hankalin ki, kuma yadda kike bala'in kaunar Lion mijin mu, dan ni na bashi ke, na san wlh ba zaki taɓa son kowa ba, bana son ki nuna musu tsanar da kika yi masu a fili, duk da yake abokin yaya Imran ba zamu yi shedar shi ba, ke bama su ba, mi sali ko yaya Akil ba zaki yi shadar abin da zai iya aikatawa akan abin da yake so ba, dan haka ki natsu komai cikin taku zaki bishi, yaya Imran ya ce zai zo wajen gyaran jiki ya same gobe da yamma idan yaya Akil ya kai mu, wai da na ce ba ya tafi Abuja ba? Sai ya ce mani wai ai daga Abuja ne zai zo ganin mu ya koma, wlh daga jin zancen yaya Imran tsara kayarsa ya yi, to ni dai nawa ido, yaya Akil kuma ya ce gobe zai yi maki komai na school, da da farko na ɓata rai, amma da na ji ke kike so, na hakura idan Allah ya yi muna da rabon fita Usa ɗin zamu fita In Sha Allah, yanzu dai ki je ku ɗan yi hira, kada ya zargi wani abin, ki saki ranki kin ji?".

Sosai ta ji shawaran Akila, kuma tana kara kaunar Akila sosai a ranta, saboda yadda take kara mata karfin gwiwa akan Lion, tana bata shawara mai kyau, tana nuna mata hanyar da ta dace, babu cuta ba cutarwa.

Rungumar juna sosai suka yi Rimsha tana faɗin "Aunty Akila nagode, Nagode sosai kin ji ko?" "Ba komai yar uwata, wlh ni kamar yadda su yaya Akil suke yan uwana haka kema na ɗauke ki, kuma daɗin daɗawa kema haka kika ɗauke ni, har kika iya gaya mani sirrin ki da ba zaki iya gayawa Jehan da kuke uwa ɗaya uba ɗaya ba, kai na ji daɗi kuma dole na riƙi ki amana saboda kema yar amana ce, yanzu dai ki je kada ya yi tunanin wani abin kin ji?" Gyaɗa mata kai ta yi alamar to daga nan Akila ta sumbaci lallausan kumatun, yar dariya ta yi har sai da dimple nata suka lotsa sosai, sannan ita ma ta sumbaci Akilar suka yi sallama, ta koma palon.

Shawaran Akila ya sanya ta samu natsuwa da farin ciki, ta ji gaba ɗaya ta saki ji, Akila yar baiwa, karama da hankalin manya, yar albarka, zama da kowa lafiya, kaunar kowa da kowa har wanda ma ya ce baya sonta, ita tana kaunar shi, ga A'afia nan bata sonta amma ita tana bala'in kaunar su dukkan su.

Hayewa ta yi saman bed ta kwanta tana tunanin yadda zata kaya, tana tunanin dole yau ta yi wa Rimsha tsawuyar dare dan Allah ya dafa masu, bata son ganin Rimsha cikin damuwa ko kaɗan.

Wayar Rimsha dake a gefen ta ne ya fara kara alamar shigowar kira, kobata ɗuba ba tasan mai kiran, Ahmad ne.

Ai kuwa tana dubawa shi ɗin ne, picking call ɗin ta yi suka gaisa tare da fara hira suna dariya, a nan ne yake tambayar address ɗin su kamar yadda ya yi wa Imran alkawari, ba musu ta gaya mashi, abin ya ɗaure mashi kai "Kaduna kumam?" Ya maimaita.

E ta amsa mashi tare da kara yi mashi baya nin in da unguwar su take.

Bata gama rufe baki ba, sai ji ta yi ya ce Heartbeat, ɗan zaro ido ta yi da mamaki ta ce "Yaya Ahmad ya aka yi kasan wannan sunan?" "Heartbeat kin san da waye kike magana kuwa? A'A ne fa" zubur ta miƙe zaune tana faɗin "Yaya Ahmad, yayan Anisa?" E ya amsa mata da shi, a tsorace ta ce "Dama kai ne mai son Rimsha?".

