Zaki complete by khadeeja candy - Chapter 13
Zaki complete by khadeeja candy Chapter 13: Zaki complete by khadeeja candy Chapter 13. Ta fada da muryar kuka tana kama hannunsa, a sannan ya jimke…
4,404 words
Ta fada da muryar kuka tana kama hannunsa, a sannan ya jimke hannunsa cikin nata alamar ya hakura kenan ya kai bakinsa ya sumbanci goshinta.
“Wannan ya zama first and last, dan ba zan dauka ba”
“Ba zan sake ba”
Ta fada tana ta kallonsa, sai ya jata jikinsa ya rumgume suka kwanta tare. After like one hour ta dan dago kanta tana kallonsa ta ce.
“Aliyu kana son haihuwa ko? Kana son yara right”
“Yes”
“Amman baka taba nuna min ba”
“Saboda karki damu ne, kuma ga lalurar da kike fama da ita shiyasa ban damu da ki samu cikin ba”
Hannu ta kai ta shafa fuskarsa.
“Zan samu ciki zan saka ka farinciki In-Sha-Allah, zan haihuwa duk inda haihuwa ta kai sai na samo ta, zan kashe ko nawa ne na haihu Aliyu just for you”
Murmushi yai ya sake sumbantarta.
“Allah ya bamu mai albarka”
“Amin”
Ta fada tana kara kankameshi.
“Amman ina son mu koma Abuja, hankali zai fi kwanciya idan muna can”
“Yaushe kike son mu koma?”
“Jibi”
“To ki fara shiri daga yanzu”
“Thank you, i love you”
“I love you too”
Lumshe ido tana sauraren sakwannin da yake aika mata masu zafi.
ATAA POV.
A lokacin da na shiga Bathroom din sai da nai fitsari a bandaki sannan na wanke shi, na fito na gyara bedroom din na fesa turare kamar yadda aka fada min, haka na bi duka dakunan na gyara ko wannen sannan na sauko da kayan mopping din na nufi inda na daukosu na aje.
“Ke je ki cire Hijab din nan karna sake ganinki da shi sai idan fita za ayi, a cikin gidan ki yi ta saka mana Hijab kina watsa mana kora”
Mama Fulani ta fada tana kallon cike da kyama daga can saman dinning da take zaune ita da yaranta suna karyawa, ba musu na nufi garejin na cire hijab dina na saka dankwali a kaina wanda hakan ya bayyana gashin kaina da na yi masa tsoro daya ya sauko har gurin mazaunaina. Da na tashi ban dawo part din Mama Fulani ba sai na wuce part din Ammy da alama ita ce da girkin tsakanin jiya da yau, domin ban same ta a falonta ba sai Anty Zee tace min Ammy tana part din Abbah amman ga abincin nan ta aje min, farfesun kaza ne a wani karamin plate sai wainar kwai da dankwalin turawa a plate daya da kuma katon burodi, da tea a wani babban kofi, duka an hade su a tray daya. Daukar tray nai zan fita sai Anty Batulu da ke murzawa fuskarta wani farin mai mai kamar sabulu ta ce.
“Ina za ki je?”
“Waje zan je na zauna na ci?”
“Zauna a nan ki ci?”
“Ammy ba zatai fada ba idan na ci a nan? ”
Sai duk suka saka min dariya.
“Hala Mama Fulani ta miki fada da kika zauna a falonta?”
Anty Zee ta tambaya sai nai kasa da kaina ban ce komai ba.
“Ammy ba ruwanta, idan ma muka saba sai ta fi son ki da mu,ba kamar wacan bakar matar ta ke ba”
Anty Zee ta fada sai Anty Batulu ta kalleta.
“Anty Zainab Ammy ta ce ki daina cewa haka”
“Ke na fada tashi kije ki Fadawa Ammy ki ce na ce Mama Fulani mai bakin hali, munafuka kawai”
Tana fadar hakan ta tashi ta nufi upstairs tana jan tsaki. jin hakan yasa na zauna a kasa na soma cin abincin hankalina a kwance har na ci na koshi, rabon da na ci abinci da naman kazan tun asibiti lokacin da Doc yake siya mana na restaurant, duk sai na ji babu dadi ina ma ace Nana na kusa da ni da na bata naman ta ci, sam bana son na ci wani abu mai dadi ba tare da Nana ba, hakan yasa na yanke shawara na shanya naman idan ya bushe sai na tarawa Nana idan naje sai na sake dafa mata shi ta ci.
“Anty Batulu zan iya shayawa idan na koshi”
“Eh to sai idan Garden za ki shanya shi, inda kowa ba zai gani ba”
Tana bani amsar na tashi tare da ragowar naman na koma gareji na dauko wani dankwalina na nufi garden din na shimfida daga inda rana take haskawa na baza naman sannan na dawo part din na gyara ko'ina kamar yadda nai a part din Mama Fulani. Bayan na gama gyaran Ammy ta shigo part din jin kamshi na tashi yasa ta murmushi tana ta yaba min.
“Kai haka na ke son yarinya da kuzari kazar kazar da ke, ai to za mu shirya kuwa idan kina son aiki ba kamar yaran gidan nan ba, manya da su amman sai dai a gyara suna zaune”
“Ai daman Anty Zainab ta fada cewar nan da kwana biyu sai kin fi son ta da mu”
Anty Batulu ta fada tana dariya, ni ma nai murmushi sai Ammy ta nufi upstairs tana fadin.
“Eh mana to me ake da mu”
Bata dauki lokaci ba ta fito rike da tufafi kusan kala biyar ta miko min.
“Ungo idan kin yi wanka sai ki canja naga jikinki sun dan tsufa”
Cikin wata irin murna da jindadi na saka hannu biyu na karbi tufafin ina godiya.
“Allah ya saka da alheri na gode sosai”
“Ba komai”
Cike da jindadi na nufi garejin dan ajewa, kasa hakuri nai har sai na yi wanka na saka sai na soma gwadawa ina ta jujjuyawa rabon da wani yai min kyautar tufafi har na manta, kana ganinsu ka san masu tsada ne, na san ba zai wuce na Inteesar ba, domin ita ce kamar ni ganin yadda tufafin suka min cif kamar daman can nawa ne. Sam na manta da zancen gyarawa Ya Muhseen part dinsa har sai da na koma Part din Mama Fulani sai ta rufe ni da fada tana ta zagina kamar wacce bata san inda na fito ba.
“Gidan uban wa kika je kika zauna? Ba na ce ki je ki gyarawa Muhseen part dinsa ba? Shine dan kin maida ni shashasha kika tafiyarki ko? Zo nan”
A tsawa ce take min fada kamin ta ce na zo, ni kuma duk tsoro ya kamani jikina nata rawa kamar nazari idona har ya fara hawaye, domin na fahimcin kiran da take min dukana za tai.
“Aa ni nace ta bari sai gobe”
Ya Muhseen ya fada yana kashe min ido daya, kasancewar duka yan 'uwansa basa nan daga ita sai shi ne a dinning din.
“Ko?”
Sai na gyada kai.
“Eh haka ne, shi yace na bari sai gobe”
“Yaushe ka ce mata haka?”
“Dazu, dauki ga abincin ki can”
Ya karasa yana nuna min kasa kusa da Mama Fulani. Sai na kasa zuwa na dauka ina ta jin tsoro shi kanshi ya lura da hakan.
“Mama gaskiya tsoron ki take”
“Tsorona dodo ce ni?”
Ta daka min tsawa. Sai na amsa mata da sauri ina girgiza kai.
“Aa”
Ya Muhseen ya tashi ya nufi inda abincin yake ya dauko ya miko min yana dariya tare da fadin.
“Ko ni da kika haifa a tsoronki na ke balle kuma ita”
“Aa ni ban haife ka ba, dana ya can sokoto Aliyu dan albarka”
Mama Fulani ta fada tana mikewa tsaye daga dinning din. Sai Ya Muhseen ya saka dariya
“Kowa ya ganshi ai yaga danki halinku daya Mama, har ya fiki rashin tausayi”
“Kanka ake ji”
Ta fada tana tabe baki sannan ta nufi kitchen, shi kuma ya miko min abinci ina karba tana fitowa daga kitchen din tana fadin
“Idan kin ci abinci ki aje wannan plate din da cup din a gurinki, da shi za a rika saka miki abinci”
“To”
Sannan na juya na fita, tea a cup din sai wainar kwai da dankalin turawa a plate din da burado kadan, ban ci komai ba kasancewar na riga na ci na bangaren Ammy na koshi, sai kawai na aje a garejin na kwanta a saman tabarma ina ta tunanin Nana, ko a wane hali take yanzu oho, gashi ba ni da waya balle na kira ta ji muryarta. After like one hour har bachi ya fara daukata na ji an taba garajen ina dagowa sai na ga Ya Muhseen cikin shiga ta kananan kaya ya dora rigar likitoci a sama, kayan sun karbe shi sosai ga fuskarsa da far'a yana aiko min da murmushi, ni ma murmushin nai masa kadan na tashi zaune.
“Zo ki bude min gate”
“Ba akwai mai gadi ba?”
“Ke nake son ki bude min”
Na tashi kamar yadda ya bukata ina gyara daurin dankwalina na fito daga garejin na nufi gate din, sai da na wuce gate biyu sannan na iso a babban gate din nai ma mai gadin magana ya nuna min yadda ake budewa na bude sannan na hango shi ya taso motar ya nufo inda nake tsaye da gudu kamar mai shirin kade ni, ni ko na ratse gefe na rufe ido ina jiran ya kade ni sai kawai na ji ya saka min ya jefeni da chocolate. Murmushi nai na duka na dauki chocolate din ina kallonsa.
“Sarkin tsoro, daman saboda na gwadaki nai kuma na ga gashin nan na ki”
Ya fada sannan yai gaba abunsa, ni da mai gadin muka bi shi da kallon mamaki, ni dai ina jin son barkwancinsa da yadda yake da son wasa da ni. Mai gadin ya riko dayan gate din ni kuma na riko dayan za mu rufe na ji an ce.
“Ke”
Juyowa nai sai na hango wani fari saraurayi tsaye jikin wani katon gate da ke facing din na su Mama Fulani yana sanye da uniform din sojoji. Ba musu na saki gate din na nufi inda yake tsaye cikin mugun tsoro domin Allah ya zuba min tsoron soja fiye da dan sanda.
“Ina wuni”
“Ina kwana dai”
Ya gyara min yana murmushi.
“A can gidan kike?”
“Eh"
“Gurin wa kika so?”
“Aiki na ke a gidan”
“Aiki?”
Ya maimaita, yana kallona kasa da sama.
“Wa kike yi ma aiki? Mama Fulani ko Ammy?”
“Dukansu”
Na amsa muryata na gargada.
“Ki daina jin tsoro ba wani abun zan miki ba. Ya sunanki?”
“Aisha”
“Ashe mamana ce ke, kina da kyau Aisha ke fulani ce?”
“Aa buzuwa ce”
“Shiyasa kike da kyau sosai ga gashi, an taba fada miki kina da kyau?”
Na shiru ina yin kasa da kaina sai yai dariya.
“Kar ki ce ban saba ganin kyawawa ba, na saba ganinsu ni ma ai kin ga na fiki kyau ko?”
Na dan dago na kalleshi sai ya shafa kansa yana dariya.
“Sunana Kamal Isma'il Isa, nan ne gidan mu kuma ni soja ne, idan kikai wani abu sai na kama ki, dan haka ki yi hankali”
Ya fada yana fiddo yar karamar bindigasa ya nuna ni da ita, aiko ba shiri na ranta cikin na kare cikin wani irin gudu da ban taba sanin ina da shi ba na zarce cikin gida, ina waigensa ya biyoni yana ta dariya.
*Littafin nan na kudi ne* *Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660* 19.
Nasir ya fada masa a unguwar da ak fada masa ya sa an bincika amman ko fulani ba a samu a unguwarba balle wasu buzaye, zancen wani ja gini duk karya ce. Jin wannan yasa Aliyu ya zabi ya cire nemanta da kokari fahimtar da ita idan ya ganta a ransa, tun da be san inda take ba, and gashi garin nemata har suna kokari mom samun matsala da Rahma, and idan ma yace dole sai ya nemota ya ai wani sabon aikine a gareshi, but he know one thing for sure tunanin zalincin da akai ma yarinyar nan ba zai taba fita a zuciyarsa ba, kyauta kuma ba zai taba gushewa a idonsa ba.
He keep himself busy these days saboda shirye shiryen da suke na zuwa Abuja ya san akwai aikin kamfaninsa yana jiransa, kamar yadda ya saba and Rahma ta masa complain cewar tana on ganin likita idan sun koma Abuja saboda matsalar haihuwarta. Da kanshi ya dauke ta suka je sukai Momynsa da Daddynsa sallama sannan naje gidansu Rahma suma sukai musu bankwana, domin tafiyarsu gobe ne. Farinciki gurin Rahma ba a magana tana ganin da zarar sun koma Abuja komai na damuwarta ya wuce, sun bar garin da Ataa take hakan zai saka hankalinta ya kwanta gashi kuma ta jin cewar idan ta je ga babban Likita kamar Doc Perry matsalar haihuwarta zata gushe, duk da acan din ma tana fargabar Mama Fulani saboda zancen haihuwa da take mata gashi kamar bata san Allah ne yake komai ba.
ATAA POV.
Ina ta gudu yana biye da ni a baya har na nufi garejin na boya sai kuma na wuce falon Mama Fulani a tunani ba zai iya biyo ni ya shigo ba, amman ga mamaki na sai ya biyoni har cikin Falon, mamaki ya hana ni cewa komai sai bin sada nai da iso, shi kuma yana ta murmushi kamar daman can mun saba irin wannan wasan da shi, zaunawa yai saman sofa yana maida bindigarsa aljihu.
“Ba ruwana idan suka zo suka maka fada”
“Ba za su min ba, sai dai ke su yi miki ke da kika kawo ni”
Ban sake wata maganar ba, gabana sai faduwa yake gudun kar Mama Fulani ta fito ta ganshi, gashi ban san mi zan ce mata ba, ban gama tunanin abunda zan yi ba sai ga Mama Fulani ta fito daga dakinta sanye da doguwar riga da alama wanka tai ta canja tufafi. A take hantar cikina ta kada tsoro duk ya bi ya cika min ciki, tana sauko ya mike tsaye a mamakina sai ganin nai ta sakar masa fuska tana masa murmushi.
“Kamal ne?”
“Ni ne Mama ya gida?”
“To ba dai Aliyu ya zo ba balle na ce, na san sai idan yana nan kake shigowa gidan nan”
Murmushi yai ya shafa kansa.
“Kawai dai yau na ce bari na zo na gaishe ki”
“Ato ka kyauta gaskiya, ka yi abun kai, ina Hajiya Uwani?”
“Tana nan lafiya kalau”
“Ke shiga kitchen ki dauko masa cup ki bude freezer ki dauko masa lemu”
Mama Fulani ta fada min, sai na juya da sauri na nufi kitchen din, ina shiga na duba inda kofuna suke na dauko tare da lemun na dawo falon na kawo a gabansa na dire.
“Mama ina kuka samu wannan mai aikin?”
“Wallahi wata wacce ta saba kawo mana mai aiki ta kawo ta mana ita”
“Okay ni kan na ce ban san da zamanta a gidan nan ba”
“Bata dade da zuwa ba”
“Okay”
Ya fada yana mikewa tsaye ba tare daya sha lemun ba yai mata sallama ya fice yana ta kallona kamar zai yi magana sai kuma be ce komai ba har ya fice.
“Zo ki dauki kayan nan ki maida su kitchen”
Mama Fulani ta fada tana daure fuska. Kamar daman umarni na ke jira sai na nufi lemun na dauka na kai kitchen na aje sannan na fito na dawo falon na zauna inda na sabawa kaina da zama na kurawa tv ido. Misalin sha biyu na rana da yan mintuna Mama fulani ta fito ta shiga kitchen ta dora abincin rana, guraren karfe biyu ta kammala abincin sannan ta fada min na dauko plate dina ta zuba min abinci a ciki, sai na tashi da sauri na nufi garejin na dauko abincin safe da ban ci ba na nufi garden na siyayarda tea Wainar kuma na cinye, daman ni ba soyayiyar dankali bane dan haka na shanya shi a inda na sanya ragowar kazar nan ta dazun. Sannan na kunna fanfo na wanke plate din na dawo part dinta na kawo mata.
“Aje kasa”
Sai na risina na aje da alama kyamata take da har ba zata iya rika plate din ba, debo abincin tai ta zuba min a plate sannan ta zuba min miyar bata saka min naman da ke miyar ba ta ce na dauka, ni kuma na dauka da sauri na fito balcony na zauna ina cin abincin a hankali. Ina daf da cinyewa Ya Muhseen ya shigo gidan da motarsa, inda manyan motoci suke yai parking sannan ya bude motar ya fito yana matsa remote din motar tana kara.
“Pretty nan kike cin abinci?”
“Eh sannu da zuwa”
“Yauwa”
Ya fada sannan ya shiga part din Mama Fulani be dade ba ya fito ya nufi wani bangare na gidan inda nake saka ran a can dakinsa yake, sai da na gama cin abincin na je na wanke plate din na maida shi gareji na aje sai na kwanta a gurin, ina ta tunanin yadda zan iya da zaman gidan, anya zan iya juye wulakanci irin na Mama Fulani? Amman ya zan yi tun da na riga na zo, Sai da la'asar na fito daga garejin nai alwala na koma nai sallah sai na nufi part din Ammy, tambayar ta nake son yi domin ita ce mai far'a da son mutane ba kamar Mama Fulani ba. Da sallama na shiga sai ta amsa min tana zaune kasa tana cin abincin.
“Tun dazu na ke nemanki ba ki shigo ba”
“Je kitchen ki dauko tuwon ki ga shi can kina cin tuwo da rana dai ko?”
“Eh ina ci”
Na gyada mata kai sannan na nufi kitchen din, sai na samu tuwon shimkafa da miyar yauki a rufe cikin wani plate an saka min har da man shanu, ga wasu manyan tsokoki a sama. Daukowa nai na fito sai na koma can kusa da kofar shigowa falon na zauna na soma ci, ba wani da yawa zan bi ba ni kaina na san cikina ya cika da shimkafar da Mama Fulani ta bani amman ina son tuwo sosai ga kuma manshanun da aka saka a sama da namomi ba zan iya barinsu ba. Ina cikin cin abincin wayar Ammy tai kara alamar kiranta akai, picking tai ta kara a kunne ban san mi aka ce mata ba na ji dai ta yi amsa da okay, sannan ta kalleni.
“Mamana kin iya zuba tuwo?”
“Eh na iya”
“To shiga kitchen ki samu plate ki bude fula gata can dinning ki zubawa Muhseen ki rufe sai kije ki kai masa kin ji”
Sude hannun na yi na tashi na nufi kitchen da kuzarina na dauko plate din sannan na dawo dinning na zuba nasa miya a wani plate din sannan na saka tuwon a dayan plate din na rufe na dauka na nufi part din Mama Fulani, Ya Muhseen kadai na samu a falon yana shan kankana da fork, ganina yasa shi murmushi ya mika hannu biyu ya karbi abincin.
“Yauwa thank you, ke kin ci abincin ki?”
“Shi na ke ci ka karani”
“To dauko ki zo nan ki karasa”
“Zan fi jindadi ci a can”
“Saboda Mama tana miki fada a nan ko?”
Ya fada yana bude tuwon.
“Kin ga kin fini cin abinci yanzu na ganki kina cin shimkafa yanzu kuma kina cin tuwo”
Murmushi nai har na soma jin kunya na baibayeni.
“Dauko min ruwa”
Na nufi kitchen din an bude freezer na dauko gorar ruwa da cup na kawo masa. Kamar daga sama na ji muryar Mama Fulani tana masa fada.
“Wai Muhseen baka kyamar yarinyar nan ne? Ka cika shige mata fa bana sin haka”
“Miye a jikinta?”
Banza tai masa tana jin haushin tambayar da yai mata, sai gyara tsayuwar jikar da ke hannunta take da alama fita za tai. Ni dai ban ce komai ba ina tsaye ina jin umarninsa ko zai sake bukatar wani abun ne, ban ji ya ce komai ba hakan yasa na fice na barsu ita da danta na koma part din Ammy. Da sallama na shiga kamar dazun, wannan karon kishingide na sameta tana kallo tv.
“Mamana amman ku fulani ne ko?”
Ta fada tana kallona.
“Aa ni buzuwa ce”
“Wane gari kike?”
“Sokoto”
“Tare da iyayenki kike zaune?”
“Babana ya rasu mama ce kawai”
“Allah sarki, ita ta turo ki aiki a nan kenan? Ina kika san Maman Salma ko yar'uwarku ce?”
“Aa ba mu da alaka da ita zaman unguwa ne kawai”
“Allah sarki, amman kina da kanen ko? Ke ce ta nawa gidanku?”
“Ni ce ta farko ina da kane amman ya rasu”
“Ayyah Allah ya jikanshi”
“Amin”
Daga nan bata sake magana ba har na gama cin abincin na tashi na maida plate din na wanke hannuna na dawo na zauna. Gefen kujerar muka cigaba da kallon a tare, sai ga Ya Muhseen ya shigo rike da plates bakinsa kunshe da nama ya miko min plates din.
“Kai kitchen”
Na karba da hannu biyu na nufi kitchen din na aje. Ban san abunda ya fadawa Ammy ba kallona kawai take tana dariya. Kamar yadda shi ma yake dariyar har na soma tsaguwa, ma tashi na bar musu falon na dawo gareji na zauna ina turo baki kamar an min wani abu. Tun da na dawo ban koma fita ba sai da magariba, shi ma sai da na sauke farilla sannan na fito harabar gidan na zauna ina ta kallon fitilun da suka haska gidan gwanin sha'awa. Ban tashi daga gurin ba sai da aka kira isha'i sannan na nufi garden da tsoro nai alwala na dawo garejin nai sallah ta sai na kwanta a gurin ina ta jin tsoron da ban san ta ina yake fito min ba, kamar jiya ba ni kadai na kwana ba, yau kan tsoro ya kamani sosai ko iska ya kada sai na ji kamar wani aljanine zai kama ni, da naji na kasa natsuwa da gurin ne na taso na koma Part din Ammy na zauna, ina ta kallon Anty Zee Inteesar da ke cin abinci a plate daya.
“Shiga kitchen ki dauko na ki”
Inteesar da fada min, ni kuma na tashi na shiga kitchen din a inda na samu abincin dazu nan aka sake aje min wani yanzu ma tuwo ne kamar dazun sai dai wannan miyar ganye ce ba kamar dazunda taie miyar yauki ba. Dauko abincin nai na fito waje falon na zauna na ci sai da na koshi sannan na tashi na maida plate din na wanke hannuna.
Haka rayuwata ta cigaba da tafiya a gidan kullum Mama Fulani da Yayanta cikin nuna min kyama suke, a gurin Ya Muhseen kawai na ke samun sakewa har dadi nake ji idan yana nan, tun ina kin sakewa da shi har na soma sakewa kwanan biyu da nai a gidan sai na ji kamar daman can na basa da gidan, sai na fara sabawa da halin Mama Fulani da kuma Ammy da bata nuna min kyama, sai dai abu daya ke damuna kwana a gareji da kuma wanka idan zan yi sai naje garden na boya a bayan itace sannan nai wanka, da sabulun da Ammy ta ba ni, idan kuma ba haya zan yi sai dai na raba a dakin mai gadin na shiga nai.
Yau ma na yi aikina kamar yadda na saba, bayan na gama da bangaren Mama Fulani na je sashen Ammy nai mata nata sannan na shiga bangaren Ya Muhseen shi ma na gyara masa nasan dakin da falon na goge komai kamar yadda na fara yi masa a jiya na fito na dawo bangaren Mama Fulani, kowa na falon kasancewar Weekend ne Ya Muhseen da Anty Maryam na zaune a kujera daya tana nunawa Ya Muhseen wani abu a wayarta, Mama Fulani kuma na zaune kasa tana mulka fulawa, sama sama nake jin tana firar dan ta nan tafe dole ta dafa masa abunda ya ke so, sai da ta gama mulka fulawar sannan ta kalleni.
“Ke je kitchen ki yanka min kabeji, yana nan a roba”
Na amsa da to ina mikewa tsaye na nufi kitchen din, yana jiyo lokacin da Ya Muhseen ke fadar cewar ina da gashi, har Mama fulani na masa fada wai yana ta abu kamar be tana ganin kyakkyawar mace ba. Karamar kujera na samu na zauna na dauko daya daga cikin wukaken da suke hade guri daya na soma yanka kabejin, ban ankara ba na yanke kaina sai jini, ban san lokacin da na kwala wani uban ihu ba na mike tsaye da sauri jikina nata rawa abun ka da mao tsoro ga shi ban saba da amfani da wuka sosai ba, rabon da naji ciwo har jini ya fito haka har na manta. Cikin sauri Ya Muhseen ya shigo kitchen din.
“Daman na san yankewa kikai”
Ya fada yana kallon yadda jinin ya samu hanya sai bulbulowa yake, ni ko ina ta kuka kamar hannun ya cire gaba daya, wanda hakan yasa Anty Maryam shigowa kitchen din tana tambayar ba'asi. Wani dogon tsaki taja ganin ganin a yatsa ne kawai na yanke amman nake wannan ihun. Hannun nawa Ya Muhseen ya riko muka fito daga kitchen din ina ta kuka sosai muka nufi kofar fita jinin nata zuba. Bangarensa yaje da ni ya dauko wani dan karamin akwati ya bude ya saka ruwan nan masu shegen zafi ya goge min gurin ya saka min wani maganin sannan ya saka min kada ya rufe min yatsan.
“Sarkin raki”
Ya fada yana kallon yadda hawaye suka bata min fuska, na turo baki waje kamar yadda yara suke idan sun ji ciwo.
“Kadan ne fa kika ji ciwon amman kin cika mana gida da ihu ke sagartacciya ko?”
Na yi kasa ta kaina ina kallon yadda yake aiko min da murmushi.
“Shikenan zaki iya tafiya”
Ina juyowa shi ma ya tashi tsaye muka fito tare, ina gaba yana bayana har muka shiga part din Mama Fulani.
“Muhseen karka sake shiga safgar yarinyar nan”
“Mi akai?”
“Na dai fada maka? Ba ita ba kai daga yau, ke kuma dauko Mopper ki goge jinin nan”
Ta karasa tana kallona, sai na nufi inda mopper take na dauko na goge duk inda jinin ya diga sannan na koma kitchen din, zan cigaba da yanka Anty Maryam ta shigo wai na zubar da wannan kabejin basa son sa na yanka wani sabo. A kwandon shara na zuba kabejin na dauko wani a freezer dake kwance na soma yankawa, a hankali nake har na gama sannan na aje mata shi na fito na nufi part din Ammy. A lokacin da na shiga falon ita kuma tana kitchen tana hada fruits salad, a falon nai zamana har aka yi azahar sannan ta fito ta miko min plate da spoon.
“Ga abincin ki”