Kenza eBookz

Waye shi complete - Chapter 13

Waye shi complete - Chapter 13

Waye shi complete Chapter 13: Waye shi complete Chapter 13. A daidai barandar wajen d'akinsu Sulaiman, Imran na tsaye yana kallonta, shi kad'ai ba tare da…

4,477 words

A daidai barandar wajen d'akinsu Sulaiman, Imran na tsaye yana kallonta, shi kad'ai ba tare da abokansa ba, akwai mutane dake ta hadaniyarsu a compound d'in, kwarjininsa ya cika idonta saboda haka ba musu k'afarta ta k'arasa wajensa.

"Kinyi kyau sosai Sa'adha, I just want a picture."

Kafin ta gama fahimtar maganarsa, ya rik'o tafin hannunta na hagu sannan ya juyar da ita gefe, masu hoton nan na tsaye suka shiga dallara musu.

A wannan lokacin Nanne taji d'umin hannunsa kamar yana zuk'e damuwar dake tare da ita ne, jikinta yayi wani irin sanyi sannan a hankali ya shiga rawa, amma abu d'aya ke yawo a ranta, Me ya sami Imran? tayi zaton zata ga murnarsa fiye da haka, a yanzu da ta riga ta zama tasa? amma ko murmurshi irin na jiya bata samu ba.

*******

Wajen karfe d'aya Addano da 'yan uwanta suka yi sallama suka tafi ganin gidan amarya daga nan kuma zasu wuce adamawa.

Yini bikin ya cigaba da wakana, a kowanne lokaci mutane k'ara zuwa suke yi, musamman wad'anda basu samu zuwa jiya ba, k'awayenta ma da d'an yawa sun zo, anata d'aukan hoto da rawar kid'an kwarya, Har saida aka d'ora wata tukunyar abincin a gidan sab'anin da farko da duk kawowa akayi daga wajen da akayi order.

Kafin La'asar muryar inna ta dashe saboda yawan magana da amsa gaisuwa. A sannan ne kuma aka fara shirye-shiryen kai amarya.

Motocin da Imran ya aiko dasu tun daga farkon layin aka jera su har bakin titi, saboda yawa mutane har canja mota suka dinga yi, sai a shiga wannan a fito.

Aka sa Nanne ta sake wani wankan sannan ta shirya cikin wata lallausar lafaya kalar lemon green, jikinta sai tashin sassanyan k'amshi na turarurruka daban-daban yake yi, a lokacin zuciyarta ta riga ta gama tsinkewa, gani take ko ku'da ne ya hau kanta zata iya fashewa da kuka.

********

"....Aljannarki tana wajensa Nanne, shi yasa nake ta maimaita miki biyayya da hak'uri, hak'urinki shi zai sa miki tausayinki a ransa sannan biyayyarki ita zata maye gurbin duk wani abu da zaki nema a wajensa..."

Kukanta ya k'aru sosai to the point that duk wata doguwar maganar data biyo bayan nan bata iya jinta, tunaninta ya cakud'e gabad'aya ya tafi can wani waje, ta damk'e hannayen Aunty Nafisa dake gefenta tana sheshshek'a jikinta har d'agawa yake saboda ajiyar zuciya. Inna da muk'arrabanta suka yi tanasiharsu suna zaiyano abubuwan da ita a lokacin ba fahimtar su take yi ba.

Daga k'arshe aka kaita wajen Baffa, a nan ma taci wani kukan ta k'oshi don bud'ar bakin sa da farko hak'uri ya fara bata, zuciyarta ta tsinke...ta yaya baffa zai bata hak'uri? akwai abinda zai tab'a yi mata a duniya da zai sa ya bata hak'uri?

Tayi niyyar ta gaya masa ita ba abinda yayi mata, ita ba a cikin damuwa take ba, auren Imran ba zai zame mata matsala ba, amma kukan dake cinta ya hana ta, tana ji tana gani aka fitar da ita daga gidansu aka sata a mota, gidan da ta taso tun yarintarta, gidan da mahaifiyarta ta tafi ta barta a cikin sa, gidan da Inna ta raine ta da dukkan kulawarta, gidan ta fara gina rayuwarta a cikinsa, da gaske ne da ake cewa aure yak'in mata, yau ta fahimci wannan yak'in da ake nufi, don a yanzu ji take kamar runduna guda zata tafi tunkara.

●﹏●

Pheeewwwwww......mun gama harkar biki, duk wata hayaniya ta k'are...komai yazo k'arshe an dai tafi da Nanne gidan Imran, abinda muke jira tun farkon labarin nan ya faru.

Anyi auren, d next agenda shine yadda zaman zai kasance, zaman wata halitta da kuma mutum a matsayin zaman aure? yadda Nanne zata san waye Imran, tunda a yanzu da gaske ta zama b'arin rayuwarsa.

Amma me kuke tunani yasa Imran ya fara canja mata tun a rana d'aya kawai?

Ina zancen masu daukan hoton nan?

May be zamu ji a next chapter.😊

***

WAYE SHI?

AYSHA SHAFI'EE

34

(☆_☆)

Mutane sun ragu sosai a lokacin duk an tafi d'akin ya rage daga su Aminah sai Aunty maryamah da Aunty Zainab kad'ai, har a lokacin Nanne na k'udundune a cikin lafayarta tana sheshshek'ar kuka.

Aunty zainab dake kan stool ta kalli agogo tace.

"Gaskiya tafiya zamu zo muyi, babu alamun zuwan dangin ango a wannan daren."

Daidai sannan wayar aunty maryama tayi k'ara, bata nan tana kitchen ita da Rahma saboda haka Aunty zainab d'in ta d'aga.

Abu daya ta fad'a Nanne ta gane inna ce mai kiran.

"Gamu nan, yanzu zamu taho wallahi bari in gaya musu."

Ta kashe wayar sannan tace da Aminah.

"D'auki jakarki, bari in kira su tafiya zamu yi."

Tana fita Aminah ta cigaba maganar da take mata.

"....Sa'adha dan Allah ki rage kukan nan, kar ya shigo ya ganki kina tayi ba k'akkautawa."

Da kyar ta had'iye shi a mokogwaronta tace.

"Yau zaki tafi?"

"A'ah sai gobe dai, ai yanzu dare yayi su Rahman zan bi."

"Dan Allah toh kizo goben."

"In naga wasu zasu zo, zan biyo su amma gaskiya ba zan miki alkawari ba."

Tayi raurau da ido kamar k'aramar yarinya.

"Gaskiya ne ai sa'adah, aure fa kika yi, dole ne ki hakura da komai ki saba da canjin rayuwarki."

Canji rayuwa, canjin rayuwarta...tun jiya take maimaitawa kanta wannan kalmar amma har yanzu ta kasa nutsewa cikin kanta, tana kallo ba yadda ta iya haka suka tafi suka barta, bayan su Aunty maryama sun k'ara binta da nasihohin da ita ba fahimtarsu take ba. Tashin motarsu da kuma rufewar gate d'in data fahimci akwai maigadi a gidan ya dawo da hawayenta, ta sake dukunkune jikinta akan gadon tana jin gidan ya mata girma, kamar wata tsakuwa guda d'aya akan faranti.

Bata san iya adadin mintunan da suka wuce ko lokacin da ya tafi ba kafin ta jiyo wani k'arar bud'e gate d'in, ta san dai kawai a lokacin hawayenta sun k'afe, sai ajiyar zuciya da take yi a hankali.

Ta rufe idonta sanda ta jiyo k'arar taku daga inda take tunanin corridor ne, ba sai an gaya mata ba ta san waye ya shigo, Imran ne, mutumin da a yanzu kowa ke kira da mijinta.

"Assalamu Alaikum.."

Wannan muryar, wannan muryar mai taushi ta shiga cikin kunnenta, sai dai yau ba a waya ba, ko kan kan hanya ko gadon asibiti, a cikin gida ne, gidan dake mallakinsu su biyu a matsayin mata da miji.

Ba tare da ta d'ago kanta daga tsakanin cinyoyinta ba ta amsa a hankali, ba lallai ne ma in yaji ba.

"Hey...." muryar ta sake shiga kanta da wani irin amo sanda ya zauna a gefen gadon sannan bata zato taji ya lalubo hannuta daga cikin lafayar.

Numfashinta ya d'an d'auke a lokacin da d'umin hannunsa ya ziyarci fatarta, kamar dazu taji wani abu na shiga jikinta yana soothing damuwarta.

"Kuka kike yi?"

Kamar mai bashi amsa sai tayi ajiyar zuciya tare da jan hanci, shima ya d'auki hakan a matsayi amsa.

"Kukan rabuwa da Inna ne?"

Bata amsa ba yace.

"In dai haka ne dan Allah kiyi shiru, ko gobe in kina so zan kaiki wajenta..."

"Kinjiiii...?"

Taji kamar ta d'ago a lokacin ta tambaye shi da gaske yake? da gaske gobe zai iya kaita gida? amma hannunsa dake nannad'e da nata ya hanata magana, wani abu ne daga cikinsu yake shiga jikinta yana goge duk wata damuwarta.

"Sa'adha..." ya kira sunanta a hankali.

"Ko mu koma yanzu sai mu dawo anjima?"

Ta d'ago da kanta da sauri ta kalle shi.

Ya salam! yayi kyau cikin wani bak'in yadi d'inkin fitted mai kyau, sannan yasa bak'ar hula wadda ta fito da d'an hasken fatarsa.

Yana kalonta da idanunsa masu kama da maik'o a cikinsu, da kuma d'an k'aramin murmushi a lebb'ensa, murmushin da a d'azu taso ganinsa kamar me. Ta sauke kanta k'asa sannan muryarta ta fito.

"Yanzu dare yayi ai." ita har ga Allah a lokacin ta yarda cewa zai iya mayar da ita gidan ne a yau, saboda haka ta k'arashe da cewa.

"A bari kawai sai goben."

Taji k'arar murmushinsa kafin ya lalubo d'aya hannun nata.

"Zo muje kiga..."

Ya mik'e tsaye rik'e da hannayen nata, ba musu kuwa k'afafunta suka mik'e suma, ya jata har jikin wata k'ofa dake gefen wardrobe, wanda ta san toilet ne, aikuwa yana bud'ewa mamaki ya kamata ganin girmansa da bata yi zato ba, gashi komai na cikinsa light Ash ne, daga toiletries har tiles d'in, sannan ga wata fitila mai k'arfi da ko allura ce ta fad'i tana zaton za'a ganta.

Ya tsayar da ita a jikin sink sannan ya koma ta bayanta ya rik'o kafad'unta, daga cikin mudubin da suke facing tana iya ganin tazarar kafad'arsa da kanta, ta san yana da tsawo amma bata san cewa banbancin ta dashi ya kai haka ba.

"Sa'adha... I want to tell you something."

Ya fad'i kowacce kalma a hankali kuma da nutsuwa, idanunsa kuma basu bar kallonta ta cikin mudubin ba, rudani da wata irin kasala suka saukar mata sanda taji ya zamo hannayensa daga kafad'arta, ya rik'o tafin hannayenta, zuciyarta ta dinga bugawa har tana jin kamar zai iya jinta.

Sannan tunaninta ya tsaya cak! ta tsura masa ido ta cikin mudubin, kwarjininsa na k'ara dulmiyar da ita, musamman idanunsa da suke da kyalli kamar ya d'iga mai a cikinsu, They were clear and deep! taji zata iya nutsewa a cikinsu ta manta da duk damuwarta.

"I want to share a part of my life with you, kiyi hak'uri na san kin gaji...amma in ya wuce yanzu, ya wuce yau bana tunanin zan iya sake fad'a miki."

Ya sake shiru yana sauraren fitar numfashinta, kamar iya abinda zai fad'a kenan kafin ya fara.

"Sa'adha tun da na tashi a rayuwata ban tab'a sanin iyayena ba, sun rasu tun kafin in san kaina, haka kuma bani da wani dan'uwa na jini, sannan rayuwata tana had'e da k'alubale da yawa, na fuskanci wahalhalu da yawa a lokacin yarintata, sai daga baya na sami tallafin wata halitta da ta rik'e ni da dukkan kulawarta, ta jawo ni jikinta, ta bud'e min sabuwar duniyar dana sami komai dana rasa a baya, 'yan uwa, d'aukaka, matsayi da kuma tarin abubuwan da a da nake musu hangen nesa.

Shi yasa nima a lokacin na d'auki dukkan soyayyata na dank'a mata, na yarda cewa bani da wani farin ciki a duniyar nan daya wuce nata.

A cikin haka sai k'addara ta jefo ni wajenki, tun daga ranar dana fara ganinki kuma rayuwata ta canja. ban san taya zan fad'a miki ki fahimta ba amma zuciyata ta fara sonki tun ranar da kuka dawo daga islamiyyar nan ke da Rahma, tun ban san ko ke wacece ba, da farko nayi kok'arin takura kaina da cewar ni da ke bamu dace ba, amma duk lokacin da nake tare dake ko na ganki sai zuciyata ta kasa daurewa.

For the first time tun lokacin da na sake sabuwar rayuwa nayi failing a wani abu, nayi failing wajen controlling zuciyata akanki, shi yasa na fara bibiyarki tun baki sani ba, har kika fara lura dani. Daga nan kuma abubuwa da yawa suka dinga had'a mu, har zuwa yanzu da Allah ya k'addara aure zai shiga tsakanin mu.

So, kome zai faru Sa'adha, kome zai faru nan gaba, I want you to keep in mind that son da nake miki da gaske ne, and it will forever be real."

Yana rufe bakinsa, ta juyo da fuskarta ta kalleshi, yana tsaye dab! da bayanta ne, saboda haka numfashinsa ya shiga busawa akan goshinta.

"Me zai faru nan gaba?" mamaki ya fito sosai a 'yar karamar muryarta.

Ya lumshe idanunsa akanta.

"I don't know, abubuwa da yawa suna faruwa a rayuwar nan, i just felt like telling you saboda gudun mistunderstanding nan gaba."

Sai tayi shiru kawai kwakwalwarta na nazari, amma nazarin ma ya kasa yiwuwa saboda yadda yake tsaye dab? da ita, tunda take bata tab'a tsayawa kusa da wani namiji haka ba, sai a yau ranar farko da ta zama matar aure.

Tunaninta ya katse, sanda ya d'ago da hannunsa a hankali ya sake juyar da ita tayi facing sink d'in, sannan ya kunna fanfon ruwa ya fara zuba.

"Kiyi alwala muyi sallah Sa'adha, mu rok'i Allah ya kore duk wani abu da zai shiga tsakaninmu."

Har tayi alwalar ta bishi jam'in sallah raka'a biyu, kwakwalwarta nazari take yi sosai na maganganunsa, amma har a lokacin abubuwa da yawa ta kasa fahimtarsu.

Bayan sun idar da sallar, ya juyo ya sake rik'e tafin hannayenta sannan yayi addu'o'i wanda da yawansu na nema musu zaman lafiya ne sannan yace da ita taje tayi wanka ta rage kayan jikinta.

Yana fita daga d'akin ta murd'a muk'ulli sannan ta cire lafayar jikinta, akwai heater a band'akin ta had'a ruwa mai d'umi sannan tayi wankan, tana yi tana kallon band'akin tana tuno nasu itada inna, tana ganin kyansa kamar me amma wannan ya ninka shi a komai.

Ta zura wata doguwar rigar bacci har k'asa bayan ta fito sannan ta feshe jikinta da turare. Har ta kashe fitilar ta kwanta sai kuma wani tunani yazo mata, ta taso ta bud'e muk'ullin sannan ta koma tana sak'e-sak'en yadda daren yau zai kasance mata.

Maganganun Imran suka yi ta yawo akanta, ta san addu'ar neman zaman lafiya abu ne mai kyau da ya dace su fara dashi, amma yadda yayi ta maimatawa da kuma addu'o'insa da suka fi yawa akai, ya sata wani tunanin.

Ta dunk'ule hannayenta tana tuno yadda a dare d'aya kawai ta fara sabawa da yadda yake rik'e su.

Kusan minti biyar sannan ya turo k'ofar d'akin ya shigo, da alamun shima wanka yayi, don ya canja kayansa zuwa wata light jallabiya, gashinsa alamun a jik'e sannan k'amshinsa ya cika d'akin.

Ya shigo cikin bargon lokacin da ta sake duk'unkune jikinta daga can k'arshen gadon, bata ko d'ago da kanta ba don idanunta na kan yatsunta, amma taji alamun kamar ya kalleta kafin yaja bargon jikinsa sannan yace.

"Allah ya tashe mu lafiya wifey."

Wani dad'i ya ratsa ta, abinda take fatan taji kenan, sai kuma yazo har da k'arin wani sunan mai dad'i. Wifey! tayi murmushi a hankali sannan ta amsa.

"Ameen."

Asuba ta gari!

●﹏●

Me kuke tunani game da abinda Imran ya gayawa Sa'adha....?

Da gaske ne maganganun ko hakan ma na daga cikin tsarinsu?

****

WAYE SHI?

AYSHA SHAFI'EE

35

Allah abin godiya, kwana na uku ina tunanin yadda zan k'arasa chapter nan, sai d'azu ina cikin wanke gashina komai ya fito POP!....so i was tynking duk ranar dana rasa idea kawai toilet zan tafi in tara kaina a famfo.....hehehehehe!😁😁

Don't mind me please!

Enjoy!😘

(☆_☆)

"Zaka jira nan da kamar minti goma ayi warming d'insu sir."

Matar dake zaune a kujerar cashier ta fad'a fuskarta d'auke da mirmushi.

Good. Imran ya amsa a cikin ransa a fili kuma sai ya d'aga mata kai sannan ya juya ya fita daga restaurant d'in ya nufi cikin motarsa ya zauna.

Yana bukatar lokaci dama, alone time d'in da zaiyi tunanin dake cikin kansa kala-kala. A driving seat yake zaune amma senses d'in hancinsa na iya jiyo masa wannan cool k'amshin da yaji a jikinta jiya, alamun har a yanzu motar bata rabu da k'amshin inda ta zauna sanda za'a kawo ta gidansa.

Komai ya riga ya kammala a yanzu, Sa'adha ta zama matarsa bisa k'okari da fasahar jaamil, saboda kusan komai daya faru shi ya tsara, shi ya tsara duk tarin abubuwan da suka faru a d'an tsukin nan, tun daga kan iyayen daya gabatar a wajen Baffanta har zuwa matan da suka je a matsayin danginsa wanda duk babu su a gaske, ya rufewa mutane ido ne kawai sunga alamun siffarsu amma babu su d'in a zahiri.

Hallucination ne kawai yayi planting a cikin idanunsu. don da ace an samu wanda zai haska su a wajen da mudubi ba zai gansu a ciki ba. Shi yasa ma mai hoton nan ya kusa kawo musu matsala, ba don Allah yasa jamil ya....

Tunaninsa ya katse, sanda wani saurayi ya kwankwasa masa glass.

"Yawwa yallab'ai gasu nan gabad'aya ne, harda receipt d'in."

Ya fad'a yana zuro masa ledojin hannunsa, Imran yayi godiya sannan ya rufe glass d'in, ya tada motar ya cilla ta saman titi haka ma zuciyarsa ma ta cilla can inda ya nufa a yanzu wato gidansa.

Tsawon shekara d'aya kenan da uzirinsu ya shigo dashi wannan rayuwar, ya bar al'adarsa da komai ya canja yanayin halittarsa, amma duk tsawon wannan lokacin bai tab'a jinsa more human ba irin jiya da yau, watakila har gobe ma da jibi...har zuwa ranar da komai zai k'are.

Sau ba adadi ya sani aurensa da Sa'adha ba abu ne mai d'orewa ba, don ko a yanzu baya tunanin suna da abinda ya wuce karfin watanni, shi yasa a jiya bayan an gama d'aura auren zuciyarsa ta karye da ganin irin d'imbin farin cikin dake faruwa a gidansu, ya hango ranar da shi d'in da kowannesu ke yabo a yanzu, zai zama abin la'ana a wajensu, a lokacin da shi d'in baya nan kuma, baya cikin wannan jikin da mutane suka sanshi dashi.

Ranar da shi kansa zai ji haushin kansa, zai k'ara yin nadama da regreting abinda yayi sau ba adadi, mistake d'in da yayi tun farko na shiga jikinta, don da ba hakan ba, da komai dake faruwa a yanzu bai kasance ba.

Da Sa'adha na can na karatunta bata zama matarsa ba, da watakila shima ya gama abinda ya kawo shi ya koma nahiyarsu, can wajen gimbiyarsa Sareefa. Amma k'addara ba haka ta tanadar masa ba, ta shigo da sa'adha cikin rayuwarsa a wani irin yanayi da yafi k'arfin tunaninsa, don da gaske ne abinda ya fad'a mata jiya.

A yanzu, ya yardarwa kansa cewa da gaske yana son ta, zuciyarsa ta nutsu da ita kamar yadda ta amince da Sareefa a baya, shi yasa ya bud'e mata wani b'arin zuciyarsa da yake babu shi a tsarinsu shida jaamil, a lokacin tausayinta ne ya kamashi ganin tana kuka, ya san ya yaudareta ne ya rabo ta da iyayenta ya kawo ta cikin fake rayuwarsa, atleast she deserve to know something that is true about him, duk da cewa ma baya tunanin ta fahimci dukkan zancensa. ba lallai ne ma ta gane ba.

Sannan yayi ta nanata zancen nema musu zaman lafiya ne saboda zamanta dashi had'ari ne, ita d'in ba abokiyar halittarsa bace, dole ne yayi taka tsan-tsan da kansa a wajenta, dole ne in yana tare da ita hankalinsa ya zama fully a jikinsa don she's so fragile to him, kamar mutum ne ya rik'a wasa da circle d'in kwanduwar kwai a hannunsa, kuma ya na yi da zummar cewa ba zai fasa cikinta ba.

Saboda haka ba zai tab'a bari zamansa da ita ya samu matsala ba, zai iya k'ok'arinsa wajen nuna mata dukkan kulawarsa yadda ba zata fahimci rashin wasu abubuwa ba, don kamar yadda ya sani kuma jaamil ya dad'a fad'a masa a jiya, akwai abubuwan da ba zai tab'a bari su faru tsakaninsu ba.

Ya tuno d'azu da yazo tashinta sallar asuba, tana baccinta peacefully a lokacin, hular kanta ta zame gefe kad'an sannan strands d'in gashinta mai kyau ya kwanta smoothly akan filon, ta rik'e fuskarta da tafin hannayenta biyu a kowanne gefe kamar k'aramar yarinya, sannan bakinta slightly a bud'e.

Yana iya jin fitar numfashinta a hankali daga tsakanin leb'b'en nata, a lokacin yaji kamar ya matsa kusa da ita ya d'ora yatsansa akan leb'b'en, yaji irin taushi da d'umin da suke dasu amma ya hana kansa.

Yadda ya barta tayi baccinta hankali a kwance jiya ba zai so ya tashe ta da wani abu da bata saba ba.

Ya lashe gefen lebb'ensa sanda ya k'araso bakin gate d'in. Tun kafin ya danna horn maigadin ya fara k'ok'arin bud'e gate din. Sunansa Malam Aminu, wani tsohon dattijo a kamfaninsu da ya d'auko shi tun sanda ya siya gidan a matsayin mai gadi.

"Sannu da zuwa Alhaji, Sannu da zuwa."

Ya fad'a lokacin daya shigo da kan motar cikin gidan. Maimakon ya amsa sai yace.

"Ina kwana Baba, mun tashi lafiya?"

"Alhmdlilahi Alhaji, Alhmdlilah. Jiya ina taso in tuna maka zancen tankin nan na baya daya fashe kuma sai naga dare yayi."

"Ya salam, na manta ne amma da kayi magana ai, yanzu to babu ruwa a ciki ne?"

"A'ah ai da yake jiya na sami b'arin wasu robobi a can baya na aikin gidan, sai na k'ona su na manne shi, to ya ragu dai amma har yanzu ruwan na zuba."

"Toh shikenan Baba, zan fita anjima sai in taho da wanda zai canja shi....ga wannan."

Ya d'auko d'aya daga cikin ledojin gefensa ya mik'o masa, ya karb'a da godiya sannan ya k'arasa ciki, ya ajiye motar a daidai balcony k'ofar falo sannan ya fita, ya kwaso ledojin ya rufe motar.

Sai da ya tsaya a gaban k'ofar sannan ya fara k'ok'arin lalubo key d'in a cikin na motarsa. sai dai kafin ya kai ga budewa ya jiyo wasu 'yan k'ananan taku daga ciki, sannan hannu yana fumbling da k'ofar, a sakan d'aya k'ofar ta wangale Sa'adha ta tsaya a gabansa cikin shigar wata doguwar riga ta orange material, rigar ta haska kalar fatarta da tayi fresh sannan ga hannayen nan nata da suka sha kunshi d'as, ya illahi! ya had'iye yawu da kyar sanda ya lura da idanunta.

Me ya same ta?

Kuka take yi!

●﹏●

WAYE SHI?

AYSHA SHAFI'EE

36

(☆_☆)

Da sauri ya taka steps d'in ya shiga ciki, sai da yazo dab! da ita sannan ya tsaya.

"Sa'adha me ya faru? me ya same ki? wani yazo ne?"

Yayi tambayar duk a lokaci d'aya sanda hannunsa ya lalubo nata, jikinta ya d'anyi b'ari amma nan da nan ya saki sanda ya shiga murza babban yatsansa a bayan hannunta.

Cikin sheshshek'ar kukan ta girgiza kai.

"Ba wanda yazo, na tashi ba kowa a gidan sai ni kad'ai, kuma nayi ta jin tafiya kamar za'a shigo amma ba kowa, sannan...."

"Shshhh..." yasa d'aya hannunsa yana goge mata hawayen a hankali.

Zuciyarsa ta matse da tausayinta, ya tuna cewa ba taba zama a gida ita kad'ai ba, ta tashi a gida mai mutane da yawa ne dole yanzu taji bata saba ba.

"I'm sorry habibty...kina ta baccinki mai dad'i sanda na fita shi yasa ban tashe ki ba, kiyi hak'uri dan Allah."

A lokacin wani gefen tunaninsa ya ayyana masa cewa shine Babban abin tsoron da ya kamata ta guda ma a yanzu. yasa hannunsa a bayanta yana zagaya shi a hankali sannan yana k'ara rada mata tayi hakuri har sai da ya tabbatar zuciyarta ta nutsu sannan ya d'an sunkuya da fuskarsa side d'in kunnenta yace.

"Ban tab'a dawowa gida wani ya bud'e min k'ofa ba Noory, this is my first time...Nagode!"

Tayi murmushi a hankali cike da kunya sannan ba tare da ta d'ago ba muryarta tace.

"Ina kaje?"

Yaji murmushin shima na shirin kub'uce masa, irin wannan courage d'in nata na burge shi, bata cika k'umbiya-k'umbiya ba.

"Baki ga note d'in dana ajiye miki ba."

Ta girgiza kai.

Ya rufe k'ofar da k'afarsa sannan ya d'ago mata ledojin hannunsa.

"Naje samo miki abinda zaki ci ne."

Idanunta suka kara girma da tambayar abinci ya siyo.

"Come on, na san jiya da za'a kawo ki anyi ta fad'a miki cewa ki kula dani koh?"

Bata amsa ba ya cigaba.

"Nima haka kowa yayi ta fad'a min, to ta yaya zan fara barin ki da yunwa da sassafen nan?"

Ta d'ago ta kalle shi da jik'akk'un idanunta da kuma d'an mitsitsin murmushi a lebbenta. Kwayar idanunta farare tas suka d'auki hankalinsa, yaji kamar zai fad'a cikinsu ne ya nutse. Subhanallah! ya fad'a a ransa.

She's so beautilful...very stunning and deadly gorgeous!

Ba tare da wani dogon tunani ba ya ajiye ledojin sannan ya kai hannunsa ya shiga tab'a doguwar jelar kitsonta da suka fito ta gefe, a lokaci d'aya kuma yana k'ara sunkuyo da fuskarsa saitin tata, ya lura ta ki'fta idonta a hankali tana kallonsa, sai da ya matso da kansa dab! da ita sannan ta rufe idanunta gabad'aya.

A hankali lebb'ensa ya sauka akan cheeks d'inta, wani waje just a mere inch from the side of her lips. Sannan a hankali yaji wani abu da bai tab'a experiecing ba a rayuwarsa, wani abu daban, wani abu sabo da babu shi a register kwakwalwarsa.

Cikin kiftawar ido jijiyoyin jikinsa suka daina aiki sannan jikinsa ya k'ame kamar dutse, yaji zuciyarsa na bugawa da k'arfi kamar zata tsaga kirjinsa ta fito, ya kasa koda kwakwaran motsi, Hannunta d'aya dake rike da nasa shine kad'ai wani abu dake rike da jikinsa, jikinsa da ya tsaya a k'ame kawai, frozen! kamar mai jirin wani abu, wani abu da zai dawo dashi duniyar zahiri.

Ring Ring Ring Ring Ring.

Wayarsa dake gaban aljihu ta zama wani abun daya janyo shi zuwa senses d'insa.

********

BAYAN KWANA UKU.

Imran bai tab'a tunanin cewa akwai wani farin ciki a duniya da ya kai wanda yake ji a yanzu ba, ya yarda cewa duk wani farin cikin duniya ya taru ne a gefe guda sannan farin cikin aure ma ya tattara a gefe guda.

Ya k'ifta dogwayen gashin idonsa a hankali yana kallon fuskar Sa'adha dake kwance a gefensa tayi pillow da kafad'unsa tana baccinta hankali a kwance, tunda yake bai tab'a ganin wanda ke bacci so innocent kamar ita ba.

Ya tuno yadda ta dinga dariya jiya da daddare lokacin da tasa rigarsa, tana cewa tayi kama da irin masu film d'in abinda dariyar nan, amma shi a idanunsa ba haka ya gani ba. she look so flushing and radiant!

A cikin kwana uku kawai yayi mugun sabawa da ita kamar yadda ya san itama ta saba dashi, don ko bata fada ba kyallin farin cikin idanunta da kuma yawan murmushinta zai shaida masa hakan, sannan ko daga yanayin maganganunta ta sake dashi saboda tana iya masa doguwar hira har ta bashi labari, wani lokacin ma tana indicating da hannunta cikin tsiwarta. Matarsa mai tsiwa ce, ya riga ya sani, Shine farkon abinda yaja hanakalinsa game da ita.

Bayan hakan ya kula ta fara sabawa da yadda koyaushe hannusa ke cikin nata, good morning kisses d'in da kullum yake raining a fuskarta da kuma sauran abubuwan da kullum yake iya k'ok'arinsa wajen daure zuciyarsa akanta, don ko sau d'aya a rayuwarsa bai taba experiencing irin feelings d'in dake nukurkusar zuciyarsa game da ita ba, wasu irin feelings ne kamar electricity suke yawo a kowacce jijiya ta jikinsa duk sanda yake tare da ita.

Kuma a yanzu tare suke yin komai na gidan, tare suka gyara setting d'in d'aya falonsu da tace baiyi mata ba sannan tare suka gyara kitchen d'in gidan, suka mayar da dukkanin kayan da aka jera cikin kwalinsu suka bar iya na amfani kawai, ya fahimci bata fiye son tarkace da kaya da yawa ba, she prefferd everything plain and simple! kamar yadda nature dinta take itama.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull