Kenza eBookz

A d u n i y a ta complt by huguma - Chapter 2

A d u n i y a ta complt by huguma - Chapter 2

A d u n i y a ta complt by huguma Chapter 2: A d u n i y a ta complt by huguma Chapter 2. Dukkansu sunyi shirin bacci amma bandashi,yana zaune gefe daya na…

4,465 words

Dukkansu sunyi shirin bacci amma bandashi,yana zaune gefe daya na gadon farouq,ya goye hannayensa a qirjinsa tamkar wani babba da yayi nisa cikin nazarin wani abu.

Motsin abban ya sanyashi waiwayowa,da sauri ya sauke hannayensa yayi qasa da kansa yana niyyar zamowa daga saman gadon

"Yi zamanka me babban suna......tunanin me ka zauna kana yi?,duk 'yan uwanka sunyi shirin kwanciya banda kai?" Farouq dake zaune tsakiyar gadon yayi hanzarin karbar maganar dama tana damunsa tun dazu

"Abba yaqi ya canza kaya,na bashi kayan bacci yaqi ya saka tun dazu" Hannu kawai abban ya miqawa farouq din,sai ya saka masa kayan baccin dake gefansa.

Kayan abban yabi da kallo yana jujjyasu a hannunsa,sannan ya maida dubansa zuwa jikinsu dukka su ukun dake sanye da wasu kalolin kayan.

"Amma faruqee ban gaya muku a bada kayan nan ba dukansu?,ina kayan dana kawo muku wancan tafiyar da nayi?" Ya qarasa tambayar yana maida idanunsa kan saddiq qaninsa.

Har wani juyawa saida cikin saddiq din yayi,saboda tunawa da yayi da kakkaifan warning din da suka samu daga wajen matar gidan akan batun.

"Abba,dukka mama ta karbesu,ta kuma gargademu kada mu sake mu sanar dakai,idan ba haka ba saita tsoma kawunanmu a ruwan zafi" Ba abba kawai ba,hatta me babban sunan saida maganar ta ratsashi duk da qananun shekarunsa,amma zuwa yanzu ya dade da yiwa kansa karatun qalubalen da suke shirin fuskanta

"Ruwan zafi?" Abba ya furta cikin tsananin kaduwa da mamaki,sai faruqee ya gyadawa abban kai. Maganar ta ladabtar d abba ta sanyashi samun waje ya zauna. Yana tsoron ci gaba da wannan tafiyar tasu......yana tsoron garin neman lada ya rufta ya buge d wucewa jahannama,ya debo marayun Allah da nufin basu rayuwa me inganci,muddin Mariya bata goya masa baya ba meye makomar yaran?,ya gobensu zata kasance?. Tambayoyin da suka dinga karafkiya kenan a kansa.

Indai haka ne ya zama dole yayi jan ido,ya zama dole yayi wuta wuta akan gidansa da iyalinsa. Ya sauke dukka nauye nauye haqqunan da suka zama wajibi dama wadanda basu zama wajibi bs,ya zama dole to itama ta bishi yadda ya kamata.

"Ba komai,tashi me babban suna ka shirya,idan kun kammala ku kashe kayan wuta gaba daya kuyi addua ku kwanta" Yayi maganar ne yana sake nazartar dakin tare da kallon guraben da ga siya ma yaran abubuwa da dama ya ajjiye saboda jin dadin Rayuwarsu a yanzu ba komai a wajen sai gurbinsu.

Sai daya kammala komai daga ainihin dakinsa sannan ya zarce dakin mariya. Ta gama shirin kwanciya tsaf tayi rub da ciki tsakiyar gado tana latse latsen waya. Fuska a hade ta daga kai ta kalleshi sau daya saita dauke kan nata ta maida ga wayarta tana sake tsuke fuska.

"Tashi zamuyi magana" Ya fada cikin yanayin dake tabbatar mata da gaske yake,da kuma zafinsa ya shigo. Sai da tayi kamar ba zata tashi ba sannan ta miqe ta zauna sosai tana gyara wuyan rigar baccinta tare da tsuke fuska da kyau.

*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*

*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*

*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*

*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*

*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*

*ZAFAFA BIYAR*

*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*

*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*

_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_

_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_

_K'ALBIM Mamuhghee_

_AJIYA A DUHU Billynabdul_

_DUNIYATA Huguma_

_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_

*hudu 2k*

*uku 1500*

*Biyu 1k*

*Daya 500*

_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_

*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*

*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA* *09033181070*

*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*

*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*

*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*

*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪

89825722 Nousaiba lawali maradi 1000cf

*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*

*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰 *D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

*Arewabooks:Huguma*

Page 05 last free page

"Asama'u" Ya kirayi sunanta da wani irin yanayi da har cikin zuciyarta ta tabbatar cewa......dukka maganar da zata gita yanzu haka daga bakinsa ,yankakkiyar magana ce wadda babu janyewa a cikinta ko kuma wani sauyi bare sassauci

"Ban rabu da mariya ba don na auro wata matar tazo ta azabtar min da 'ya'ya ba,ina tsananin qaunar 'ya'yana fiye da soyayyar da nake yiwa kaina,duk soyayar da zaki gwadamin bata da alfanu rana ko kuma fa'ida a gareni muddin ba zaki so 'ya'yana ba......asama'u,na rantse da Allah,dai dai da rana guda na samu wulaqanci cin amana ko tsanantawa diyoyina bisa ganganci bawai kuskure ko ajizanci irin na dan adam ba bazan raga miki ba"..... Wani dum taji har tsakiyar kabta,batabtaba kawowa dukka maganganunsa zasu kai har wannan iyakar ba,bata tana tsammanin abun yayi zurfi haka haka ba,da ake gaya mata yana da son yara batabtaba kawowa yakai har wannan bigiren ba.

Zuwa sanda zatakai qarshen tunaninta shi din ya jima da miqewa yana kallonta

"Bazan fasa tafiye tafiye na wajen neman halak da neman abinda zan rufawa kaina da iyalina asiri ba......ba kuma zan kwashe diyoyina na kaisu wanin guri ba,gaki gasu nan asamau,dukkan abinda kika qudirta yi kada ki fasa koki sauya ra'ayi" Ya qarashe fadi yanajin wani irin daci saman harshensa,bai kuma dakata ya saurareta ba ya juya a nutse yana barin dakin nata.

Har sanda ya bacewa ganinta bata dauke dubanta daga bakin qofar dakin ba,ta qanqance idanu tana kallon qofar tare da jin dacin kalamansa suna gauraya kowanne sashe na jikinta. A taqaice dukka bayanansa suna auna mizani da kuma adadin iya matsayinta kenan a wajensa?. Bata shigo gidansa don ta fita ba,don muhallin dame muhallin duka sunyi mata,amma kuma bata shigo bautar d'an kowa ba,hakanan bata shigo don a takata ko aci mata zarafi ba bare kuma a hanata sakewa.

Shawara take buqata kawai a yanzu hala,don gaba kura ne baya sayaki,ta kula dasu ko ta barsu komai ta fanjama fanjam?,to amma fisabilillahi zai yiwu kuwa ace ta buge da bautar d'iyoyin da ba ita tayi Jigilar daukar ciki da kuma rainonsu ba?.

Matsawa tayi kusa da wayar landline dake gefan gadonta,ta latsa lambobi tana fatan sashen kamfanin sadarwar ya sadata da matar data kira take mararin magana da ita. Ba'a dauki dogon lokaci ba sukayi mata hakan,saita qarasa sauke dayar qafar tata qasa tana zama sosai yadda zatafi jin dadin amayar da abinda ke cikinta.

Yanayin yadda suka gaisa kadai zai gaya maka akwai shaquwa me zurfi da tsohuwar sanayya a junansu.

"Ya nake jinki haka sama sama?" Daga saya bangaren ta tambayeta. Sai data aje dogon tsaki sannan ta fara magana,zuciyarta cike da wannan bacin ran da batasan ranar da zai wanke daga zuciyarta ba

"Barni kawai......dukka shirina har yanzun bai tafi a yadda na jima ina tsarawa ba"

"Wani abunne kuma?" Kai ta rausayar tana jin kamar ta qifta idanuwanta ta budesu ta tarar babu kowa tsakiya da gefannin rayuwarta da mijinta,daga ita saishi

"Yarannan haleema......bayansu ya sake kwasomin riqon marayu,bayan wadannan din har yanzu ban gama da matsalarsu ba......" Daki daki ba tare data rage komai a abinda yake faruwa ba ta shimfida mata,sannan ta dora da fadin

"Inajin kamar naje gurinsa ayita ta qare haleema,na meye zaa dinga doramin nauyin da bai zama wajibi a kaina ba?" Ajiyar zuciya haleeman ta sauke

"Ashe qarya kikeyi,baki shirya zaman auren ba" Haleema ta katsi numfashinta sanda taji tana shirin sake dorawa da wata mitar

"Kamar yaya?,ya zakice haka bayan kinsan komai?" Ta tambayeta tana tsuke gira tare da mamakin amsar data bata

"Eh to ai dole nace haka,wani lokaci sam baki da wayo asama'u,yaransa biyu da yake mutuwar so ki gaza riqesu?,bakisan ta hanyar riqon da zaki musu bane zaki samu fiye da abinda kike hange ko hasashe daga jikinsa?" Ta qarashe maganar da sigar tambaya,tambayar data dauki dukka tunanin asama'u ta jefashi wani guri me nisa

"Amma haleema,saina zama baiwar yara har hudu?" Ta yiwa haleema tambayar tana jinjina girman abun,tamkar wadda aka dorawa nauyin wanke kashinsu da fitsarinsu gami da ci dasu tsahon kowacce rana da wuni na rayuwarta

"Bance haka ba,ban kuma goyi bayan hakan ba,yaransa sune dolensa,su zaki kama ki riqe,saura kuwa wannan baida hurumin tilasta miki zama dasu,idan ma baki riqesu ba bakiyi laifi ba,kedai yaransa su zama makamin zamanki a gidan,yo asama'u kona ganin ido ne ke ba zaki iya ba?.......".

Dadewar da sukayi saman waya sa haleema iya adadin karatun data samu daga gareta,ta kwanta ne tana juyawa tare da tauna yadda zata dauki shawarwarin haleema tayi aiki dasu,ta yaya zata danne zuciyarta da dukka wani abu da takeji tayi yadda haleema ta kwatanta mata?.

*_W A S H E G A R I_*

Dukka su hudun suna zaune a gabanshi,yana jansu da hira cikin yanayin da zakayi tsammanin shi din wani babban yayane a garesu bawai uba ba.

Da idanu yake karantarsa,har yanzu dai bai sake ba kamar yadda ragowar 'yan uwansa uku suke a sake. Har yanzu a darare yake,dararewar data sanyashi yaji a ransa akwai abinda ya hanashi sakewar.

Har cikin rai da gangar jikinsa a yanzun da suke gabansa yake jin kamar dukka su hudun mallakinsa ne,shine ya haifesu. Inda yana da iko tabbas zai maida agogon rayuwarsu baya ya mantar da al'ummar da suka sanshi dama na unguwar cewa shi din ba shine ya haifesu su biyun ba.

Tun daga nesa da take takowa cikin falon idanuwanta yake kansu. Sunyi wanka dukkaninsu sun kuma shirya cikin shaddodinsu masu kyau,wadanda tayi imani cikin sabbin kayan daya saba tahowa da yaranne. Sake maida idonta tayi a kansu,a nutse yake qwarai fiye da dan uwansa,ba wani karsashi a tare dashi ko kuma rawar kai,saidai kuma haka siddan takejin muguwar matsananciyar tsanarsa shi da dan uwansa.

Ta yaya tun bata aje nata yaran ba ace wasu yaran sun shigo sun sake cinye gurbi da muhallin mutum biyu bayan gurbin mutum biyun da yaran gidan suka cinye?. A yanzun idan har ta soma aje nata yaran kenan saidai su tashi daga na biyar?,ya za'ayi ta bari haka ta kasance?.

Sai data iso dab dasu sannan ta iya controlling kanta tayi sallama. Dukkansu suka daga kai suna dubanta banda abba da ya kauda nasa kan kadan gefe don da haushinta ya kwana.

Qoqarin gaidata sukayi,ta amsa tana binsu da kallo daya bayan daya,wannan ya sanya kowa ya sake kama kanshi a cikinsu,bansa me babban suna wanda tun daga kallon farko bai sake daga kansa ba bangaren da take.

"Ina kwana abba?" Ta gaidashi cikin matuqar qoqarin daidaita kanta idanunta zube kan kayan breakfast dake gabansu.

"Lafiya lau" Ya amsa mata a taqaice yana rufe plate din fried egg din daya gama ci.

"Yau nayi bacci me nauyi ban samu tashi na hada abincin safe ba"

"Eh laraba tayi.......don dama fita nakeso muyi" Ya amsa mata yana miqewa.

"Ina haka da safiyar nan?" Tayi masa tambayar cikin son sanin komai

"Makarantarsu Faruqee,inason na yiwa su me babban suna registration,next week idan Allah ya kaimu su koma tare baki daya" maganar tayi mata kama da almara ko kuma ba zata. Tana tantamar akwai hikima ko hankali kuwa cikin maganganun abban?,ta yaya zai dauki yaran maqota ya kaisu makaranta me kudade masu ciwo haka?,makarantar dako yaran cikinsa da taji nawa ne school fees dinsu saida taji kishi da baqincikin abun?,ta kuma bashi shawara a fakaice ya kusa sau biyar akan ya sauya musu da wadda bata kaita ba.... Ko don yadda shima wani lokaci ta lura kaman yawan school fees din yana dan takurasa?.

Abinda ya darsu a ranta me girma ne,tana da abubuwan da takeson ta fadi masa amma girman bacin rai da kuma abinda ya tsaya mata a wuya ya hanata cewa komai har suka tarkata suka fice daga falon.

Idan nace ta samu nutsuwa tun daga fitarsu har dawowarsu to zance ne kawai. Sanda suka tashi dawowa din kuma sun dawo da dukka tarkacen kayan amfani na buqatar rayuwa na yau da kullum. Komai hurhudu ya siya,amma kaf cikin siyayyar bataga tsinke nata ba

"Somin tabi kenan hatsin gara a buta......tun yanzu?" Wani sashe na zuciyarta ya ayyana mata. Ai juma'ar da zatayi kyau tun daga laraba ake ganeta. Tun a rana ta farko ta soma karantar iyakokinta?,dukka kuma akan yaran da suka kasance tamkar wata tsintacciyar mage?. Yaran da basu da GATA ASALI ko wani GALIHU?. Ita kuwa asama'u yaushe?,yaushe zatayi wannan SAKEN?. Muddin bata bazama su ba lallai anyi asarar haihuwarta,muddin bata ganar dasu kuskuren maida UBAN WANI NASU BA bata cika MACE BA....

*_BAN TABA KOMAI BAFA CIKIN LABARIN......BAN FARA KOMAI BA A CIKI_*

*_zazzafan labari ne tsakanin SABREEN DA MUHAMMED FU'AD_*

*_BANBANCIN RA'AYI TSARI DA AQIDA_*

*_MUMMUNAN ZATO DA GURGUWAR FAHIMTA_*

*_TA YAYA RUWA DA WUTA ZASU HADU GURI DAYA?_*

*_ZALLAR QIYAYYAR MAHAIFIYA HALITTA MAFI SOYUWA A DUNIYA_*

*_BAHAGUWAR BIYAYYA BISA TILASHIN ZUCIYA BA DON RAI YANA SO BA_*

*_GWANA KUMA QWARARRIYA WAJEN SACE ZUKATA DA ALJIHUN MAZAJE DAMA ASUSUNSU GABA DAYA_*

*_KARKI SAKE AYI BABU KE_*

*_WANNAN SALON YASHA BANBAN DANA SAURAN_*

*DUNIYATA(MUHAMMAD JADDA)*

*DUNIYATA(SABREEN)*

_GA HANYA MAFI SAUQI DA ZAKI KASANCE DA ZAFAFABIYAR FAMILY IN SHA ALLAH_👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾

*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*

*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*

*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*

*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*

*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*

*ZAFAFA BIYAR*

*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*

*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*

_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_

_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_

_K'ALBIM Mamuhghee_

_AJIYA A DUHU Billynabdul_

_DUNIYATA Huguma_

_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_

*hudu 2k*

*uku 1500*

*Biyu 1k*

*Daya 500*

_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_

*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*

*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA* *09033181070*

*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*

*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*

*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*

*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪

89825722 Nousaiba lawali maradi 1000cf

*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*

*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰 *D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

*Arewabooks:Huguma*

Page 06 ___________________________

*_TURQASHI_*

*_BIGI SAI BIGI_*

*_BABBAN GORO SAI MAGOGIN QARFE_*

*_TASTED AND TRUSTED_*

*_TASTED AND TRUSTED_*

*_TASTED AND TRUSTED_*

*_Kina da burin samun ingantaccen TURAREN WUTA me TSANANIN KAMA GURI?_*

*_TURAREN WUTAR DA ZAKI SANYAWA DAKI AMMA HATTA DA LABULAYE KAYAN SAWAN DAKE SAQALE A DAKIN SU KAMA DA QAMSHI?_*

*_TURAREN WUTAR DA KUJERUNKI ZASU KAMA QAMSHI DARAM?_*

*_KI BANKADA LABULAYENKI KIJI SASSANYAN QAMSHI?_*

*QAMSHI IYA QAMSHI 24HR*

*HUMRA ME TSAYAWA A ZUCIYAR ME GIDA*

*NASAN ZAKI TAMBAYI KANKI A INA ZAN SAMU WANNAN?*

*INCENSE BY KABO DAUGHTER*

*_tayi muku tanadin abubuwa da yawa irinsu_*

Khumra Turaren wuta Kulaccam Lablab Oil perfumes Original musk tahara Multipurpose spray

*karki kuskura kada kiyi ganganci ayi babu ke,kai tsaye tuntubeta ta wannan number*

08032119803

Ko ki lalubeta ta nan👇🏾👇🏾👇🏾

*Instagram handle_incense by kabo daughter*

*Facebook_kabo daughter*

*Twitter_kabo daughter* __________________________

Tayi zaune kawai saman kujerar falon tana duban kowa d'ai d'ai da yadda yaran keta walwalarsu da sabgoginsu. Ta yita juya zancan haleema a ranta,anya zata iya kuwa?,zata iya jurewa?,daga bisani data tabbatar muddin taci gaba da zama a wajen zata karya dukka tsarinta saita yunqura kawai ta miqe tana bar musu falon.

Cikin satin ya tabbatar yayi musu dukkan abinda ya dace,ya kuma sauke duk wani abu da uba zai saukewa 'ya'yansa,tun daga suturunsu xuwa takalmansu,kayan makaranta hadi da jaka takalmi da duk wani abu daya zama dole ga dan makaranta.

Zai iya cewa Kansa da kansa sauyi ne na dare daya yazo cikin rayuwarsu,duk kuwa da cewa har yanzun.....daidai da second dayahasashe,koda da wasa irin na qwaqwalwa zuciyarsa bata taba hasashen ta manta da abubuwa guda ukun nan da suka shafi rayuwarsa ba......suka shigeta da wani irin yanayi,yanayin daya tilasta canzawar zubi da kuma tsari na dukkan feeling na zuciyarsa da gangar jikinsa.

Abbansa Jadda

Da kuma uwa uba mahaifiyarsa da zuciyarsa ke mata wani irin bahagon kallo.

Halitta mafi girma da daraja cikin rayuwarsa......amma kuma dukkan wani matsayi da girman suna da halittar ta mallaka baya jinsa ko dis cikin jininsa da zuciyarsa.

Eh tabbas......a tsukin kwanakin rayuwarsu tayi wani wawan sauyi,saidai nashi sauyin ya tsayane cak iya zahirinsa. Darare da yawa suna wucewa cikin idanunsa. Alfijir dake cikin kowacce asubahi da Ubangiji ya halittama kwanakinmu sun sha ketowa ta cikin qwayar idanunsa. Ta tsakiyar qwaqwalwarsa yana jin kamar an tsatssagarta da wani abu me kaifin tsini

"Me yasa maama taqi zama damu?,me yasa ta kasa jurewa lalurar Abbey?"

"Saboda bashi da komai yanzun,saboda shi talaka ne" Amsar da kullum yakeji ana rada masa kenan cikin kunnuwansa. Sau tari yakan sanya dukka tafukan hannayensa ya toshe qofofin kunnuwansa wai ko zasu daina jiyo masa wannan amsar......waiko amsar tambayarsa zata iya sauyawa?.....saidai aah,koda wasa bai taba jin amsar nan ta sauya ba. Tun baya daukar gaskiya ake rada masa ana kuma sake jaddada masa har zuciyarsa ta gamsu da hakan.

"Indai haka ne maama ita tayi silar mutuwar Abbey......indai haka ne maama itace tayi ajalin jadda" Abinda yake gayawa kansa kenan a duk sanda ya kalli fuskarsa dake dauke da qananun shekaru

"Amma ta yaya ta kashesu?" Tambayar da daya kasa lalubo amsarta,saidai yasan koda duniya zata taru ta hanashi wannan tunanin bazai taba kankaruwa daga qwaqwalwarsa ba har ABADA.

*******

Safiyar litinin ce dake dauke da yawaitar hazo da kuma lullumin sanyi daya soma tun a daren shekaran jiya. Cikin dakin nasu a cikin su hudun kowanne shirin tafiya makaranta yake yiwa kansa don ba wanda baya iya yiwa kansa da komai da komai a cikinsu,daga su Faruqee da suke 'yan gidan,har su da suke baqi ko kuma ace 'YAN RIQO. Kusan za'a iya cewa banbancinsu dasu Faruqee din shine,mamarsu da babansu dukkansu suna a raye,sannan komai tsanani suna da gatan dangi da kuma muhallin da zasu kwana a ciki. Amma ta fuskar samun cikakken gata da kulawa na iyaye,sun tashi kusan a mizani guda,don sun rasa kaso tamanin a cikin dari sanadiyyar RABUWAR AUREn mahaifansu.

"Ya kamata kayi ka gama,wannan laqai laqai din naka ba abinda zai haifar mana sai bata lokaci,kasan dai abba ya koma a motan haya zamu je yau" Faruqee dake saba school bag dinsa yace da saddeq dake kurba shayin da Faruqee ya hado musu dukkansu suka gasa cikinsu.

Kusan ya zame musu jiki,duk randa mahaifinsu ya sanya qafa ya koma Lagos lunch box dinsu yakan koma hoto,zancan breakfast kuwa saidai da tsananin rabo Faruqee ya faki idanunta ya hada musu tea susha su wuce kaman yau. Tasha kamashi bayan anyi hakan,tasha gargadarsa amma a banza wai man kare,gobe ma sai ya qara. Tun tana hukuntashi ta hanyar duka har yakai shekaru sha biyar. Tayi niyyar masa wani wawan duka,amma da yake ance qashin namiji dana mace ba daya bane saita samu targade a hannun nata madadin shi yaji rauni.

Yayi dariyar ranar kaman ba gobe,ya dinga maimaitawa qaninsa

"Alhakina ne". Hakanan taji jiyyar hannun nata ba tare da kowa ya sani ba. Tun daga ranar ta canza kalar horo,saita hadashi da aiki me tsanani,kota hanasu abinci a ranar gaba daya. Irin wannan horon yafi mata dadi idan ya zamana abba baya gari,idan kuwa yana nan abubuwa da dama saidai tayi haqurin dole ta tarasu sai randa ya wuce.

Saddiq da musaddiq ne a gaba,sai shi da Faruqee a bayansu.

Kana musu kallon farko zasu burgeka,ka kuma dauka set din tagwaye ne guda biyu,don dukkansu kusan sa'annin junansu ne. Yanayin zubin kyan halitta da suke dashi,ga kuma wadatacciyar tsaftar uniform da Faruqee bai yarda wahalar cikin gidansu ta sanyashi qazanta ba.

Ba wanda gabansa bai fadi ba cikin su ukun bayan ratsowarsu ta falo da zummar fita daga gidan idan ka dauke me babban suna da ya dauke idanunsa daga kanta tuntuni.

Qafarta daya saman daya tana karkadata a hankali,kamar yadda ta zube musu idanunta tana binsu da kallo kamar qwayar idanun nata zasu zuba a waje.

A darare dukkansu suka gaidata,saidai idanunta suna kanshi ganin yadda ya gaidata hankali kwance,sam kuma kwata kwata babu wannan razani da kuma d'ar d'ar dake kwance a fuskokin 'yan uwansa dake takawa cikin sanda suna fatan wucewa daga falon lafiya.

"Zo nan dan qaruna!" Ta furta da wata kakkausar murya tana sake jin haushi da tsanar yaron. Dukkansu suka waiwayo,ta sake binsu da ido

"Duk ku dawo nan" Ta kuma fada tana gyara zamanta.

Ba wanda ya musa mata suka tako dai dai da dai dai suka zube saman carfet din

"Kai don ubanka waye yace ka shiga kitchen ka taba madarar gidan nan?" Ta jefawa Faruqee tambayar tana watsa masa zagi da hannayenta.

Kiran uban da tayi shi ya sauka har tsakiyar zuciyarsa ya sosata. UBA wani abu mafi daraja da yake ganin kimarsa cikin DUNIYARSA fiye da uwa,ubansa da kuma ABBAN Faruqee mutane biyu da basu da tamkar da bayajin zai iya jurewa zaginsu. Idanunsa ya maida ya lumshe yakuma yi qas da kansa yana hadiyar wani abu me tauri da zafi tamkar shi mama ke tambaya. Wai haka iyaye mata suke ne marasa tausayi?,marasa imani?,me yasa iyaye maza yaketa gani da tambari da dukka wani tabo na tausayawa 'ya'ya?,me yasa kalmominsu suke tsauri akan 'ya'ya cikin rashin tausayi da kyautatawa?.

"Makaranta zamuje,kuma yunwa mukeji"

"Ubanka nace......saboda ubanka ne ya kawo madarar shine kake ganin kana da right na shigarmin kitchen yadda kakeso?"

*_Dukkan godiya sun tabbata ga Allah_*

*_yadda muka fara lafiya Allah yasa mu gama lafiya_*

*_kusa kurai da zaa gani a ciki ajizanci ne irin na dan adam,da fatan za'ayi afuwa a kau da kai_*

*_Don Allah don Allah ina roqo da fatan zaku zama masu uzuri a gareni,saboda yanayin sabgogin rayuwa,kowa ya sani yau da gobe tana iya sauya bawa daga ainihin yadda aka sanshi_*

*_duk sanda kuka samu wani sauyi tattare dani game da tsaiko na posting,tsahon pages da sauransi,ina kyautata muku zaton soyayyarku gareni zata sanya ku zama masu yimin uzuri_*

*_ina godiya qwarai game da yadda bakwa gajiya da bibiyata,da bibiyar zafafa biyar gaba daya_*

*_alkhairin Allah yakai muku a duk inda kuke,tare da fatan ubangiji zai tsareku kuma daga dukkan abunqi_*

*_na gode qwarai,kuma in sha Allah a duk sanda dama ta samu zaku samu komai fiye da yadda kuke so ma cikin wannan tafiya ta DUNIYATA_*

*_LABARIN ZAI TABO BOYAYYAR MATSALAR DA MUKE FAMA DA ITA,na muku alkawarin nishadi da sassanyar soyayya kan bigiren salon da kukafi so😍🥰_*

*MU KASANCE TARE IN SHA ALLAH DAGA FARKO HAR QARSHE*

*HUGUMANKU CE* *D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

*Arewabooks:Huguma* Read My Book "DUNIYA TA🌏" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997 ________________________

Page 07

Dif sukayi dukkansu,ba wanda ya iya tanka mata a cikinsu. Daga can qasan zuciyarsa yake jin wani irin zugi fushi da kuma radadi,don meye zata dinga zagin iyaye a gaban 'ya'yansu?,shi abban me yayi da har ya cancanci a zageshi?.

"Badai makaranta zaku ba?,ku tashi ku bacemin da gani". Kaman dama suna jiran wannan umarnin ne daga gareta dukkansu suka miqe din kusan lokaci guda,kowa yana yunqurin barin gabanta kamar yadda ta buqata

" Harda su kaza a cin danqo?" Ta furta tana kama haba idanuwanta a kansa

"Kai dan qaruna ina zakaje?"

"Makaranta mana maama,ko kin manta tare muke zuwa?"

"Na manta uban masu gida,saika karanta min,don ubanka da can makarantar suka damu da zuwa?,shine yanzu saboda wuce gona da iri da samun waje har suke rawar jikin tafiya?.to wallahi kuda makaranta saidai idan anfi qarfina" Ta fada tana kada hannu da kyau cikin hargagi tana nunasu da yatsa.

Hukuncin nata yazo masa a bazata,don bai taba tsammanin zatayi hukunci me tsauri har irin haka ba. Yaji abun ya taba ransa qwarai,domin a yanzun bashi da wani buri daya rage masa saina KARATU. KARATU shine cikar burinsa qwaya daya tal daya rage bai qarasa mutuwa daga zuciyarsa ba,yana jin zai iya bada kominsa don yayi karatu,zai kuma iya jure dukkan wata wahala tsanani ko tsangwama saboda karatu. Ko a yanzun yana daya daga cikin abinda ya sanya zuciyarsa ke qarfafa,tana sake jadda masa zai dauki komai ya kuma jure komai din saboda ingantaccen ilimin da yake hangowa zaya samu. Dole ya daga idanunsa da suka fara sauya launi ya kalleta dasu

"Kalleni da kyau......ba wani karatu da zakuyi cikin gidan da ba na ubanku ba,idan kuma kallon mamaki kake yimin ai uwarka yafi kamata ka yiwa wannan kallon,ita kanta ta kasa jurewa zama daku sai ni da bani da galihu akeson hadani da alaqaqai,to wallahi yadda ban samu yadda nakeso ba,haka kuma ba zaku samu ba......."

"Me kikeso ayi mama?" Ya furta tana aje numfashinta daga tijarar da takeyi. Tsananin mamakin yaron takeyi yadda yakeyin komai cikin dakiya da taurin rai dana zuciya

"Ko baka tambaya ba ai zan gaya maka kuma dole kabi,ka sauke wannan munafukar jakar ku wuce ciki,sudai da babu yadda zanyi dasu gidan ubansu ne saisun dawo,a sauka lafiya" Ta fadi tana nunawa su Faruqee hanya da yatsa.

"Mama.....amma" Zakayimin shuru ko sai ka jawo kuma na hanaku?" Wani dunqulallen abu ya hadiye can qasan ransa yana jin kamar ana masa suya

"Kudin mota"

"Kudin ubanka dai,sayyadarku zaku taka sisi bazan bayar ba" Ya fada tana zazzare masa idanu hadi da dukan hannun kujerar da take kai

"Ku tafi Faruqee don girman Allah" Ya furta da rinannun idanunsa da kuma muryarsa da tayi laushi qwarai yana duban Faruqee din,don kunnuwansa sun soma gajiya da jin zagin da take nausawa bawan Allahn da baisan hawa ba baisan sauka ba.

Kallon kallo suke ma juna shida Faruqee din,kowanne cikinsu zuciyarsa cike take fal da zallar bacin rai daya haurawa shekarunsu. A zahiri tausayin me babban suna shi yafi rinjaye a zuciyar Faruqee. Ba yau ba ba kuma jiya ba ya sani......muddin ka ambaci kalmar UWA ko mahaifiya a gabansa takan zame masa kamar tabo ko kuma ciwo koda ba dashi kake ba,ballantana a yanzun da aka kirata muraran.

Abun ya jima da zame masa kamar wani ciwo,tunda zancan ya bulla cikin unguwa sai ya zama abun yamadidi da magana tsakanin maqota da mazauna unguwar. Sam baa tallafi rayuwarsu ba,ba'a agajesu ba,ba wanda ya waiwaya ya dubi tsanani bayan tsananin da suke ciki,ba wanda ya bawa rayuwarsu tallafin da zai rage musu radadin da sukeji,a maimakon haka,sai suka debo DAFI na cecekucen maganganu akan rayuwarsu suka sake watsawa ciwuka da raunukan dake ciki zukatansu shi da d'an uwansa.

"Kaje Faruqee" Ya sake maimaita masa yana tsareshi da ido. Ya karanci komai ta cikin idanunsa,ya karanci abinda yake nufi da maganarsa,don haka bai qara koda minti daya ba ya kama hannun musaddiq suka suma takawa suna barin falon.

"Na dawo gareka" Ta furta cikin izza da dagawa tare da jinta can saman qololuwar isa da kuma 'yanci

Readers Also Read