Kenza eBookz

Triplets book 2 complete - Chapter 47

Triplets book 2 complete - Chapter 47

Triplets book 2 complete Chapter 47: Triplets book 2 complete Chapter 47. "Daddy please stop talking about this Roshan, let's continue our practical" ba su…

4,458 words

"Daddy please stop talking about this Roshan, let's continue our practical" ba su wani damu ba dan ya ce bai son hirar kakansu Roshan, dan saboda har yanzu suna ɗaukar Michael kamar ƙwaƙwalwarsa bata dawo normal gaba ɗaya ba, hakan yasa ko ya ce baya son wani basa damuwa.

Haka suka ci-gaba da karatun har karfe 6:30 daidai, bedroom nasa ya wuce ya sake yin wanka ya shirya cikin kananan kaya masu kyau, full Jeans har kasa da kuma T-shirt kamar dai yadda ko wani cikakken musulmi yake dressing, yanzu ya daina yawan saka crazy ma, dressing nasa yake yi na cikakkun mutane masu cikakken hankali.

Bayan ya gama shirinsa ya feshe jikinsa da perfume mai daɗin kamshi, sannan ya fito, word room ya fara shiga ya duba Musharraf, har lokacin barcin wahala yake yi Bawan Allah.

Kan shi Micheal ya shafa yana faɗin "Allah ya saka maka uncle, In Sha Allah zaka samu lafiya" ya kai karshen maganar yana manna mashi kiss a goshinsa.

Daga nan ya wuce zuwa waje, kai tsaye parking space ya nufa, kamar yadda suka saba fita zuwa masallaci, haka yau ya fita shi kaɗai, duk sai ya ji babu daɗi, tunani yake yi anya zai iya rabuwa da Musharraf kuwa? Yanzu ma zuwa masallaci shi kaɗai ma ya ji wani iri, ba dan sallar farilla bane da ba zai je ba, amma haka ya daure ya nufi masallacin. Sai da ya yi sallar isha sannan ya dawo gida, lokacin su kuma Tga jirginsu ya ɗaga zuwa Naija, karfe 7 daidai suka tashi.

Sai da Michael ya kara shiga word room ya duba Musharraf sannan ya dawo palo suka ci abincin dare, lokacin kuma karfe 8:40, part nasa ya koma bayan sun kammala.

Yana shiga ya kwaso takardunsa na makaranta, kafin ya fara karatun boko sai da ya tusa karatun Alqur'ani mai girma suratul humaza da Musharraf ya gaya mashi yau da asuba, bayan ya tusa kaman sau uku sai ya rufe tare da yin addu'a kamar yadda Musharraf ya koya mashi, sannan ya buɗe takardun sa ya fara dubawa yana nazari akansu, abin da ya shige mashi duhu sai ya shiga goggles ya duba, idan ya duba bai gane ba ma sai ya kira Lion a waya akan ya mashi karin bayani, da yake Lion yana son ya yi karatun sosai haka zai zauna yana mashi bayani dalla dalla. Ta ko'ina Michael yana samun taimako a kan karatu, daga daddy har Lion, ga Musharraf shiyasa a take yake haddace duk wani abin da aka koya mashi

Sai wutaren karfe 11 sannan ya tashi ya yi wanka ya yi shirin kwanciya tare da tattare takardun ya mai da su in da suke, shiryawa ya yi cikin wando dogo da riga mai ƙaramin hannu, kayan ba su da nauyi, suna da kyau sosai launin brown colar, kalar gashin kansa kenan.

Bayan ya gama ne sai ya fesa air freshener a ɗakin nasa tare da rage gudun Ac ya fito waje, kai tsaye word room ya sake nufa, kamar dai ɗazun Musharraf na ta barci har lokacin, yanzu ma addu'a ya yi mashi tare da manna mashi kiss a goshi ya gyara mashi bargon da likitocin suka rufesa da shi, ya haurar mashi zuwa saman kirjinsa sannan ya koma bedroom nasa.

Addu'ar barci ya yi ya kwanta tare da kiran Lion video call dan suka ga juna. Umm jini ba wasa ba.

A lokacin Lion ya na zaune a tsakiyar bed nasa, ya yi sallar isha tare da wanka ya shirya cikin kayan barci launin sky blue masu shegen kyau, ba karamin kyau ya yi wa kayan ba, ga idanuwansa nan sun yi wani irin yanayi mai kayatar da mai kallonsu saboda yana jin barci, barci ne a cike a cikinsu amma bai kwanta ba, yau idanun nasa sai suka yi kama da sleeping eyes, sai wani lumshe su yake yi, ga red lips nasa nan har wani ja suka kara suna kyalli kamar ya shafa lips balm, shi dama haka face nasa take, tana sheki kamar me, soft skin ɗin nan nasa ba'a magana wajen laushi da sheki.

"My Lion barci kake ji ne?" Da gera ya amsawa Michael ɗin akan yes barci yake ji.

"Okey to ka kwanta mana" ɗaura wayar ya yi a gaban laptop dake a gabansa domin ya sami dama yana aiki yana kallon Michael ɗin da kyau "I can't sleep now" Cikin sauri Asif ya ce "James ko?" Gera ɗaya ya ɗaga mashi alamar e.

"Allah zai biya ka da gidan aljanna My Lion" sai lokacin ya dawo da kallon shi kan Micheal ɗin daga kan laptop ɗin, ba karamin daɗin furucin da Asif ya yi ya ji ba, amma ba wanda ya iya gane cewa ya ji daɗin hakan saboda bai nuna alama ba.

"Yaushe zaka dawo?" Michael ne ya tambaya. Sai da ya ɗauki 1mins sannan ya ce "I don't know but know good night" ya kai karshen maganar yana ƙoƙarin katse kiran "I really missed you my Lion" shine abin da Asif ya faɗa wadda yasa Lion dakatawa bai katse kiran ba.

Kallon kasar ido ya yi mashi kafin ya ce "Ba zaka canza ba kenan?" Cool murmushi Asif ya sake yana faɗin "Yah in dai akan kune ina nan yadda nake" Shiru ya yi mashi bai sake magana ba.

Sai hira Asif yake yi mashi amma yaki tankawa kawai aikinsa yake yi, idan da sabo sun saba, hakan yasa Asif bai damu ba, can kuma sai ya ce "Asif you have class by 7, so good night" ya yi maganar a sanyaye.

Mamaki ne ya kama Michael, yaushe Lion kuma yasan suna da class karfe 7, kenan yana bibiyarsu ne? Ko me.

Yana tsaka da tunani ya ga Lion zai katse kiran "I love you" shine abin da ya furta jinjina mashi kai Lion ya yi tare da katse kiran ya ajiye wayar a gefensa ya cigaba da abin da yake yi.

Sai wuraren karfe 1 na dare sannan ya ajiye laptop ɗin ya fito palonsa ya ɗauki maltina da glass cup ya zauna saman sofa, bayan ya sha ya ɗan jima a wajen yana tunanin rayuwa, haka kawai ya ji lallai yana son taimakawa yan Nigeria, domin ya san suna da kwakwalwa da basira kawai masu taimaka masu ne suka rasa. Sai wuraren karfe 1:50 sannan ya miƙe ya shiga cikin ɗakinsa.

Kara fesa air freshener ya yi bayan wanda Imran ya fesa mashi, sannan ya kure gudun Ac, sanyayyar sanyin Ac da kuma kamshin air freshener ne kawai ke tashi, abin ba'a magana, ya kayatar matuka.

Ya haye saman lallausan bed nasa ya yi addu'ar barci ya kwanta, tun da ya zo Nigeria baya shiga cikin bargo saboda zafi, haka yake kure gudun Ac ya kwanta, amma sai ya ce a hakan ma zafi yake ji.

Yana kwanciya ba jimawa barci ta yi awon gaba da shi, asuba ta gari.

Washigari su Akil suka shigar da rahoto da komai wa yan sanda dan gane da Aafia, kamar yadda ya yi wa su Rimsha alkawari haka ya kai su gyaran jiki da kunshi tare da wanke kai, kuma har da Umaishansa ya haɗa.

Suna a wajen gyaran jikin ne Imran ya zo ya same su, a nan Akil ke gaya mashi abin da yake faruwa na ɓatar Aafia, ta shiga tashin hankali sosai shima, sannan ya fara tunanin ko dai bibiyar family'n su ake yi ne, ga Jelly shiru yanzu kuma Aafia anya lafiya kuwa?.

Tunani cike fal ransa ya karisa cikin saloon ɗin wajen su Rimsha, tana zaune ta bakin kofa a palo kenan, da yake ciki da palo ne, to a can jiki ake gyaran kai da jikin, palon kuma na zaman wayan da suka yi rakiya ne, akwai kujeru har da Ac, wajen gyara ne babba na ƴaƴan manya.

Imran ya samu an gama wa Rimsha nata ana yi wa Akila da Umaisha kuma suna ciki, ta yi kyau sosai da sosai, kunshin ba karamin kyau ya yi mata ba, amma sai da suka goge ɗan ragowar nata da ya rage a kafar tata kafin su yi mata wani, ga shi ta sha gyaran jiki, an kara fito mata da soft skin ɗin nan nata sosai da sosai, sai wani kayatatcen sheki take yi, abin ba'a magana.

Imran. Lokacin da idanunsa suka sauƙa a kanta sai da ya ji wani irin, sai da gabansa ya faɗi, ta fito kamar tauraruwa mai haske a sararin samaniya cikin hudun dare.

Kujerar gefenta ya zo ya zauna, ya jiki ya fara yi mata, da fara'a ta amsa mashi da sauki. Rimsha kenan idan kaga fara'arta to da Imran ne ko Akila, su kawai take yi wa dariya a yanzu.

Hannayenta ya riƙo cike da kulawa ya fara magana "Rimsha zuciyata ta kasa yarda cewa ba wani abin da yake damun ki, dan Allah ki gaya mani menene yake da munki? Ni fa yayan ki ne, idan har baki gaya mani ba waye kike da shi yanzu a duniyar nan da zaki gaya mawa?" Sunnar da kanta kasa ta yi tana ɗan mutsu mutsu da hannunta alamar bata ji daɗin riƙeta da ya yi ba.

Ganin haka yasa ba musu ya saki mata hannun nata yana kara nanata mata tambaya akan me yake damun ta.

"Yaya Imran ba wani abin da yake damu na, idan da akwai da zan gaya maka".

Nisawa ya yi kafin ya ce "Amma me yasa da kika ga Saif kika suma? Me yasa a ganin sa na biyu ma kika suma? Ranar da hakan ta faru naje bedroom naki da daddare dan na duba ki saboda sumar da kika yi, ina tsoron kada ya ja maki wani ciwon da cikin dare, shiyasa na shiga ɗakin ki da daddaren, na same ki kina kuka kina faɗin Allah ya cire maki son shi ki huta, wanene wannan? Tun jiya na kasa runtsawa saboda kina cikin damuwa, abin ya tsaya mani a raina, idan na barki haka to tabbas ban riƙe amana ba, sannan duba da abin da Dr ya ce na akwai abin da kike so wadda ya haifar maki da matsalar nan, da kuma abin da nagani kuma naji da kunnena kina faɗa daren ranar, hakan yasa na tabbatar da e da gaske akwai wanda kike matukar so ne, dan Allah kada ki ɓoyewa yayan ki wanenen? Ko dai Saif ɗin ne?".

Zaro ido sosai waje ta yi, nan take ta ji numfashinta na fita da sauri sauri, dafe kanta ta yi tana faɗin "A'a yaya Imran ba shi bane, ni babu wanda nake so".

"Rimsha ko ki ƙi ko ki so Saif shine wanda kike so, domin daga kiran sunan sa kin razana, sannan ranar nan da kika kawo mashi ruwan sha, yanayin yadda kika kira sunan sa kafin ki suma hakan ya kara tabbatarwa da lallai akwai wani abin a kasa wadda sai yanzu na gane menene, yanzu haka da ga gida nake na je ne ba wanda ya ganni, na bincika dan na gano menene ke damun ki, a cikin kayan da kika zo da shi naga zanen fuskar Saif wadda wannan zanen kuma ba jiya ko yau aka yi shi ba, ya ɗan jima, hakan yasa na kara tabbatarwa da e tabbas Saif kike so, na tambaye ki ne kawai dan ina son in ji da ga bakin ki, akwai hujjoji da dama wadda suke nuna e lallai Saif shine mutumin da kike so, amma meyasa zaki ɓoye mani? Nifa yayan kine, bugu da kari kuma ni kaɗai ne wanda zai iya haɗa ki da Saif a faɗin Nigeria, ko dai so kike ki cuci abokina ne? So kike ki hana shi samun zankaɗeɗiyar mace kamar ki" ya yi maganar sa ta karshen cikin raha, kuma ya yi ne dan yasa ta dariya saboda yaga ta shiga matsanancin yanayi mara kyau.

Ai kuwa tana jin maganar tasa ta karshen sai da ta yi murmushi, gyara zama ya yi ya ci-gaba da magana "E mana naga alama so kike ki hana Abokina samun mace ɗaya tamkar da million, amma fa Jelly na tafi tom, nima jelly ta ɗaya ce tamkar da million a waje na, kina son kiyiwa Lion bukulu ko? Ki yi mashi bakin cikin samun wannan zankaɗeɗiyar, kyakkyawar, kuma.....". Bai karisa ba ya yanke maganar yana kallonta

Dariya ta yi har sai da dimple nata gefe dukka biyu suka lotsa sosai, cikin dariya ta ce "Yaya Imran ka bari bana so".

Ɗan kwanto da kansa kaɗan ya yi ya leƙo fuskarta yana faɗin "Eyee waya ganta a gidan Lion matsayin amarya, wow gaskiya abin fa zai bada wani kala mai kayatarwa, ni dai koma me ni zan rako ango sayan baki". Ya kai karshen maganar yana dariya

Hannu tasa ta rufe fuskarta tana ta dariya, ga flowers da aka zana mata a hannun nata ba'a magana, sun fito sosai, da ta rufe fuska ba karamin kyau ta yi ba.

Zuba mata ido ya yi yana kallon tsantsan farincikin dake a kan fuskarta, wadda tun da suka haɗu bai ganshi a tattare da ita ba, hakan yasa ya fara tunanin ya zama dole ya san taya zai ɓullowa lamari har ta samu kusanci da Lion, dan ta dawwama a cikin farinciki haka, a nasa tunanin idan ta samu kusanci da Lion shikenan one day one time zai fara sonta, bai san cewa abin dai to ga shi nan ne, yana ɗaukar kamar zuciyoyin iri ɗaya ne.

Sosai ya nutsa cikin tunanin yadda zai ɓullo wa abin, har aka gamawa su Akila gyaran jikin, suka fito palon wajen suka same shi, gaisawa suka yi sannan ya biya masu kuɗin suka fito suka isko Akil cikin mota zaune yana jiransu.

Yana ganin su ya fito wai zai je ya biya kuɗin, Akila ce ta gaya mashi yaya Imran ya biya, to ya amsa da shi sannan suka shiga cikin mota, Imran ya tambaye shi ya batun school na Rimsha, nan ya gaya mashi ai kamar yadda ya yi alkawari to ya cika, gobe zata iya fara zuwa, amma da kayan gida zata je kafin nan a bata uniform daga baya.

Sosai Imran ya ji daɗi sannan ya musu sallama ya tafi. Sayyaya Akil ya kai su, suka sayi kayan makarantar Rimsha, irin su jaka da takalmin da sauransu, sai murna take yi, har suka dawo gida bakinta ya ki rufuwa.

Bayan sun dawo ne, suka haɗu su ukun suka fara aikin girki da gyaran part ɗin Imran ɗin, shi kuma Akil ya wuce aikin neman Aafia.

Suna aikin suna hira, Akil tana ba su lecture akan maza, ita kam Rimsha kunya kamar zata nutse cikin kasa, sai wani yan kame-kame take, tana gyaran kayan miya, ɗan zungurar ta Akila ta yi tana faɗin "Ai ina gaya maki ne yadda zaki shawo mana kan mijinmu idan Allah ya kaddara, ki rikita mana shi, sai ya fara kuka yana baby ina son ki, kin san nifa Hajiya Batula mummy'n Aunty Abla ta gama gaya mani abubuwan gyran jiki idan na yi aure, kuma ina karanta wani book na Princess Teema, so nasan abubuwa da dama, dan haka ku kasa kunne ku saurare ni, ga shi ma Hajiya Batulan ta ce zata zo biki gidansu wannan Dr Nawid da ya zo jiyan, da muka yi waya da ita da safe ta ce mani zata zo biki a gidan, zata kawo mani ziyara duk da cewa Ammie bata son ta, amma zata zo, kanwar Abba ce fa, yar autan su, ina matukar kaunar ta, idan ta zo sai ta kawo mani dilka mai bala'in kyau da gyara jiki, da kuma su humra masu bala'in kamshi, a mai duguri take aure, wayyo Allah idan aurena ya zo, zaku ga gyara, akwai abubuwa, sai dai babu mijin, sai tarin wayan nan samari marasa lissafi akai, (🤣) duk ba su yi mani ba, shiyasa bana kula kowa, ni fa ina ji a jikina mijina wani shahararren sarki ne, irin shalele ɗan gatan nan, baby ina kake ne ka zo mu yi aure in tarairaya ka kamar yadda mummy Abla ta ke wa daddy Abla, ta ce habibi ga shuwayi (shayi) nan na kawo maka, ita fa mummy Abla bata kiran shayin ma kai tsaye idan zata gayawa daddyn Abla, wlh sai ta kara lanƙwasa shi ta wani ce suuwayi, sau biyu ina zuwa gidan ta, na ga abu iya ganin ido na, yaya Imran ya yi wa Ammie wayo ya kai Ni, nima yanzu ina son babyna ya zo mu yi aure na fara lanƙwasa sunan shayi". Ta kai karshen maganar tana kwashewa da dariya ita da kanta.

Sake baki Umaisha ta yi tana kallon ikon Allah wajen Akila, Akila ta fi karfinsu, wai shuwayi kai jama'a.

Ita kuma Rimsha yar dariya ta yi kafin ta ce "Aunty Akila ni fa ba ni ba zancen aure kawai ki kyale ni".

"Uhm shi kuma fa? Ina zaki kai mana shi, kuma wlh kin ji na gaya mani irin mijin mun nan sai da lanƙwasa sunan shayi, idan ba haka ba, kina ji kina gani za'a kwace maki shi, dan ma sa'an ki ɗaya baya kula kowa, da mazan da matan duk ba su ishe shi kallo ba, amma fa ki sani wlh sai kin dage, ta fannin gyara bani da matsala da ke, kina yi sosai, sai dai sauran harka, shi kuma karki ji komai zan gayawa mummy Abla zata ɗaura ki a network, zaki rikita mana oga da salon soyayyar ki". Umaisha kam ai tuni ta fara ɗibar lecture saboda ta ga abin fa e yana da amfani dan jiya taga amfaninsa iya ganin idonta.

Sai zuba masu zance Akila take yi, da yake bata san da zancen ɓatar A'afia ba, kuma Akil ne ya kara gayawa su Irfan akan kada a gayawa Akila da Umaisha za su shiga tashin hankali sosai da sosai, hakan yasa ba'a gaya masu ba.

Suna tsaka da aiki ruwan sama ya ɓalle, da gudu Rimsha ta fita zuwa cikin ruwan nan, sai mamaki su Umaisha suke yi, suka tsaya a bakin kofar palo suna ta kallonta.

Daga karshe dai Akila ma shiga cikin ruwan ta yi dan abin ya kayatar da ita sosai, haka suka rinƙa wanka cikin ruwa.

A ɓangaren su Lion kuwa.

Su Tga sun sami isowa Nigeria, sai dai ba su shigo da wuri ba, saboda sun ɗan tsaya a Spain na ɗan lokaci dan karɓar wani saƙon na Lion, sai wuraren karfe 3 na yamma suka shigo.

Motar da Lion yasa aka kawo mashi daga gidan gwamnan Kaduna yasa sojan dake yi masu girki ya je da motar Airport ya ɗauko su, kunna map sojan ya yi ya tafi ɗauko su

Tun da ya ɗauko su a hanya suke karewa Nigeria zagi har suka iso gida, kai tsaye parking space sojan ya wuce da su, Tga ne da Tyrone, yana kashe motar suka fito waje suna karewa gidan kallo.

A harabar gidan daga ɗan gefe can Tga ya ga wayan nan yan kwacen wayar da Lion yasa aka shigo da su, da alama kuma Lion ɗin ya mance da su, dan suna ta ɗan gefe sun yi kneel down a cikin rana, abin da ya sa Tga ma ya gansu saboda da suka fito daga cikin motar, ya tsaya kewaye gidan yana kwaɓe fuska kamar wadda ya ga kashi, wai gidan kwata-kwata bata wuci lambun daddy ba, kewayen da yake yi ne yasa ya gansu, ai kuwa ba ɓata lokaci ya tambayi sojan dake a bakin gate me suka yi? Nan ya gaya mashi abun da suka gaya mashi da bakinsu sun aikata, ɗaure fuska sosai ya yi yana kare masu kallo, kamar wasu almajirai yan datti da su, duk sun yi Tsuru-tsuru da su, da alama yunwa ya ci ganiyarsu sosai ne.

"ka ajiye mani su ina zuwa, bari na yi wanka na ɗan huta, zan zo in basu horo, dan dama hannuna yana ɗan yi mani kaikaiyi ga shi kuma ba za mu sami damar isa ga James yau ba sai gobe zamu yi masu diran safiya, yanzu dare ya yi ba mu shigo da wuri ba, hannuna na kaikayi sosai zan zo na sosa akan su" Cewar Tga kenan, kamar dai yadda kuka sani ne ya yi magana cikin harshen turanci, yana kai karshen maganar kuma ya wuce cikin gida.

(Yan kwacen waya Allah ya jiƙan ku😭)

A palo ya isko Tyrone yana tsaye yana yan kalle kalle "What are you waiting for?" Tga ya tambaya yana nufar staircase ɗin, bin bayan sa Tyrone ya yi yana faɗin "You am waiting for".

A tare suka haura sama, suma dai kamar Imran da kamshin perfume ɗin nasa suka gane ɗakin da yake.

Suna ƙoƙarin shiga cikin ɗakin, shi kuma Imran na fitowa, karo suka yi da shi, ya ɗan yi baya yana faɗin "Sorry".

Wani wawan damka Tga ya yi mashi a wuya, rai a ɓace ya ce "Who are you?!".

Allah sarki Imran ya ji shaƙar manya ya kasa magana, sai zare ido yake yi kamar zai mutu, kara matse mashi wuyar da karfi Tga ya yi dan mugunta, kuma abin da yasa ya yi mashi hakan kawai dan ya ganshi ne da kayan Hausawa wato shadda, hakan yasa yasan cewa shi musulmi ne, kuma ko ban faɗa ba kunsan kiyayyar musulmai dake a zuciyarsa.

Da gaske kashe Imran ya yi niyar yi, ya shaƙesa sosai, sai zaro ido waje Imran yake yi yana ƙoƙarin cire hannun Tga ɗin daga wuyarsa, amma ina ya kasa, saboda ba riƙon wasa ya yi mashi ba.

Kamar daga sama suka ga Lion ya damki hannun Tga ɗin, tun bai yi kokarin ɓanɓareta daya wuyar Imran ɗin ba, Tga ya yi maza ya saki Imran ɗin, ya buɗe baki zai yi magana kenan Lion ya kai mashi wani irin wawan duka a gefen kumatunsa, wadda yasa nan take ya zube kasa akan gwiwowinsa jini ya fara zuba daga bakinsa ciki kuma har da hakwaransa guda biyu da suka fita, idan baku mance ba dama Lion yana jin haushin abin da Tga ya yi wa Musharraf, saboda shi ma a yanzu musulmi ne, ba zai so a taɓa musulmai ɗan uwansa ba, to shima da biyu ya yi wa Tga wannan dukar, na daga ɗaya ba ƙari.

Imran na tangal tangal yana kokarin faɗuwa Lion ya riƙoshi tare da ɗan manna shi da jikinsa ya sanya hannu yana ɗan shafa masa wuyar tasa, ya ji wuya sosai.

Dawo da kallonsa kan Tyrone ya yi da wayan nan dara daran blue eyes ɗin nasa, tun bai yi magana ba Tyrone ya wuce da sauri ya koma palo ya ɗauko mashi ruwa mai sanyi ya kawo.

Karɓa ya yi ya buɗe tare da kafa wa Imran ɗin a saitin bakinsa, sosai ya karɓi ruwan ya fara sha.

Bayan ya sha ya samu natsuwa ne Lion ya sake shi tare da wucewa ciki abinsa.

Wucewa Imran ya yi ya fita ya nufi in da za shi yana mai kara waigo Tga, yau ya ci bakar wuya, ya ji kamshin lahira, daga yin karo a rashin sani kawai sai yunkurin kisa, tab lallai wannan akwai bakar zuciya.

Tga dai ya ɗan jima a haka kafin nan ya ɗan wastsake ya yi ƙoƙarin miƙewa, sai da Tyrone ya dafa mashi sannan ya miƙe suka karisa cikin ɗakin.

A balcony suka isko Lion yana tsaye yana kallon gari. Ɗan gefensa suka tsaya har suna haɗa baki wajen cewa "Good evening sir".

Ya ɗauki lokacin da akalla zai kai 10mins kafin ya fara magana gently in a cool voice ba tare da ya kalli in da suke ba "What Imran did to you da har kake kokarin kashe shi?" Murya na sarkewa ya ce "Ya buge ni ne".

"General ina hana ka zalinci amma baka son daina wa ko? I want you to know something, shifa zalunci baya ta ɓa kai mutun ga nasara, I knew ba wai dan ya bugeka ne yasa ka yi kokarin kashe shi ba, kai kasan dalilinka so as from now babu ruwanka da shi, kome ya yi maka ka gaya mani, sannan ka sanar da sojojin nan su canza position daga wajen da suke ɗin nan, su matsa zuwa gaba" To Tga ya amsa da shi sannan ya ciro wayar sa daga aljihunsa, ya kira Captain ɗin da ya jagoranci sojojin da suka zo da su ɗin.

Da sojoji 10 kawai suka zo, saboda sun ce gaba ɗaya state ɗin da James yake a ciki ma su kaɗai sun ishe state ɗin, bare ma iya wajen da yan ta'addan suke zasu yaƙa, hakan yasa suka ɗauki sojoji kaɗan, suma dan sun san ba shakka sai sun yi musayar wuta ne da yan ta'addan shiyasa.

A takaice dai yau su Tga a Naija suka kwana, tun da ya zo ya yi wanka ya cire riga ya fara yawo haka, dama kunsan halinsa baya son zafi, daga shi sai Three quarter yake yawo, haka ya je ya kama wayan nan yan kwacen wayar ya rinƙa azabtar da su, yasa sojan dake girkin nan ya saka mashi wani karfe a wuta ta yi jawur ya rinƙa sanya su suna danme karfen da hannunsu, sun sha azaba sai ihu suke yi, sun gwammaci mutuwar su akan azaban da Tga yake yi masu.

Lion kuwa lokacin sallar mangariba suka fita shi da Imran kamar yadda suka saba zuwa masallaci, Tga bai ma san sun fita ba, yana wajen azabtar da yan kwacen waya, shi kuma Tyrone yana zaune da sojan dake a bakin gate suna hira.

Sai da aka yi sallar isha Lion ya dawo gida, shi kuma Imran ya nemi iznin zuwa gidan Abbi dan ya ji ya ake ciki batun case ɗin Aafia, bai dai gayawa Lion abin da ke faru ba, ya dai ce mashi zai je ya gaishe da uncle ɗin sa, da haka suka yi sallama.

Tga kuma sai da ya tabbatar ya gama gashewa yaran nan hannayensu sannan ya musu azabar da sai da suka fita hayyacin su kafin ya kyalesu zube a wajen, ya shige cikin gida, yana zuwa ya yi wanka ya fito ya ci abinci ya shige ɗakin kasa ya kwanta abinsa ,sai barci dan gobe akwai babban aiki a gabansu.

Shi kuma Tyrone tare da sojoji biyun nan ya kwana, Imran kuma karfe 9 daidai kamar yadda suka yi da Lion haka ya dawo.

Yayi mamakin ganin Lion ya yi barci tun karfe 9, abin ya bashi mamaki sosai, wanka ya yi ya shirya shirin barci ya kwanta a gadonsa.

Har ya fara barci sai kuma ya tuna da abin da ya faru tsakaninsa da Tga ɗazun, cikin sauri ya miƙe ya zo ya sanyawa kofarsa Key abinsa, ya koma ya kwanta ya yi barci.

(Asuba ta gari mutane na!!🥰🤗)

Washigari, cikin zumuɗi Rimsha ta shirya yaya Akil ya kaita school, bayan sun yi girki sun ci sun ƙoshi kenan, sai daɗi take ji.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull