Kenza eBookz

Uwar sadiku complete - Chapter 36

Uwar sadiku complete - Chapter 36

Uwar sadiku complete Chapter 36: Uwar sadiku complete Chapter 36. Haka hayakin da ya fita daga robar ya nannade yayi sama suna kallo ya bace, suka yi…

4,498 words

Haka hayakin da ya fita daga robar ya nannade yayi sama suna kallo ya bace, suka yi cirko-cirko. Abban ya karasa ya daga robar a kasan ba tare da ya dauka ba. Wani abu ne a ciki kamar kwan agwagwa sai dai shi akwai rubutu a jiki. Suka dan matso suka zubawa abun ido. Abban ya fara karanto ayatul kursiyyu a fili ya tofawa wannan robar sannan ya ci gaba da jan ‘la haula wa la kuwwata illa billah’; yasa hannu ya zaro kwan a hankali. Babu nauyi kwata kwata, yana dubawa ya ga kwan ya tsage kuma babu komai a ciki; kamar bawon kwan ne kawai. Ya juya yana karanta rubutun da yake jikin bawon kwan; sunansa ne da sunan mahaifinsa da na mahaifiyarsu aka rubuta da jan rubutu. Sai kuma aka rubuta sunan Aisha da na iyayenta da bakin rubutu kuma aka sokeshi da jan rubutu.

Cikin sanyin murya Saddiku yayi tambayar da kowa yake son yi ya kasa

'Abba menene wannan din kamar abun aljannu?’

Ba tare da ya dauke idonsa daga kallon abun ba yace

'Ban sani ba Saddiku, amma dauko min wayata a falo tana chaji na kirawo Malam Liman Muji. Tunda ma abun ya fita a gidan kada muje ya cutar da wani.’

Nan da nan Saddiku ya fice.

Su Murja da Zahra duk sun kasa magana sai kallon-kallo kawai sukeyi suna zare idanu. Ba jimawa Saddiku ya dawo ya mikawa Abban wayar yana cewa

'Baba ma ya kirawoka ga missed calls nan har biyar.’

Yana karbar wayar ya kawar da missed calls din Yaya Bello ya lalubo lambar Malam Liman ya kirawo. Aka yi sa'a yana kusa don haka ba tare da bata lokaci ba ya ce gashi nan zuwa. Daga su Murja har su Zahra duk jikinsu yayi sanyi don haka gaba daya suka hakura da aikin suka fara diban kayan da zasu fito da su suna fitowa dasu falon.

Kafin su gama Malam Liman ya bugo wayar Abba ya sanar dashi yana kasa, ya umarci Saddiku da ya shigo da shi. Ya sauko daga saman da sauri.

Yana zuwa bakin kofar falon kasan ya ci karo da Yaya Bello yana sallama a bakin kofar. Bayan ya amsa gaisuwarta yace

'Saddiku Ina Abban naka ne? Lafiya dai kuke gaba daya? Ina kannenka? Ina ta kiran wayar Abban baya dagawa.’

‘Yana nan, aiki mukeyi a dakin Mommy. Malam Liman ne yake jiransa a waje yace na shigo da shi, bari na kirawoshi sai nazo na kirawo Abban.'

Yaya Bello ya karasa shigewa falon yayinda Saddikun ya fice da sauri.

Jummai ta fito daga kicin da taji motsin Yaya Bellon, bayan ta gaisheshi tace

'Suna sama ma shi da su Hajiya Murja ne, bari na kawo maka ruwa.’

Kafin ya amsa ta koma kicin din.

Tana shigewa Saddiku suka shigo tare Malam Liman, bayan sun gaisa da Yaya Bellon Saddiku yace

'Cewa yayi ka hawo saman.’

'To bismillah.'

Ya bi bayansa.

Sadik din ya juya yacewa Yaya Bello

'Baba kazo muje saman Abban yana can.’