Babbar magana, Rimsha ta haɗa kuɗi da kuɗi kuma mulki da mulki faɗa, ta haɗa gwanki da Gwanki ita kuma tana can tana tunanin uban su a kuɗi da mulki, zuciyarta na a wajen Lion, wannan wace iriyar jarabawa ce? Lallai akwai rikici ba kaɗan ba, domin kuwa baban A'A SALAHUDDEEN idan ya samu labari to zai iya sanyawa a ɗaure Nawid ma da gaba ɗaya familyn sa, kuma su ɗauru ma har igiya ta saura, Ya Allah kasa Lion ya so Rimsha ya ɗauketa duk wannan rikici ta kauce, domin idan ba Lion ba babu wanda ya isa ya kwace ta daga family'n A'A SALAHUDDEEN, ga shi family'n sa basu da mutunci, sun raina talakawa, ganin talaka suke yi kamar takalmar sawarsu, yau ake yinta. Duk wayan nan zan tuka Akila ke yin sa a cikin zuciyarta, a yayin da shi kuma Ahmad sai hello yake ce mata. Soyayya mai saka Duk wani kuɗi da mutun yake ji da ita ya ajiye ta a gefe, banda haka me A'A SALAHUDDEEN zai yi da Rimsha? ga ruwa kuɗi abin da ake cewa kuɗi a tattare da shi, ga kuma uwa uba siyasa, kai anya ba mafarki nake yi ba kuwa. Akila kenan ta kasa wani kata ɓus sai tunane tunane take yi a ranta, abin ya kulle mata kai.

"Heartbeat ki yi mani magana mana, dama Rimsha kanwar Prof ce?" Da kyar Akila ta iya sai ta natsuwarta ta ce "E yaya Ahmad, kanwar mu ce" "Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun rashin sani yafi dare duhu, yanzu kenan ita ce ɗazun ya ce zai bani na ce bana so, to Alhadulillah dai tun da abin ya zo da haka, ya zo mani da sauƙi, ranar Friday ina nan shigowa, nan da kwana huɗu kenan, dan Allah heartbeat ki kula mani da ita sosai kinji ko bugun zuciyar mu?" Gyaɗa mashi kai ta yi, ta ruɗe sosai tana al'ajabin abin, in dai mutun zai iya fitowa daga family'n A'A SALAHUDDEEN ya mutu akan Rimsha sosai haka, to da izinin Allah shima Lion zata iya yi wu ya so ta, kai A'A SALAHUDDEEN sune fa kasar nan gaba ɗaya a yanzu, kuma shine yaron *ABDULLAHI ABUBAKAR SALAHUDDEEN* na farko, yana da kanne mata huɗu da maza biyu, dukkansu basa a kasarnan suna England, ita kuma Anisa daddyn nasu ya rabu da maman nata ne yasa suka dawo Kaduna da zama, A'A yana bala'in kaunar Anisa sosai, saboda mamanta tana da kirki, da farko daddyn su ya so kwace Anisar, sai da Ahmad ɗin yasa baki sannan ya barta wajen maman nata, gaba ɗaya Family suna mutuwar kaunar Ahmad, shiyasa idan ya yi magana ba'a cewa aa, a yanzu haka duk cikin ƴaƴan *ABDULLAHI ABUBAKAR SALAHUDDEEN* Ahmad ne kawai yake a Nigeria sai Anisa da dama bata taɓa fita ba, suna da ruwan tsabar kuɗi abin da ake kira da asalin kuɗi ba kaɗan ba, abin ba'a magana, sannan duk cikin familyn SALAHUDDEEN Ahmad ne kawai ya ciri tuta yake iya zama da talakawa, yana da kirki sosai da sosai da kaunar mutane, yana da kyauta da saukin kai, ba shi da girman kai ko kaɗai, bai ɗauki rayuwa a komai ba, sai ita Anisa ta biyu, ita ma akwai izzar jinin baban nata a tattare da ita, sai dai itama zama da mamanta yasa take kaunar mutane, kun dai san tarbiyar uwa dole na daban yake, to wannan ma haka ne.

Kamar zautatciya haka Akila ta faɗa duniyar tunani, ta ruɗe sosai, dan bata taɓa zaton hakan ba.

Da Ahmad ya ga ji da magana, sai ya katse kiran, dan yanzu bai wani damu ba, tun da ya san har in da suke, idan suka mashi ba daidai ba suga diransa cikin Kaduna a daran nan, TO FA!!

(Akwai cakwakiya kenan, ni dai na haɗa kaya na zuwa wajen babyn daddy da kuma daddy, wato gidan Abbi.)

Su Aunty yau duniya ta samu, miji ya dawo sabo, sai tarairayar abin ta take yi, har wani liliya shi take, yau ansha soyayya an bar Ayla a Palo, almost 2 hours tana zaune a palon tana tunanin nata Babyn.

Sai can ya shigo palon bakinsa ɗauke da sallama, cikin sauri ta miƙe zaune tana faɗin "Sannu da shigowa daddy" hararar wasa ya wurga mata kafin ya ce "To mummy" "Mummy kuma daddy?" Ta faɗa tana zaro ido.

Saman sofar kusa da ita ya zo ya zauna yana fiskantar ta ya ce "Me ya kwantar da ke a palon nan? Kuma me kike tunani?" Sunnar da kai kasa ta yi, tana wasa da yan yatsun ta, kasa-kasa ta fara magana "Babu komai dama muna hira da Aunty ne sai Abbi ya dawo suka wuce ciki, shine sai na kwanta nima a nan ina jiranta" "To tunanin me kuma kike yi?".

Yar murmushi ta yi kafin ta ce "Tunanin ka mana daddy". Bai san lokacin da ya saki cool murmushi ba, har cikin zuciyarsa ya ji wani sanyi ta ratsa shi (ko wani Namiji yana son ace ana yi da shi, ko da kuwa ba'a yi, matukar za'a ce ana yi da shi, to ba makawa zaka juya shi yadda kake so.)

"Baby dama kina tunani na ne haka?" Gyaɗa mashi kai ta yi tare da faɗin "E ina tunaninka sosai ma". Cike da zumuɗi ya ce "Okey gaya mani tunanin me kike yi akan mijin naki?".

Wayyo bata iya karya ba, kuma bata iya ɓoye abu ba, sai ta gaya mashi gaskiya tana ta tunanin ya za su yi idan suka yi aure. Ai kuwa bai san time da dariya ta kubce mashi ba, hannayenta ya riƙo yana faɗin "Babyna Allah wasa wasa kin iya soyayya fa, oya gaya mani waye ya koya maki? A tunani na sai na koya maki, ashe dai kin iya" ɗago da kai ta yi tana kallon kyakkyawar fuskarsa. "Daddyna Rimsha ce ta koya mani, ta iya abubuwan soyayya sosai, zama da na yi da ita ne na koya, kuma aunty ma tana daɗa koya mani wasu ai".

(Rimsha tamu sarkin soyayya ba🥰 ita ta koya mata)

Ɗan masowa kusa da ita ya yi yana faɗin "Da gaske?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e.

"Wow ki ce na shirya kenan ba? Zan sha soyayya ko?" Yana magana yana kallon yadda take guntse dariya,

Zata yi magana muryan Abbi ya katse su yana faɗin "Kai kai kai kwarto a gidana da tsakar rana ban sani ba! Maik me nake ganin nan". Da yake sun saba wasa haka, sai ya fara murmushi yana ɗan shafa kansa.

Aunty kuma dake biye da Abbin a baya, sai murmushi take yi ta ce "A'a yayana ba kwarto bane, matarsa ya biyo kamar yadda kai ma ka biyo matarka" "Yauwa Sadiya gaya mashi gaskiya dai, ni mata ta na biyo" Ita kam Ayla kamar zata nitse kasa saboda kunya.

