Triplets book 2 complete - Chapter 56
Triplets book 2 complete Chapter 56: Triplets book 2 complete Chapter 56. Yar dariya Aseef ya yi kafin kuma ya ɗaure fuska sosai, nan take yanayin sa ya…
4,441 words
Yar dariya Aseef ya yi kafin kuma ya ɗaure fuska sosai, nan take yanayin sa ya sauya, yanzu dai cike da shagwaɓa ya fara magana "My James Uncle T ne yake bawa uncle Musharraf wahala, everyday idan na tafi school, before na dawo sai ya bashi horon sojoji, idan na tambayi uncle Musharraf ɗin what is happened to him sometimes nake ganin face nashi da kuma bodynsa somehow, sai ya ce mani nothing, kuma i knew there is something behind between him and uncle T dan na taɓa kama shi yana sanya uncle Musharraf ɗaga gun Ak, kuma tana cike da bullet sosai, ranar har ciwo sai da hannun uncle Musharraf ya yi, ina son gaya wa Lion amma bana son wata matsala ta faru a gidan kuma, kasan Lion zai bawa uncle T punishment mai tsanani, hakan kuma zai ɗaga wa daddy hankali, ina da tabbacin Lion yana busy this two days ɗin nan, i think that is the reason why baya bincinkan camarorin gida, da kuma abin da yake faruwa Kum......."
Bai kai karshen ba Areef ya dakatar da shi cikin tsawa "What uncle did to Uncle T da har yake ba shi horon sojoji Kuma?". "My blood you already knew that gaba ɗaya yan gida they hate Muslim people's, so the reason why uncle T ke azabtar da shi kenan, because he is a Muslim".
Rai a matukar ɓace Areef ya ce "Ya zama dole uncle T ya karɓi hukuncin zalincin da yake yi, before na tafi sai da nace mashi ya sauƙe wannan rawanin zalinci dake a kansan nan ya ajiye, amma yaki, yanzu dai zan gayawa Lion please ya sanya a kawo mani uncle na nan kasar, idan na sami lafiya sai mu koma tare, in na dawo Allah sai na sanya uncle T ya kwance wannan rawanin zalinci dake a kansa ya ajiye...."
"My blood why zaka raba ni da uncle Musharraf, you know shi kaɗai nake gani yake rage mani kewar ku fa". Girgiza kai ya yi yana faɗin "No Aseef ya zama dole na ɗauki uncle, ko so kake na barshi uncle T ya cigaba da wahalar da shi ne?" Girgiza kai ya yi alamar a'a. "To ka gani, idan ka gama Exam ai kai ma zaka bi yo mu sai mu koma a tare, so kada ka damu, ka mai da hankali sosai akan karatu."
To Aseef (Michael) ya amsa da shi, daga nan suka cigaba da hira, sosai Areef ya bashi labarin Rimsha bai ɓoye mashi komai ba, dan dama haka suke, da James da Michael sirrin su kusan ɗaya ne, abin da ɗaya ya sani da wuya ka ji ɗaya bai sani ba.
Wani irin daɗi Aseef ya ji ya ce sam Areef sai ya nuna mashi a ina Rimsha ɗin take, ai kuwa bai hana shi ganin ta ba, da hannu ya yi mata alama da ta dawo gefensa ta saman pillow da yake kwance su yi magana da ɗan uwan shi, ba musu ta miƙe ta je.
Ba ƙaramin farinciki Michael ya ji ba, da alama ma ya fi Areef murna, dan har da dariya ne akan face nasa ba iya mirmishi ba.
Ita ta fara ce mashi good morning, sai daɗi yake ji, ga fara'a palala a face nasa, ya amsa mata gaisuwar tare da tambayar ya take, lafiya ta amsa mashi da shi, "My Name is Aseef what of you?" Farinciki yasa bakinta ya ki rufuwa "My name is Rimsha" ta bashi amsa.
"Wow Rimsha nice name, cos the way am seeing your face like you are under 15 years" Ya yi maganar yana tsareta da wayan nan brown eyes ɗin nasa, ba ƙaramin mamaki Imran ya sha ba, dan ya san halin Michael sarai lokacin da suke school, amma ya akayi yau yake magana da Rimsha haka? Abin da bai sani ba shine ƙwaƙwalwar Michael ta da da ta yanzu ba ɗaya hace, da kamar ma za'a ce ba shi bane, yanzu kuwa shine, cikakken mutun mai imani da natsuwa, yanzu ne ainahin wanene shi ta bayyana.
"Yah Yaya Aseef am under 15 years, am 14 by age" Shiru ya yi yana tunanin shekarun Lion da nata shekarun, anya kuwa hakan zata yi wu kuwa? Ya tambayi kansa, Areef ne ya katse shi da cewa "What are you thinking?".
Ɗaga kai sama ya yi tare da juya manyan idanun nan nasa, kai a ɗage ya dawo da kallonsa kan Areef ɗin, ya kashe mashi ido ɗaya tare da ɗaga gera ɗaya kamar wasu munafukai, Areef bai san time da dariya ta suɓuce mashi ba, dan ya gano hanyar da Aseef yake, wato idan Allah ya ƙaddara abin da suke fata, na Lion ya yarda ya auri Rimsha zuwa ɗaya zai yi mata ba dawo sai dai a ɗauki gawarta, wato ta yi mashi karama, hakan yasa Areef satar kallon ta, ita kam ba abun da ta gane, tama yi kasa da kanta tana wasa da yatsun hannunta.
Dawo da kallonsa kan Aseef ɗin ya yi har lokacin yana ɗage da kai sama yayin da idanunsa kuma suke a gefe yana kallon Areef ɗin, da larabci Areef ɗin ya fara magana bai san cewa Rimsha tana jin larabci ba, ba kuma ya son ta ji abin da suke cewa ne, shi James yana jin yaren china amma Michael baya ji, larabcin ma James ɗin ya mance ne Michael baya ji, sai yana yi mashi kamar tare suka koyi komai.
"Kai Areef baka da kirki, me yasa zaka yi wannan tunani, ai zata girma...." Bai karisa maganar ba Aseef ya dakatar da shi da cewa "Which kind of language is this?".
Shafa fuskarsa ya yi sai lokacin ya tuna ashe Aseef fa yanzu yake koyan karatu, hakan yasa ya dawo magana da English ɗin kawai, tun duk wani baƙon yaren da yake ji Aseef baya ji sai English.
"My blood tayi ko? Kana ganin ta dace da Lion?" Cikin sauri Aseef ya jinjina kai yana faɗin "Yah sosai ma, saboda shi is so beautiful and she have innocent face, the way am looking at her like she is so silent, zata iya hakuri da mu, you knew yanzu wadda zata iya hakuri da mu ne muke buƙata, but seriously i pity her more than your expectations, saboda magana ta gaskiya you knew mu da muke TRIPLETS nasa ma, bamu taɓa gane ina ya dosa, kullun a murɗe yake, yana cikin gindayar da mutane, duk duniya ba wanda yake iya cankan ga abin da zai yi ko wanda ba zai yi ba, sai kana zaton shi a nan sai ka ga ya ma wuce nan, to be honest zata sha bakar wuya, ni for my on bana ji a jikina Lion zai bari ta zauna kusa da shi ma, bana jin wannan abin zai yi wu, amma anywhere shawarar da zan baku dai a nan ita ce, kada ku sanya yarinyar nan ta je kusa da shi ya yi mata kisan farat ɗaya, ku ɗauki alhakinta banza, wlh ni na sani idan ba wani kwakwaran dalili, kai in jin ko harbina da bindiga aka zo yi ta tare mani Lion ba zai barta a kusa da shi ba, ba zai yarda da ita ba, ko me zata yi mashi, amma zan taya ku thinking na wani solution ɗin wata kila mu dace, kuma ku yi tunani mai zurfi kada ku zo ku yi dana sani, for my on choice yarinyar ta yi sosai" dawo da kallonsa kanta daga kan Areef ya yi ya cigaba da cewa "My sister kin dai ji abin da na faɗa, iya gaskiya na gaya, ni bana karya, so is better for you ki iya takunki, ki ɗauki action mai kyau, dan bana son mu rasa wannan innocent face ɗin naki, ina ga ko daddy bai yi wa Lion irin sanin da ni na yi mashi ba, saboda ni nafi zama tare da shi, ko Areef ba zai gaya mani asalin wanene shi ba, duk da cewa nima ban san shi ciki da waje ba, dan ba komai zaka iya ganewa a tattare da shi ba, amma na san abubuwa da dama shiyasa kika ji na faɗi haka, so ki kula, idan da son samu ne ma, ki yi zaman ki sai na zo Nigeria sai mu san abin yi".
Areef ne ya tari numfashinsa da cewa "Yah Aseef abin da ka faɗa dukka gaskiya ce, ni kaina da abayane kace mani zan iya zama da mace haka mu yi hira, wlh zan ce karya ne kuma never in my life, so amma musulci ba wasa ba, In Sha Allah Lion zai so ta, ya yi aure muma mu yi aure, mu cika addininmu, amma na san ba nan kusa bane, yanzu ma abin da muke so ai ba zai ko kusan samuwa ba, shiyasa nace mata kada ta bari hanya ya rinƙa haɗa su, ta bari sai na sami lafiya, idan na sami lafiya shikenan, zan iya shiga ɗakin sa na kwanta kuma na kirata ta kawo mani abu, ko ta zo kuma ba zai ce komai ba, saboda kasan baya shiga abin da bata shafe shi ba, idan muna tare zan iya kiranta ba zai yi magana ba, amma yanzu dai bari na sami lafiya first".
Jinjina kai Aseef ya yi yana faɗin "Shawara mai kyau, hakan ma ya yi, kuma dama shiyasa nace ta bari sai nazo Nigeria, Lion baya kallon mutane da abubuwa, abin da yake gabansa kawai yake yi, amma ina da tabbacin idan tana yawan zama kusa da mu, wata rana dole zai so ganinta, kuma dole zai samu kwanciyar hankali a tattare da kasancewar a gidan, saboda idan ya ga muna tare da ita, zai ce e lallai tana da kirki, kuma zai so sanin wace ce ita da har muke tare da ita haka, zai yi bincike a kanta ko da bai gaya mana ba, kuma ina fatan daga nan shima zuciyarsa zata aminta da ita".
Jinjina kai shima Areef ya yi alamar gaskiya Aseef ya faɗa.
Kada ku mance duk wannan magana da suke yi, suna yi wa Rimsha kallon a matsayin kanwar Imran uwa ɗaya uba ɗaya ne fa, to ya kenan idan suka ji cewa shima Imran tsintota ya yi? Ba abin da ya haɗa su kuma bai san ina ƴan uwanta suke ba, kuna tunanin za su yarda da ita kenan? Kuna tunanin za su bari ɗan uwansu ya aure ta? Saboda fa kirkin Imran yasa suke sonta, dan kun ji sunce Imran mutumin kirki ne, suna son shi fiye da tunanin mai tunani, a cewarsu dukka family Imran mutanen kirki ne kamar shi, BABBAR MAGANA.
Miƙewa Imran ya yi ya nufi waje dan Akil ya kira shi yana kofar gida ya kawo kayan Rimsha.
Bayan ya karɓo ya dawo ne ya zo ya ce mata ta tashi ta je ta shirya zuwa school, to ta amsa mashi da shi, tare da yi wa Areef sallama da fatan samun lafiya sannan ta wuce ta barshi suna hira da Aseef nasa.
A gurguje ta yi wanka ta shirya cikin abaya blue color tare da hijabi ba mayafin rigar ba, time ya tafi almost 8:5 yanzu, sun zauna hira da su Areef, Imran ma bedroom nasa ya wuce dan ya yi wanka ya shirya ya zo ya kaita school.
Bayan ta gama shiri ne ta fito palo, wani irin nishaɗi ta ji lokacin da hancinta ya shako mata daddaɗar kamshin perfume nasa, da alama ya wuce a palon, zama saman sofa ta yi tana rataye da hannu ɗaya na school bag ɗin ta a kafaɗa, ga hijabinta har kasa launin blue kalar rigarta, ta yi kyau sosai, ba wani make up ko kaɗan a face nata, soft skin ɗin nan nata sai wani sheki yake yi, colan skin ɗin nata ya kara fitowa sosai, sai wani murmushi take yi ita kaɗai zaune shiru, idan ta tuna maganganun Aseef in da yake cewa mawuyacin abune Lion ya barta ta matso kusa da shi, sai ta ji gabanta na faɗu wa, me yasa kowa a cikin shawarar da zai bata sai ya ce mata kada ta haɗa hanya da shi? Ta tambayi kanta a cikin zuciyarta.
Bata kai ga samin amsar tambayar ba Imran ya fito yana faɗin "Let's go". Shirye yake cikin manyan kaya na wani haɗaɗen yadi mai kyau coffee colar, kayan sun mashi kyau sosai, shima yana da kyakkyawar saje irin na daddyn Jelly, daga wajen bakinsa kuma akwai kewayayyen gashi mai kyau sosai a wajen, kamar dai daddyn Jelly.
Gaba ya yi ta bi bayansa, a palon kasa suka hango Lion saman dining table yana latsa laptop ga kuma kayan abinci a gabansa, amma bai fara ci ba, sojan dake yi masu girki ne tsaye akansa yana jiran umarni kawai ya zuba mashi abincin. Shirye yake cikin wasu shegun tsadaddun kaya, wandon jeans ne ask color mai bala'in kyau, daga ta sama kuma high neck t-shirt ne white color, rigar ta kama jikinsa sosai hakan yasa kakkarfar surar jikinsa daga ta sama ta bayyana, ya ɗaure kyakkyawar gashin kan nan nasa a baya, kamar dai kullun wannan guntu na gaban goshin nasa yana nan, while face nasa na sanye da black glass mai bala'in kyau, idan kaga lips ɗin nan nasa, sai ka rantse da Allah yasa lips stick, har wani kyalli suke yi saboda yana ɗan ciza su time to time, gaba ɗaya kamshin perfume nasa ne ya gauraye gaba ɗaya cikin palon.
Rimsha da aka ce kar tana yawan kallonsa, amma ta kasa ɗauke idanunta daga kanshi, sai kallonsa take yi sosai, ji take tamkar ace ya zama nata, shi kuwa yana fuskartar gefe bai ma san suna yi ba, ya dai san mutane sun shigo palon, amma bai nemi sanin koma su waye bane.
Kasa kasa Imra ya ce mata ta je ta yi sallama da Areef yana zuwa bari su yi magana da Lion, to ta amsa mashi da shi sannan ya nufi ɗakin Areef ɗin, tana tafiya tana waigo Lion, ba ƙaramin tafiya da imanin ta ya kara yi ba, ya ruɗa mata kwakwalwa yau ɗin nan sosai da sosai.
Tana shiga ta sami Areef ya gama magana da Aseef yana latse latse a wayar Lion ɗin, daga ɗan gefa ta tsaya tana gaya mashi zata tafi school, dawo da kallonsa kanta ya yi kafin ya ce "Okey waye zai kai ki?" "Yaya Imran" ta bashi amsa.
Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Idan ya kai ki dawowa yake yi ko?" Jinjina mashi kai ta yi alamar e, girgiza kai ya yi kafin ya ce "Haka ba zai yi wu ba gaskiya, dole ki samu tsaro sosai, saboda yanzu ke ba kamar sauran mata bane, nasan ba za'a rasa maza masu karan kwana da zaku yi maki magana ba, ni bana son haka, komai namu saboda ne wadda mu kaɗai muke fara amfani da shi, dan haka Lion ma sabuwar mace za mu sama mashi wadda ba wanda ya isa ko da sunan wasa ya yi gigin yunkurin tinkarar ta bare ma har ya ce yana sonta, bari Prof ya zo, sojan dake bakin gate ya kai ki school, Prof ya je ya nuna mashi school ɗin, kuma ya yi gadin ki sai an tashi ya dawo da ke, zan gayawa Lion ya karo wasu sojojin guda biyu wadda za su rinƙa tsaron bakin gate ɗin, daga yau wancan ya zama mai tsaron ki, kuma nasan a wannan gaɓar Lion zai yarda, domin ya sani cewa duk wanda yake tare da mu, idan bamu ba shi tsaro ba mun ɗauki alhakinsa, kuma ma yasan wannan dokar mu ce, kuddin mutun yana a karkashin mu to yana cikin tsaro".
To ta amsa mashi da shi tare da yi mashi godiya. Tana rufe baki sai ga Imran ya shigo bakinsa ɗauke da sallama.
Kusan a tare ita da Areef suka amsa sallamar, kamar yadda ya gayawa Rimsha haka ya gayawa Imran, haka kuwa akayi, da sojan suka tafi, sai bayan sun tafi ne da Lion ya shigo karɓar wayarsa a hannun Areef ɗin, a nan ne yake sanar da Lion alfarman da yake nema, yana son abar wancan sojan ya rinƙa bawa sister Imran tsaro, shiru Lion ya yi bai yi magana ba, har ya gama abin da zai yi, zai fita ne sai ya ce "Idan sojan ya dawo ka sanar da shi nan da leƙa waje ban yarda ya sake yi ba, nan ba kasar su Prof bane? Before sister tasa ta zo nan waye ya ke bata tsaro? Ko a ƙarƙashin mu take ne? Idan ka sake yi mani irin wannan ranka zai ɓaci, ai ba a karkashin mu suke ba bare mu basu tsaro" Ya kai karshen maganar tare da ficewa abinsa.
Sai lokacin Areef ya tuna ashe ba kasar su ba ne, kuma ashe basu cike takardan zama a karkashin su ba, tunani ya fara yi ta yadda zai samawa Rimsha wannan takarda ta cike, idan ta cike shikenan tana karkashin kulawar Lion, ba zai bari wani abin ya same ta ba, addu'a ya fara yi Allah yasa Lion ya zo da takardan, idan ya zo da takardan wlh sai ya ɗauko mata ta sanya hannu ko me zai faru, lokaci guda kuma wani tunani ya faɗo mashi, ina maman su Prof take da har ta bar sister Prof a nan, da ya ke kuma su yin hakan ma ba wani abu bane a wajen su, sai bai wani damu ba, bai kuma kawo komai a ransa ba, ya san su a wajen su ma yarinya tana iya barin gidan iyayen ta koma gidan saurayinta ta zauna, kuma iyayen suna gani ba wani action da za su ɗauka akan hakan.
Tunani cike fal ransa har barci ya yi awon gaba da shi.
Imran kuwa suna fita sai da suka sayawa Rimsha abin da zata yi breakfast da shi, sannan ya bata 1k lokaci ya kure sun zauna hira da Areef bata yi girki abin da zata ci ba, tun da bata iya cin nasu ba.
Bayan sun je school ɗin Imran ya dawo ya barsu ita da wannan sojan a school ɗin, kowa sai kallonta yake yi, kowa yana son sanin wace ce ita, da soja yake gadin ta, sojan ma kuma Bature ga shi fari tas da shi kyakkyawa mai kirar jarumai, daga student har malamai sai kallonsu suke yi.
Da lokacin shiga class ya yi, har cikin class ɗin sojan ya shiga, ya zauna a kujeran da malami yake zama yana fuskartar ɗaliban, fuskar nan tasa babu alamar wasa ko kaɗan, shiyasa gaba ɗaya ɗaliban suka razana, class ɗin ya yi tsit tamkar babu kowa, ga Rimsha yar firitu agab shi, dan bata kai kirjinsa tsawo ba, da kaɗan ta ɗara cikinsa tsawo, amma a haka yake bata tsaro, duk in da ta je yana biye da ita, kai Allah ka bamu arziki mai albarka.
A ɓangaren su Ayla kuwa, yau zata fara zuwa school, sosai mijinta ya shirya ta, kamar yadda yake shirya jelly ta tafi school haka ya shirya ta ita ma, ta yi kyau sosai, shima ya shirya cikin wata haɗaɗɗiyar yadi ash color, ya yi mashi kyau sosai da yake yana da haske.
Da farko ma cewa ya yi shi zai yi mata girki tayi breakfast, dan akwai kitchen a part ɗin nasu, amma sai Aunty ta rigashi ta aiko masu da abinci, ba dan ya so ba, ya zuba mata girkin Auntyn tayi breakfast sannan suka fito suka nufi cikin gida, sun jero kamar wasu taurari.
A bakin kofar shiga palon su Abbi suka yi karo da Irfan yana fitowa, har wani faɗuwar gaba ya ji ganin su da ya yi a tare, bawan Allah har yar rama ya yi, kakalo mirmishi dole ya yi tare da miƙawa daddy hannu yana faɗin "Barka da safiya bappa".
Da fara'a daddy ya miƙa mashi hannu yana faɗin "Irfan baka da lafiya ne?" Girgiza kai ya yi kafin ya ce "A'a bappa lafiya ta lou, yanzu shiga na ciki ma sai da Sadiya ta tambaye ni ko bani da lafiya ne, wai me kuka gani kuke tambaya tane?".
Ayla ce ta caɓe zancen da cewa "Yaya Irfan ka rame ne mana, ina kwana?" Dogon numfashi ya ja tare da sauke wa a hankali kafin ya ce "Lafiya lou Aliya kin tashi lafiya?".
Lafiya ta amsa mashi da shi, sai wani kauce masu yake yi, baya son ganin fuskar Ayla, shi kuma daddyn jelly ya tsai da shi akan lallai sai ya gaya mashi menene yake damun sa, kafewa ya yi akan lallai shi ba abin da ke damun sa, haka suka hakura suka kyale shi ya wuce su kuma suka shige cikin palon.
Zaune suka isko Aunty saman dining table, cikin zolaya daddy ya ce "Sadiya kina cin ye mani kuɗi sosai fa, yanzu tun ban tashi barci ba kin haye saman table kin fara ciye ciye ko? So kike yi ki ja mani wata matsala ko? Wai ba ance kada ki rinƙa cin abubuwa masu nauyi ba har sai kin kara samun sauki ko? Shine kike ta ɗurawa da sanyin safiya salon ki jamin sake mai daki asibiti na kashe kuɗi na ko?."
Hararar wasa ta wurga mashi kafin ta ce "Kai da nake renonka ɗin ne zaka yi mani wata magana? Ni fa yanzu Aunty babba ce, ka zama kanina Yaya Maik tun da ka kame mani yar kanwata ka shige da ita part naku na zama aunty babba".
Harara shima ya wurga mata da manyan idanun nan nasa yana karisawa wajen table ɗin, "Ina kwana?" Ta faɗa tana murmushi.
"Yanzu kenan kika tuna da gaisuwar ko? To ni dai kin shirya wa matata lunch box nata ne, ko kuma in shiga kitchen da kaina?".
Kai kallonta kan Ayla dake tsaye ta sunnar da kai kasa ta yi, sai wani ƴan kame kame take yi, "Yaya Maik yanzu ni da nake Aunty babbama ni ce zan shirya maku lunch box ko?" Ɗaukar apple ya yi kwara ɗaya ya wuce ya nufi kitchen yana faɗin "Da dai ban iya girkin bane da sai ayi mani rigima, amma tun da na iya matata ta wuci gori".
"Eyeee irin wannan soyayya haka? To ni dai dawo na shirya mata, ai na san yau zata je school, dan haka na shiryawa yar kanwata komai da komai, Ayla wai kame kamen me kike yi ne? Ki je kitchen ki ɗauko box ɗin naki mana".
To ta ce tana ƙoƙarin nufar kitchen ta jiyo voice nasa daga ciki yana faɗin "No bari na ɗauko mata da kai na, sai ma na binciki me a ciki tukun nan, dan ita ba komai zata ci ba yanzu".
Murmushin kawai Aunty ke yi ta ce da Ayla ta zo mana me ya tsai da ta a can, ba musu ta kariso wajen table ɗin cike da kunya suka gaisa, cikin raha kasa kasa dan kar daddy ya ji Aunty ta ce "Ke jiya da kika wani ce mani daddy da zafi baki ji kunya ba sai yau ko? A lallai yarinyar nan". Ta kai karshen maganar tana dariya.
Ita kuma Ayla hannu tasa ta rufe fuska tana tunanin a yaushe ta ce wa Aunty daddy da zafi kuma, bata san cewa a gigin barci ta yi maganar ba.
Lunch box ɗin ya ɗauko ya fito yana faɗin "Ina yaya Deen?" "Yana barci bai tashi ba" Aunty ta bashi amsa.
Hararar ta ya yi kafin ya ce "Ke kuma har kin tashi kin haye saman table ko?" "E mana ka sani ko dalili ya sanya ni hawa saman table ɗin? Kai ma fa yaya maik wlh wasa wasa ka iya sa ido".
Ɗan zaro ido ya yi kafin ya ce "Serious fa abin da nake tunani ne ya saki cin abinci da sassafen nan? Ba likita ya ce ba zaki sake iya ɗaukar ciki ba?".
Guntun tsaki ta ja tana turo baki ta ce "Da farko dai ban san me yasa nake jin yunwa safe da dare daga jiya zuwa yau ba, na biyu kuma likita bai isa ya yanke hukuncin abin da ya shafi Ubangiji ke bayarwa ba, Allah ke bada haihuwa ba wani ba, so babu likitan da ya isa ya ce ba zan haihuba ko zan haihu, wannan hurumi ne na Aarahman".
"Haka ne zancen ki gaskiya, to Allah dai yasa abin da muke tsammani ne, mu dai mun wuce sai na dawo" ya faɗa yana barin wajen table ɗin tare da riƙo hannun Ayla da ɗayar hannunsa ɗayar kuma ya ruƙe mata lunch box ɗin suka fice daga palon, da kallo Aunty ta bisu har suka fita, sai fatan Alkhari take yi masu a zuciyarta.
Yau ma kamar daren jiya, da motar Abbi suka fita, tana zaune a front seat ta kwantar da kanta tana kallon hanya.
"Me babyn daddynta take tunani ne?" Ya tambaya yana kallonta ta cikin mirror motar, dawo da kallonta kan shi ta yi tana murmushi, "Daddy kai nake tunani mana".
"Da gaske?" Ya yi maganar cike da jin daɗi, kuma ya yi magar daidai lokacin da ya ɗauki titin makarantar tasu.
"E daddy da gaske kai nake tunani".
Cool murmushi ya saki tare da jawota jikinsa yana kara gudun motar dan su isa da wuri ya samu ya rungumeta da kyau.
A kuwa cikin ƙankanin lokaci suka isa makarantar, yana kashe motar ya rungumeta da kyau a jikinsa yana faɗin "Baby zan yi kewarki sosai wlh, yanzu sai fa karfe ɗaya zaki dawo, kai anya zan iya kuwa?". Tana daga lafe a kirjinsa ta ce "Daddy nima fa ina jin kamar ba zan iya jimawa ban ganka ba".
Wani irin daɗi ya ji burinsa ya fara cika, haƙarsa ta fara cin ma ruwa, ɗago haɓarta ya yi tare da haɗe bakinsu waje guda, nan take suka shiga bawa juna hot kiss.
Sun shagala da kiss na juna agogon dake ɗaure a hannunsa ta buga mashi karfe 8 ya yi, da kyar ya iya zame bakinsa daga nata tare da sake ta yana faɗi "Muje na kai ki". To ta amsa da shi, kusan a tare suka fito suka nufi cikin school ɗin.
Cikin ƴan mintunan da ba su wuci goma ba ya gama komai ya fito ya shiga motarsa zuwa gida ya bar ta a school ɗin, har ga Allah yana kewarta fiye da tunanin mai tunani, haka ya koma gida ya kwanta cike da damuwa.
After some hours 👌
Gidan Lion.
Bayan Rimsha ta dawo daga school, tare da sojan nan, cikin gida ta nufa kafin ta shiga bedroom nata Imran ya dakatar da ita ya ce ta shirya da wuri su je gidan babbansa su yi wa daddyn Jelly murna ya yi aure. To ta amsa da shi, cike da zumuɗi ta shige cikin bedroom nata.