Wata kishiya complete by sa'adat - Chapter 50
Wata kishiya complete by sa'adat Chapter 50: Wata kishiya complete by sa'adat Chapter 50. Yau tinda Ya tashi yaketa bincike a dakin tako ina, besan dalilin…
3,348 words
Yau tinda Ya tashi yaketa bincike a dakin tako ina, besan dalilin bincikenba, yana binciken yaga kudinnan da dr ya bashi yabawa Almuqri'ah a drower ya dauko kudin ya rungume a kirjinsa yana hawaye hadi da tunano reaction dinta data amshi kudin. "Meyasa zaki tafi ki barni a matsifa irin wannan...ya rabbih menayi kayimin wannan jarabawar... Ina sanki wlhi, ya Allah kasa ba hakkin iyayena bane yake bibiyata..." Ya karashe yana me kara fashewa da kuka kmr ransa ze fita harda shasheka, a kwanakinnan ya fara tunanin anya ba hakkin iyayensa bane ke bibiyarsa yasa yashiga wannan mummunan halin, yanzu fa beda maraba da mahaukaci, dan duk wanda ze kallesa zesha ko mahaukaci ne. Hannu ya kai ya jawo drower din kasa , se kuma yaga wata takka fara a ciki harda baze dauki takaddarba se kuma yasa hannu ya dauka hannun nasa na rawa, ya bude takaddar yaga rubutu da blue din viro.. "Rubutun dr..." Ya fadi a bayyane ba tare daya karanta note din dake cikin takaddar ba. Yabi rubutun da ido ko a mafarki aka nuna masa hand writing din dr zesan cewa hand writing dinsa ne. Jikinsa na kakkarwa ya fara karanto note din kamar haka. "Ina fatan kina lafiya Almuqri'ah, wannan kudin naki ne nasan zakisan kona menene dakinga kudin,, ina fatan zaki tsaya ki nutsu kiyi aikin daya kawoki gidan Abdoljalal cikin Aminci...kakarki tana nan cikin aminci itama, Allah ya bada sa'arh ya dauramu a kan saarh Amin ya Allah..." Abdoljalal yaci gaba dabin rubutun da kallo yayinda zuciyarsa je tsuma, ya kasa fahimtar me rubutun ke nufi, tabbas de yasan rubutun dr ne, ,abu daya ya fahinta wato aikin da Almuqri'ah tazoyi gidan kenan dasa hannun dr.."to meyasa zeyimin haka?'' Cewar abdoljalal, nan take zuciyarsa ta chanza lamarirrika, ya mike a zabure yana fadin. "Munafukinka na gindinka..." Ya fice a dakin kafafuwanta ko takalmi babu, sanye yake da jallabiyar maroon ta Almuqri'ah Abdoljalal dinne yase mata.. Ahamad dake zaune bakin get yaga Abdoljalal ya tunkarosa gadan gadan seya shiga mamakn lafiya, ya mike tsaye zumbur, ya zubowa Abdoljalal ido, yau kusan 2weeks kenan ko masallaci Abdoljalal din be fito yaje ba, a daki yakeyin sallah. "Akwai matsala..." Ahamad ya fadi yayinda zuciyarsa ke dukan uku uku. "Dakko mota da hanzari kajani zuwa office din dr mus'ab..." Cewar Abdoljalal da takaddar ke hannunsa yanata kara karantawa. Ba tare da ahamad ya masa musu ba, sbda yadda yy mgnr ya tabbatarwa da ahamad wani bala'in ya kunno kai.ya nufa packing space kusan a tarema suka karaso packing space din abdoljalal yashiga gaban motar, ahamad yaja motar suka fice a gidan yana kallan rigar dake jikin Abdoljalal be dace ya fita da ita ba amma beda yadda zeyi, be isa yace masa ya koma ya cire ba.
Paid book ne 08101626484 43 "Kai kayi maza maza kayi sauri da motar nan fa..." Cewar Abdoljalal, dayake ganin kmr ahamad baya sauri, shi kuma dukya kagu ya ganshi gashi ga dr mus'ab, kwata kwata beyi tsammanin abinda dr ya aikata garesa ze aikata din ba, ashe maciyinn amana yake tare dashi be sani ba.sune kalaman da Abdoljalal keta juyawa a cikin kansa yayinda yakejin zuciyarsa kmr zata fashe. Ahamad ya kara gudun motar sbda mgnr da Abdoljalal yayi. Tafiyar 15mnt ta kaisu office din dr, ko packing ahamad be gama yi ba Abdoljalal ya fito daga motar cikin sassarfa ya nufa cikin asibitin yayinda yazama abin kallo sbda rigar jikinsa, wasu suka hau kakkauce masa saboda a zatonsu mahaukaci ne. Direct office din dr mus'ab abdoljalal ya shiga, yaga baya office din. Dan hk ya fito yaga wata nurse ya tambayeta ina dr?, a tsorace ta bashi amsa da "Beso ba yau..." Tayi hanzarin barin gun sbda itama a zatonta mahaukaci ne. Abdoljalal ya fice a asibitin ya koma mota ya kalli ahamad yace "muje gidansa..." Ahamad ya tada motar hadi da tambayar Abdoljalal "Meke faruwa ne ranka ya dade.." Abdoljalal yayi banza dashi kmr beji shi ba sam ko mgna ma bayaso yayi sbda azabar turiri da tashin hankalin dake cikin zuciyarsa. Ahamad be kara cewa komi ba yaja motar suka fice a asibitin zuwa gidan Dr mus'ab. Ba jimawa suka isa sbda gidan da asibitin ba nisa. Ahamad nayin packing abdoljalal ya fito , direct ya nufa part din dr mus'ab zuciyarsa a zafafe. Bako sallama ya fada falon Dr din, ya taddashi zaune kan kujerarsa ta 3ct ya rafka uban tagumi yau ko office be fita ba, ya hana kuwa zuwa part dinsa sbda dmwar da yake ciki. Kwatsam yaga jalalu ya fado falon nasa, ya dago ya zuba masa ido,cikin zallar mamaki, yaga yanayin dabe saba ganinsa a ciki ba a kan fuskarsa, kallon bnza kawai yake binsa dashi da kallan kaskanci. "Maciyin amana kawai.." Jalalu ya fadi hadi da karaso ya cukumo wuyan dr mus'ab ya dago takaddar dake hannunsa ya nunawa dr din,dr ya kalli takaddar, nan take ya tuna da Sadda ya rubutata da hannunsa yasata a tsakiyar sadakin Almuqri'ah. "Asirinka ya tonu maciyin amana kawai,,ace dakai za a hada baki anaso a cuceni ..mugu azzalumi,seda na fara zafafa a soyayyar yarinyar kuma seku hada baki kasata ta gudun min da ciki...wallahi ka gaya mata ta dawomin da cikina ko yau -yau dinnan insa a rufeka,, mugu azzalumi ni na daukeka da zuciya daya ashe kai ba hakan bane azzalumi mugu makiri, aniyarka ta sharri seta bika, nayi nadamar saninka a rayuwata, wlhi da zuciya data nake zaune dakai ashe kai akasin hakan ne..." Ya karashe mgnrsa hadi da fashewa da kukan takaici da zallar bakin ciki, wato besan da makiyinsa yake zaune ba se yau. Dr mus'ab ya bishi da ido cikin zallar dmwa da tashin hankali, yadda abdoljalal ke jefo masa kalamannan cin amana ba karamin dmwa ya jefa dr a ciki ba amma sede yamasa uzuri sbda rashin sani ne ke dawainiya dashi wanda yafi dare duhu. "Maciyin amana, Azzalumi insha Allahu se ubangiji yayi kaca-kaca da rayuwarka, kuma wlhi wlhi in baka fito min da yarinyarnan ba, kun bani ciki na ba, wlhi se nayi sharaarh dakai in zanyi yawo tsirara sena wulakantaka mugu azzalumi kawai..." Abdoljalal ya fadi still yana kukan bakin ciki. dr ya bude baki domin yama jalalu bayani amma yaki bashi daman hakan gashi ya shakure masa wuya sosai, yana kokarin ya kwace amma sam ya gaza sbda karfinma ba daya ba, kalan yadin ba kalan zaren bane, koda goma ta lalace dole ne tafi biyar albarka, zaki zaki koda kuwa gawarsa ce, in namin daji duka gani se hantar cikinsu ta kad'a. Jalalu ya dinga ma Dr maganganu masu zafi ya hanashi mgna kana a karshe ya fice ya bar falon nasa, byn ya kankara masa warning din in har gobe be fito masa da Almuqri'ah ba an bashi cikinsa ba wlhi sede Kawai dr yaji sammaci. Yashiga mota ahamad daketa kallansa yynda yaketa huci,ahamad ya kara tabbatar da babu lafiya. Yaja motar suka fice a gidan, har suka isa gida jalalu na kukan bakin cikin abinda dr ya masa. Ahamad nayin packing jalalu ya fito a daddafe yana mejin jiri ya nufa dakin Almuqri'ah yana shiga yaga dr zaune a gefen bed din Almuqri'ah ,abdoljalal na fita a gidansa shima ya hayo mota ya nufo gidan nasa cikin gudu, shiyasa ya rigasu karasowa gidan. "Dan Allah ka saurare ni frnd pls, wlhi bazan iya cin amanarka ba, duk inda naga wanda zeci amanarka ko ze cuceka wlhi se inda karfina ya kare, har raina zan iya badawa a kanka jalalu, kai mutum ne kmr yadda mahaifinka yake mutum pls ka saurareni..." Dr ya fadi yana kuka shima yayinda idanuwansa sukayi ja-ja-jawur kmr gauta be taba shiga tashij hnkli irin na yau ba. "Baka da abinda zaka gayamin.." Jalalu ya fadi shima yana kara kwallah kmr ze haukace yakeji, duniya ta masa zafi, ya zauna kasan dakin ya dafe kansa da hannayensa yana kuka fin tunanin me karatu kmr karamin yaro... Dr ya dinga masa magiya kan ya tsaya ya sauraresa,,da kyar jalalu ya yadda ya tsaya ya saurari me Dr zece masa.dr ya leka ya kira ahamad suka dawo dakin tare, kana dr ya fara zayyanowa jalalu labarin komi daga farko hatta labarin su Almuqri'ah da ammah (fatima) ta bashi be boyewa jalalu ba, ya kira isma'il a waya, domin shida ahamad ne shedarsa se nurse mami a duniya. Jalalu ya kara fashewa da kuka amma na farin ciki. "Ashe da Aure a tsakanina da Almuqri'ah,,gaskiya kai aboki ne na amana, kai abokine da babu irinsa a yanzu , ka gamamin komi mus'ab..." Jalalu ya fadi yana kuka hadi da nadamar maganganun daya gayawa mus'ab,ya rungume mus'ab din a jikinsa sosai, dukkaninsu suka fashe da kukan soyayyar junansu. Abdoljalal yadingama dr godiya mara iyaka, ya dinga rungumarsa kmr ze maidasa ciki seda Ahamad ya koka shima, baya tunanin a duniya akwai mutane irin dr mys'ab a halin yanzu, abokan yanzu duk munafukai,kai inka samu me sanka duniya ka riga dakai saarh, me sanka daya yafi makiyi dubban dubbai, (Ya ilahi dan Annabi SAW ka barni da hubb har abadan Abidina Amin ya ilahi)
Ranar nan gidan dr ya kwana yanata kara bawa jalalu labarin komi yadda ya gudana. Abdoljalal yaji kmr ansashi a aljannah yaji ddh daya zamana Akwai aure a tsakaninsa da Almuqri'ah, dayasan cewa an biya mishi sadaki ai da bugun dazema durinta seyafi haka,,abdoljalal ya dingama dr mus'ab da isma"il da ahamad godiya dasa Albarka mara iyaka, a duniya byn iyayensa beda kmr mys'ab da Isma'il da ahamad, da hajiya kande ma, shi kadai yasan meze nusu na Alkhairi, Amma fa adduarsa garesu bazata yanke ba. Adduarhsu daya yanzu Allah ya bayyana Almuqri'ah.
*Adamawa yola* Yau kimanin watanta biyu da kwana goma a gidan hajiya Ummusalma, ba karamin kulawa suke bata ita da yayantaba, yaran sun Fara wayau sosai zuwa yanzu, kasancewar duk sunada girman jiki gasu yan lukataye gwanin ban sha'awah, yara hudu reras lafiyayyu, kamannin yaran maza da Abdoljalal ya kara fitowa rass, sannan itama macen kamanninta da ummusalma ya kara fitowa sosai, a kullum yaran na gurin me martaba da ummusalma suke jigilar yaran,yaran dun zame musu farin ciki sun wanye musu kewar jalalu dake ransu, har ummusalma tayi yar kiba sbda zuwan yaran gidan. Yau ta kasance juma'ah ce, ta tashi sallar asubahi taji wani abu ya fita a jikinta da tsananin karfin tsiya, tayi wata iriyar atishawa, ta duba gabas ta duba yamma bataga kowa ba a dakin, daman yaranta badasu take kwana ba a gun ummusalma suke kwana dame martaba. Ta nufa bandaki a tsorace, ta kara kiba tayi bul-bul da ita tayi fresh ainun ummusalma na bata kulawa ta musamman tako ina ta kara cika, duk wata gaba ta jikinta ta bude ta kara kyau surarta ta kara bayyana kmr zata fashe. Tashiga bandaki tana brush, brush din yazo faduwa a hannunta zuwa kasa, tace subhanallahi, mamaki ya cikata jin subhanallahin datace ya fito ba gargada, ta kara fsdi kusan 7tyms, nan take taji alamar bakinta yakoma dai-dai yanzu ita ba bebiya bace, ta rasa ina zatasa rayuwarta dan farin ciki, a guje ta fice a toilet din, ta dice a bangaren nata yayinda tsoro da firgici suka rufeta, ta nufa pat din su me martaba, tana shiga ta taddasu har daki suna sallah, yaranta kuma nata bacci a gadansu. Su me martaba suka idar da sallar shida ummusalma, ta dago ta kalleta cikin tsoro tasha wani abin be yasameta,. Nan Almuqri'ah ta bude baki tayi magana, kaf suk farin ciki ya rufesu suka dinga godiya ga mahalli. Nan Almuqri'ah ta zube tayi sujjadar godiya ga Allah , bata taba tsammanin bakinta ze bude ba, ai rnr baki har baka dan murna, ga muryarta me azabar zakin tsiya. Mommy ummusalma ranar sadakar datayi dabance, Almuqri'ah kam wuni tayi tana ibada ta godiya ga ubangijin sammai da kasai.
*Kaduna* Yau kimanin watansa daya da sanin labarin komi nasa da Almuqri'ah,. Tinda ya tashi yau yaji iyayensa kawai yakeson gani sbda su masa adduarh ya fita a matsifar nan da yake ciki, tayuma ko fushin rashinsa garesu ne ke dawainiya dashi. Dan haka da wuri ya shirya yasaka jallabiyarsa, ya kira ahamad yace yase musu jirgi zuwa adamawa yola. Ahamad yashiga mamaki mara misaltuwa hadi dajin dadih kuma, domin ba a mamaki da ikon Allah komi yayi farko zeyi karshe. Ba bata lokaci yase musu jirgi zuwa adamawa yola. Abdoljalal ya fito ze shiga mota saude ta fito ta watsa masa wani banzan kallo ta amso asirinta boka ya tabbatar mata da zuwa yanxu jalalunta ya koma yadda takesonshi. "Maci amana, dan iska mazinaci, zanga ai yanzu nida kai waye ze bar gidannan,, seka tsugunna ka rokeni gafarar cin amanata dakayi kana zakaci gaba da zama a gidannan.." Cewar saude datake tunanin jalalun da ne. Daman Abdoljalal yana ciki da haushinta yanzu duk yabi ya tsaneta sbda sanadinta ne Almuqri'ah ta bar gidan, shi a halin yanzu beda abarda ya tsana kamar hajiya saude, ya rasa ma meyasa tashigo masa rayuwa a matsayin mata, shide yasan bashi ya aureta da hayyacinsa ba. "Ke ni kk zagi..." Ya fadi a hasale, kawai ya rufeta da duka harda nauyi a bainar nasi, ya danneta ya dinga nauyi tana kukan neman agaji, ahamad na gani yaki dakatar dashi,sbda shima yana ciki da haushinta se ci masa mutumci takeyi kullum sbda ta koresa yaki tafiya. Securities na kallo amma basu iya su hana ba, .... Seda ahamad yaga jalalu na niyar kashe saude dan har ihunma gagar yinsa tayi kana ya kira wasu daga securities suka dagashi a kanta da kyar, ya barta a sume ya shiga mota yanata bambamin matsifa yana durawa sauden ashar, yace ta bar masa gidansa karya bari yadawo yasameta. Ahamad yace securities su zuba mata ruwa inta farfado su gaya mata sakon oga in kuma bata farfado ba su kaita asibiti. Yashiga mota ya bar saude nan yashe da rabe-raben nonuwanta na guguna, duk tabi ta zabge kibar asarar nan yanzu babu se uban baki datayi, domin yanzu maima yadena amsarta, hatta da gawayin girki yafita kyaun gani da harke. Ahamad yaja mota suka fice a gidan zuwa Airport. Securities suka zubawa saude ruwa ta farfado da kyar byn an antaya mata robar bottles water guda ashirin da tara. Data farfado ta kasa tashi ko ina a jikinta karaya ce ga uban jini nata zuba a goshinta, , ta daku iya dakuwa a gun jalalu. Securities suka kwashi saude daketa kuka tana kiran ohhh yesuuu,,,!! Tana ihu irin na radhin tawakkali , securities suka nufa asibiti da ita. Suna kaita aka amsheta a zaton doctor din daya dubata ma Assident ne, se tambayarta yakeyi babbar mota xe tifa ta bigeta,,,saude ta dinga dura masa ashar,,, dr yaja baki yayi shiru a zatonta ko ta bugu ne a kwakwalwa, dan haka aka mata dauri tako ina datayi karaya, dr ya mata transfer zuwa asibitin mahaukata, ya kira motar asibitin suka dauketa zuwa can asibitin mahaukatan, sede doctor ya gayawa wadanda suka kawota inda zasuje su sameta.
Suna airport ,suka shiga jirgi, cikin hikimar ubangiji jirginsu ya lula sama zuwa yola. Haka kawai jalalu kejinsa a farin ciki mara misaltuwa.
Sefa hkri da typing error. Allah yasa mugama lafiya paid book ne 08101626484.
44 Cikin cikon ubangiji suka isa yola,. Abdoljalal da Ahamad suka sakko daga cikin jirgin, abdoljalal ya kalli ahamad yace "Waze daukemu zuwa gida?'' Ahamad yace "A, sir na kira waziri isma'il na gaya mishi gamu a hanya ya turo a daukemu gasu nan ma sun iso..." Ahamad ya karasa mgnrsa hadi da nuna inda motoci guda biyu sukayi packing. Suka karasa ga motocin suka shiga suka nufa gidansu Abdoljalal se numfashi kawai jalalu yake saukewa, yana mamakin kansa wai yau shine zeje gidan iyayansa da kansa, ada baya tunaninma ze gane gidan iyayen nasa se yau yaji sun dawo zuciyarsa sabbi fil,yana tsananin san iyayensa amma besan meyasa ya banzatar dasu ba ada,. Suka isa gidan dreva yayi packing ya fito, ya shiga bin gidan da kallo kmr bakon duniya. ma'aikatan gidan seda sukayi da gaske suka gane Abdoljalal ne sbda lalacewar da yayi,ya kasa takawa daga inda ya fito daga motar, maaikatan gidan suka shiga karasowa suna zubewa hadi da kwasar gaisuwa, Amsawa abdoljalal yakeyi yana me binsu da ido... Tini labari ya isarma hajiya Salma wadda ke zaune a falonta bayanta goye da dan Almuqri'ah mesunan me martaba wanda akece masa nor, se macen wanda akecewa Aflah datake hannunta. Mamaki ya rufe ummusalma da labarin da jakadiya ta kawo mata na Abdoljalal yau a gidan. Kasa daurewa tayi ya karaso ta fito zuwa inda yake still Norr na bayanta Aflah na hannunta, ta nufo inda Abdoljalal yake gadan gadan. Tin daga nesa taga ya lalace ya rame tamkar bashi ba kawai seta fashe da kuka, Abdoljalal shima yana ganinta ya fasheda matsanancin kuka yana mebin yarinyar hannunta da ita da kallo, besan meyasa ba yana ganin yarinyar yaji gabansa ya yanke ya fadi. Karasawa yayi ya rungume Ummihnsa yana kuka tana kuka jakadiya ta amshi yarinyar hannun ummusalma da norr dake bayanta.. Sosai jalalu ya rungumeta jikinsa yana kuka me tsuma zuciyar me saurare, kaf maaikatan gidan suka zagayesu suma duk suna kuka, banda Almuqri'ah wadda batasanma me akeyi ba tanacan part dinta tana fama da Isma'il da Abdoljalal yau rigima suketayi mata, da ita da nanny dinsu se fama sukeyi dasu.
"Alhamdulillahi yau jalaluna yadawo gareni ubangini ya Amsa Adduarh ta...ya ilahi na gode maka..."ummusalma ta fadi still tana kuka,,yayinda me martaba ya karaso inda suke shima yanzu labari ya taddashi har part dinsa, ya zubo musu ido bayanta. Shima ya fasheda kuka ganin lalacewar da Abdoljalal yayi, ya karaso ya rungumesu su duka da jalalun da ummusalma, ya rungumesu sosai shima martaba yana hawaye.... Seda sukayi 30mnt a haka kana suka dunguma zuwa part din me-martaba hajiya salma ta kasa raba jikinta dana Abdoljalal, shima hakan, yau farin ciki mara misaltuwa iyalan ne martaba suke ciki. "Meya sameka babana dukka lalace haka?'' Ummusalma ta fadi cikin damuwa da zallar soyayyar danta. Abdoljalal ya fashe da kuka sosai hadi da zamewa kasa ya shiga rokon mahaifiyarsa da mahaifinsa yafiya, nan kaf duk sukace sun yafe masa. Ya kara fashewa da kuka sosai ya shiga gayawa iyayensa irin kaddarar da yake ciki ,da duk abubuwan daya wakana tsakaninsu da isma'il da dr mus'ab, duk haduwarsu Da Almuqri'ah seda ya fadima iyayensa komi be boye musu ba. Me martaba yaji dadin hakan sosai, ummusalma ma taji dadin hakan, suka dinga sawa isma'il da mus'ab da Ahamad da nurse mami, and kande albarka domin jalalu be boye musu komi ba, sunji ddh sosai domin dasa hannunsu ne da kuma temakon Adduarh jalalunsu ya dawo garesu yanzu sede suyi fatan Allah ya bayyana matar Abdoljalal din. Me martaba ya kira jsma'il ya masa godiya harda kuka, kana ya kira Mus'ab ya masa godiya yama ahamad dake kusa dashi godiya sosai tamkar ze tsugunna masa, har nurse mami seda me martaba ya amshi lambarta ya kirata da kansa ya mata godiya nan take ya mata kyautar manyan kudaden data fita a talauci na har abadan. Me martaba ya saje kiran mus'ab yace yanzu yanada bukatar Ammah taxo yola ta zauna dasu.. Mus'ab yace toh..nan take yase mata jirgi ya kawota kasar yola dmn tini mys'ab ya sanar da ita ba a ga Almuqri'ah ba sbda beda choice fole seda ya gaya mata ammah tashiga dmwa sosai amma ta dauki kaddara. Ammah ta iso duk suka taru a falon me martaba anata jajantawa juna, se yanzu Abdoljalal yaga Ammah ya miko gaisuwa cikin girmamawa.... Nan de suka shagala a murna har tare suna tareda juna, se 12:am suka rabu, Ammah ta nufa part dinta da ummusalma ta ware mata akwai komi na bukatuwa a ciki. se girmamawa hajiya Ammah akeyi wato fatima tako ina. Duk abunnan da akeyi Almuqri'ah bata sani ba, seda jakadiya tazo ta shaida mata itama tashiga murna sosai, domin tasan labarin dan Ummihn a gurin ummihn ta sanar da ita komi.... Jalalu yayi kwanan farin ciki a ranar , yasamu ya danci wani abun yau sbda Ammah data matsa masa sosai. yanzu dmwarsa daya Almuqri'ah da cikinsa.