Triplets book 2 complete - Chapter 78
Triplets book 2 complete Chapter 78: Triplets book 2 complete Chapter 78. Tana tsaye tana tunani har ya fito ya sameta. Kasa kasa ya motsa laɓɓansa ya ce…
4,453 words
Tana tsaye tana tunani har ya fito ya sameta. Kasa kasa ya motsa laɓɓansa ya ce ta zube gwiwowinta a kasa. Cikin sauri ta yi kasa jikinta na ta ɓari sosai, dama ga zazzaɓi. Rai a ɓace ya kara kallon hannun nata, a rayuwarsa ya tsani zanen lalle kamar me, kyamar abin yake yi fiye da tunanin mai tunani, wannan dalili ta sanya shi yin amai dan ya ci abin da ta taɓa da hannunta mai lalle.
Gaban mirrorsa ya nufa ya ɗauko wani chemical dake a cikin drawers na wajen, ya dawo wajen da take duƙe.
Gently ya ce mata ta bashi hannunta, jininta na karma ta haɗe hannunta dukka biyu ta miƙa mashi.
Babu tausayi ko kaɗan a face nasa haka ya zuba mata wannan chemical ɗin a hannayenta. Wani baƙin azaba ne ya dira mata lokaci guda wadda ya sanyata sakin wani irin kuka mai sauti tare da ratsa duk wata zuciya mai imani da tsautsayi, amma fa shi kokaɗan babu alamar tausayi a face nasa, ta yi mugun ɓata mashi rai ba kaɗan ba. Nan take hannayen nata suka fara zubar da jini sakamakon chemical ɗin ya farfasa mata fatar jikinta.
A takaice ya ce ta yi mashi shiru ko kuma ya take wuyarta a nan, ba shiri ta ja bakinta ta yi shiru, tana jin azaba ta haɗiye kukan nata kamar an ɗauke wutar nepa.
Bayan ya gama zuba mata chemical ɗin ya rufe robar tare da maida shi mazauninsa yana faɗin ta goga hannun nata da kyau dan tsabar rashin imani da baƙin mugunta.
Hawaye wani na bin wani haka ta fara goga hannayen nata cikin na juna chemical ɗin yana kara ratsata.
Sai da ya tabbatar gaba ɗaya zanen lallen ya fita sannan ya ce ta miƙe ta je ta cinye abincin nan duka, kada ta rage ko kwara ɗaya, sannan ta kwashi kayan abincin ta je ta zubar da su a bola baya son ya sake ganinsu dan ta taɓa da hannunta kai lalle.
BABBAR MAGANA taya za'ayi ta cinye abinci kula guda, kula ma kuma ba ƙarami ba, sannan ga sauran kuloli na su ferfesu da sauransu, ga kuma su fruits, kun dai san halinsa idan ya yi magana whikenan babu wanda ya isa ya sanya shi ya sauya ko da kuwa me zai faru. (DA RABON CIKIN RIMSHA ZAI FASHE YAU)
Da kyar ta iya miƙewa ta nufi wajen abincin, tana mai danasanin zuwanta duniya ma baki ɗaya, ƴar tsawa ya daka mata akan ta fara wanke jinin hannayenta ta daina ɓata mashi ɗaki, kuma ta yi maza ta fara gyara mashi ɗaki wajen da chemical da kuma jininta ya ɓata kafin ta zo ta cinye abincin.
Ta rasa ya zata yi, ta rasa a ina zata wanke hannun nata da ya ce ta wanke, shin in je toilet nawa ne ko dai yaya? Ta tambayi kanta da kanta.
Ganin babu mai bata amsa yasa ta nufi waje tare da runtse ido tana mai jiran jin wani tsawar tasa, ai kuwa hakan ne ta faru domin kuwa sai lokacin idanunsa suka sauƙa akan kunshin kafarta, wannan dalili yasa ta sake jin voice nasa ya ce ta dawo ta ɗauki chemical ɗin da kanta ta zubawa kafarta ta goge kunshin nan, Allah sarki kunshin da aka yi mata jiya jiya.
Tana hawaye ta dawo da kanta ta ɗauki chemical ɗin daga wajen da taga ya ajiye, shi kuma komawa saman bed nasa ya yi ya zauna tare da cigaba da latsa laptop nasa kamar ɗazun.
