'yar baiwah complete - Chapter 2
'yar baiwah complete Chapter 2: 'yar baiwah complete Chapter 2. Tun bayan tafiyat 'Yar Baiwah Baaba kullun cikin cewa take harda Dan zazzabin ta na kewar…
4,101 words
Tun bayan tafiyat 'Yar Baiwah Baaba kullun cikin cewa take harda Dan zazzabin ta na kewar jikar tata kullun ta lisafe da ko kwana nawa yar baiwa tayi a birni kullun tunanin ta yanxu a wane hali jikarta take sai dai zuciyarta tana hayamata duk Inda yar baiwa take to addu,ar da take mata yana tare da ita da A kullun baaba sai taiwa Rukayya addu,a kuma batason taji lbrn komai indai ba firar mutuniyar ta bane hakan CE ta kasance ko a wuri mahaifinta sai dai yana da jarumta baya nunawa dankar ya karyawa baaba zuciya haka suka kasance gidan shuru shuru har na tsawon sati biyu tun basu saba ba har yazama jiki suka saba kowa yadan fara sakin jikinsa aka dawo yanda ake da saidai kuma in an tuna ayi kewa sabo kenan.
Maman ussee😘
🙎 'YAR BAIWAH 🙎9⃣ Maman Ussee Ruky da Sajeeda zaune a dakinsu sunata fira sai dariya kakeji wow gsky nazata inaje skull din nan zan fuskanci Matsala, ashe ba haka nan bane, kai dadina dake tawajena tsoro gareki, ninasan ba abinda zai faru kawai dai kedince akwai tsoro. Kinga tashi kar muyi latti kinsan halin mutumin naki mai tajwid akwai disgi ni kuma na tsani mutun mai disgi hakafa ranar safa CE kawai bansaba ya hanani shiga ajin Ruky tace OK kinsan dai gobe akwai Hadda ko saboda haka yau. Ba, bacci Dan kar muje bamuyiba kinga gbe akwai skull cox Hutu yakare yanxu da dare zamu rika yin Hadda dinmu,
Bayan sun kammala ne suka fito sanye da uni din Islamiyarsu sama sama suka ci abinci Dan karsuyi latti ayi musu duka sauri sukeyi Rukayya rike da hannun Fadil yayin da Sajeeda take rike da hannun Abdallah Dan a kafa suke zuwa Islamiya tun bayan ranarda Daddy yakaisu, Sunci sa,a suna shiga ana tare yan latti kai tsaye ajinsu suka nufa. Bayan sun aje su Abdallah a nasu ajin. Ai kuwa basu tsiraba Dan koda suka je mai tajwid yariga yashiga hkr suka fara basa dakyar suka ci sa,a yabarsu suka shiga bayan shanyasun da yayi a waje haka yakaraci darasin sa yabar ajin. Basu suka tashi ba sai misalin 6:pm aka tayar dasu kowace daliba ta kama hanyar zuwa gidansu, Ruky da Sajeeda tare da yan kannesu suma suna dai daga cikin masu zuwa gida kasancewar magrib ta kusa da isarsu gida kowane ya nufi dakinsa Dan bayarda farali suna idar da Sallah falo suka xo , a nan suka tararda mummy itama ta fito yaran Daddy sannuku har kunyi sallar ne eah OK to Allah ya karba ya bada lada suka amsa a tare ameen mummy, yadai Ruky hope ba matsala a skull ko karki damu da sannu zaki sabane fatana kawai Allah yataimaka yabada sa,a kuma a dage kunji eah suka sake amsawa, haka sukata fira jefi jefi kiran sallar Isha ne ya tayardasu bayan sun kammalane suka fito domin cin abincin dare, Anan suka tarar da Daddynsu Dan rabon da suganshi tun safe daya ajesu a skull gaida shi suka fara kamin nan kowa ya zauna a set dinsa mummy tayi serve din kowa akaci akasha aka koshi sai kowaya kama gabansa yayinda Ruky da sajeeda suka fara tilawar Haddan su dakuma assignment dinsu bayan su kammala sukayi addu,a suka kwana sai. bacci.
Kashe gari haka ta kasance tun wuri suka kimtsa suka fito inka gansu kanar wasu twins gwanin sha,awa yau ma Daddy ne yakaisu skull daga nan ya wuce GT Bank da acan yake aiki bayan an kare Assembly kai tsaye kowace daliba ajinsu ta nufa Dan daukar darasi Sajeeda da Ruky a tare suke tafiya har class dinsu kowace ta zauna a set din ta kamin class master yaxo yakira register daga nan kuma Malami mai lesson ya shigo ya fara gabatar musu da lesson.
Maman Ussee😘
Naga sakonku nagode sosai da kulawa nasoyana Allah yabar zumunci.
🙎 YA RBiAWAH 🙎 1⃣0⃣ Maman Ussee
Time din break yayi Sajeeda da Ruky suka fito waje class sunayin break yayinda sauran student ke lamarin gabansa, Ruky nikuwa Sajeeda kinsan abinda yake bani mamaki a,a saikin fada wan nan malamin nan na daxu mai disga mutane din nan kinga yanda yabar ummy nata zuba surutu ya kyaleta amma na tabbatar da wani member din class ne daya sha zagi yau kuma na ga sai wani shige mata yake kodan yaga tafi kowa girmane a class din, hey are u jealous 😀 Ruky takai mata duka wane irin jealous kuma ni ina ruwana dashi kawai dai naga hakan baidaceba ne shiyasa na gaya miki OK to kawo takalminki na ajiye miki kije ki gaya musu ustaziya Rukayyatu 'YAR baiwa 😏 dalla Banason rainin hankali daga kawai na fada miki Abu shikenan sai ki wani canja min magana 😀😀😀 dariya sajeeda tayi hardasu kyalkyatawa kamar zata fado kasa aiko Ruky ta ji haushi ta kwashi kayanta fuu ta fice daga wurin hava ke kuwa sorry mana tsayani muje tare INA ko saurarenta bataiba ta fice class abinta sai daga baya ta saiko suka shirya kamin adawo break.
Sannu sannu.bata hana zuwa sai dai a Dade ba,a kai ba yau su Ruky zasu zana end of second term examination, a cikin skull kuwa bawanda baisan Sajeeda Abubakar &Rukayya Sa,eed ba komai nasu atare sukeyi duk Inda kagansu tarene ba abinda yake rabasu ko a gida ma hakan ne gasu da ilmi uwa uba kyau gasudai ba wani girmane dasu ba Dan daka gansu zaka yarinta karara a tare dasu sai dai sunada ladabi ga girmama na gaba dasu a class inkaji suna surutu to lallai Abu mai mahimmanci suke tattaunawa. Baruwansu da wasu frnds sudai barsu da karatu Dan kullun abinda Daddynsu yake jaddada musu kenan kosunyi fada to yanxun nan zakaga sun shirya al,amarinsu yana mutukar.birge jama,a ko unguwarsu bamai cewa sun tsokaneshi Dan su karatun ne kawai yasha musu kai alhmdllh cikin sa,a suka fara Rubuta exams dinsu har suka karashe akayi holiday,
Murna gurin Rukayya ba,a magana Dan dama ta matsu ayi Hutu Dan taje Raba dama Daddy yace da anyi Hutu zasuje tare suyi one week sai sudawo sabida islamiyarsu dayake sunyi nisa sosai, bayan sun dawo gida da kwana biyar suka daga sai Raba gabaki dayansu harsu Fadil da Abdallah ai kuwa kuxo kuga murna wurin Baaba kamarme taga yan jikokinta musamman ma Yar baiwa taga yanda tayi Haske ta goge hardasu kiba gwanin sha,awa kai lale marhabin da yan sokoto cewar Malan sa,idu nan nan kawai yake da 'ya'yan nasa yanajin wani farin ciki a ransa yarsa CE ta dawo haka tubarkallah masha Allah, bayan an nutsa kowa yaci ya koshi aka fara sabuwar fira yayinda suka gode sosai da namijin kokarin da Daddy yayi musu godiya suka ka rayi da fatan alkhairi, satinsu daya a Raba suka juyo yar baiwa kawai suka bari koshima badan sunsoba saidan rokon da Baaba tayine shi,isa suka barota ta kara sati sai Daddy yazo ya dauketa sukoma, bayan kwana biyu Baaba na zaune itada Rukayya suna tadi take tambayarta bawata matsala daiko eah bakomai lfy lau wllhi bakiga yanda ake bani kulawa ba sosai da sosai to madalla ai hakan akeso Allah dai yasaka musu da alkhairi Rukayya ta amsa da ameen amin shiyasa nake sonki Baabata dankin iya addu,a 😀 dariya Baaba tayi tace ja,ira har yanxu dai sakarcin naki nanan Ruky tace to in ban maki ba wanikeda shi Wanda yafiki ai kekadaice dagake. Bakari 🙊 tabdi wai yar baiwah yaushene kika iya surutu haka lallai zaman birni ya saka ki iya magana 😳ai baaba Dan baki zauna da Sajeeda bane haka take kamar parrot indai surutune uhum menene fara kuma me Ruky zatayi in banda dariya aikuwa Baaba takaimata duka ta goce tsaya kiji parrot akecewa inaga sai naje sake skull dinmu kin kara wayewa ja,ira kekam dai Allah ya shiryeki ta CE ameen tana murmushi. Maman Ussee😘
🙎YAR BAIWAH 🙎1⃣1⃣ Maman Ussee😘
Satin Rukayya biyu daddy yazo yadauketa suka koma sokoto cike da kewar iyayenta musamman ma Baaba dasuka shaku sosai, Haka Rayuwa taci gaba da kasancewa yau farin ciki gobe akasin haka dama ita rayuwa haka ta gada , amma a wurin Rukayya abin ba,a cewa komai Dan kullun cikin farin ciki take yayinda duk tayi sallah saita Roki Allah yasa kama daddy da aljannah hakama mummy dakuma iyayenta. Haka suka karaci holiday dinsu har ya kare duk Wanda yasan Rukayya ada idan yaganta a yanxu bazai ganetaba inhar ba farin sani yayi mata ba Hutu kwanciyar hankali haiba kwarjini duk sun baibayeta batada wala matsala a skull ma hakan ne Dan so dayawa tasha samun kyaututuka da dama awajen malamai kai harma da students akan baiwar da Allah yayi mata ilmi. Ba,a magana Dan ko quiz za,ayi to Ruky da sajeeda na ciki haka ma divert ko inter schools compotions za,ayi to dolene asaka yar baiwa ga tada da speach mai dadinji dakuma saurare takowane fanni gata ilmin addini Dan kuwa saura kadan ta Haddace alkur,ani mai girma, Sajeeda namatukar son Rukayya kamar yan uwanta na jini haka take jin ta kamar uwa daya uba daya suke ba,abinda Rukayya zata CE tanaso Sajeeda. Batace tana sonsa ba koda kuwa. Baimata ba a duniya inhar kanason kaga. Baccin ran Sajeeda toka taba Yar baiwa haka ma ko a wurin Rukayya batason ko kadan taga yar uwarta cikin damuwa kuma sajeeda bata taba jin haushi ko kyashin Rukayya tafita ilmi ba duk da dai itama tanada nata iya gwargwardo wadan da basu sansuba cewa ma suke yanbiyu ne kasan cewar tun bayan dawowar, Ruky a gidansu Sajeeda Daddy bai taba ban-ban ta musu kayaba kai harta takalmi da sarka iri daya ake saya musu hakan yayiwa mummy dadi sosai yanda Daddy yadauki Ruky kamar sajeeda baya taba nuna wani banbanci duk abinda zai iya yiwa sajeeda to tabbas zai yiwa Rukayyama, duk da yasha samun yan korafe korafe a gurin Abokanansa dakuma wasu amma indai ya fahimci ba maganar arzikice takawo kaba, tun daga ranar kun raba hanya dashi bayason sa 👀 ido Dan yasan duk abinda yayiwa Rukayya Dan Allah yayi kuma yanada tabbacin zaisamu ladansa a gurin Allah . Haka abin yake ko a wurin mummy indai kawayenta suka fara kushe Rukayya nan da nan zata watse mutun komai dangartakar ta dashi kuwa ita a ganinta ko ba ita, ta haifi yar baiwa ba ai Abbanta ciki daya suka fito dashi kuma duk abinda zai cutar da Rukayya bata sonsa Dan tasan duk abinda tayi Dan zumuncine kuma Dan Allah da fatan samun lada a gun Allah. ( Anya a wan nan zamanin zaka iya samun Dan uwanka maisonka da kaunarka saboda Allah kuwa zumuncin yanxu sai a hankali kowa nasa kawai yasani Ya Allah kabamu ikon so da kuma kauna ga yan uwanmu, Ameen ya Ra bbi). Rukayyace zaune a falo tana koyawa su Abdallah home work dinsu Sajeeda kuma na gefe tana Dan duba wani English litreture mummy kuma ta fita da yake yau ba Islamiya kowa na abinda yasa a gaba sallamar Daddyce ta sa kowannensu dago kansa sama Dan amsa sallama Sannu da dawowa Daddy, yauwa yaran Daddy sannunku da gida umman taku har yanxu bata dawo. Bane wan nan zuwa biki haka har yamma tayi gashi inaso muje gidan wani amininah da muka Dade bamu haduba baya kasar jiya yadawo muje muyimai. Barka da dawowa ko bakwaso 😊 sukayi ga aki dayansu Daddy muje basai munjira mummy. Ba kawai cewar Sajeeda yes Daddy kinji Abdallah , no gsky daddy ajira sai mummy tazo inyaso sai mubarshi sai anjima da dare muje Daz my gal shiyasa nake sonki dan kinada hankali ba kamar wadan nan ba Sajeeda ta turo. Baki fadil kuma gwalo yayi mata ta kaimasa doka ya goce ya boye bayan Sister Ruky plzz my sist kice karta dake ni to meye namin gwalo ai nima watarana Daddy zai yabeni bakaman kai ba ko little bro cewa da Abdallah eah hakane Sist kyalesu shida sister Ruky, muma watarana rana sai mun musu gwalo dat my bro oya give me five suka tafa ita dai Ruky murmushi kawai tayi itama tace da fadil leave them kaji sweet.bro dina itama sajeeda ta kwai kwayeta kaji sweet bro dina Ruky ta jefa mata pillown kujera ta gudu ita da Abdallah zuwa daki hmmmm Sajeeda da Ruky kenan everlasting friend
Maman Ussee😘
I love you All my fans 💋
🙎 YAR BAIWAH 🙎1⃣2⃣ Maman Ussee😘
Misalin karfe 8:30 mummy da 'ya'yata suka shirya cikin shiga ta alfarma kowansu yaci gayu, Daddy ne ya leko ohh wai haryanxu baku kammala bane koyaya? Nop we r ready kai kadai kawai muje jira OK let go. Gida ne na alfarma Wanda ya amsa sunansa gida, ba karya naira tasha kuka a gidan Dan an zuba dukiya a duk fadin Sama road ba gidan da yakai kayatuwar gidan kai tsaye Daddy cikin gidan ya nufa yayinda mai gadi ya wangale get suka shiga, Wow Aljannar duniya lallai gskyr hausawa ne dasuka CE na zaune baiga gariba habar gidan tamkar a kasar turai duk da dai darene amma tamkar rana saboda hasken lantarki, gefe daya motocine a gibge, an jera su Reras a car pack, sai kuma a center akayi wani Dan round aka shuka flowers ruwa nata bulbulowa kamar korama hasken fitillu ya haske ko,ina ba, cewa komai dayan gefen kuma wurin hutawa ne da kujeru sai rumfa tsayawa na fada muku gayatuwar gdn bannar lokacine, iya haduwa gidan ya hadu sosai kai tsaye car pack Daddy, ya nufa yayi packing, kamin nan suka fito zuwa cikin gidan, Wornder shall never end kunga Fallon gidan kuwa😳 wasu kayatattu. Royal chair's, na hango kai sun hadufa ba karya masu kudi suna sha,aninsu. Gefe guda Dining area ne dauke da wani katon dining table tsarin falon komai red an white ne kai hartama da paint din falorn red ne da white kai nasha kallo fa saura kadan nadan saki layi nadai yi sauri na saita kaina Dan karsu dagoni😜, Daddyne yafara zaunawa tare dasu Abdallah kasan cewar shi ba bako. Bane a gidan in yazo kai tsaye yake shiga ba wani dar dar, mummy kuma tare da Ruky da Sajeeda, Wata matace tashigo da ganinta mai aikin gidance sannuku da zuwa Bari na kira Hajiyar tana sama bawani bata lokaci aka fara cika musu gabansu da cima kala_kala, yayinda kuma Daddy ya daga waya ya sanarda abokinsa isowarsu Dan yasan halin matar gidan inta itane saidai su kwana anan baxata sakko. Ba , Bayan min tuna kadan sai ga shinan ya sakkon mutun mai baiba da kamala ga kwarjini, da murmushi sa ya tarbi abokin nasa ya rungumeshi aka fara gaisuwar yaushe rabo, Alhaji Basheer kenan Amini kuma uban gida a wurin daddy mutun ne mai son mutane kowa nasane yanada daraja Dan Adam baya wulakanta talaka duk Wanda yaxo gunsa zai tarbeshi kamar nasa ga taimako sabanin uwargidansa Hajya kubra macce mai fada ga nuna isa batason talaka ya rabi mijinta Dan ma Alh Basheer na tsaye ne kuma yana takwarata da Allah kadai yasan tsiyar da zata tsula. 'Ya'Yansu shidda Abubakar Umar Usman da Aliyu sai kuma twins Afra&Afnan bayansu bata sake haihuwa. Ba, Abubakar shine babban dansu sai Umar ke bimasa duk da bawata tazarace tsakaninsu ba Usman da Aliyu ma bawani nisa a tsakaninsu, bayan ta haifi Aliyu tadan jima bata sake haihuwa ba har an cire rai sai Allah yabata cikin afra da afnan Alh Basheer yayi murna kwarai da gske kasancewar bashida yara mata duk maza ne adalinlin hakane su Afra suka taso cikin gata sosai ba iyaye bakuma ga yayunsu ba .
Bamai takura musu sai abinda sukaso sukeyi tun suna yara abindai ba,a cewa komai idan kanaso kaga fadan Hajya to taba mata yan biyunta ba abinda sukeso a duniyar nan Wanda Hajiyarsu bata musu(Jan kunne👂Hatara iyaye mata mukula sosai da sangarta 'yayanmu dominsu amanace awanjemu ki👉 sani Allah zai tambayeki game da tarbiyar da kika. Baiwa 'yayanki dolene mu tsawatar musu Dan ance kaso naka duniya ta kishi inkaki naka duniya ta soshi haka zancen yake Allah yasa mugane Ameen) Alhaji Basheer rikaken Dan kasuwane kuma shahararren mai kudi Wanda ketashen kudi a wan nan zamani duk da dai ba sa,an daddy. Bane kusan Allah mai hadin zumunta. Wata rana ne Alhaji. Basheer yaje Bank dinda daddy ke aiki domin ya cire wasu kudade nashi sai aka samu akasi bai samu yanda yakeso ba kuma gashi tafiya zai yi yarasa mafita shine daddy ya taimakesa yasamu kudin iya adadin abinda yakeso to tun daga ranar yazama duk indai kudi yakeso a bank dinsu Daddy to Daddyn kawai zai nema hartakai ma daddy da kansa ya sha kawoma Alhaji Basheer kudi har gida wan ne yasa sukayi sabo har Alhaji Basheer yakan Dan saka daddy wani abu Wanda yake na sirri kuma ayimasa yanda yakeso batare da ansha wahalaba wan nanne dangantakar Daddy dakuma Alhaji Basheer , Bayan sun gaggaisa Ruky da Sajeedama suka gaida shi cikin girmamawa, sosai yaran suka bashi sha,awa ya yaba da hankalinsu sosai har yake tambayarsu ajinsu nawa da skull dinda suke suka bashi amsa kai tsaye ya CE gaskya kunada kokari so keep it up duk Kansu dariya sukayi sukace Insha Allah , Jim kadan sai ga Hajya Kubra manta manta anfito ana wani tako daya bayan daya kamar,batason taka kasa tana wani nuna is a ,daga saman stairs falon ta nufa gurin da su Daddy ke zaune anata labaran duniya shida Alh su mummy kuwa hankalinsu nakan palasma TV dake jikin bango suna kallon news. Au Alhaji wai baki mukayine,murmushin taikaici yayi, yana mai jinjina hali irin na matarsa , Eah kawai yace mata yaci gaba da abinda ke gabansa . Sannuku kawai tace dasu takoma warta dama ko sakowarda da tayi taga Alhaji ya matsa mata da kirane shine ta sakko taga meyene gaidata su Sajeeda suka shiga yi a dakile ta amsa tayi ficewarta Alhaji baiji dadin abinda tayi ba ammato ya ya iya. Wuraren 10:30pm suka yima Alhaji Basheer sallama ya dauki kudi yabasu sukaki karba aikuwa yayi juyin duniya sukaki saida yanuna bacin ransa kamin nan, daddy ya umurcesu dasu karba kishi Sajeeda CE ta amsa Ruky kam ki tayi saboda kunya. Muje zuwa
Maman Ussee😘 Kuyi hkri aiki ne yamin yawa shiyasa but insha Allah gobe zanyi mai yawa nagode sosai masoyanah🙏
🙎 YAR BAIWAH 🙎1⃣3⃣
Maman Ussee
Da isarsu gida kowa, yanufi dakinsa Dan kwantawa, a huta yaukam ba, zancen fira , Ruky da Sajeeda wanka kawai sukayi sai alwala kowacce ta nemi shifida, sai. Bacci
Kashe gari tun safe suka tashi bayan sun kammala ayunkan gida kai, tsaye dakin mummy suka, nufa bayan sun gaidata da. Ne , Suka nufi dakin daddyn su, shima sukayi gaidashi, kamin nan sukaje suka ci gaba da sauran yan aikace aikacen gida Dan mummy bata barinsu girki saidai ta nuna musu amma har yau bata sake musu girki ba acewarta su yarana har, Yanxu baza ta sake musu komai ba, sai nan gaba iya kacinsu shara sai wanke wanke , da sauran Dan abinda , baza,a rasa ba. Time din break nayi kowa ya halara mummy tayi saving din kowa, aka fara cin abinci , bayan an kammala ne Daddy ya ke tambayar su daya bayan daya koda matsala ne Dan, Dama haka yakeyiwa kowa. Daga nan duk mai bukatar wani abu saiya fada kowa yace , Bakomai Daddy ya wuce zuwa Bank. Dan yau ba skull ana hutun good Friday ne yaran yau basa zuwa skull , Bayan sun kamala aikinsu sai suka tambayi mummynsu sunaso, ne suje dubo wata yar class dinsu datake, nan unguwarsu . mum tace dasu karsu Dade suyi sauri su dawo , tau suka amsa kamin nan suka dauki hijabs dinsu, Suka ficce daga gidan , gidansu Hafsat suka nufa nan ne bayan layinsu da sallamar su suka shiga cikin gidan, bayan sun gaida umman Hafsat sai suka shiga dakin Hafsat din, bayan yan gaishe gaishe , suka fara fira irin nasu na yan makaranta, Basu suka dawo ba sai bayan an taso daga salar jumma,a dayake yau Friday ne , kai tsaye gida suka nufa koda sukaje mummy tayi baki bayan sun gaida sar da bakin mummy dakin su suka shiga suka sayi sallah bayan sun kammala, suka fito suka Debi abincinsu suka koma dakin su, sunata wasa da dariya batare da wata damuwaba yan biyun mummy kenan!!!
Maman Ussee😘 Note Dan Allah kuyi hkr wllhi kwana biyu bana jin dadin ne amma yanxu naji sauki zanci gaba dayi muku insha Allah nagode sosai da kulawarku💯
🙎 YAR BAIWAH🙎1⃣4⃣
Maman Ussee
Safiyar Talata tun safe suka tashi suka fara shirye 2 na zuwa skull, bayan sun kammala da komai da komai Daddynsu yadaukesu yakaisu bayan ya ajiyesu sai ya ficce zuwa wurin, aikinsa Su Abdallah da Fadil ma nasu bangaren suka nufa, yayinda Sajeeda da Rukayya, suma suka wuce, zuwa assembly, ground, After ankare Assembly duk student's suka ficce, zuwa classes dinsu Dan daukar darasi, bayan Class master din su Ruky yashigo ya kira register, sai aka fara gabatar musu da lesson din nasu . Kwanci tashi baya hana zuwa yau har su Sajeeda da Rukayya sun rubuta JSCE lafiya lau murna gurin Daddy da Mummy kamar me, Haka Rayuwarsu taci gaba da kasancewa har lokacin da exams dinsu ya fito Daddy yayi musu alkawarin zai canja musu skull dan ya yaba da kokarin yaran yayinda Alhaji Basheer shima yayi alkawarin zai bada nasa contribution, din idan zasuje gaba Dan shima yaran suna birgesa, more especially Tarbiyarsu ga girmama nagaba dasu, Kamin karshe Hutu Daddy yakai Rukayya da Sajeeda Raba domin suyi hutunsu acan , sunsha Hutu kam Dan saida sukayi kusan wata Daya acan ba karamin Dadi hakan yayima Baaba Dan tana matukar son Rukayya , bayan sun dawo, Hutu kuma sai suka dukkufa zuwa Islamiya Dan dama sauran kadan su sauke kuma Daddy yayi musu alkawarin sai sun sauka zai kaisu SS one Dan dama hakan sukeso badan ma sunje Hutu a Raba ba da yanxu sun sauke hakan sukeyi kullun akaci sa,a kuwa Rukayyace ta fara sauka bayan Sati daya Sajeeda ma tasauke Murna da Daddy yayi. Bata misaltuwa kullun saiyayiwa yaran sa addu,a Allah yakara musu basira Alhmdllh Addu,arsa ta karbu Dan kuwa ga sakamakon hakan yagani. A tare daddy ya hada musu walimar sauka a gida bayan an gabatar musu da wata walimar a makaranta, ba laifi kam an taru bayan an gabatarda yan naseehohi akayi musu addu,a sai yan kayan rabo da akayi bayan an rufe taro da addu,a kowa ya watse, Daddy ne zaune da yaran sa anata wasa da dariya uhuum Abban yara wai mexai hana ka kokarta ka kai su Iman ne naga can ana karatu sosai ko cewar mummy Daddy ya nisa eah haka ne amma kudin ne , sunyi yawa kuma nafiso nakaisu Inda zasuci gaba da Hadda Dan ,dama nayi shawara zan kaisu, Sultan Abubakar Maccido Islamic college, koya kika gani ,ai Ruky da Sajeeda najin haka su fara murna yeee Thanks much Daddy we love u Daddy Allah yakara budi sukaje suka Rungume Daddyn nasu suna murna ,daga nan kuma aka ci gaba da hirar duniya kamin time din sallar magrib yayi , Dad yaja su Fadil zuwa masallaci yayinda su Sajeeda da Rukukayya suka shiga cikin dakin su domin gabatar da Sallar magri b. Bayan kwana biyu Daddy yadaukeso sai new skull dinsu dayake akwai masu yin day a ciki akwai kuma masu yin boarding Daddy baya da Ra,ayin barinsu suyi boarding, Day yasaka su bayan ya yayi musu registration, da duk wani abubuwa da yakamata sanda akayi musu interview, aka basu classes saidai ba,a ajesu a class daya ba kamar yanda sukeso , badan ransu yaso ba,haka suka hakura Dan bayanda zasuyi, haka suka zauna a new skull din taso dayake akwai Dan banbanci kadan Dan yanxu sai 4:pm suke tashi dan, skull din hade take da Islamiya Ruky da Sajeeda baruwansu dashiga harkan da banasu ba hakan cema tasa basuyi wasu sabbin kawayewa ba Dan acewarsu kowa ya tsaya matsayin sa Inda Allah ya ajesa , kwana biyu sukayi suna a cikin makaranta akan BAIWAR Ilmin da Allah yayi musu abin sai Wanda yagani Teachers suka fara sonsu duk Inda kaji cikin skull zance Sajeeda da Ruky akeyi Abin yafara bawa wasu student's din haushi Dan yanxu da wuya ayi wani skull conpotiong ba dasu ba gasu da kyau kamar diyan laraba da yawa ss3 student, sun sha musu gargardi akan wasu malaman, abin har mmki yake baiwa su Ruky Dan su a tsarin su ba soyayya a halin yanxu Dan Daddy baya barinsu ko da wasa balantana ma a skull dayake dokar makaranta CE .
Maman Ussee😘
🙎 YAR BAIWAH 🙎 1⃣5⃣
Maman Ussee😘