Triplets book 2 complete - Chapter 65
Triplets book 2 complete Chapter 65: Triplets book 2 complete Chapter 65. Ganin abin da yake faruwa ya sanya Imran karisowa wajen da sauri yana faɗin…
4,454 words
Ganin abin da yake faruwa ya sanya Imran karisowa wajen da sauri yana faɗin "Rimsha lafiya me ya kawo ki nan..." Bai kai karshen maganar ba idanunsa suka sauƙa a kan wayar Lion dake a saman cinyarta ga shi kuma Lion ɗin yana tsaye yana fuskartar hanyar fita daga palon, so yake ta yi gigin miƙo mashi wayar nan na lahira ya fita jin daɗi, idan kuma bata miƙo mashi wayar ba nan ma ball da ita zai yi domin ya fi karfin ya duƙa ya ɗauki wayar sannan kuma baya son dukanta tana zube a kasa haka, idan ya ce zai daketa a haka to zai iya kasheta ba tare da ya sani ba shiyasa yake son sai ta ɗago tukun nan ta sha mahaukacin mari.
Imran ne ya ɗauki wayar tare da ce mata ta wuce ɗaki, cikin sauri ta miƙe zata gudu, "Come here!" ya daka mata ƴar tsawa.
Tsorata da razana da jin voice nasa ya sa ta yanke jiki ta faɗin ƙasa sumammiya a wajen.
Kallonta Imran ya yi kafin ya maido da kallonsa a kan Lion ɗin, ganin ta suma ya sa Lion ya wuce ya nufi waje dan ya lura wannan yarinya idan ya ce zai taɓa ta ma mutuwar tsaye zata yi mashi a wajen, yanzu daga magana ma ta sume masu a waje, ina ga kuma tasha marinsa ai shikenan kuma sai mutuwa.
Zura wayar a aljihu Imran ya yi kafin ya nufi wajen da take sume, hannu yasa ya ɗauketa cak, duk jikinta ya saki ta yi wani irin da ita, da kyar Imran ya iya kai ta bedroom nata domin yanzu ya tashi barci jikinsa babu kwari.
Saman bed nata ya kwantar da ita yana faɗin "Ko wani tsautsayi ya saki haɗuwa da Saif da sassafen nan, shin me ma ya fito dake oho?".
Sai surutu yake yi kasa kasa da haka ya fita daga cikin ɗakin ya bi bayan Lion domin ya kai mashi wayarsa.
A palon kasa ya iskoshi saman table yana cin abinci, ba ƙaramin mamaki Imran ya sha ba ganin yau yana cin abinci da safe haka.
Gefensa ya zo ya zauna tare da ajiye mashi wayarsa a gefen nasa, shiru Lion bai kula shi ba har ya kammala cin abin da yake yi sannan ya miƙe tare da ɗaukar wayar tasa ya nufi kofar fita, sojan da yake yi masu girki wadda kuma shine yake serving nasa abin ce, shine ya bi bayansa dan bayan girki da serving ma shi ne driversa, ɗayan sojan kuma yana bakin gate ne kawai, baya motsawa ko nan da can.
Har ya kai bakin kofa ba tare da ya jiyo ba ya ce da Imran "I don't want to see this girl again, idan ta bari muka sake haɗuwa...." Bai karisa magana ba sai ya ce "Ka tashi mu tafi yau da kai zamu yi tafiyar, kai zaka ja motar".
Godiya ga Allah Imran ya yi domin yasan cewa saboda shine ma yasa yau Lion bai take Rimsha ba, ba dan haka ba da wani zancen ake yi yanzu, duk da basu wani hira sosai amma Lion yana dannewa yana yi mashi kara sosai, saboda har ga Allah yana kaunar Imran fiye da tunanin mai tunani, yau ba da ban Imran ba da tabbas ko Rimsha bata mutu ba kaɗan ne zai rage mata na rai a jikinta, ko Areef ne ya yi mashi irin bugewar da Rimsha ta yi mashi har wayarsa ta faɗi sai ya wanke mashi fuska da mari bare kuma wata bare, kuma badan sumar da ta yi ba da sai ya doɗe mata kunne da mari koda guda ɗaya ne dan gobe ta kula amma Allah ya taimaketa ta suma.
Har bakin mota sojan dake yi masu girki nan ya rakasu, Imran ne ya ja motar shi kuma Lion kamar kullun wanan izza tana nan gidan baya ya shiga.
Da gudu Imran ya figi motar suka bar gidan, dan Lion baya son tuƙin mota a hankali, hakan ba karamin ɓata mashi rai yake yi ba ya fi son yaga ana sharara uban gudu da mota.
"Saif ina muka nufa ne?" Imran ya tambaya yana kallonsa ta cikin mirror motar.
Ya jima kafin ya fara magana a nutse "For now dai ka fara zuwa gidan cin abinci ka sayi breakfast daga nan mu wuce babbar masallacinku ina son nayi magana da malamanku".
Sosai Imran ya ji daɗi ko ba komai Lion a duk in da yake yana daraja malamai na ko wace kasa, yana mutuntasu, kafin musulunci ta zauna a zuciyarsa sosai aikawa yake yi a ɗauko mashi malaman a kawo mashi har wani gidan hutawarsa dake a cikin daji ta bakin ruwa, wajen babu mutane haka kawai ya zaɓi da ya je ya yi gini a can, amma yanzu da musulunci ya ratsa shi yana iya tashi da kansa ya je ga malamai, yana kuma girmamasu.
Babban abin farinciki wadda ya sanya Lion zai je wajen malamai shine dan su yi wa Areef addu'a tare da sauƙar Al Qur'ani mai girma, duk da ya sanya a kasarsu ana yi masu amma bai ishe shi ba, yana so a nan ma ayi masu.
A ɓangaren Rimsha kuwa, good 3 hours ta ɗauka a sume kafin Allah ya sa ta farfaɗo, baiwar Allah har wani wiki wiki ta yi kamar wadda ta ci uban gudu ta ƙoshi, ta tsorata ainun ba kaɗan ba.
Da kyar ta iya sauƙowa daga saman bed nata ta nifi toilet, wani irin wahalallen jirine yake ɗebanta saboda yunwa da take ji, sai faman dafa bango take yi domin ta isa toilet lafiya ba tare da ta taɗi ba.
Allah ya taimaketa ta shiga toilet lafiya ta yi wanka ba tare da ta faɗi ba, tana fitowa ta nufi wajen trolley ta dake a cikin dressing room na ɗakin, sauri sauri ta shirya cikin wata daguwar riga abaya black color, ta yi kyau sosai sai dai har lokacin jiri sosai take ji.
Bayan ta gama shiri fes sai tashin kamshi take yi, da kyar ta lallaɓa ta nufi waje. Kitchen ɗin ta sake komawa dan har ga Allah yunwa take ji, sai dai a wannan karon tana tafiya ne tana sanɗa kamar wata ɓarauniya, sai lallaɓawa take yi dan kada su sake haɗu, yau gaba ɗaya yasa ta ji bata son sake yin ido huɗu da shi, tsoronsa ya sa zuciyarta ta sake yin nesa da shi sosai, gaba ɗaya ta ji jikijta ya mutu, bata fatar rana irin ta yau ta sake zuwa a cikin rayuwarta, sai dai kuma fa son shi da kauna shi kara ninkuwa ya yi a cikin zuciyarta, wani irin azababben son take yi mashi wadda baki bai isa ya iya furtawa ba.
Har ta fito palon kasa babu kowa, Kitchen ta sake wucewa nan ma babu kowa, duba kayan abinci ta yi da wasu abubuwa da zata buƙata, kwata kwata babu indomie bare su supaght amma dai akwai dankalin turawa dan suna cinsa suma, sannan akwai nama da kuma kwai sosai da sosai, nama da kwan (eggs) sun fi komai ma yawa a cikin kitchen ɗin, sai wasu kalolin cimar da bata taɓa ganin irinsu ba, tunawa ta yi da yadda ta ga sojan nan yake haɗa ɗanyen kwai da ɗanyen nama waje guda yana kwaɓawa, wani iri ta ji ajikinta, abicinsu sai su, bai dafa namanba ya zuba ɗanyen kwai ya kwaɓa kafin ya yi shi kamar yam balls ya soya bayan ya zuba kayan haɗi kenan.
Guntun tsaki ta ja a fili ta ce "Allah ya kiyaye, ba a dafa nama ba ake soyawa, shima soyawar sai a rasa dame za'ayi sai da kwai, bayan nan a zuba wasu shegun kayan haɗi marasa kan gado, Allah ya sawwaka ya kiyaye na ci irin wannan abincin, anyama waƴan nan suna da maggi kuwa? Naga ranarma kamar kazarsu ba maggi, ko dai wani abin suke sakawa a matsayin maggi ne? Oho dai matsalarsu ce, amma anya abincin nan zai yi karni kuwa? Na san dai GAR ba zai taɓa cin abu mai karni ko wari ba, dole dai akwai yadda suke yi wa wannan irin abincin nasu dan kada ya yi wani abin da ba shi ba".
Ta ɗan jima tsaye tana surutanta kafin ta wuce ta ɗaura ruwa a saman gas da wani ɗan ƙaramin kyakkyawan pot mai shegen kyau da tsada, sai kyalli jikin pot ɗin yake yi tamkar yanzu aka fitar da shi daga kwalinsa.
Bayan ta ɗaura sai ta ɗauko dankalin turawa ta ɗebo daidai yadda take buɗakata tare da ɗebo kwai guda uku sai nama kuma ta ɗauki na kaza, bata ɗauki kazar gaba ɗaya ba sai ta yanki rabi ta mayar da rabi cikin freezer, sannan ta buɗe drawers dake a cikin kitchen ɗin dan neman irin su Maggi da su mai (oil) ta sami mai amma bata sami maggi ba sai dai wasu kayan haɗin wadda bata ma san tayaya ake amfani da su ba, ajiye wa ta yi ta koma wajen ɗayar freezer a nan ta sami fresh kayan miya masu kyan gaske, tattasan manya manya Tomatoes ɗin kam zaka ce mutun ya tsara shi, dan ko ance ka yi halittar Tomatoes da kanka ba zaka wuce yin manya manya masu kyau fresh kamar su ba, ga attarugu manya da su chilling pepper, albasar su ma wani irin smoot jikinsa yake gasu manya farare tas.
Ɗebar abin da take buƙata ta yi ta koma gaban gas ta fara aikinta.
Bayan ta haɗa abubuwan da zata buƙata dan yin jalof ɗin dankalin, ta gyara komai ne ta wuce ta fita a kitchen ɗin, ɗaki ta koma ta duba jakar school nata ta ɗauko 1k da Imran ya bata tare da ɗaukar hijabi har kasa ta sanya a jikinta ta nufo waje dan ta je ta sayi maggi.
Tana fitowa ta isko sojoji guda biyun nan, da mai yi masu girki sai kuma mai gadin gate ɗin suna zaune saman wasu lafiyayyun luntsuwa luntsumar kujeru masu kyau da tsada a bakin gate ɗin.
Sannu ta yi masu zata wuce ta fita sojan dake yi masu girki ya daka mata wani mahaukacin tsawa wadda ya sanyata yin baya a sukwane.
"Where are you going?!!" Ya faɗa fuskarnan babu annuri ko kaɗan, ita bata san cewa gidan Lion sai da izininsa ake shi kuma sai da izinin sa ake fita ba, shiyasa ranar da Akil ya kawo mata kayanta sai da ya kira Imran akan ya zo ya karɓi kayan sun hana shi shiga.
Cikin rawar murya ta gaya mashi maggi zata sawo a waje, tsawa ya kuma daka mata akan ta wuce ta bashi waje ta koma cikin gida ko kuma ya yi kwallo da ita, sojan dake tsaron gate ɗin ne ya dakatar da su da cewa ta koma bari ya saya mata maggin, shi har ga Allah Rimsha ta yi mashi, tun ranar da ya fara ganinta, shiyasa ya yi mata sauƙin kai har da cewa zai je ya sawo mata maggin.
Da mamakin sojan dake yi masu girki yake kallonshi, miƙewa ya yi ya nufi waje, tana tsaye tana kallonsa jikinta sai kerma yake yi, har ga Allah tana tsoron sojoji sosai amma a haka zuciyarta tayi mata rashin adalci ta kamu da son GAR.
Har ya kai bakin kofa zai fita sai kuma ya juyo cikin harshen turanci ya ce ta bashi kuɗin Nigeria dan shi dollars ne ke gare shi, kuɗin kasar su gaba ɗaƴansu suke da shi, tun da suka zo basu fita waje ba bare kuma su ce zasu je canjin kuɗi.
Cikin sauri ta miƙa mashi 1k dake a hannunta, jujjuya kuɗin ya yi yana karewa kuɗin mu kallo kafin ya ɗago ya tambayeta me sunan abin da zai saya mata sannan kuma a ina zai saya mata ɗin.
Cike da tsoro ta ce mashi ko ta zo su tafi tare ne? Girgiza mata kai ya yi ya ce ta zauna a gida domin fitarta sai ya fi zama masu haɗari akan nasu fitar, duk wanda ya shigo gidan idan suka bari ya fita ba da sanin Lion ba sai ya hukuntasu, sannan kuma su har ga Allah suna yi mata kallon tana da matukar muhimmanci tun da har Lion ya iya bari ta zauna agidansa abin da a baya ko da gigin wasa basu taɓa ganin makamancin hakan ba, basu san cewa darajar Imran ta ci ba, Imran ya yi wa su Lion abin da ba zasu iya mashi wani wulakanci ba shiyasa kawai take gidan.
Wucewa sojan ya yi ya fita shi kuma ɗayan yana zaune kamar wani gunki yana latsa waya, fara zagaye gidan ta yi tana ƴan dube dube, ba karya gidan ya haɗu iya haɗuwa.
Can ta hango kamar mutane ne a ta bayan wajen garden ɗin gidan, da sauri ta karisa wajen, waƴan nan masu kwacen waya da Lion ya kama ne, suna zaune sun gama cin abincin da sojan ya basu.
Ganita yasa suka fara kallonta daga sama har kasa, cikin rawar murya suka gaisheta dan a tunaninsu matar gidan ce da yake ta zumbula hujabi har kasa kamar wata matar liman.
Mamaki ne ya kamata akan me ya kawo su gidan nan kuma, sun ci bakar wahala kamar ba gobe sun koɗe sosai, bayan abinci da ake basu ba wani abu kuma da ake basu sai horar wa, yanzu ma an barsu ne su gama cin abinci, da zarar sun gama sojan nan zai zo ya dasa daga basu wahala da yake yi, bayin Allan har sun gwammaci da basu zo duniya ba saboda bakar wahala da suka sha a gidan THE GENERAL OF THE ARMY'S duk sun rame sun zama kamar kashi da rai.
Da sauri ta juya ta bar wajen ta koma bakin gate ta tsaya, bayin Allah nan sun bata tausayi sosai da sosai.
Ta jima tuna tsaye a wajen kafin nan sojan ya dawo, shi kuma ɗayan ko ɗaga ido bai yi ya kalleta ba, kuma dama shi ba ya ganin abin da ba'a gabansa take ba, ma'ana abin da bai shafeshi ba, horon Lion ne shi, sun fi kusa da Lion shiyasa ya ke yin ɗabiu irin na Lion ɗin, yake kwaikwayon ogan nasa.
Miƙa mata pack na maggin ya yi tare da canjin 200 pack ya saya mata, karɓa ta yi tana mashi godiya, ya sha tafiya kafin ya cinma shago, danma dai ba tafiyar yara yake yi ba, dakunsa ɗaya daidai yake da koma na ƴara.
Wucewa ta yi ta koma cikin gida, da ido ya bita har ta kurewa ganinsa sannan ya koma saman kujerar da yake zaune ɗazun ya zauna yana faɗin "Mark i really like this girl, the way she is talking the way she is walking hey i like everything about her".
Ba tare da mark ya ɗago ya kalle shi ba ya ce "Are you fall in love?" Cikin sauri ya girgiza kai alamar a'a shi ba son ta yake yi ba domin suma da alama babu aure ko soyayya a tsarinsu, bai ji kunya ba ya gayawa mark shi dai kawai sha'awar ta yake yi ba soyayya ba.
Jinjina mashi kai Mark ya yi tare da miƙewa ya koma cikin gida.
RIMSHA
Tana tsaye a gaban gas tana faman juya jolof ɗin dankalinta da bai ji wani kayan haɗi sosai ba sai gayyar tattasai da nama da kwai, ba su curry da sauransu wayan da ta saba, sai dai nasu wadda bata san ya ma ake amfani da su ba, sai kawai ta yi girkinta a haka.
Tana tsaka da aiki kamar daga sama taga an ɗauki tukunyar dankalin nata daga kan gas ɗin sai cikin abin zuba shara aka wurga, a razane ta ɗago kanta tare da juyowa dan taga wanene, wannan Mark ɗin ne mai yi masu girki, yana tsaye fuska babu annuri ko kaɗan, da hannu ya nuna mata hanya akan ta fita masu a kitchen ɗin nan, duk ta buɗe masu ko'ina da warin abincinta shiyasa ya ɗauki tukunyar gaba ɗaya ya jefa a abun zuba shara.
Bakin cikine yasa ta rushe da kuka tare da wucewa da gudu ta haura sama, tana shiga bedroom nata ta faɗa saman bed tana kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro, baiwar Allah tana jin yunwa sosai kukan nata ma baya fita sosai.
Sai da ta yi kuka mai isarta sannan ta miƙe ta ɗauki wayarta ta fara kiran layin Imran, bugu ɗaya ya ɗauka, cikin kuka ta gaya mashi yunwa take ji kuma ta yi girkinta soja ya zubar mata.
Hakuri Imran ya bata tare da ce mata yanzu Akil zai zo ya ɗauketa suje gidansa su wuni sai ya dawo zaizo ya ɗauketa, cike da murna ta amsa mashi da to sannan suka yi sallama.
Shiryawa ta yi fes ta fito waje, kai tsaye gardin na gidan ta nufa ta zauna a saman ɗaya daga cikin kyawawa kuma tsadaddun kujerun dake a wajen, tana zama ta fara kiran Akila a waya dan ta turo mata number daddyn Jelly su gaisa da Aylarta.
Sau uku tana kiran layin Akila amma Akila bata ɗaga ba har Akil ya iso, sojan nan ya hana shi shiga gidan ita kuma ya hanata fita, domin idan baku manta ba dokace ba'a shiga ko fita sai da izinin Lion.
Kuka ta fara yi tana kiran layin Imran, ta gama cin burin yau zata wuni da su Umaisha amma sojan nan yana son hana ruwa gudu.
Bugu ɗaya Imran ya ɗauka, cikin kuka ta gaya mashi wai ba zata fita ba har sai Lion ya bada izinin ta fita, hakuri ya bata tare da ce mata yanzun nan zai je ya yi magana da Lion ɗin yana cikin mota shi kuma Imran yana cikin banki zai ciro masu kuɗi, da haka suka yi sallama da ita akan ta bashi minti biyar yanzu zai fito daga cikin banki ya sami Lion a mota kada ta damu...........
Nima dai na wuce sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai , LONG PAGE HOT COMMENTS 🔥 [12/11, 5:38 PM] AMINA KABIR CAPS: 💖💖TRIPLETS💖💖
E77-78💖
Bugu ɗaya Imran ya ɗauka, cikin kuka ta gaya mashi wai ba zata fita ba har sai Lion ya bada izinin ta fita, hakuri ya bata tare da ce mata yanzun nan zai je ya yi magana da Lion ɗin yana cikin mota shi kuma Imran yana cikin banki zai ciro masu kuɗi, da haka suka yi sallama da ita akan ta bashi minti biyar yanzu zai fito daga cikin banki ya sami Lion a mota kada ta damu.
Shiru ta zauna tana ta hawaye ga bakar yunwar da take ji, shi kuma Akil ransa ya yi mugun ɓaci dan haka sai ya wuce abinsa ya koma gida tun da abin ya zama raini wayo.
Koda Imran ya koma mota ya gayawa Lion bukatarsa, sai da Lion ya ɗauki good 20mins kafin ya ɗauki wayarsa ya yi sojan massage akan ya bar Akil ya tafi da ita.
Bayan minti ɗaya da tura saƙon sojan ya sake turo mashi saƙo akan Akil fa ya tafi, gayawa Imran ya yi Akil ya wuce, sosai Imran ya ji babu daɗi, kuma yasan halin Akil ko ya ce ya dawo ya ɗauketa wlh ba zai dawo ba, dan shi ba'a yi mashi walaƙanci a waje ya kuma koma wannan waje, babbar damuwar Imran ɗaya Rimsha tana jin yunwa, bai ɓoyewa Lion ba ya gaya mashi cewa Rismha tana jin yunwa kuma ta yi girki sojan ya zubar mata ga shi kuma su ba yanzu zasu koma gida ba kuma bata iya cin kalar abincin su ba.
"And so what?" Shine abin da Lion ya ce mashi, bai damu ba dan dama yasan za'ayi hakan, jan motar kawai ya yi yana ta tunanin Rimsha har suka bar bankin suka nufi babbar masallacin Jumma'a.
A ɓangaren gidan Abba kuwa, Akila na tsaka da barcinta misalin karfe 8 na safe wayarta ta fara kara, hakan ya yi sanadiyar farkawarta daga barcin ta mai shegen daɗi da take yi.
Daga ta cikin bargo ta sako hannunta ta ɗauki wayar tata a saman bedside drawer ta mai da hannun nata cikin bargon.
Idanunta duk barci ta yi picking call ɗin, murya can kasa kasa ta ce "Hllo mijin matar shi". Daga ɗayar ɓangaren Irfan ya sauƙe nauyayyar ajiyar zuciya kafin ya ce "Matar Mijinta ba dai har yanzu barci kike yi ba?".
Turo baki ta yi kamar tana a gabansa ta ce "Yaya Irfan Allah ni sai ka biyani barcina".
"Heartbeat kin fara ko? Zaki fara rikitani ko?" Kara shagwaɓe murya ta yi cikin salon magana mai jan hankali ta ce "Allah ni da gaske nake yi yaya Irfan ka biyani barcina, haka kawai ka kama ka tasheni daga barcina mai daɗi, to ba zan yarda ba kawai ka biyani" ta kai karshen maganar tare da fashewa da kukar shagwaɓa har da wani ƴarfe hannu da kafafu kamar tana a gabansa.
Ai kuwa ba shiri ya fara rarrashinta, duk ta ruɗa bawan Allah, har wani haɗe words yake yi wajen rarrashin nata, kin yin shiru ta yi har sai da ya ce mata to ga shi nan zuwa yanzun nan sai ya goyata ta mai da barcin, sannan ne ta yi shiru tana kara turo baki kamar biro.
Sallama suka yi akan bari ya shirya yanzun nan ya zo, cike da murna ta katse kiran dan tana son ganin yayan nata kuma masoyinta, yana ranta sosai, daga daren jiya zuwa yau ta yi kewarsa sosai.
Tana katse kiran tana ƙoƙarin ajiye wayar idanunta suka sauƙa akan massages da suka shigo, ɗan taɓe baki ta yi kafin ta fara buɗe massage ɗin, wasu tun karfe biyar aka turo su, wasu kuma karfe 6 wasu 7, na farkon ta fara karantawa kamar haka.
"Amincin Allah tabbata a gareki my angel, ina fatan kin tashi lafiya, kuma ina fatan Allah yasa mafarkina aka yi jiya da daddare dan nidai nayi mafarkin ki gaskiya, na yi mafarkin ina goye da angel ɗina, so fatan kema dai kin yi nawa, na barki lafiya sai kuma anjima".
Sake buɗe sako na biyu ta yi "My angel sarkin barci kuma sarkin shagwaɓa, ina matukar kaunar wannan shagwaɓar taki, ina son jin yadda kike cewa I love you please ko zaki faɗa mani ko sau ɗaya ne?".
Daɗin massage ɗin yasa bata san time ɗin da ta furta I love you a fili ba, sai dai kawai jin word ɗin ta yi ya fito fili, ƴar murmushi ta saki kafin ta buɗe next massage "A gaskiya kin iya furta kalmar so my angel" cikin sauri ta duba time da ya aiko sakon 7:5 yanzu kuma 8:12 ne mamaki ne ya kamata yaushe ya ji ta ce i love you bayan yanzu ta yi maganar, massage ɗin kuma tun awa ɗaya baya ya turo, bata kara ruɗewa ba sai da ta ga massage na gaba in da yake cewa.
"Sarkin ruɗewa, kina mamakine dan nace kin iya cewa i love you tun baki faɗa ɗin ba? To ki daina saurin ruɗewa ki rinƙa yin tunani kafin ki ruɗe, mafiyawancin abin da nake faɗa dangane dake hasashen sa kawai nake yi, yanzu ma na yi hasashen zaki ce i love you ɗin ne yasa na yi maki wannan massage ɗin tun kafin ki faɗa, cos bana son ki rinƙa yawan ruɗewa shiyasa na gaya maki ta yadda zaki gane, idan ba haka ba muka cigaba a haka na san wata rana sai na kai yi asibitin kwakwalwa saboda ruɗewa, so kada ki rinƙa ɗaukar komai na daga magana ta kamar nasani ne na faɗa, hasashe nake yi kuma kowa zai iya yin hakan, idan hasashena gaskiya ce ki ajiye mani hot kiss zan zo na karɓa anjima da daddare, bye sako daga ɓoyayyen masoyi, Majoon ɗin Laila kuma Romeo'n Juliet".
Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauƙe kafin ta ajiye wayar tana faɗin "To meyasa baka bar mani hanyar da zan yi maka reply ba? Ina son ganin nima ina yi maka reply".
Ta kai karshen maganar tare da sauƙowa kasa daga saman gadon ta nufi toilet dan ta yi wanka ta shirya yaya Irfan nata yana zuwa, sai dai fa ba yaya Irfan ɗin take tunani ba ɓoyayyen masoyi take tunani, shine a cikin ƙwaƙwalwarta da zuciyata, ya iya tsara kalamai da kuma kula, daga gani yana da wasa da dariya bayan iya soyayya, daga gani gwanine wajen iya kula da mace, domin kuwa daga saƙonninsa zaka fahimci hakan.
Bayan ta yi wanka ta fito ta ɗan gyara bedroom ɗin nata sannan ta shirya cikin wata atamfa pink color da ratsin baki ɗinkin riga da sket, kayan sun zauna a jikinta sosai da sosai, takalma plat shoe baki ta ɗauko tare da mayafi shima baki sannan ta feshe jikinta da perfumes nata masu daɗi, simple make up ta yi ta yi kyau sosai ba karya.
Saman bed nata ta zauna farinciki ya sa kwata kwata bata jin yunwa a yanzu, bata da burin da ya wuce yaya Irfan ya zo ta ganshi.
Sai murmushi take yi ita kaɗai, tana zaune a wajen wayarta ta fara kara, cikin sauri ta ɗauki wayar dan a tunaninta yaya Irfan ne, tana duba mai kiran sai ta ga unknown number, cikin zunuɗi ta ɗauki kiran domin har ga Allah tana kewar jinsa.
Cikin sanyin murya ya ce "Assalamu alaiki warahmatullahi taala wa barkatuhu my angel".
Ɗan ciro wayar ta yi daga kunnenta tana duba screen ɗin dan ta ji muryar ya yi mata kama dana wani da ta sani, tabbas jiya da ta ji muryar ta ji kamar ta taɓa jin makamancin wannan zazzakar murya a rayuwarta sai dai ta rasa a ina ne, to yau ma da ta sake jin voice ɗin nasa da kyau ya sake fito mata karara kamar ta taɓa jin wannan murya, mamakine ya kamata.
Jin ta yi shiru yasa ya ce "Lafiya kuwa heartbeat me yasa kika yi shiru?".
Kakalo murmushi dole ta yi kamar yana a gabanta, cikin sanyin murya ta ce "Wlh ina tunani ne na ji muryarka ya yi mani kamar na san shi". Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Mai yi wu wa amma dai da kamar wuya gaskiya, yanzu dai bama wannan ba gaya mani me zaki ci na kawo maki?".
Ƴar waigawa ta yi ko zata ga ta ina yake kallonta da har yasan bata ci komai ba. "Heartbeat na gaya maki ki daina wahalar mani da kanki, Shiyasa fa ɗazun na gaya maki mafiyawancin lokaci hasashen abu nake yi akan ki, duk da wata zubin idan bana aikin komai e tabbas ina tsayuwa in kalli duk wani abin da kike yi amma ba ko yaushe ba, wani sain canka kawai nake yi saboda na yi maki farin sani, na san abubuwan da zaki yi da wadda ba zaki yi ba, hakan yasa ma hasashen nawa yake zuwa gaskiya".