Yarima suhail complete Novel - Chapter 51
Yarima suhail complete Novel Chapter 51: Yarima suhail complete Novel Chapter 51. Hajiya tsohuwa tad'ibar mawa, koda taba su sumayya suma k'in kar6a sukayi…
2,369 words
Hajiya tsohuwa tad'ibar mawa, koda taba su sumayya suma k'in kar6a sukayi saida tanuna bataji dad'iba sannan suka kar6a sukayi mata godia.
Koda yaya rauda tazo nan tad'ibar mata nasu da na mama sannan tabata kud'i dayawa tace na su baba ne, nan taware wasu tace natane ita da aisha. Sosai sukanuna farin cikinsu sukai mata godia.
Hata tacigaba da zama wajen sultana sadiya tana samun kulawa sosai daga kowane 6angare ga gyara da takesha wajen hajiya tsohuwa, Ameer yaro me farin jini da shiga rai kulawa yake samu sosai dan baima cika wuni wajen Zarah ba indai ka gansa ankawo mata toh yunwa ce takeji.
Shi kansa suhail saida ummi taimasa dagaske sannan yarage shige ma Zarah.
Ranar da tayi arba'in kitso da k'unshi tasha, sannan bayan sallar magrib aka maidata part d'inta, mamakine yakamata ganin ancanza mata kayan d'akinta komai sabo.
Bayan tayi sallar isha'i wanka tayi tashirya cikin wasu sleeping dress masu kyau, feshe jikinta tayi da turaruka masu k'amshi sosai.
Lokacin da tafito har an shirya ma Ameer dan haka tasa wata kuyangarta tad'aukesa suka nufi part d'in yarima.
Gani tayi shima komai ancanza masa sabo room d'insa ya burgeta sosai. Kar6an Ameer tayi daga wajen kuyangar tasallameta, ahankali tatura k'ofan bedroom d'in tashiga kwance tahangosa saman gado yai pillow da hannuwansa.
Ganinta yasa yatashi zaune tare da mik'a mata hannu cikin sauri ta iso inda yake, mik'a masa Ameer tayi sannan tazauna gefensa, murmushi suka sakar ma juna yace baby dafatan kin dawo lafiya? Tun d'azun nake ta jiranki ammah shuru, hmm Nasan dai ba wani missing d'ina kikayi ba, ni kad'ai nayi missing d'inki.
Rungumesa tayi tace hearty wlh nima nayi missing d'inka tsayawa nayi ind'an kimtsa sannan inzo wajen rabin raina.
Wani irin kallo yai mata mai d'auke da sak'onni wanda yasa saida taji wani yar a jikinta, cikin sauri tasadda kanta k'asa.
Kallon Ameer yayi da yake baccinsa sannan yamik'e yaje yakwantar da shi yadawo nan yakwanta saman gadon.
Biyosa zarah tayi takwanta k'irjinsa tace hearty kayi hak'uri nima kasan kunyarsu ummah ne da nakeji ammah ai da tuni na gudo wajen mijina abun alfaharina dan nayi missing d'insa sosai.
Rungumeta yayi yana shafar bayanta yace baby aike bakya laifi duk abinda princess tayi daidaine dan ta cancanta tunda har tasace zuciyar suhail ai ba abinda yai saura, dole yahak'ura yabita yadda duk takeso.
K'ara shigewa tayi jikinsa tace hearty kaima ka sani da ace ana bud'e zuciya aga sirrin da yake cikinta da tuni na bud'e maka kaga abinda yake cikinta.
Janyo hannunsa tayi tad'aura saman k'irjinta tace duk wani bugu da zuciyata zatayi tare da sonka takeyinsa.
Tsura mata juna ido sukayi suna karance duk wani sirri da yake cikin ransu, zarah ce cikin sauri tazame jikinta tazauna saman gadon tana jin wani iri. Inda yarima yamaida idanunsa yalumshe yana jin sonta yana fizgarsa, cikin sauri hannunsa har k'yarma yake nan yajanyota yarungume tare da had'e bakinsu waje guda yafara kissing d'inta, cikin dabara yarabata da duk kayan da suke jikinta nan yacigaba da sarrafata son ransa gabad'aya yafita hayyacinsa nan yaita mata sumbatu.
Zarah tausayin mijinta yakamata ganin yadda gabad'aya yarikice mata ita kanta ta san ya yi missing d'inta sosai.
Ta wahala sosai a hannunsa ya sa mata albarka ya fi ak'irga.
Bayan komai ya lafa yarima d'aukanta yayi sukaje sukayi wanka bayan sun gama d'aukota yayi yamaidota saman gado yakwantar da ita sannan shima yakwanta yarungumeta a jikinsa cike da shauk'in sonta, wata irin runguma yayi mata kamar zai maidata cikin ciki har saida zarah tayi 'yar k'ara sannan yasafsafta rik'on,
Cikin dare koda Ameer yafarka saidai yarima ne yaje yad'aukosa daga cikin gadonsa dakyar yasamu zarah tatashi shima saida yataimaka mata sannan tabashi yasha.
Bayan ya k'oshi shi yaita riritashi inda zarah takoma baccinta har saida sultan yai bacci sannan yarima yakwanta.
Washe gari bayan sunyi breakfast zaune suke suna hira cikin nishad'i, mik'ewa yarima yayi tare da rik'o hannun zarah yace sweetmee taso muje kiga wani abu.
Mik'ewa tayi tabi bayansa koda suka shiga gaban dressing mirror yatsaya da ita sannan yatsaya a bayanta yace tarufe idanunta.
Koda tarufe sarka ce yasaka mata da zobe sannan yadamk'a mata keys a hannunta yace tabud'e.
Wuyanta tabi da kallo tana shafa sark'an da yasaka mata cikin jin dad'i sannan takalli keys d'in da suke hannunta juyowa tayi tafuskancesa tace hearty wannan sark'an kamar ta gold ce yanzu tawa ce?
Murmushi yayi tare da d'aga mata kai yace tabbas ta gold ce ga d'ankunnen nan, wannan keys d'in kuma d'aya na motar da nacanza miki ne d'ayan kuma na gidane na mallaka maki halak malak.
Zarah rasa me zatayi tai shin farin ciki ko me? Fashewa tayi da kuka tare da rungumesa tace nagode, nagode, nagode sosai hearty Allah yak'ara girma da d'aukaka Allah yarabaka da iyayenka lafiya, bansan me zanyi inbiyakaba dan Allah kafad'amin abinda zanyi wanda zaisa ko kad'anne kaji dad'i a ranka.
Rungumeta yayi yace kidaina yi min godia dear dan kin riga kin gama min komai dan akowane lokaci kina faranta min rai, saidai ince Allah yabaki masu yi miki kema, yanzu dai muje inbaki labari medad'i.
Haka yajata suka dawo parlour suka zauna nan sukacigaba da hira.
_______________
Kamar yadda yai ma Dr mu'az alk'awali hakan ko akayi dakansa yarubuta takardar neman masa transfer ya aika da ita, batare da 6ata lokaciba akayi requesting.
Gidan da zasu zauna ma shi yasiya masu nan mu'az yadawo hospital d'in yarima yacigaba da aiki.
Zumunci ake sosai tsakanin jamila da zarah.
A ranar da tayi arba'in ranar yad'auketa yakaita gidansu tayi wuni daga nan yawuce da ita gidan Aisha, saida yajera kwana ukku yana kaita gidajen 'yan uwa day abokai.
_*A gurguje please*_
Sumayya da salim sosai kawai ake zubawa daga k'arshe dangin salim sukazo suka neman masa auren Sumayya ba a wani sa bikkin dayawaba, ahaka har akayi bikkin aka kaita agadas, sukaita zuba soyayyarsu me tsafta ga yaransu atare da su, sosai sumayya takejin yaran a ranta dan jinsu take kamar ita tahaifesu.
Yaya rauda ma Alh munir zuwa yayi yanemi gafara a bisa abinda ya aikata mata, dakyar yasamu yashawo kanta ta yafe mashi nan yanemi yafiyar iyayenta, daga baya yanuna yanaso ya aureta da ta nuna ba zata aminceba saida yanuna shi dagaske tsakani ga Allah yake sonta sannan ta amince sukayi aure.
_*BAYAN SHEKARA UKKU*_
Yarima kud'i sun zauna ya k'ara kyau da cika, sarauta ta k'aru.
Wani d'an yarone kyakkyawa wanda bazai gaza shekaru ukku ba naga ya shigo dagudu cikin maganarsa da bata ida k'warewaba yana kiran daddy daddy daddy dagudu yafad'a jikin suhail da yake kwance saman cinyar zarah d'aukansa suhail yayi yad'aura saman jikinsa yace little prince wa yata6a min kai?
Cikin gwarancinsa yace daddy wajen meenal zaka kaini.
Shafa kansa yayi yace yanzu ko zan kaika.
Zarah da take saurarensu 6ata fuska tayi tace haba hearty kasa akaisa kawai ko yaje wajen hinde takaishi magana fa nakeson muyi ganin kana waya yasa najira kagama.
'Dago kai yayi yakalleta yace sorry sweetmee me kikeso kice ina saurarenki, chocolate yamik'a ma Ameer nan yafara sha. murmushi tayi sannan tace yauwa d'azun naji kana waya ka ce asa sunan su mama cikin wad'anda zasuje aikin hajji ka mance wanchan shekarar duk tare kabiya mana mukaje?
Murmushin shima yayi yace eh ina sane so nake sukoma, kema naso mukoma ammah hakan bazai yuwuba saidai muje umara tunda mefaruwa ta riga da ta faru.
Ido tazuba masa cikin rashin fahimtar maganarsa.
'Daukan sultan yayi yamik'e yace bari inje inshirya inzo inkaisa gidan shaheed wajen meenal daga chan zan wuce fada tunda gabad'aya yanzu memartaba ya daina shiga sha'anin mulkin ya sakar min komai....yana fad'in haka yawuce yashige bedroom d'insa.
Zarah da kallo tabisa cike da son mijin nata sai kuma chan tamik'e tabisa bedroom d'in ganin sultan tayi zaune saman gadon yarima yana shan chocolate yana game da wayar yarima, inda yarima yake cire kayansa zai shiga wanka, takawa tayi ta isa inda yariman yake nan tashiga tayasa fuskarta d'auke da murmushi, rungumeta yayi jikinsa yace sweetmee wannan murmushin fa?
Kwantar da kanta tayi saman k'irjinshi tace hearty baka bari muka ida magana ba zaka fita.
Shima k'ara rungumeta yayi yace kijirani da nadawo zamuyi magana kinsan a yanzu haka nasan waziri yana chan yana jirana dan shima so yake ya aje mulkin yadamk'a ma shaheed.
Cikin wata irin murya tace toh shikenan hearty muje intayaka yin wankan.
Nan suka shige toilet sukabar Ameer zaune yana shan chocolate yana game.
A tare suka fito kowa d'aure da towel suna dariya nan suka shirya, ido tazuba ma suhail lokacin da yake sa alkyabba, juyowar da zaiyi nan suka had'a ido murmushi yasakar mata yace sweetmee wannan kallo haka ai sai kija infasa fita.
Fari tayi mashi da ido sannan tace duk cikin sonkane hearty, rungumota yayi tare da had'a goshinsu waje guda suna aika ma junansu wani sihirtaccen kallo, muryar Ameer sukaji ya ce daddy kazo kakaini wajen meenal,
Janye zarah yayi daga jikinsa yarik'e hannun Ameer sannan yace baby bari muje sai mundawo.
Duk'awa tayi tace Ameer so kake daddy yatafi yabar mummynka ko? Girgiza kai yayi cikin maganarsa yace a'a mum kibari inmuka yi wasa da meenal zanzo inkaiki wajen granny sultana.
Shafa kansa tayi tare da bashi peck a goshi tace toh shikenan my boy ina jiranka. Shima peck d'in yabata a kumatu sannan tad'ago takalli yarima tace please hearty kar ka dad'e.
Kar kidamu baby zan dawo dawuri, hannu tasa tarufe ma Ameer ido sannan tayi ma yarima kiss a baki.
Murmushi suka sakar ma juna tace adawo lafiya my heartbeat. Allah yasa baby nan tad'aga masu hannu har suka fita.
Take masa baya guards d'insa sukayi nan yasa Ameer a mota yace akaishi gidan shaheed sannan yawuce yagaishe da su memartaba da yake fama da ciwon k'afa bayan sungaisa yaje yagaishe da su ummi da sultana sadiya daga chan yawuce fada.
Wajen k'arfe takwas koda yadawo yatarar da zarah har tayi bacci nan yai shirin baccinsa sannan yahau gadon kallon zarah yayi da tabaje tana ta kwasar bacci ahankali yad'age rigarta yakai hannu yana shafa cikinta daga k'arshe yad'aura kansa saman cikin.
Jin abu samanta yasa tafarka daga baccin da bata dad'e da fara yinsaba, kallon yarima tayi tashafa kansa sannan tace hearty me kakeyi nan?
Murmushi yayi batare da ya d'ago kansaba yace ina gaisawa da baby na ne.
Zaro ido tayi tace wane irin baby? Sai a lokacin yad'ago yakalleta yace Wanda yake manne a cikinki. Karufan asiri ni banda komai.
Murmushi yayi yace taya kike tunani zan k'ara bari kisamu ciki batare da nagane ba, wanchan karen ma dande ban maida kaiba ammah ai naga alamomi kawai jin kai ne yahana intabbatar da hakan.
Ajiyar zuciya tasafke tace toh taya akayi kagane ina da ciki bayan ni kaina bansan da shi ba.
Rungumota yayi jikinsa yace baby ko kin mance ni doctor ne? Insha Allahu nan da wata shidda zaki haifo min wani babyn.
Zaro ido tayi tace nashiga ukku yanzu har ina da ciki wata ukku batare da na saniba?
Jan hancinta yayi yace toh kidai shirya ni d'in kinsan ba ma wasa bane.
Marairaicewa tayi tace toh ammah duka fa Ameer shekararsa ukku.
Toh ai ya ma kwana biyu ai na gama wasa duk bayan shekara biyu zaki dinga haihuwa Insha Allahu k'ara ma kishirya dan mijin nan naki yana da son yara, wlh zarah indai kece bazan damuba dan inaso inga kin haifar min yara kodan susamu irin tarbiyanki, dan halayyarki ce ta kirki tacanza min rayuwa, tabbas na yarda kud'i basu bane rayuwa, rayuwa medad'i itace aginata akan ilimi na addinin musulunci, duk kud'in mutum indai baida ilimi toh bai cika mutum ba yana da tauwaya a rayuwarsa, a kodayaushe ina k'ara gode ma Allah da yamallaka min ke a matsin matata tagari wlh wani lokacin har ji nake kamar ba zan iya rayuwaba in babu ke, zarah kece komai nawa, ina fata zaki cigaba da haifamin yara masu irin tarbiya da hak'urinki wad'anda duniya zatayi alfahari da su.
Rungumesa tayi kamar zata maidasa cikin ciki hawaye suna fita daga idanunta tace nagode sosai mijina Allah yabarmu tare, duk abinda kakeso toh nima shi nakeso dan ka riga ka zama ni nima nazama kai fatana Allah yabarmu tare har k'arshen rayuwarmu, ka gama min komai a rayuwata kaine silar dawowar duk wani farin ciki nawa, a kodayaushe bakina cikin yi maka addu'a nake dan addu'a ce kawai zanyi maka inbiyaka abubuwan da kakemin, kaduba kaga gidan da su mama suke zaune yanzu babba ne sosai kuma kai kamallaka masu, sannan duk wata sai ansafke masu kayan abinci, hatta su yaya rauda baka barsuba kullum cikin kyautata masu kake sannan.......cikin sauri yarima yasa hannu yarufe mata baki yace baby ya isa haka duk abinda nayi ma su abba cancantace tasa haka ko da ace bana aurenki zan iya yi masu fiye da haka, kukan ya isa haka dear indai ba so kike nima inyiba, cikin sauri tagirgiza kai tace a'a kar kayi,,,harshensa yasa yashiga lashe mata hawayen fuskarta bayan ya gama nan yashiga yi mata rad'a a kunne chan sai suka saka dariya gabad'ayansu, turesa zarah tashiga yi tace nak'i wayon naka ni kak'yaleni.
Rik'o hannunta yayi yace please dear kitaimaka min. Tallabo kansa tayi tatura bakinta cikin nasa nan suka shiga kissing d'in juna kowa yana nuna ma d'an uwansa k'warewarsa cikin salon so daga k'arshe yarima suhail yajanyo blanket yarufesu.
_Laifin dad'i k'arewa_
_*Alhamdulillah* anan muka kawo k'arshen wannan novel mesuna *YARIMA SUHAIL* abinda muka fad'a daidai Allah yabamu ladar kurakuren da suke ciki Allah yayafe mana_
_Fatan alkhairi agareku dukkan masoyana naji dad'i kuma nagode ma Allah akan yadda wannan novel d'in yasamu kar6uwa sosai a wajenku_
_Duk wani wanda nata6a 6atamawa ina fata zai yafemin domin duk d'an Adam ajizine tsakanin harshe da hak'ori ma ana sa6awa balle tsakanin mutane, Allah yayafe mana gabad'ayanmu al'ummar musulmai_
_Daga k'arshe ina taya dukkan d'aukacin al'ummar musulmi murna akan wannan wata mai albarka da zamu shiga, ina fata Allah yabamu ikon shiga watan ramadan lafiya sannan yabamu ikon azumtarsa, ya ubangiji kasa muna daga cikin bayinka wad'anda zaka 'yantar a cikin wannan watan me albarka_
_Sis Nerja'art takuce a duk inda kuka kasance masoya,😍👍_
_Comment_ *Nd* _Share_
_Sis Nerja'art✍🏻_