Ita kuma da kanta ta zubawa kanta chemical tana kuka ta goge wannan kunshi na kafarta tas, sannan ta miƙe kafar tata sai jini yake yi ta nufi waje.
Tana fita bedroom nata ta nufa, tana shiga ta zube gwiwowinta a kasa tare da sakin wani marayar kuka, tana cikin yi sai ta tuna da abin da ya ce ne ta zo ta gyara mashi ɗaki, hakan yasa ta miƙe da sauri ta nufi toilet nata.
Wani irin bakin azaba ta ji lokacin da ta zuba ruwa a kafar tata da hannun nata, wani irin zogi da raɗaɗi suke yi mata, jikinta har lokacin kerma yake yi, ita tunanin yadda za'ayi ta cinye abincin da ya ce ɗin nan ne ma yake damunta.
Haka dai ta wanke kafar tata da hannun nata duk sun yi jawur da su, chemical ɗin duk ya tsastsage mata soft skin nata, duk wanda ya ganta a halin da take a ciki sai ya tausaya mata tare da matsa mata kwallah.
Da kyar ta iya jan kafarta ta koma ɗakin nasa, gyara wajen da ya baci da chemical da kuma jininta ta fara yi, sai da ta gyare shi tsab, sannan ta zauna ta fara cin abicnin kamar yadda ya saka ta.
Shi kuwa tamkar babu shi a ɗakin, ya fasa cin abicin ya hakura, dan already ta riga da ta tayar mashi da zuciya, komai ya ce zai ci yanzu amai zai sanya shi, idan baku mance ba dukka TRIPLETS shegen bala'in kyakkyanin ke gare su na fitar hankali, amma ɗan gara Areef da yake ya rayuwa a wurare daban daban wadda hakan ta sanya kyakkyanin tasa ta ragu, Lion da Aseef kam ba'a magana kyankyaninsu ya wuci tunanin mai tunani, ya wuci misali.
Wani irin wahalallen amai ne ya zo mata lokacin da ta fara cin abincin nasu, amma saboda bala'in tsoronsa yasa ta haɗiye amai ɗin, ta daure ta fara cin abincin, wani irin ɗanɗano ne abinci nasu yake da shi wadda ita dai bai yi mata ba kwata kwata, haka abincin nasu ya yi mata.
Tun tana ci da ɗan daɗin rai har ta fara kuka mai sauti, wlh tamkar babu Lion a cikin ɗakin nan, da kukan nata ma ya isshe shi tsawa ya daka mata akan ta dai'na damunsa ko kuma ya taketa a nan, ta gama cin abincin nan ta je ta gyarawa su Mark ɗaki.
Yau taga bala'i da tashin hankali, bata taɓa tunanin rashin imaninsa ya kai har haka ba. Tana tsaka da cin abincin tana kuka hannunta kuma yana jini har lokacin,
GOBE IN SHA ALLAH BOOK 2 ZAI KARE. [12/20, 5:34 PM] +234 906 579 6460: 💖💖TRIPLETS💖💖
E93-94💖
Yau taga bala'i da tashin hankali, bata taɓa tunanin rashin imaninsa ya kai har haka ba. Tana tsaka da cin abincin tana kuka hannunta kuma yana jini kaɗan kaɗan har lokacin.
A haka Imran da Areef suka shigo suka same ta.
Wani irin bakin ciki Areef ya ji lokacin da ya ga me yake faruwa, Rimsha cikinta ya cika kamar zai fashe, ga shi kuma yanzu ne ma ta ci rabin abincin dake a cikin kular, ga kuma su ferfesu a gefe sannan ga fruits da su drinks, a ina zata zuba su kuma? Ga shi ya ce ko ɗiko na abin dake a kan tray ɗin kada ta tage mashi.
Imran kam kasa jurewa ya yi ya saki Areef ya juya da sauri ya fice daga cikin ɗakin dan gudun kada zuciyarsa ta buga, shi kuma Areef ya ma rasa me zai ce, ya rasa ta ina zai fara yi wa Lion bayani akan ya yi wa Allah ya rabu da yarinyar nan haka.
Sosai ya tsare Lion da ido yana kallonsa yayin da ita kuma take lodan abinci, tamkar Lion bai san ana ganinsa ba, kamar bai san da shigowarsu ɗakin ba, aikin gabansa kawai yake yi.
Wucewa Areef ya yi izuwa in da take zaune, a gefenta ya zauna tare da ɗaukar spoon suka fara cin abincin tare, ko sannu Lion bai ce masu ba, shi kuma Areef bai lura da hannun nata ba.
Da kyar da zufa suka kammala cin abincin nan, dukkansu sun kasa shan ruwa saboda bala'in ƙoshi, ita kam magana ma ta kasa yi sai nishi sama sama take yi.
Da hannu Areef ya yi mata alama akan ta kwashe kayan abincin ta fita da su waje, tana nishi da kyar da makyarkyata ta miƙe tare da ɗaukar kayan ta fice tana jan kafa.
Zuba mata ido Areef ya yi yana kallon yadda kafarta ya yi wani irin tsage tsage yana fitar da jini kaɗan kaɗan, tunawa ya yi da ɗazun kamar ya ganta da kunshi a kafarta, kenan chemical Lion ya zuba mata a jiki dan baya son ganin kunshin, Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun wannan wace iriyar bala'i ce, ya faɗa a ransa tare da miƙewa da kyar shima saboda ciwonsa ya haye saman bed ɗin na Lion yana tunanin ta yadda zai ɓullo wa Lion dan su warware wannan matsala a tsakaninsu.
Ita kuwa tana fita bedroom nata ta wuce da kayan abinci, saman carpet ta ɗaura tray ɗin tare da nufar toilet da gudu ta rinƙa sheƙa amai kamar wadda aka yi wa wahayin aman.
Amai take zubawa babu kama hannun yaro, baiwar Allah tun tana iya gani sosai har idanunta suka rufe, wani irin jirine ya kwasheta tana ƙoƙarin zubewa kasa a cikin toilet ɗin Imran da ya shigo tun ɗazun ya tsaya yana kare mata kallo, cikin zafin nama ya tarota ta faɗa jikinsa tana jan numfashi da kyar da kyar.
Zuba ruwa a cikin baff ɗin wanka ya yi tare da surka na zafi dana sanyi sannan ya ɗauketa kacokam ya sumdumata cikin ruwan.
Sai sauke wahalallen numfashi take yi, wani irin yanayi ta tsinci kanta mai wuyar fassarawa. Shi kuma juyawa ya yi ya fita daga cikin toilet ɗin dan ya bata dama ta yi wanka ko zata samu karfin jikinta.
Yana fita ya wuce bedroom na Lion, nan ya isko Areef kwance saman bed, daga baya ya tsaya yau iya ɓacin rai ya shiga ɓacin rai fiye da tunanin mai tunani, akan kanwarsa kam ba zai iya juran wannan walaƙanci ba, dole su bar gidan nan yau.
Cikin natsuwa ya ce "Saif zan ɗauki kanwata mu koma gida tun da Areef yana nan!" Shiru Lion bai tanka mashi ba, dama kuma yasan ba zai tanka a yanzu ba, sai time da ya ga dama.
Haka kuwa akayi sai da Imran ya ɗauki tsawon 20 mins a tsaye kafin nan gently ba tare da ya ɗago ba ya fara magana "Ba bu in da zaka je har sai na bar Nigeria, sannan kuma wannan yariya ƴar aikin muce, idan kuka matsa mani to wlh daga nan har Washington DC zata tabbata a ƴar aiki, so zaka iya komawa bedroom naka!!". Ya yi maganar with he's full confidence tare da nuna isa tamkar shine wanda ya haifi Imran ɗin, wannan isa da ya nuna ma ko Abban Imran baya nuna shi ba
Shiru Imran ya yi domin ba yadda zai yi, ba ta yadda zai fita gidan ba tare da izinin Lion ba, kuma ma ko da ya fita Lion yana zaune a cikin ɗaki zai sa a dawo da shi, wannan wace iriyar bakar kaddara ce? Ya tambayi kansa, shi kuwa Areef kashewa Imran ɗin ido ɗaya ya yi tare da yi mashi alama akan kada ya sake magana, domin idan ya sake magana za'a iya samun matsala, zai jawa Rimsha wata bala'in ce, gara kawai su kyale shi zuwa nan da kwana biyu idan ya sauƙa ya huce to sai su tunkare shi da zancen ta daina yi wa su Mark aiki, amma yanzu kam su kyale shi tukunnan tun da a yaune abin ya faru.
Jiki ba kwari Imran ya juya ya fice daga bedroom ɗin ya koma na Rimsha dan yaga wani hali take a ciki baiwar Allah.
Ta gama wanka sai faman dafa bango take yi dan ta fito daga toilet ɗin, wani azababben ciwo kanta yake yi mata, wani irin duhu duhu take gani a cikin idonta, lokaci guda gabaɗaya ta sauya tamkar ba ita ba.
Riƙota Imran ya yi suka kariso cikin ɗakin, saman bed nata ya zaunar da ita tare da ɗauko mata wani abaya daga cikin kayanta sannan ya zo ya sanya mata a jikinta kafin ya ce ta kwance towel ɗin bari ya je ya maida cikin toilet , ba musu ta ɗan miƙe ta kwance mashi, nan take ta fara rawan sanyi na zazzaɓi.
Bayan ya mai da towel ɗin cikin toilet ya dawo ya bata maganin da Areef ya bata ɗazun, sannan ya ce ta haura saman gado ta kwanta, haka ta haura ta kwanta ya ja bargo ya rufa mata tare da yi mata addu'ar barci ya fito ya barta kwance, zuciyarsa cike fal da tunaninta.
Bedroom nasa ya wuce a in da ya je ya yi wanka shima ya haye gadonsa tare da kashe wayarsa dan yau baya jin zai iya hira da jelly ɗin ma, yana cikin yanayi mara daɗi.
Shi kuma Areef yau a ɗakin Lion ya kwana, a tare suka kwana.
A ɓangaren Akil da Umaisha kuwa, kwance Umaisha take saman gado daga ita sai wata ƴar shegiyar riga mai ƙaramin hannu wadda ta tsaya mata a iya cinya, ba pant kuma babu bra a jikinta, haka zalika kwanciyar da ta yi yasa rigar ta yi sama, santala santalan cinyoyinta a waje, sai wani yauki take yi tana wani kara bin lafiyar gado, da alama cikin nata ɗan son jikine.
Ɗaure da towel a kugunsa ya fito daga toilet, yayin da yake riƙe da wani karami kuma yana goge kansa da jikinsa da shi.
Wani irin yawu ya haɗiye ganinta da ya yi a haka, wurgi da towel ɗin hannunsa ya yi ya haye saman gadon yana faɗin "Wife kina haukata yaya Akil sosai".
Juyowa ta yi suna fuskantar juna, turo bakin nan ta yi cikin yauki da shagwaɓa ta ce "Yaya Akil dan Allah ka matsa mani jikina ciwo yake yi mani".
Bakinsa ya kawo saitin kunnenta yana faɗin "Yanzu zan baki abin da ya fi matsa jiki, gwaggo batula ta wani ce mani wai na barki sai babynmu ya yi kwari idan ba haka ba zan iya zubar da cikin, ina ba zan iya ba, Allah zai tsare mana babynmu dan haka ajiye zancen gwaggo Batula a gefe, bari na kara mani wani babyn dan mu sami twins tun da wanan ɗin bai yi girma ba, 2 weeks ne kawai, bari yau na karo guda biyu, idan kin kasa haihuwa sai na taya ki".
Ita ma da yake yar nema ce sai ta mirgino ta shige jikinsa, riƙeta sosai ya yi tare da kawo bakinsa daf da kunnenta kasa kasa kamar wani na yi masu laɓe ya ce "Wife kin san fa aka ce mace tafi daɗi idan tana da ƙaramin ciki, dan haka bari na shanye daɗin dukka na more kafin ki haife cikin na kara maki wasu, dan Allah ƴaƴa dozen nake so".
Ita dai bata yi magana ba sai wani nanukar jikinsa take yi ɗan cikin nasu ma da gulma wai ɗumin jikin babansa yake son ji kullun, shiyasa take ta wani kara shige mashi jikinsa, shi kuwa ganin haka yasa ya fara bata a jikinta ba kama hannu yaro.
A ɓangaren gidan Abba kuwa yau ma kamar kullun Akila dai an zuba love da masoyin ɓoye fiye da tunanin mai tunani, sai dai kuma fa yau ma sai da ya saka ta kuka da salon soyayyarsa, haka kuma ya zauna ya zama mata kamar karamin yaro, yana zuba shagwaɓa yana rarrashinta har sai da ta yi shiru, sannan ya yi mata kamar jiya, ya ce ta bar wayar manne a kunnenta bari ya zuba mata zafafan kalamai har zuwa ta yi barci.
Haka kuwa akayi, ya kasheta da kalaman da sai da ta yi mafarkinsa, wani irin barci ta yi mai cike da nishaɗi tare da begen masoyin nata.
Idan muka koma gidan LION kuwa, a wannan dare dai Imran ne ya sake miƙe wa da kansa ya je ya yi sauran aikin Rismha da bata kammala ba, sannan ya dawo ya kwanta.
DREAM (Mafarki)
Misalin karfe biyu na dare, zaune take a cikin palonsu na sama, daga ita sai wandon jeans guntu zuwa santala santalan cinyoyinta, ta sama kuma wata yar riga ce mara nauyi wadda ta tsaya mata a iya cibiyarta, hannunta riƙe yake da wani tsadadden haɗadɗen cup mai shegen kyau wadda ke ɗauke da custard da spoon a ciki, a hankali take ɗeba da spoon tana kaiwa ɗan bakin nan nata, sai wani murmushi take yi tana cikin nishaɗi sosai.
Daga ta bayanta ta ji ya zuro mata hannu izuwa saman wuyarta, ko bata juya ba ta san wanene domin kuwa kamshin perfume nasa ya isar mata da saƙon wanene ɗin, ɗebar custard ɗin ta ta yi zata kai bakinta, cikin sauri ya sanya hannun nasa a bakinta ya rufe mata, a lokacin kuma tana gab da kai spoon ɗin cikin ɗan bakin nata, hakan yasa custard ɗin ta zuba mashi a hannunsa.
Ƴar kara ya yi mata a shagwaɓe, da sauri ta ajiye cup ɗin tare da riƙo hannun nasa in da custard ɗin ya taɓa ta lashe tas sannan ta cigaba da lasar hannun nasa.
Ɗaukar ɗayar hannunsa ya yi ya ɗaura a saman shafaffen cikinta yana shafawa a hankali,. Cikin nata a shafe tamkar bata taɓa zuba abinci a ciki ba.
Wani irin dogon numfashi ta ja tare da sauƙe wa a hankali, matso da ɗan bakinsa ya yi saitin kunnenta, kasa kasa ya ce "Meesha mu je ciki in baki wani abu mai daɗi kin ji ko?" Ɗan juyo da face nata ta yi da nufin ta yi magana, bata kai ga yin maganar ba ya manna mata kiss a kumatunta yana faɗin "Please mu je mana, abun daɗi fa zan baki".
Okey ta ce mashi tare da miƙe wa ta juyo suna fuskantar juna, wani irin ihu ta kurma da ganin cikin kwayar idanunsa, a razane ta farka daga barcin da take yi, sai haɗa wani uban zufa take yi tamkar ba gobe, da alama zazzaɓin nata ya sauƙa, jikinta har kerma yake yi.
Da kyar da addu'a da ambato sunan Allah ta samu ta mai da barci, domin ba zata iya tashi ta yi nafila ba saboda rashin lafiya da take a ciki, ta kasa tashi hakan yasa ta gwammaci komawa kawai ta kwanta zai fiye mata alkhari.
Da kyar ta samu ta iya mayar da barcin nata, cike da danasanin mafarkin Lion da ta yi a yau.
Washegari sai karfe 7 ta samu dama ta iya tashi daga barcin wahala da ya ɗauketa tun bayan sallar asuba.
Wayarta da Imran ya ajiye mata a saman bedside drawer ta fara dubawa, nan fa ta sami miss call na new number har kala uku, ko wani number kuma ya mata miss call zai kai guda biyar.
Shiru ta ɗan yi tana tunanin waye zata fara kira a cikinsu, daga karshe dai ta yanke shawarar bari ta kira ta farkon da ta fara kiran nata ta ji ko wanene.
Bugu ɗaya aka ɗauki kiran, cike da zumuɗi ta ce "Hello Rimsha". Duk da halin da take a ciki hakan bai hanata sakin cool murmushi ba, cike da so da kauna ta ce "Anaya ke ce dama?" Daga ɗayan ɓangaren ta ce "E Rimsha nice na ga jiya baki zo school bane shi ne yanzu na gama shiri daddy zai kai mu sai nace bari na kira number da kika bani na ji ko lafiya". Daga jin yadda take magana tana cikin matuƙar faricniki tare da jin daɗin samun Rimshan a waya.
Kara faɗaɗa murmushin Rimsha ta yi kafin ta ce "Anaya wlh kaina ne kawai yake ciwo Shiyasa ban zo ba, amma gobe zan zo In Sha Allah". "Subhanallah Allah sarki Rimsha Allah ya baki lafiya, to idan na dawo school zan ce daddy ya sanya driver ya kawo ni gidanku sai na duba ki ko? Wannan shine numberta ki yi saving kin ji?".
"To Anaya amma sai na fara gayawa yaya Imran zaki zo tukun nan, idan ya yarda to Shikenan sai na kiraki na gaya maki" to Anaya ta ce sannan suka yi sallama sai murmushi Rimsha take yi, baki ya ki rufuwa, haka ita ma Anaya ɗin, tana matukar Kaunar Rimsha sosai, ita ma Rimshan tana matukar kaunar tane sakamakon ta ce Anayar tana yi mata mugun kama da Jehan, tamkar ƴan biyun Jehan ce ita, harta shekarunsu kusan ɗaya ne, sai dai Jehan ta ɗan fi Anaya kaɗan amma bacin haka komai har tafiyarsu yanayin magana komai iri ɗaya, sai dai kuma Anaya tana dariya, ita kuma Jehan ba sai na sake faɗa ba, kunsan kwata kwata bata ma san me murmushi ba bare kuma dariya, wannan shine kawai banbancin Anaya da Jehan,. Kada ku mance JEHAN da Nawazudden take kama sosai.
ANAYA AZHARUDDEEN SALMAN SULTAN nasan daga jin sunan kun san wace ce Anaya a wajen su Rimsha, sai dai kuma ita Rimshan bata sani ba, domin bata san wanene Azharuddeen ɗin bama, daddynta kawai ta sani, sai kuma yanzu da ta san cewa su Imran ma ƴan uwanta ne.
To musan waye Azharuddeen kaɗan a tare, nasan daga jin karshen sunansa na SALMAN SULTAN kun fahimci cewa ɗan uwane ga NAWAZUDDEN SALMAN SULTAN, to Azharuddeen dai shine Hasan ɗin Nawazudden, Professor ne lecturer a jami'ar Ahmadu Bello University Zaria, sai dai mazaunin cikin garin Kaduna ne, a nan yake shi da family'nsa baki ɗaya, yana da gida a zaria a in da yake sauƙa ya kwana sai ranar Friday ya dawo cikin Kd wajen family'nsa, shararren mai kuɗi ne na bugawa a jarida, bayan Professor ne kuma yana da kampanoni da dama a faɗin kasar nan wadda take amsa sunan SALMAN SULTAN, ƴaƴan sa uku, babba namiji ɗaya mai suna Feroz shine babba mai shekara 18 yanzu a duniya, sai kuma Anaya mai shekara 15 a duniya, sai autarsu Zaira mai shekara 14 sana'ar Rimsha kenan, da yake matarsa babbar likita ce sai ta ɗauki hutun haihuwa tun daga kan Zaira ta ce ta yi auta ba ƙari.
Azharuddeen wato Hassan yana bala'in Kaunar ƴaƴan nan nasa fiye da tunanin mai tunani, hala zalika yana kaunar ƴan uwansa su Abbi, da su yake kwana da su yake tashi, yana yawan bibiyar lamuransu, shi ya rayu da su na tsawon lokaci, daga bayane ya zame kansa daga garesu, amma Daddyn su Rimsha tun yana yaro ya barsu, hakan yasa da wuya su iya gane shi a yanzu, idan dai ba shi ne ya ce masu shine wane ba, amma fa lokacin da ya fito takarar shugaban kasa sunansa ya fara yawo a duniyar Africa baki ɗaya, har gida PROF AZHARUDDEEN ya zo dan ya ganshi ido da ido domin ya tabbatarwa da kansa wannan kamanni dake a kan fuskokinsu, amma ko da ya zo Daddyn Rimsha ya ce sam ba shi bane Hosain, sunane kawai ta yi iri ɗaya wadda kuma ana iya samun hakan a cikin jama'a tunda dai duniya da faɗi take, Azharuddeen ya ji ne kawai amma bai yarda ba, abin da kuma yasa ya kyale daddyn ya tafi dan saboda kada ace sai yanzu da daddyn ya yi kuɗi ya zama wani shi ne za su neme shi, hakan yasa kawai suka kyale shi, amma ba su cire tuhumar akan cewa shine Hosain ba, haka zalika suma su Abbi sun tuhumeshi ne saboda sunansa, suma ya musa masu saboda wani dalili nashi da bamu sani ba, wata kila sai gaba za su buɗe mana komai mu sani. WANNAN SHINE TAKAITATCEN WAYE AZHARUDDEEN SALMAN SULTAN IN KIYA HASSAN A YANZU, SAI MUN SHIGA CIKIN LABARIN KUMA ZAMU SAN AINAHIN TOSHEN KAN ZANCE AKAN FAMILY'N.
Ajiye wayar ta yi bayan sun gama magana da Anaya, cikin sanyin jiki ta sauƙo kasa daga saman gadon ta nufi toilet, ruwa mai zafi sosai ta zuba ta yi wanka da shi, sannan ta fito bayan ta ɗauro alwala dan ita kullun cikin zama da alwala take.
Shiryawa ta yi cikin riga da wando kamar yadda ta saba, sannan ta sanya takalmin flat shoe mai shegen kyau, ta yi kyau sosai kamar ka sace ta ku gudu ka je ka ajiyeta kayi ta kallo dan kyau, sai wani kara cika take yi kwana biyun nan, tamkar ba ita ba, idan ta yi murmushi Yanzu wani irin lotsa dimple nata yake har wani irin rami yake yi saboda ta kara kumatu, har lokacin hannunta basu dai na yi mata zafi ba, hannun ya fi yi mata zafi domin dayawa ya zuba mata chemical ɗin a hannu, a kafa kuma ita ce ta zuba da kanta, so kaɗan kaɗan ta zuba, ba sosai ba, da hannu da kafar duk sun kumbura, kun san idan fatar mutun ta tsage dole wajen ya kumbura, a hakan ma dan daren jiya da tana barci Areef ya shigo ɗakin ya shafa mata magani, da yake jiya taci wuya sosai, da ta kwanta ko motsawa bata yi ba, wani irin barci mai nauyi ne ya ɗauketa, hakan yasa bata ma san time da Areef ya shafa mata maganin ba.
A hankali ta fito palon sama, kamar kullum babu kowa a palo, wuce wa ta yi ta nufi kasan benen dan ta je ta gaishe da Areef, sai tashin kamshi take yi abinta.
Da sallama ɗauke a bakinta ta shigo cikin ɗakin, yau yana zaune ne a saman sofa set dake a cikin ɗakin, daga shi sai singlet fara tas da three quarter zuwa gwiwa, ya yi wanka, kai Allah ya yi wa TRIPLETS halitta, wani irin sihirtaccen kyau na musamman ne ke gare su, sai kallon shi take yi, yau ma kamar jiya cikin zolaya ya ce mata "Da gaske Lion ya fini kyau, amma dai jiya da nace maki kafarsa ya fi nawa kyau wasa nake yi maki, halittar kafarmu duk iri ɗaya, amma dai ya fini kyau sosai gaskiya".
A yau dai bata ɓoye fuska ba, sai ma ɗan ɗaure fuska da ta yi jin ya amfaci sunan Lion, ta tuna azaban da ta sha daren jiya ne.
Kamar dai ko yaushe, gefensa ya nuna mata ta je ta zauna yana faɗin "Dan Allah Rimsha ki yafe wa ɗan uwana, kada ki ce zaki dai'na son shi saboda abin da ya faru jiya, duk abin da ya ɓata mu zamu gyara, shi kuma zai biya ki amma sai gaba, ina sa ran haka, kiyi hakuri saboda mu kin ji ko?".
Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e ta ji. Wayarsa ya ɗauko ya fara kiran layin Aseef video call, dama tun ɗazun Aseef ya takura mashi akan ya haɗa da RIMSHA ya ce mata sorry da abin da ya faru,. Allah mai iko wai yau family'n William jacop ne za su cewa wata sorry, sorry ma kuma ga mace, tab lallai musulci duniya ne, musulci daban take, idan Allah ya yo ka a musulmi to ko tabbata ka yi kana gode mashi baka biya shi ba, addini mai sanyi, mai sauƙi, tausayin na kasa, girmama iyaye, kamanta adalci, rashin wariya, kaunar juna, Allah mun gode maka da ka yo mu a musulmai.