Ya mike gabobinsa babu kwari don ya zata wata lalura ce ta sami Abban wadda tasa ba zai iya saukowa ba zai ce a zo da mutum.

Suka bi bayan Saddiku suka haye saman.

Cirko-cirko suka tarar da su Abban a daki babu mai magana, yana ganin yayansa yace

'A'a! Yaya a ina ya samoka?’

'To na kasa nutsuwa ni din ma, sai waya nake maka baka dauka ba sai na zata wata matsalar ce a gidan.’

'Ta ba za a ce babu matsalar ba, ku karaso.’

Suka karasa ciki suka gaggaisa a tsattsaye. Abban ya nunawa Malam Liman robar wadda take ajiye a kasa da kuma kwan a kan murfin yayi masa bayani sannan kuma ya mika masa kwalbar fiya-fiya da ya jefe a aljihu. Suka tsuguna gaba daya Abban yana sake yi musu bayanin hayakin da ya fita daga cikin robar Liman yana dubawa.

Jimawa kadan yace

'Inna lillahi wa Inna ilaihi rajiun!’

Ya bi mutane dake dakin da kallo gaba daya sannan ya cewa Abban

'To ka san idan mutum ya mutu duk wata tashin-tashina barinta ake yi. Yanzu a nan waye bare wanda ba dan uwan ita marigayiya ba? Don ka ga idan da wanda ba zai rike mata sirri ba sai ya fita.’

Ya nuna su Yusra yace

'Wadannan dai yaranta ne ka san su, wannan yayana ne shi kadai gareni dan uwa, wadannan kuma yayarta ce da kanwarta uwa daya uba daya.’

Yaya Bello yace

'Bari na jiraku daga falo nan.’

Liman yace

'Ai ba ma sai ka fita ba ina ga duk nan amintattune, sai dai kawai zan bamu shawara duk abinda muka ji muka gani mu barshi a nan mu cigaba da yi mata addu'a.’

Duka suka amsa sannan yace

'Gaskiya wadannan abubuwan guda biyu da ka bani tsafi ne ko sihiri, hayakin da kuka ga ya fita ba zan yi mamaki ba idan aka ce aljani ne to amma ba zan sani ba tunda ban gani ba. Ko ma menene ya fitan bana jin zai tsaya nan kusa tunda kamar ya sami ‘yanci ne.’

Ya mikawa Abban karamin kyallen da ya zaro daga cikin kwalbar ya cigaba

'Ka ga wannan gutsure na na rigar wanda aka yiwa sihirin gashi nan. Sai a tattara wadannan tarkacen a kona sannan a binnesu tare da zancen, wadanda suka rigamu gidan gaskiya Allah ya yafe musu.’

Sukayi dif kamar ruwa ya cinyesu kowa da abinda yake tunani. Sai da Malam Liman ya gaji da shirun yace

'Kai Saddiku sai ka kwashi wannan ka kona ka binne shike nan a cigaba da addu'a.’

Abba yace

'Malam babu wata matsala idan an one din.’

'Babu wata matsala. Ai na riga na tofesu da ayoyin Allah kuma tunda me shi ta rasu ba zai yi tasiri ba. In ya so dai yara su karanta suratul bakara a gidan don a sami natsuwa gaba daya.’

Yayi musu sallama Abba da Yaya Bello suka bi bayansa don yi masa rakiya.

Suna fita Murja ta kalli Suwaiba tace

'Uhm! Ina ga sai mu tafi, ragowar kayan ma dawo. Ko kuma bari Abban ya dawo sai na tsaya mu kona wannan tarkace.’

Suwaiba tace

‘Allah ya kyauta.’ Suka fara hada kayansu don tafiya; gaba dayansu kowa zuciyarsa a jagule har Yusra wadda ta kasa magana. Nan falon saman suka zauna suna jiran Abban. Tunani kala-kala ne yake yawo a ran Yaya Murja; to yaushe Zahra ta fara tsafi? Ga shi ta mutu? Kuma ga dukkan alamu Abban take yiwa wanda gashi yanzu ya gani.

Haka suka zauna har Abban ya dawo saman suka yi masa sallama cike da jin nauyin abinda ‘yar uwarsu ta aikata suka fice cike da tsananin damuwa da mamaki. Godiya daya suke yiwa Allah da Liman yace kada a fita da zancen don haka ma suka fice ba tare da sun cewa Abban komai ba a kan zance.

Suna tafiya Abban ya koma dakin ya rufo kofa yayin da Yusra da Saddiku suka shige dakinsu.

UWAR SADDIKU

Written by Sakina Yazid (Innar su Amal)

45

Su Yaya Murja suna fita daga gidan suka wuce gidanta don dama a nan zasu ajiye kayan da suka kwaso kafin su san abinda zasuyi da su. A dakinta suka zube a gajiye cike da damuwa. Kowa ya kasa magana saboda damuwa.

Jimawa kadan Suwaiba ta dubi Murja ta kirawo sunanta, sai dai kafin ta fadi abinda take son fada hawayen da take tarewa ya kwace. Itama Murjan ta kama share kwalla, sai da sukayi mai isarsu sannan Suwaiban ta goge fuska tace

'Yaya kin ga yanzu dole mu bar maganar Abban Saddiku ya auri Rahma, tunda na san mu kanmu kallonmu kawai yake yi. Wannan abun da Yaya Zahra tayi ai dole ya zata duka haka danginmu suke. Aishan kuma da muke kokarin mu kare yara daga fitnarta kinga ashe ba itace mai fitnar ba.’

Cikin tsananin damuwa tace

'Hmm! Suwaiba ai dole a bar wannan maganar tunda jiyan nan dama na yiwa Rahman maganar itama ta sakawa idonta toka tace ba zata aureshi ba kada ma mu soma maganar. Watakila ko ita ta san da wadannan abubuwan da Zahran take yi shi yasa taki shiga gidan.’

'Babu mamaki, amma dai ina mamakin yanda akayi Zahra ta zama haka. Kullum fa nusar da ita nakeyi yanzu dubi abubuwan da muka gani, da wanne ido zaka fuskanci ubangiji ka yi wannan aika-aikar?’

Nan suka dauki lokaci suna jimami da jajantawa, sai da aka fara kiran azahar sannan Suwaiba tayiwa Murja sallama ta tafi.

……..

Tunda Abba ya shiga dakin ya rufo kofa ya zauna a gefen gado ya zuba fuskarsa a tafukan hannunsa cikin damuwa. Tunani sun yiwa kwakwalwarsa yawa don haka bai ma san me yake tunani ba.

'Zahra.'

Ya kirawo sunanta a karo na babu iyaka cike da matsanancin mamaki.

To shi kuwa me yayi wa Zahra zata cutar da shi da Aisha? Me yayi zafi har ta barar da imaninta? To tun yaushe take wadannan abubuwan?

'Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!’

Ya fada a fili yana goge fuska. So yake ma ya fitar da hawaye ko zai ji sanyi a ransa amma ko digon hawaye idonsa ya kasa fitarwa.

Lallai wadannan sune abubuwan da Aisha ta san ana yi mata har take jin ba zata zauna da Yusra ba. Yanzu haka Yusran ake turawa tana binne mata irin wadannan abubuwan shi ya sa tace ba zata zauna da ita ba; kuma bai ga laifinta ba a yanzu. Domin ko shine ya san halin Zahra to da tuni ya dade da rabuwa da ita.

Ya daga hannu sama kamar mai addu'a yace

'Allah ka hana yarana bin wannan hanyar da uwarsu ta bi, Allah ka shiryesu ka hana su shirka.’

Kwalla ta gangaro kan fuskarsa, ya sa hannunsa ya share.

Sai a lokacin ya samu ya hadiye malolon da ya tokare masa makogoro.

Yanzu wannan dabi'ar Zahra ta dora Yusra a kai? Lallai yana da aiki. Zahra bata yi masa adalci ba, ta cutar da shi.

A take nadama ta rufe shi, bai taba nadamar auren Zahra ba kamar yanda yakeyi yanzu.

Yanzu ya zai yi da wannan matsalar?

Haka ya wuni a dakin yana ta tufka da warwara shi kadai, don ko masallaci bai fito ya je ba balle ya nemi abinci.

Yanda ya wuni cikin damuwa haka shima Saddikun ya wuni.

Itama Yusra haka ta wuni, sai dai ita damuwarta ba me yawa bace. A iya tsawon rayuwarta ta san kullum Mommy tana tsaye a kan nema musu kariya, wannan abubuwan da aka samu a dakin Mommy din ta san suna cikin wannan kariyar wanda Mommy din ta sanar da ita duk addu'oi ne don haka ita bata ma ga wani abun tashin hankali a ciki ba. Fatan ta daya Allah ya sa kada wata cutarwar ta samesu saboda wadannan abubuwan da aka kona.

—----- Yana dakin har bayan karfe uku, sai wajen la'asar yunwa ta dameshi. Yana fitowa ya hango abincinsa a kan dining table don haka ya zauna ya ci. Yanda yaji gidan shiru ya san yaran sun tafi makaranta don haka yana gamawa ya sauko ya sami Jummai a tsakar gida ya tambayeta in Saddiku, ta sanar da shi Saddikun yace mata ya fita amma kafin magriba zai dawo. Yayi mata sallama ya fice ya nufi gidan Yaya Bello.

Ya san sai dare ya kamata suje gidan su Aisha, to amma zaman dakin ya isheshi. Gara ya bi Yayan gidan su tattauna ko ya samu zuciyarsa tayi sanyi.

Tun a farkon layin ya hangi Yaya Bello yana tsaye da ‘yan unguwa, yana wucewa shima Yayan yayi musu sallama yabi bayansa. Yana yin parking Yayan ya karaso suka hadu, bayan sun gaisa suka wuce cikin gidan. Yaran da Ummansu duka basa nan sun tafi biki sai Muhammad kadai, bayan ya kawowa Abban ruwa ya koma dakinsa.

Sukayi shiru na dan lokaci, jimawa kadan Abban ya ajiye kofin ruwan da yake hannunsa yace

'Na kasa nutsuwa Yaya, ace ina zaune da mace shekaru masu yawa kowa yana kyautata mata zato ashe matsafiya ce ban sani ba?’

Yayi gyaran murya

'Gaskiya dai nima har yanzu ina mamaki; don ka ga da ace a lokacin tana raye an ce ka zabi daya ko ita ko Aisha to tabbas na san da mu da duk wani danginka zamu ce ka rabu da Aisha ka dauki Zahra, ashe itace bara-gurbin.’

Ya jijjiga kai

'Yanzu Yaya ya zan yi da Aisha? Wallahi ina sonta kuma bana jin a yanzu a shekaru na zan iya wani kara aure. Kuma a halin yanzu Aishan ita kadai ce na yarda zata rike min yaran nan amana. Kuma…’

Da hanzari ya katse shi

'Uhm! Abinda ka gani game da Zahra ai ya isa ya tabbatar maka dan Adam bashi da tabbas ko?’

'Da wannan Yaya, amma ka san dan Adam kowanne da dabi'arsa fa. Wallahi a zaman da nayi da su da ace Aisha ce ta rasu ta bar min yara ba zan iya bawa Zahra rikonsu ba don na san ba zata rike min amanarsu ba. Amma ka ga Aisha, bata da matsala. In dai ta amsa tace zata yi abu to tabbas zata yi kuma cikin aminci. Matsalarta daya kafiya da taurin kai, gashi ita ko dan wayon nan da ake yiwa mata a lallabasu idan dai bata son abu to baka isa kayi mata wayo a kansa ba idan kuma tana son abu to tana da kafiya a kansa.’

Yaya Bello ya gyada kai yace

'Hakane. To yanzu ya za ayi? Tunda ka ga da anyi sallar Magriba ya kamata mu wuce gidan nasu.’

'Wallahi Yaya ban sani ba, da ma za su dan kara mana lokaci na samu nayi tunani sosai. Ka ga fa ga dukkan alamu irin kulle-kullen da muka samu a dakin Zahra irinsu ake aika Yusran tana binnewa Aisha, kuma ai ka ga da cutarwa sosai.’

Nan ya bashi labarin yanda ya kusan shekara baya iya shiga gidan Aishan saboda wari da yanda aka hako abun warin a gidan Aishan, har ya gangaro kan sakonnin da yaji a wayar Zahran wadanda suke nuna cewa tana da hannu wajen barin cikin da Aishan ta yi har sau biyu. Cikin mamaki Yaya Bellon yace

'Ikon Allah! Lallai matar nan ta dade tana cutar da kanta, don tabbas wannan kanta ta cutar.’

Suka sake yin shiru na dan lokaci, sannan Abban ya cigaba

'Kaga yanzu ni so nake Aishan ta dawo nan da wani satin, kafin nan na gyara gidan. To amma ban san yanda zan yi da Yusran ba, duka wata dabara da nake da ita wadannan abubuwan da na ji na gani sun shafe min ita. Dama ace ita Yusran zata samu Aishan tayi mata magana ta nuna mata ba zata bata matsala ba to da tabbas na san Aishan zata yarda.’

'Haka kake gani?’

'Gaskiya Yaya haka nake gani?’

'To idan muka je wajen Baffan nata kawai ka amince musu a kan za ka dauke Yusra da Nana. In ya so ko nan wajena sai ka dawo min dasu daga baya sai ka sa Yusran a gaba ta bata hakuri. Kuma ko ma bata karbe su ba nan din sai muyi zamanmu in ya so ka barta da wadanda ta zaba.’

Ya jijjiga kai cikin damuwa

'Yaya ni bani da damuwa idan yarana suna wajenka na san lafiya za a rike min su, amma zan so ace suna cikin gidan a tare gaba daya.’

'To ya za ayi, kaga dai yanzu wadannan abubuwan da muka gani ya tabbatar maka da abinda Aishan take tsoro. Kaga ita kanta Yusran tana bukatar a tsawatar mata a sauketa daga kan waccan tarbiyyar da uwarta ta dorata a kai. Ka bari ayi hakan, idan aka kwana biyu sai a lallabi Aishan mu ga abinda hali zai yi.’

Kai kawai ya dagawa Yayan don shima bai hango wata mafita ba bayan wannan.

Yayan ne ya tsinke shirun da suka yi, yace

'Kuma idan ka koma gidan ka tara yaran gaba daya ka sanar da su cewa Aishan zata dawo gidan, ita kuma Yusra ka sanar da ita zata dawo nan saboda tana yiwa Aishan rashin kunya. Amma idan ta fi son zama a can din to ta nemi Aishan ko a wayane ta bata hakuri.’

‘In sha haka zan yi.’

Nan suka zauna suka cigaba da hirarrakinsu, sai gefin magriba ya yiwa Yayan sallama ya nufi gidan don ya shirya ya dawo su tafi wajen Baffan Aisha.

__ Lokacin da Yaya Abubakar ya sanar da su an fasa haduwa da su Abban Sadik sai da magriba Aishan da Anti Uwani har sun shirya don tafiya gidan Baffan. Da suka ji haka sai suka fasa shirin suka bari sai bayan la'asar sa je.

Can wajen azahar Zahida ta shigo gidan da yaranta. Bayan sun gaisa da Hajiya ta dawo falo inda ta zauna wajen Aisha. Kafin su gaisa ta zaro sabuwar waya a kwalinta ta mika mata tana fadin

'Ga wayarki inji Abban Afra, yace rasit din yana ciki kuma kina da canjin dubu daya da dari biyar don an dan sami ragi.’

Ta karba tana dariya

'Kai shima don Allah harda wani canji. Wallahi kamar kin san jiya saura kadan na fasa wayar nan don takaici, ko awa nawa zata yi tana caji da ka cire daga socket zata dawo babu caji, lallabata kawai nakeyi.’

Nan suka bude wayar suka kunna da yake ya riga yayi mata caji suka cigaba da dubawa. Jimawa kadan suka koma kusa da socket Aishan ta saka tsohuwar wayar tata tana duba abubuwan da suke ciki don Zahidan zata bawa ta kaiwa Abban Afra a sayar mata da ita. Ta tura hotunanta da videos wadanda take so zuwa sabuwar wayar, tana ta dube-dube tazo kan recording wanda wayar takeyi idan tana waya. Ta dubi Zahida tace

'Kinga yau naga inda wayar nan take tara min hira. Kin san nace miki kullum na gama waya sai naga an saka min recording saved amma ban san a ina ake saving ba.’

Suka fara budewa suna sauraro, wasu suna dariya don yawanci hirarrakinsu ne su biyun.

Recordings din suna da yawa sosai don haka suka dinga tsallake wasu suna bude wanda suke son ji. A hankali ta zo kan wani recording guda daya da lambar Zahra, tayi murmushi yake tace

'Ga na mutuniyarki.’

Tayi mamakin ganin recording din don a zamansu bata jin sun yi waya da Zahra ya kai sau biyar. Ta danna ta kunna suka fara sauraro kamar haka:

“‘Dama Abban Sadik ne bai shigo ba kuma na kirawo wayarsa bata shiga shine nace ko lafiya.’ ‘Lafiya kalau, yayi bacci.’ ‘Um, t….’ ‘Kema ina baki shawara kije kiyi baccinki, idan dai mijinane Yusuf uban Sadiku to bazaki sake jin duriyarsa ba. Ya manta dake ya goge babinki a rayuwarsa, ko da me kike takama kuma ya fi karfinki, duk lokacin da kika gaji sai ki tattara kayanaki ki koma gidanku. Kuma don Allah kada ki sake kirana a irin wannan daren muna kwance da mijina.’”

Zahida tace

'Ta kafawa kanta hujja ta tafi ta bari a duniya, aikin banza.’

Aishan tace

'Uhm.'

'Kada ki goge tura a sabuwar wayar, kin san fa in an jima muka je su Baffa kokari zasuyi ki koma ki zauna da wannan muguwar yarinyar tata. Wannan zai iya zame miki hujja tunda duk abubuwan da tayi miki abubuwa ne da babu wanda ya gani.’

'Hakane.'

Ta tura sabuwar wayar suka cigaba da abinda sukeyi.

Sai can wajen karfe shida saura suka shirya ita da Zahida da Anti Uwani suka nufi gidan Baffan.

__

Dawowar su Rukayya kenan daga islamiyya don ko uniform basu gama cirewa ba.

Bayan ya amsa sannu da zuwan su ya nufi saman, har ya kusa shigewa sai kuma ya ga gara yayi magana da yaran ko zai fuskanci wani abu kafin suje wajen Baffan Aishan. Ya juyo ya dawo falon kasan, ya kwalawa Yusra kira, bayan ta fito daga dakin yace

'Yusra ku sameni a falon sama yanzu ke da kannenki da Saddiku.’

Ta amsa ta koma dakin.

Ba tare da bata lokaci ba suka fito gaba dayansu suka sameshi a falon ya a zaune. Kowa ya nemi waje ya zauna yayinda Sumayya ta wuce ta zauna a jikin Abban. Ya kare musu kallo sannan yayi gyaran murya yace

'Allah shine me rayuwa, dukanmu muna cikin bukatar Mommy Allah ya dauki ranta. Hakuri kawai zamu yi sannan kuma mu cigaba da yi mata addu'a. Zuwa next week in sha Allah za a fara aiki a gyara gidan gaba daya, idan aka gama Antinku zata dawo nan mu zauna gaba daya.’

Idonsa yana kan Yusra yana lura da yanda take ta faman murgude baki tana kau da kai. Ya dubeta yace

'Zata zauna ne ba don a sake muku uwa ba sai dai ita din ma uwarku ce don haka akwai bukatar kuyi mata biyayya kuma ku bata hadin kai mu zauna lafiya. Sai dai ke Yusra tace ke da Nana kuna yi mata rashin kunya sosai, me yasa.’

Yusran ta bude baki zata yi magana Nana tace

'Abba ni dai ba ni bace.’

Yusran ta kawar da kai tace ‘Abba ni babu wata rashin kunya da nake yi mata, ni da bana ma kulata yaushe nayi mata rashin kunya?’

Abban ya bude baki zai yi magana Saddiku yace

'Wallahi Abba tana yi mata rashin kunya sosai, ranar sadakar uku Mommy ma baka ga yanda ta bangajeta ba kuma Anti Aishan bata ce mata komai ba.’

Idon Abban yana kanta tana hararar Saddikun. Yayi gyaran murya yace

'To ka ga kenan ba za a sami zaman lafiya a gidan ba tunda abun ya kai da bangaza wataran za ta kamata da kokawa.’

Tace

'Wallahi Abba ba haka bane, ni yaushe ma na ganta balle na bangajeta?’

'Itama da kanta ta gaya min abubuwan da kike yi mata kuma kin san dai ba zata yi miki karya ba. Yanzu kina da kwana uku ki kirawota a waya ki bata hakuri ki sanar da ita kin daina yi mata duk wani abu na raini, idan kin kirawota zata gaya min. Kin ga shikenan sai muyi zamanmu lafiya babu wanda ya raina wani. Amma idan baki kirawota ba to Babanki Bello yace sai dai ki koma gidansa don wajensa ne ta kai kararki. Ki kirawota ki bata hakuri zata sanar da shi in ba haka ba gidansa zaki koma komai za ayi miki kamar a nan. Tunda kinga ni ba zan iya saba maganar Yayana ba don ban raina shi ba kamar yanda ke kika raina naki Yayan har kike murguda masa baki a gabana.’

Suka yi shiru na dan lokaci.

Babu wanda yayi magana, don haka Abban yace

'Shikenan, ga kiran magriba nan mu tashi muyi shirin sallah.'

Ya tsallake su ya nufi daki yayinda su kuma suka nufi benen da nufin saukowa.

Tun a kafar benen Yusra ta fara mita ita kadai

'Wallahi bata isa na bata hakuri ba, ni da gidan ubana na ga wanda zai koreni sai dai kowa ya koma gidan ubansa wallahi.’

Har ya murda kofar dakin zai shiga sai kuma ya fasa ya dawo ya samesu a kafar bene don haka duk abinda Yusra ta fada ya ji. Bai kula da ita ba yace

'Sadik idan ka shirya ka jira ni mu tafi masallacin tare.’

Suka wuce shi kuma ya koma dakin yana mamakin Yusra.

Bai taba sanin lalacewar Yusra ta kai haka ba, tun kafin ma aje ko ina ta sanar ba zata bi umarninsa ba. Lallai gara ya barta taje gidan Yaya Bello don ya san ba zai yi mata a hankali ba. Watakila idan ya cigaba da addu'a Allah ya sa ta canza hali.

Nan da nan ya shirya suka tafi masallaci tare da Saddikun, suna dawowa ya shirya ya wuce gidan Yaya Bello.

……….

Tun a hanya ya sanar da Yaya Bellon yanda suka yi da Yusra, nan suka yanke maganar cewa kawai Yusra da Nana su dawo gidan Yayan.

Suna isa suka tarar Baffa da Yaya Abubakar suna jiransu.

A falon Baffa suka zauna gaba daya; Aisha, Anti Uwani da Zahida suna gefe yayinda Baffa da Ya Abubakar suke gefe sai Abban da Yaya Bello da suma suke gefe.

Tunda ya zauna yake kallon Aishan; tayi kyau tayi fes kamar bata da wata damuwa. Yanda yaki ya dauke idonsa daga kallonta ya sa ta sunkuyar da kai. Yaya Bello ne ya kula da halin da ake ciki ya tabo Abban.

Gaba dayansu suka gaisa da su Baffa da Anti Uwani.

Baffa yayi gyaran murya yace

'Yusufa me ya hadakane da amaryar taka har ta taho gida, duk da tace ba kaine kace ta taho ba?’

Nan ya mayarwa da Baffan yanda sukayi kamar yanda Aishan ta fada.

Sukayi shiru na dan lokaci, Baffa yace

'To tazo da wasu dalilai wadanda suka sa take jin ba zata iya zama da yarinyar ba, amma gata nan sai tayi bayani a gabanka kaji.’

A nan Baffa ya bawa Aishan umarni tayi bayanin abubuwan da Yusran takeyi mata da ma wasu abubuwan na cutarwa da Zahran ta dinga yi mata. Ta dora da

'Duk abinda za ayi kuma ita ake turowa ta shigo min da shi gida. Sannan kuma kullum muka hadu da ita sai ta gaya min bakar magana don kawai ina kawar da kai ne.’

Baffa yace

'Wannan maganar zargi a barta tunda kinga malamai ma sun ce wasu abubuwan aljanu ke son cutar da kai sai su nuna maka cewa wani ne daka sani.’

Tace

'Baffa wasu abubuwan idan tayi min da kanta take gaya min ko ta aiko Yusran ta gaya min.’

Kafin suce wani abu ta zaro waya ta kunna recording din da suka tsinta dazu na muryar Zahra. Kowa yayi kasake yana sauraro. Abba ya sunkuyar da kai zuciyarsa tana kara kuntata, muguntar Zahra da jahilcinta har ya kai haka?

Suna gama ji Yaya Bello yayi gyaran murya yace 'To Baffa dama muma hakuri muka zo mu bayar, kana zaune da mutum ne bisa kyautatatwar zato baka gane lokacin da yake sauyawa. Wadannan matsololi duk mun ji kuma ita Yusra da kanwarta Nana da ake magana in sha Allahu gidana zasu koma in ya so sai suyi zamansu da sauran yaran. Yanzu dai ana gyara a cikin gidan nan da sati biyu za a gama in ya so ita Aishan sai ta koma.’

Cikin farin ciki Baffa yace

'To Alhamdulillah, hakan yayi. Allah ya shirya mana zuri'a da mu gaba daya.’

Ya dubi Aisha yace

'Shatu ki dinga hakuri kin ji, yaro ko naka ne wanda ka haifa wani sai dai kayi hakuri da shi a lallaba. Bana jin ki da yara sai dai mu raka ku da addu'a, tunda gashi ita da take baki matsala bata nan don Allah sauran kuyi zamanku lafiya. Kuma ku sani mutum yana barin mugun hali ya shiryu musamman wanda ake tsaye ana masa addu'a don haka idan ta canza hali ita din ma duk ki hadasu ki rungume.’

Tace

'To Baffa.'

Yaya Bello yace

‘Akwai kuma yaran wajen Aishan su biyu idan babu damuwa sai ta taho da su duk su hadu a nan suyi zamansu gaba daya.’

Yaya Abubakar yace

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull