Kenza eBookz

A d u n i y a ta complt by huguma - Chapter 18

A d u n i y a ta complt by huguma - Chapter 18

A d u n i y a ta complt by huguma Chapter 18: A d u n i y a ta complt by huguma Chapter 18. "To" Kawai ya iya cewa da ita,ya sani basai an gaya masa…

4,471 words

"To" Kawai ya iya cewa da ita,ya sani basai an gaya masa ba,maamah din tayi nisan da batajin kira,hakanan dukkan wani bayani da zaice zaiyi mata yana zaman bata lokaci ne kawai a wajenta.

"Yanzu bayan kamfanin diamond ai ina sanya ran zuwa yanzu addu'ata ta cicciba Muhammad izuwa mallakar wasu boyayyun mafanunnukan ko?" Ta fada tana murmushi tare da tsare musaddiq da kallo.

Dubanta yayi sosai,yana ji har cikin zuciyarsa da gangar jikinsa bai gamsu xa yanayin tambayar tata ba,don haka girgiza mata kai kawai yayi

"Bansan komai a kanshi ba maamah tunda ba sashe daya muke dashi ba" Wani abu ne ya tsaya mata a wuya,amma sai tayi qarfin halin danneshi ta amsa masa da

"Haka ne......amma dai baka ce bakasan qarfi da nauyin kudaden da suke shigo masa ba ko?" Sake daga kai yayi yana dubanta zarginsa yana sake tabbata

"Bana ce ba maamah.....abune da ya shafi sirrinsa kuma ba a qarqashinsa nake aiki ba.....ni ina qarqashin farouq"

"Eh to.....maganar gaskiya sai yanzu na fahimci kimiyyar da ta sanya amina tayi kutin kutin din cusa danta wa Muhammed kai kuma ta rabaka dashi.....kana jininsa wanda bashi da na biyunsa a duniya amma bakasan komai nasa ba?.....wanda ni nayi imanin a yanzun inda zan zaunar da shi saddiqun nayi masa ire iren tambayoyin da nayi maka din yana da amsar kowacce fes?.....wannan itace hanya mafi sauqi da zata samu salwantar da fu'ad da dukka abinda ma ya mallaka". Idanunsa ya runtse yana jin zafin mummunan zaton da maamah din ke jifar 'yar tahalikar dashi.....matar data zame musu bango majingina,matar data zabi farincikinsu akan nata.....matar da silarta ne a yau suka zama dukkan abinda suka zama din.....suka kawo izuwa matakin da suke kai a yanzu......matar da banda ita da yanzu shi da muhammad din duka da take taqama dashi ba'asan a wacce shiyya nahiya ko yanayi suke ba.

"Maamah..." Ya fada yana bude idanunsa a kanta ba tare da ya shirya tsaida maganarta ba.

"Duk yadda kike tunanin anni fa ba haka take ba.....idan baki godewa anni ba bai cancanci ki jefeta da mugayen zato ba......kamfanin nan da rayukanki suke baci akai asalin diamond din da aka samu ba hamma bane kawai ya sameshi ba.....a lokacin suna tare da BB farouq......"

"Amma shi ya haqo shi kuma ya samu nasarar tsira dashi.......ka dauka bansan dukka wannan ba?" Tayi maganar tana tsareshi da idanunta da suka cika da bacin rai. Lallai sai sun nuna mata fifikon matar can akanta?,bayan bata da masaniya akan sanda ta dauki cikinsu bare kuma haihuwarsu?.

"Eh hakane.....amma shi BB farouq baida sha'awar harkar diamond noma yafi so shi yasa......"

".......shi yasa aka fidda haqqinsa aka bashi nasa kason......dukiya ta zama ta muhammad sh kadai......amma duk da haka basu qyaleshi yana amfana da abarsa shi kadai ba.....saboda nasa kason da nasa bangaren na haqar ma'adanai yafi noma albarka da kawo samu,shi yasa suka tattare shi suka kuma dora masa dukan lalurarsu suna zuqeshi sannu a hankali.....suka kuma nesantaka dashi.....suka haramta maka sanin komai daya shafeshi ta cusa danta" Ta qarashe maganar da wani irin ciwo da emotiona daga zuciyarta

"Maamah....." Ya kira sunanta yana son dakatar da ita. Baya qaunar ko kadan wadannan kalaman marasa dadin sauraro suna fita daga bakinta zuwa kawunan mutanen da suka yiwa rayuwarsu tsaiwar da babu wani mahaluki daya taba yinta

"Ni na zabi fannin noma da kayan abinci......basu suka sani ba....ba wanda ya bani shawara....."

"Musaddiq!.....ina fada kana fada duk akan mutanen can?,to waishin ko zaka koma cikin aminatu ta sake haifarka a matsayin danta bani mariya ba?". Maganar yaji tayi tsauri da yawa,kuma ya sani uwa uwa ce komai lalacewarta,hakanan ba'a canzawa tuwo suna,don haka ya miqe tsam,don dama a qagare yake da wannan zaman da baiga ma'anarsa ko alfanunsa ba. Ya dauka zasuyi hira ne irin ta d'a da uwa?,ya dauke zata tambayeshi bayan ta barsu yaya suka rayu?,ya dauka zata nuna nadaman barinsu da tayi sun basu gama zama mutane ba?,sai gashi gaba daya hasashenta da hangenta ba'a nan yake ba?,da gaske ne abinda zuciyarsa take raya masa ta biyo DAUKAKARSU DA DUKIYARSU NE?.

"Allah ya baki haquri ya huci zuciyarki,sai da safe.....na barki lafiya" Ya fada yana juyawa a hankali yana fita daga falon zuwa farfajiyar gidan.

Da kallon takaici ta bishi,shi kansa me sukuni da wadata ne wanda zai iya kashe mata ko nawa take buqata ballanta a gangaro kan muhammad,mahaukatan kudade ke shigo musu daga harkar noma kayan abinci da sauran kayan masarufi da sukeyi,kuma su rabasu cikin qasashen Africa dama qasashen qetare. Tana da dukka information daidai gwargwado a kansu.....amma sai gashi wadatar kowannensu yanason zame mata hoto.

Yadda ranta yake a bace sai zama ya gagareta,takai ta kawo kusan sau uku tana ji har cikin zuciyarta ya dace ta gaggauta daukan mataki,ya kamata tayi wani abu akai kada komai yaci gaba da tafiya a haka. Daidai sanda takai dab da qofar taji horn na mota da kuma shigowarta farfajiyar gidan,bata bi takai ba amma zuciyarta tana mamakin baqon daren da sukayi.

Mintina uku kawai tayi sallama cikin falon. Sallamar data sanya maamah din waiwayowa tana amsa mata fuskarta babu walwala.

Sanye take cikin wani lafiyayyen lace ruwan zuma. Kallo daya tak zakasan cewa ba na qananun mata bane,ba kuma qananun kudi aka sanya aka mallakeshi ba haka dinkin boubou din da aka zuba masan. Zagayayyen dauri ne saman kanta da zai gwada maka adadin wayewarta da kuma zurfinta a sanin data yiwa duniya. Mayafinta na yafe a kafada daya,daga hannayenta har zuwa wuyanta adon sarqa zobe da bangles ne da babu ko tantama da shakka na gold dinne. Ita din idan ka kalleta baifi ka bata shekaru arba'in da biyar ba,saidai kuma ta dara hakan,don a yansu tana dosar cika shekaru sittin ne a duniya.

Daga bayanta wata macece wadda duka ba zata haura shekara arba'in ba. Riqe da wata kyakkyawar handbag wadda babu ko tantama jakar matar dake gaba ne saboda dacewa matuqa da tayi da kayan jikinta.

Maimaita sallamar tayi a karo na biyu tana duban maamah fuskarta a sake. Wannan ya sanya maamah din tayi qoqarin sakin tata fuskar gami da sakaya damuwarta a gefe,cikin mamaki da tarba me kyau ta matsa gareta tana tararta

"Hajiya......isowar yaushe?" Ta tambayeta tana murmushi

"Tun shekaran jiya fa?,gajiya nayi ma na gudo,amma ason dan ahalan sai farkon sabon wata zamu dawo" Ta furta tana neman wajen zama.

Zaman itama tayi a kujerar dake fuskantar tata

"Da kyau.....ai ya kyauta wallahi,ko yanzu aikin huta ko?"

"Yadda ya kamata kuwa.....wai nikam musaddiq nake gani yana fita sanda nake shigowa da mota?". Dan tabe baki kadan maamah din tayi sannan ta amsa cikin salon rashin bawa maganar muhimmanci

"Shine mana"

"Hala bai ganeni ba,don baiyimin magana ba"

"Ko ya ganekin ma babu lallai ya miki magana ai harira" Ta amsa mata boyayyar damuwar fuskarta tana bayyanar da kanta.

Kallon tsanaki hajiyar mamallakiyar sunan harira ta yiwa maamah kafin tace

"Ban gane me kike fada ba mariya" Qarasa bawa sauran boyayyar damuwarta qofa tayi ta fallasa kanta,don tambayar sa harira tayi mata ta zama tamkar susa ce tayi mata akan ciwonta

"Ina da damuwa harira.....ina da damuwar da har kwanan gobe na gaza gano maganinta".

A nutse hajja harira ta waiwaya ta dubi 'yar aikinta,wadda ke tsaye daga gefe,tunda suka shigo taketa faman gaida maamah din amma bata ma jita ba bare ta amsa

" Ajiyemin jakar ki fita daga waje ki jirani" Ta fadi mata. A ladabce ta ajiye jakar sannan ta juya da hanzari tana ficewa,abinda ya bawa hajja harira damar maido hankalinta ga maamah

"Nayi tunanin kawo yanzu kinyi nisa daga dukkan wani abu me suna damuwa daga randa dan cikinki ya zama mamallakin kamfanin diamondchore?"

"Daga sannan sabuwar damuwa ta fara hajja harira" Maamah din ta furta ranta yana matuqar quna

"Idan na kalli yadda kike fantamawa hajja sai na sake tabbatarwa kaina lallai akwai aiki a gabana......aikin kuwa shine YADDA ZAN MALLAKE 'YA'YANA". Wani irin duba hajja hariran take mata,sai kuma ta kyabe baki

"Keda wanne baccin kikeyi da baki aikata hakan ba mariya?,wanne gangancin ya kaiki?,bakisan daga ranar da Allah ya yiwa 'ya'yanki arziqi ba.....akwai tarin mutane da dama da suke marmarin juye matsayinki su haye kai ba?.......kin ganni nan mariya?,kaf 'ya'yana babu wanda ya isa ya aiwatar da wani abu komai girmansa kuma komai qanqantarsa ba tare da sanina ko yardara ko sahalewata ba.....ke koda matansu ko 'ya'yansu zasu yiwa kuwa sai da sanina da yardaya,a cikinsu babu wani gida da bansan me yake gudana a cikinsa ba 24hrs......yanzu haka katafaren gini na sanya sukeyi na bai daya duka zamu zamana a muhalli guda....." Kai kawai maamh ke gyadawa,a yau ta yarda ta miqa wuya ta kumayi surrender kan cewa harira ta fita shu'umanci,iya yadda tae bada.labarin cike da izza da alfahari kawai ya isa gaya maka gaskiyar haqiqanin zahirin abinda ke faruwa kenan......jikinta ya isa ya sake qarfafa maka zancanta.....tsanin alfahari da takeyi yayin bada labarin kuma zai gaya maka yadda take jin dadin yadda take tafi da rayuwarta. *D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

PAGE 48

"Inaso na zama uwa mafi gata a duniya harira,inason na zama uwa mafi izza akan yaranta......inason na zama uwa mafi zama abar alfahari abar nunawa a duniya....inason 'ya'yana su dawo qarqashina.....na mulkesu kaman yadda ubangida yake mulkar bawansa......su zamana a tafin hannuna kamar yadda jariri sabuwar haihuwa yake zama a hannun mahaifiyarsa".

Wani murmushi hajja harira ta saki tana duban maamah

"Lallai mariya burinki me girma ne......amma dai kinsan ki baro kari tun ran tubani ko?,ko mu da muka raini yaran har suka girma muka aurar dasu,bamu gusa ko nan da can ba muna gabansu suna gabanmu sabunta ayyukanmu mukeyi akai akai.......munayi matansu sunayi,wanda keda nasara shike samun rinjaye.....ballantana ke,yaranki ina da tabbacin suna buqatar gagarumin aiki kafin samun saituwarsu akan bigiren da kikeso".

"Abinda ya wuce ya wuce hajja harira.....yanzu meye abinyi?" Gyara zamanta tayi sosai tana bawa maamah dukkan hankali da nutsuwarta

"Akwai plans guda biyu,plan A da plan B......idan A baiyi aiki ba zamu wuce zuwa na biyu"

"Kamar?" Ta tambayeta cikin matsuwa da jin bayanin komai

"Yauwa......na farko akwai wajen mutumina da zan kaiki wanda shi yakemin aiki akan komai da kowa......"

"Kai....kai.....amma kin gama min komai" Maamah ta fada tana gyara zamanta da kyau fuskarta na washewa da madaukakiyar fara'a,saboda ta hangi zuwan nasararta a nan kurkusa......ta hangeta tana fantamawa fiye da yadda hajja harira ke fantamawa din.

"Ba komai fa.....zaman tare ai ba qarya bane....zaki zayyane masa dukkan abinda kike da buqata wanda nake da imani a kansa mallaka sai yadda kika juyasu.....akan mansur ya fara yimin aiki,lokacin da yayi aure sai na fuskanci wani abu,maganata qasa take da maganar matarsa,dukkan umarni da zabi nata ne sai abinda taga dama sai kuma abinda tace.....a sannan na farga,amma in gaya miki inayi yarinyar nan tana nata har daga qarshe na hadu da DAN DUMA....tuni na saka ya qara mata wuta a gidan,mansur ya saketa tayi gaba,tun daga ranar dukkan wanda zaiyi aure a cikinsu nice nake zaba masa yarinyar da nakeso ya aura din,wadda zan cimma buqatuna ta hanyarta,wadda zan juyata ba musu ba kuma damuwa......to kema wannan shine plan B dinki idan na farko yaqi aiki"

Shuru maamah tayi tana jinjina kai,lallai duk iya yadda take ganin mulki da isa da kuma izzar hajja harira ta wuce nan. Wannan shine cikakken ma'anar HAMSHAQIYAR UWA ko kuma CIKAKKIYAR UWA. Idan so samu ne tana son kamar haka ko sama da haka

"Amma banajin musaddiq zai qara watanni shida ba tare da yayi aure ba"

"Ko yau yau zaa daura auren kina iya ruguzawa,ki maye gurbinta da wadda kikeso" Ta fada kanta tsaye cikin confidence.

"Waye babbar damuwarki a cikinsu?,muhammadu?" Kai ta jinjina. Tafi damuwa da kamashi a hannu fiye da musaddiq. Tasan waye fuad din,yana da tsauri da tsananin da ita kanta tayi imanin mafi rinjayen aikin a kansa zaa gabatar

"To ki manta da batun musaddiq me sauqi ne"

"Haka ne wannan" Ta fada tana murmushi,tana jin cewa qarshen matsalarta yaxo,tana jin cewa lokaci yayi da zata cika muradanta

"Yaushe zamu tafi zuwa wajen DAN DUMA?,kinsan ba'a bori da sanyin jiki" Ta karkata tambayarta ga hajja hariran cikin zumudi da farinciki,tana jin bacin ranta yana zagwanyewa.

Tunda suka fito daga wajen a cikin jikinta kawai takejinta uncomfortable. Haka kawai take jin kamar akwai wani abu,tayi dukkan research da idanunta hankali da kuma tunani bata ga wulgin kowa ba,hakanan bataga alamun ana bibiyarsu ko wani abu da yayi kama da hakan ba. Saidai har suka soma nisa da wajen bata samu nutsuwa ba,abinda muddin ta soma jinsa a jikinta zaiyi wahala idan baby afkuwar wata matsalar.

"Me napep idan zaiyuwu ka kaini madabo.....zan qara maka wani abun" Tacewa me abun hawan. Malam ne yaketa fado mata a rai,dattijo kuma kamilallen mutumin,ma'abocin nutsuwa karamci da kuma ilimin addini.

Asalin haduwarsu ta fara ne a ranar da zasu rabu da ameen,daya daga cikin mazan da suka taba shiga rayuwarta dama tarihinta. Abun yaso ya kwabe mata har ameen din yaso fahimtar ainihin wace ita ba tare da takai ga fita daga layin ba. Ya sanya aka biyo sahunta tiqa tiqan qattin dake gadin qofar gidan nashi harda rakiyar karensu guda daya.

Malam din shi ya musu kaca kaca,ya kuma hada harda ameen din daya tako da kansa,ya nuna masa daraja da martabar mace,sunaji suna gani yayi saving nata a hannunsu ya wuce da ita sukaci gaba da takawa a qafa har titi.

Ita dinma a hanya bai qyaleta ba,ya dinga yi mata fada bawai don ya fahimci wacece ita ba?,ko ya fahimci ainihin abinda ya hadosu. Donme tana diya mace zata bari takai gefin magriba a irin wannan unguwannin?. Haka kawai taji ranta ya nutsu da dattakonsa da kuma addininsa,rana ta farko da wani ya taba yi mata fada irin wannan tun bayan shudewar iyayenta. A daren ranar tayi kuka tayi kuka,kukan kuma kukan dadi ne na yadda yau aka samu mutum qwaya daya daya tsaidata da zuciya daya yana mata fada kanshi tsaye. Tun daga wannan ranar malam din ya zame mata daya daga cikin mutanen da suke da martaba a idanunta. A duk lokacin da kudi suka samu takan dauki wani abu tayi tattaki taje ta gaidashi,ta kuma bayar wa almajiransa tace ayi ma iyayenta da suka rasu sadaka.

Matarsa tana da matuqar kirkin da ta dauketa kamar diya kaman yadda malam ya dauketa diya a wajensa. Duk sanda zataje gidan bata gaza fahimtar wasu abubuwa daga sabreen. Macace mai matuqar hikimar da sai da takai daga qarshe ta karanci wace sabreen din,sai ya zamana itama bata fiya boyewa inna komai ba muddin ta tambayeta din,gidan sai yake zame mata wajen samun nutsuwa a wadansu lokutan.

Unguwar madabo,daya daga cikin tsaffin unguwanni dake birnin kano,wadda take da dadadden tarihi. Hakanan ta tara malamai da masana addini masu yawan gaske.

Tsukukun loko ne da ko adaidata sahun a matse yake shiga,wannan ya sanyata ta nemi ya ajiyesu daga bakin babban lokon da zaka karya ka shiga qaramin. Ta bude jakarta ta sallameshi,sannan suka fara takawa ita dasu zuwa ciki.

Tun a rumfar dake qofar gidan ta tabbatar malam baya nan,don babu tabarmin karatu,hakanan daliban nasa sai jifa jifa kowa yana sabgar gabansa,don haka kai tsaye suka wuce zuwa ainihin cikin gidan.

Da sallama a bakinta suka kutsa kai,gidan yana nan kamar kullum cike da tsafta. Ba kowa a filin gidan sai hayaqi dake fitowa daga kitchen da alamu ana gab da kammala tuwon dare. Yaransu bakwai da malam,maza hudu mata uku kuma dukkansu sun aurar dasu,don haka inna ce kadai ke rayuwa cikin gidan,sai babbar jikarta da aka kawo mata don ta tayata zama.

Sake sallamar tayi,kusan lokaci daya aka amsa mata daga kitchen din da kuma rumfar dakin inna. Cikin qasa da second daya wadda ke kitchen din ta fito. Matashiya ce da duka duka bata wuce sa'ar huda ba,murmushi sosai take saki,ta baro cikin kitchen din tana goge hawayen fuskarta da hayaqi ya sanya mata tana takowa

"Adda sabreen.....kece yau a gari?" Miskilin murmushin nan nata ta saki

"Inji maqi baqo ko rumasa'u?" Sai ta saki 'yar dariya tana kamo haneefa

"Muje yau inna taga su auta,tanata zancanku tace kwana biyu shuru,gashi batasan muhallinku ba bare ta binciki ko lafiya?,layinki Kuma kwata kwata baya shiga" Ta qarasa maganar tana riqe da hannun haneefa wanda tuni sukayi gaba zuwa dakin innar.

Sai a sannan da rumasa'u tayi zancan layinta baya shiga ma ta tuna yana daya daga cikin layukanta da suka tafi hutu,sai ta taka a hankali tana bin bayansu zuwa ainihin falon innar.

Dare dare ta samu haneefa gefan cinyar inna. A duniya gidan yana daga cikin gidan dasu haneefa din keson azo,don sai ya kasance musu kamar wani gida daya qwaya tak na 'yan uwansu da suke iya ziyarta su kuma sake,sakewar da basa iyayinta cikin ainihin gidan mahaifinsu.

Da murmushin tambayar da taji innar na yiwa haneefa ta qarasa shigowa ciki

"Wa'alaikumussslam.... .ina nan ina tuhumar amaryata me takeci naga tana ta tsaho?,kunyi nisan zango wannan karon AMEENATU(real name dinta kenan)". Murmushi ta kuma saki,a duk sanda innan ko malam sukayi kiranta da sunan ba wanda ke fado mata a rai sai mahaifinta. Shike yawaita kiranta da sunan,sunan da ya kasance na qanwa ga mahaifinsu guda daya tak da aka haifa a tsakanin su maza su uku,tazo kuma ta rigasu rasuwa a wajen haihuwa tabar nata yaran mata duka su uku.

"Kuna raina inna....abubuwa ne suka sha kaina" Ta fada tana zama itama.

Gaisawa sukayi sosai ta tambayeta malam

"Malam yau duka bai zauna ba,ya tafi kasuwar qauye,amma yana hanya nasan in sha Allahu".

Kamar kusan kowanne lokaci idan sunzo gidan,komawa take 'yar kallo,nadra haneefa harma da hudan suke sabgoginsu.

Lumshe idanunta tayi tana sauke boyayyar ajiyar zuciya. Ta tabbatar yau ta faranta musu ta kuma rage musu kewa qunci da takurar zama waje daya. Tana so ta dinga kaisu guraren da zasu dan sha iska,amma tana tsoron koda da kuskure suga wani abu da zai iya affecting tunaninsu.

Suna matuqar son a zo gidan,amma kuma duk dadewar da za'ayi ba'azo din ba ba zasu taba tada mata zancan ko suyi qorafi koda kuwa sau daya ba,har sai ranar da sukazo din.

A nan sukayi sallar magariba,sukaci kuma tuwon dare. Suna haramar tafiya malam din ya dawo.

Sosai shima yaji dadin ganinsu,ya bude kuma duk abinda yazo dashi din kama daga rake,gyada,quli kabewa,dinya da sauransu ya diba musu. Walwalarsu ta dadu sosai a sannan,duk sai da suka fice da zummar zasu tafi ya rage saura Sabreen din,ta xuge jakarta ta fiddo kudi ta aje gaban malam

"Malam ayimin sadaka,sannan ayi mana addu'a". Kudin ya kalla sannan ya kalleta.

"Zan miki addu'a aminatu koda baki bada komai ba....."

"Malam bakai na bawa ba,yaran malam na bawa"

"Idan kin fita waje ki raba musu da kanki kamar yadda aka saba" Ya tareta

"Malam don Allah kayimin alfarma ko rumasa'u ta raba musu,tabbas don dare yayi ne da bazan karya maka tsarinka ba,malam kai kemin fadan kaiwa dare a waje" Ta fada murya a karye. Tanason masa ihsani,amma mutumin yana da wani irin kamewa da gudun duniyar data tabbatar bazai karbi komai nata ba

"Shikenan,Allah ya karba.....kici gaba da kula da qannenki da kanki"

"In sha Allah malam" Ta fada tana yin qasa da kanta kunya da nauyinsa suna kamata. Tana jin kamar inna ta gaya masa wani abu a kanta ko zata gaya masa,saidai ta sani ko daya innar nada cikakkiyar kamalar da bazata taba fadin sirrin wani ba *D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

PAGE 49

Tunani ne kala daban daban cikin kanta sanda suke abun hawa har suka isa gida.

Banda hadiyya data samu tana zance a farfajiyar gidan nasu bata hadu da wani babba ba sai yara dake dan kai kawo a tsakar gidan nasu. Zuciyarta a karye take bude musu qofar dakin. Wannan shine tabbacin basu da wani sauran gata.....ba wani wanda ke tsaye yana jiran dawowarsu......babu wani da zai tambayi ina sukaje?,me yasa suka dade wuni sur a waje?,ba wani me musu barka da dawowa,dasu dawo da kada su dawo duk daya.....ire iren wadannan abubuwa ke qara mata wata qaqqarfar zuciya tare da jin cewa.....ZATA SADAUKAR DA TATA RAYUWAR don samarwa rayuwar qannenta gobe me kyau.....zata zame musu makwafin uwa da uba,dukkan wuya da dadi.....zata hanasu dandanar duk wani kalar baqinciki na rashin gata dama rashin abun kulawa da rayuwarsu.

Dukansu a qoshe suke kuma a gajiye,don haka basu jima ba kowacce ta nema wajen kwanciya,don dama ita haneefa suna shigowa ta bingire a wajen.

Sau biyu tana yaye labulen tana duban tsakar gidan nasu. Wanka takeso ta fita tayi saboda yadda gajiya kebin jikinta,uwa uba ma kuma ita din tun asali mutum ce data saba da yin wanka da dare kafin ta kwanta,saidai kuma daga baya abun ya zame mata qalubale babba,saboda kallon da ake mata da wasu idanu na daban.

Yadda ta fita dinnan ta wuni a waje ba zata iya kwanciya haka ba,don haka taci gaba da dabuwa. Akwai daukewar qafafu sosai,wanann ya bata daman cire kayan jikinta ta daura zani ta kuma lullube sassalkan gashinta da babban towel,ta dauki kayan wankanta.

Tana shirin fita nepa suka kawo wuta,don haka ta tsaya ta kashe solar din dakin ta maida musu nepa sannan ta fito.

Ta tsaya daga bakin famfonsu tana tarar ruwa. Tsakar gidan tarwai da haske,kuma tsaf tsaf dashi,dabiar gidan qwaya daya tal dake burgeta,wanda idan ka dauke wannan babu wani abu dake burgeta cikin gidan dama jama'ar gidan gaba daya.

Allah yasa har ta gama tarar ta wuce wankan ba wanda ya fito. Ta kammala ta nade jikinta da zanin ta dauro towel din a sama ta fito.

Tana duqe baqin famfon tana daura alwala. Bude toilet din wankan da akayi ya sanyata daga kai. Sukayi idanu hudu da ita,saita miqe sosai ta tsaya maimakon dazun da take duqe tana daura alwala.

Kallon bibo din takeyi kamar yadda itama ita take kalla,tun daga qafafunta har zuwa kanta da yake lullube da towel.

"Ha'illallahu.....mahammadurrasulillahi......ke duniya ina zaki damu?,aah?yanzu wankan ma sai kinzo gida?" Bibo taja qaramin salati sannan ta kama haba tana sake qarewa sabreen kallo.

Wani abune yazo ya yiwa sabreen tsaye a wuya,ta lumshe idanun takaici. Ta gama fahimtar zahirin abinda bibo ke nufi......ta kuma gama fahimtar abinda inda ta dosa,saidai kafin ma ta sake daga qafarta ta sake jin muryarta

"Kiji tsoron Allah 'yar nan......ki daina sanyawa mala'iku suna tsaida iyayenki cak cikin kabarinsu......yanzu wannan wankan....." A fusace da kuma wani irin zafin nama ta waiwaya tana duban bibo,abinda ya sanya towel din kanta zamewa sumarta ta fito.

Bata qarasa ba itama sai tabi kan nata da kallo. A bushe yake ba kuma alamun damshi ko lema,hasalima ta nannade doguwar sumar tata da tayi gado ta uwa da uba a tsakiyar kanta ta cusata guri guda,wannan ya sanya bibo din hadiye abinda taso fada din.

"Ke zaa cewa kiji tsoron Allah,kuma zan maimaita miki kiji tsoron Allahn" Ta fadi da ita a nutse sannan ta fara takawa tana dosar dakinsu.

Idanma tace zata riqe zafin da qirjinta yakeyi da suya to tabbas ta yiwa kanta qarya,don haka ta sulale saman kujerar falon ta saki wani marayan kuka.

Bibo na daya daga cikin qalubalen rayuwarta,bibo na daya daga cikin mutane na gaba gaba da suke mata wata irin adawa mara fasali ba tare da tasan meye ne ta tsare musu ba. Ta jima a wajen tana kuka har sai da fuskarta tayi wani pink pink,sannan ta samu ta sauya kaya taja jikinta zuwa kan gadonta ta kwanta tana rufe idanunta tare da sauraron bugawar jini daga kanta wanda keson komawa ciwon kai.

Sassanyan ringing dinnan shine ya sakata bude idanunta. Shaf ta mance da batun wayar sai yanzu da tayi kuka. Tunawa tayi tayi alqawarin kai wayar a yau,kada ma su tsammaci ko ta gudu da sune,wannan ya sanya ta miqa hannunta qasan pillow din data ajeta dazu ta dauko da nufin dagawa ta basu uzurin gobe in sha Allah aje a karba.

Bata wani tsaya bata lokacin duba me kiran ba,tunda tasan koma waye zai kira a irin wannan lokacin tabbas makusanci ne,don haka ta shafa ta daga ta kuma Kara a kunnenta.

"Assalamu alaikum anni?" Ya furta cikin husky voice dinsa dake cakude da wani irin nannauyan sauti dake nuna izza da zatin mamallakin muryar. Yayi sallamar a sanda yake tsakiyar system da kuma tarin tarkacen takardun dake dauke da plan na ginin sabon kamfanin samar da kayan qyale qyale na mata mafi tsafa da daraja da za'a dinga qawatashi d wani yanki na diamond d gold.

Wani yankewa gabanta yayi ya fadi,zuciyarta kuma ta buga sosai har tana jin sautin bugun cikin kunnuwanta. Batasan dalili ba batasan kuma me yasa taji hakan ba,sai ta buda bakinta a hankali da muryarta da tayi nauyi saboda nauyin dake cike a qirjinta

"Ba ita bace". Shuru ne ya biyo bayan fitar sautin nata. Ita tana bawa kanta tabbacin wancan mutumin ne daya kira duba da shurun da aka sakeyi mata kaman dazu,shi kuma kwanyarsa tana son alaqanta sautin da muryar mara kunyar yarinyar nan data dag masa waya.

Kusan a tare suka daga wayar daga kunnuwansu. Ta samu tabbacinne ta hanyar karanta sunan dake yawo saman screen din.

Sauke wayar yayi daga idanunsa,yaja siririn tsaki yana kashe wayar. Sautin tsakin yakai mata har kunnenta,wani mummunan baci taji ranta yayi. To ita meye nata a ciki da har zai bita da tsaki?,waye wannan daya cika izza haka?,wanne irin mutum ne me izgili da rashin sanin daraja da martabar dan adam?,don kawai a bisa kuskure wayarsu ta fado cikin kayanta sai ta zama abar wulaqantawa?. Samun kanta tayi da latse wayar kawai ta kasheta gaba daya ranta yana suya,cikin ranta kuma tana yiwa kanta alqawarin a gobe wayar ba zatakai sha biyu na rana ba a hannunta zata kira busari yakai musu duk inda suke.

"Wanne irin wulaqanci ne da rashin sanin abinda kukeyi da zaku ci gaba da barin wayar anni a wani wajen?" Fuad din ya furta daidai sanda ya kira musaddiq.

"Kayi haquri hamma,ta fadi inda za'a karba anje ba'a samu ba,anyita kiran wayar kuma ba'a dagawa".

"Koma meye banason na sake kira naji muryarta.....kuyi magana da ita idan wayar takeso ta sauke layin daga kai,ka sanya ayima annin swapping a dauki wata wayar a hada mata".

" Ka kwantar da hankalinka me babban suna,banjin yarinyar tana da niyya ko nufin riqe wayar nan,akasi kawai dai aka samu da ajizanci irin na dam adam......tana da kirki qwarai,ita ta kaini asibiti ta kuma zauna dani har sai da musaddiq ya iso". Wata sassanyar iska ya saki daga bakinsa,sai yanzu ya tuna inda yasan muryar

"Itace mara kunyar yarinyar nan data tsaya tana yiwa mutane fada akai don ta kaisu asibiti?" Ya jefawa anni tambayar da nutsatsiyar muryarsan nan.

Murmushi ne ya subucewa annin. Tasan halin fu'ad qwarai da gaske. Yana da tsananin kamewa da rashin son shiga sabgar kowa

Readers Also Read