"Maik Sadiya kun saka mani kanwata jin kunya haka ba, gaskiya baku kyauta ba, Aliya ta so ki zo abin ki, kai kuma Maik kada na sake ganin ka a nan, kawai ka zo zaka tsara mani yar kanwata, to wuce ka tafi mun san halin ku maza". Gaba ɗayan su kayatatcen murmushi ne akan fuskokinsu.

Da gudu Ayla ta miƙe zata gudu wajen Abbi, da sauri daddyn Jelly ya riƙota yana faɗin "Au sai kika yarda da yaya Deen, za ki bar mijinki ki gudu wajen shi? Kina ji fa cewa ya yi kada na sake zuwa wajen ki, zaki yarda da hakan? Zaki yarda daddyn ki ya yi maki nisa?" Kallon Abbi ta yi sannan ta dawo da kallonta kan shi, gera ɗaya ya ɗaga mata alamar yana jiran amsa.

Kasa-kasa ta ce "A'a ka yi hakuri ni nafi son zama da kai". Tafi Aunty ta sa tana rangaɗa guɗa, shi kuma Abbi cewa ya yi "Eyeee to ba ku isa ba, dole ku zo ku shiga da ga ciki, ni za ku yi wa tsiya, Maik Aliya lallai kun riƙa, ke wato kin fi yarda ki zauna da shi, to wlh Jumma'a mai zuwa ina ɗaura maku aure sai ki bishi ku je ku zauna a part nasu, amma ni ba za ku min iya shege a nan ba".

Sai dariya suke gaba ɗayan su, ita kuma Ayla ta sunnar da kai kasa tana jin wani irin farinciki mai ratsa jiki a tattare da ita, sosai dukkansu suka ji daɗi, domin burinsu dama ta samu farinciki da natsuwa, ta rinƙa mance damuwar da take a ciki, wannan dalilin yasa ma dukkansu suke yawan wasa da ita, shima Abbi ya san tarihinta domin daddyn Jelly ya gaya mashi komai, Aunty kuma da suka shiga ɗaki yanzu ta gaya mashi cewa daddyn Jelly na son ta, ba karamin farinciki ya ji ba, domin ya san zata samu kulawa sosai wajen shi.

Kasa kasa ya ce "Babyna kunya ta kike ji ne?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e, zai sake yin magana aunty ta riga shi da cewa

"Yaya Maik yanzu dai na dawo bayan Ayla, ka sakar mana hannu atom".

"Wai ke Sadiya duk wannan hali da nake a ciki ba ke kika jefa ni ba? Ina zaman zamana kika sani yin soyayya ba shiri, to kuma yanzu sai dai ki zuba ido, wai ma hannunki na riƙe ne ko hannun matata?" Ya tambaya yana zaro mata idon nan nasa cikin wasa.

Cikin sauri Abbi ya tari numfashin su da cewa "Dakata ai hannun matata ya fi karfin ka riƙe matso nan Halima ta" dariya suka yi, ta faɗa jikinsa tana faɗin "To ni dai mijina ko ina zan bugi kirji in ce nawa ne, kai kuma taka har yanzu for sale ce" wani irin kallo ya wurgo mata da dara-daran idanun nan nasa kamar ball, yana ƙoƙarin yin magana kenan Abbi ya riga shi da cewa "Mai da wukar, Aliya taka ce kai kaɗai ba for sale ba ce, ni dai na baka ita amana, ka kula mani da ita sosai, idan kuma ka shirya ranar Friday sai a ɗaura auren a wuce wajen, idan ya so daga baya za'a yi su walima da sauransu, tun da tana son ka, ta faɗawa Auntyn ta da bakinta tana son ka ni ban ga wani abin ɓata lokaci ba".

Sakin hannayen nata ya yi yana faɗin "Ai gaskiya yaya Deen matar nan taka yar sa ido ce, ni ko na yi auren ma ba zan zauna a nan ba, zata saka mani ido sosai, kuma gaskiya ina son abar mani baby na tayi karatu" ya kai karshen maganar tare da nufar hanyar fita daga palon.

"Kai dawo nan, yanzu Halimar kake cewa yar sa ido a gaba na? To baka isa ba, dawo maza ka kwashi albarka ko ka yi Sa'a auren naka ya yi albarka ku haifo mana wani Hosain ɗin tun da wancan ya guje mu" Jin sunan Hosain yasa ya juyo yana faɗin.

"Yaya Deen in dai albarka Sadiya mai sa ido ne bana so, kuma ta dai'na sakawa matata ido, sannan Hosain fa ya tura mani later kafin wayan nan abubuwa su faru, shine ashe ya samawa company na wannan contract ɗin a lokacin, ko yana ina bawan Allah nan oho, ni bani wayarka ma bari na kira Imam in ji ya ake ciki"

Miƙa mashi wayar Abbi ya yi yana faɗin "Ai Hosain zuciyar bala'i ke gare shi, kyale shi idan suka gama guje gujen nasu za su dawo ne ma, muna nan muna jiran su, kuma duk halin da muke ciki yana sane, abin yana bani mamaki, kaga hakan ya nuna cewa yana kusa da mu kenan"

Karɓar wayar daddyn Jelly ya yi yana faɗin "Haka ne yaya Deen, shikenan ai tun da yana cikin ƙoshin lafiya ba wata matsala, amma dai ni ɗin ne kasan ba zan iya jure rashin shi ba, domin tsakani na da shi yafi kusa akan tsakanin shi ɗaku".

"Haka ne Maik to yanzu ya batun auren dai" Jin haka yasa Ayla ta wuce sama da sauri abinta. Bin ta da kallo daddyn Jelly ya yi har sai da ta kurewa ganin sa, sannan ya ce "Yaya Deen ka kunya ta mani mata fa, ni ina son a barta ta yi karatunta, amma dai za mu yi magana idan muka haɗu a masallaci sallar mangariba" ya kai karshen maganar tare da ficewa da sauri.

"Gaskiya Halima na ji daɗi da Maik zai yi aure, koba komai zai saku natsuwa, kwata-kwata fa shakarunsa ba za su wuci 38 years ba, amma ya azabtar da kansa da zama ba mata" "38 years kuma Abbi?! Kai ya naji shekarun nasa kaɗan?" Yar dariya Abbi ya yi yana faɗin "Wlh 38 years ya ke da shi zuwa 39 haka".

"To ita kuma Jelly shekarunta nawa?" Aunty ta kara jefa mashi tambaya tana mamaki "Ina jin 16 years take da shi, kin san Maik tun yana ɗan shekara 20 ya yi aure saboda bala'in Hadiza, hakan yasa ma bayan ya yi auren ya tattara ya koma Kano da zama, dan ya ɗan hutawa fitinarta, da aurensa bai fi shekara ɗaya zuwa biyu ba suka Haifi Jalila, ranar kuma da mahaifiyarta ta haifeta a ranar Allah ya karɓi rayuwar uwar, daga lokacin Maik ya mai da hankalinsa ga kasuwancinsa, yana kula da Jalila sosai da sosai, ba yadda ba mu yi da shi ba akan ya yi aure amma ya ki, na so ɗaukar Jalila na riƙe mashi ita, nan ma yaki yarda, yan uwan mamata sun zo ɗaukarta daga Katsina suma yaki basu, akwai wasu yan uwan maman nata a Kano, suma sun jarraba ɗaukarta amma yaki yarda, haka ya shawala ya reni kayarsa, daga karshe kuma Allah ya raba su, Maik bai taɓa rabuwa da Jalila ko daidai da na rana ɗaya ba, sai wannan ɓatar da ta yi kinga kuwa dole ya shiga tashin hankali".

Sosai Aunty ta tausaya mashi ta kuma kudiri niyar sai ta sanya shi agaba har sai ya yarda anyi auren nan da wuri, zata rinƙa gyara mashi Aylarsa sosai har sai ya kasa hakura ya ce a ɗaura kawai. (Kai Aunty kema ba baya ba🤔🤣 wai sai ya kasa hakura ya hmmm 🤣)

Wucewa Abbi ya yi ya nufi kofar fita, yana yi mata sallama, cike da so da kauna, yau ansha love komai ya wuce kamar ba'ayi ba.

Yana tafiya ta zauna saman sofa tana godiya ga Allah da sauƙaƙa mata komai, abubuwa suka zo mata cikin sauƙi.

Zaman minti 10 ta yi a wajen sai ga Hajiya Hadizatu ta faɗo mata cikin palo babu ko sallama, bata bi ta kan ta ba kawai ta haye sama abinta, binta da ido kawai Aunty ta yi tana mamakin jahilci irin nata.

Ɗaki ɗaya daga cikin ɗaku nan dake a sama ta shige ta kwanta a saman bed wai ta dawo gidan mijinta. (To fah akwai rigima kenan, Hajiya Hadizatu manya, mu dai bari mu matsa gaba ato)

A ɓangaren daddyn Jelly kuwa yana fita part nasu ya wuce, a palo ya tsaya ya kira Engr Muhammad Imam da wayar Abbi, a nan ya samu sakon da ya birki ta mashi ƙwaƙwalwa, wannan sakon kuma ba wani saƙo bane fa ce baban Muneer ya tura wa Engr Muhammad Imam wannan Video na daddyn Jelly, ya kuma ce ya bawa daddyn Jelly nan da sati uku idan bai bayyana ya kawo Jelly an ɗaura masu aure da Muneer ba, to kamar yadda ya turawa Engr Muhammad Imam wannan video haka zai turawa duniya baki ɗaya. Babbar magana.

Har wani jiri daddyn Jelly ya fara gani bawan Allah, zama ya yi a saman sofar su yana hawaye, yana dana sanin wannan rayuwa tasa, sosai Engr Muhammad Imam ya rinƙa bashi hakuri tare da gaya mashi shi ya goge video ma daga wayarsa, kuma yasan shiri aka yi mashi, yasan halinsa mutumin kirki ne shi, yasan na zai iya aikata hakan ba.

Godiya ya yi wa Engr sannan suka yi sallama ya kashe wayar ya zauna yana tunanin mafita, haka kawai zuciyarsa ke gaya mashi ya gayawa yan uwansa halin da yake a ciki, ko da akwai wani abin da za su iya taimaka Mashi da shi, shiru ya yi yana tunanin waye ya kamata ya gayamawa, haka kawai ya tsinci kansa da yanke wa kansa hukuncin ya gayawa Imran, domin Imran shine yasan komai nasa, yafi yarda da shi sama da kowa, kuma yasan Imran ya san halinsa dan haka zai masa kyakkyawar fahimta.

Ba tare da dogon tunani ba ya kira layin Imran ɗin, bugu ɗaya ya ɗauka a lokacin yana tare da Lion, shi yana kwance saman gadon, shi kuma Lion yana zaune a bakin gado yana latsawa, dan aiki yake yi sosai akan case ɗin James da batun zuwan su Tga.

Ba tare da ɓata lokaci ba daddyn Jelly ya sanar da Imran duk abin da yake faruwa, tashin hankali iya tashin hankali Imran ya shiga, har wani miƙewa zubur ya yi zaune a tsakiyar gadon, nan take zufa ta fara tsastsafo mashi daga gefe da gefen fuskarsa, a ruɗe ya furta "Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun wannan wace iriyar bala'i ce" ko kallon in da yake Lion bai yi ba, kamar ba shi a ɗakin.

Sosai ya rinƙa bawa daddy hakuri yana bashi baki.

Bayan sun gama wayar ya zauna shiru ga zufa sai kara tsastsafo mashi yake, fuskarsa ta yi sharkaf, gaba ɗaya jikinsa ya yi la'asar, dama akan wannan dalili Jellyn sa ta bar gida? Ya ilahi ya lillihi, nan take ya fara ganin jiri, ɗakin na juya mashi, haka idanuwansa ma suka fata juya mashi kamar fanka, dafe kansa dake matsanancin sara mashi kamar zai fashe ya yi yana ambato sunan Allah.

Ba tare da ya ɗago ya kalle shi ba ya kyasta mashi wayan nan fareren dogayen kyawawan yatsu nasa a fuska, gently ya ce "Prof be a man mana, why ka ke yin abu like Asif? Even Asif ba zai yi hakan ba? Tell your uncle da ya turo mani da number guy ɗin, zan duba case ɗin because of you".

Saboda farin ciki Imran bai san time da ya kurma ihu ba, kallo ɗaya Lion ya mashi ya haɗiye ihun yana faɗin "Wow thank you so much, i really appreciate, i really like this my uncle, yana da...."

Bai kai karshen maganar ba Lion ya ɗaga mashi hannu alamar ya ishe shi haka nan, baya son surutu.

Bai wani damu ba tun da Lion ya shiga case ɗin ya san 2 hours ya yi yawa za su damko baban Muneer kuma ya sha bugun maza, domin duk abin da daddyn Jelly ya faɗa Lion yana jin su, hakan yasa ya ce zai shiga case ɗin, domin daga maganar mutun yake gane mai gaskiya da kuma mai karya a cikin su, yana aiki da ƙwaƙwalwarsa sosai, da ƙwaƙwalwa yake tace abu, so ya gane daddy jelly yana da gaskiya daga cikin maganar tasu.

Sai zumuɗi Imran yake, ya kira daddyn Jelly ya ce ya tura mashi number baban Muneer, kin tura mashi daddyn Jelly ya yi dan yana tsoron kada Imran ɗin ya kira shi ya ce zai zage shi ko wani abin, shi kuma ya ji haushi ya saki Video wa duniya, hakan yasa ya ce shi ba shi da number a kansa, bai san cewa mai gayya mai aiki ne na shiga case ɗin ba.

Daga jin maganar daddyn Jelly na bai da number a kansa Lion ya san karya yake yi, abin kuma ba karamin haushi ya bashi ba, dan bai son mutun makaryaci, dan haka sai ya ce da Imran ya kyale shi ba zai yi aikin ba, Imran kamar zai yi kuka ya ce kada ya damu zai samo mashi number a hankali, shiru ya yi bai sake magana ba, daga haka Imran yasan cewa e fa ba zai shiga case ɗin bane, domin baya magana biyu.

Tsabar takaici har sai da idanuwan Imran suka cika da hawaye, ko ajikin Lion sai ma miƙewa da ya yi ya shiga toilet dan yin wanka.

Yana shiga toilet Imran ya fara zubar da hawaye, kafin Lion ya fito ya sha kukansa dan bakin ciki.

Shiryawa ya yi cikin wata kyakkyawar tsadaddiyar jallabiya fara tas, ya feshe jikinsa da wannan fitinanniyar perfume ɗin nasa, sannan ya gyara dark black curly hair sa tare da sanya black face mask a face nasa, ya dauki wayarsa ya nufi waje yana faɗin "Remain 20mins ayi sallar mangariba ka same ni a masallaci" daga nan ya fice abinsa.

Da kyar Imran ya iya miƙa wa ya fito ya nufi nasa ɗakin, wanka ya yi ya shirya shima cikin jallabiya fara, sauri-sauri ya fito dan har an fara tada hiƙama da yake akwai masallaci a unguwar tasu, suna ji ta lasfiƙa.

Duk wanda Lion ya wuce shi sai ya juya ya kallesa dan ya ga waye mai wannan kamshin turaren, perfume ɗin tana da karfi ne sosai.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull