A d u n i y a ta complt by huguma - Chapter 3
A d u n i y a ta complt by huguma Chapter 3: A d u n i y a ta complt by huguma Chapter 3. "Ka koma ka zare wadannan kayan,don basu dace da agola irinka…
4,454 words
"Ka koma ka zare wadannan kayan,don basu dace da agola irinka ba,tabbas da 'ya'yan da mahaifiya zata wofantar dasu,ta tsallakesu ta gudu ta barsu to ba'a banza ba......don haka banga dalilin da uwar data haifeku bata tausaya muku ta zauna daku ba ni zan tausaya muku ba......tunda kun iso inaga ya kamata me mana wanki da guga ya tafi hutu hakanan,ka shiga dakin ajiyar kayan wanki ka debo duk kayan da ka gani ka fita dasu bayan gida wajen fanfunan can ka wankesu......wallahi wallahi kace zaka saka iskanci a aikin kaga ikon Allah,banaso kuma azahar tayi maka baka kammala ba". Baice komai ba yakau da kai ya soma takawa yana komawa dakinsu ranshi yana wani irin tafasa da suya. Tsanar maama tana sake wani mahaukacin tasiri cikin ransa. Inda bata tafi ta barsu ba duk tsanani duk wuya,komai girman talaucinsu sunfi gaban a goranta musu,don da iyaye ake ado,sune abun adon diyoyinsu.
Me yasa ta aikata hakan?,me yasa ta kasa jurewa?,tsabar son kai ne irin na jinsin DIYA MACE da ya tabbatar a yanzun haka halittarsu take?.ko kuma son duniya da qyale qyalen cikinta ne ya rudeta?. Me yasa batayi haquri ba kaman yadda Abbie ya dinga kira mata?. Har yau har kwanan gobe sashen qwaqwalwarsa da ya nadi muryar Abbie ta qarshe.....magiyar Abbie ta qarshe akan roqarta ta zauna ya gaza goge su......ya gaza goge wannan rarraunan sautin nasa daga nemory dinsa. Abinda ke sake aza masa wata mahaukaciyar wuta,tare da dasa masa fara kallon halittar diya MACE a baibai.
Yana cire kayan saddiq yana kallonsa,a duk sanda zuciyar dan uwansa ta motsu shine mutum na farko dake fara fahimtar hakan. Ya kammala cire kayan tsaf ya musanya dana gida sannan ya juya ya adana na makaranta yana musu kallon tsanaki,dukka ruhinsa da zuciyarsa tana makarantar,yana wassafa malami na farko ya fita zuwa yanzu,malami na biyu kuma na dab da shiga ajin komai yana ciki.
Hannu ya sanya ya share fuskarsa yana qoqarin lanqwasa zuciyarsa. Farat daya qaunar da yakewa karatu ya ninku a zuciyarsa ganin abba ya bashi dukkan wata dama da zaiyi karatun,sai gashi farat daya tana nema ta zama silar da zaiyi nisa sosai da MAFARKINSA?. _________________
*_CIKIN DUBU DABAN TAKE_*
*_TABBAS AKWAI TURARE AKWAI MUNA TURARE_*
*_NA GWADA NA GANI_*
*_YA SUBHANALLAHI_*
*_QAMSHI NA TASHIN KAN ME GIDA_*
*_QAMSHIN DAKE DAGAWA KISHIYA HANKALI_*
*_NATACCEN QAMSHI DAKE KAMA GURI DARAM_*
*_WANNE GANGANCI NE YA SAKAKI TSAIWA SANYA?_*
*_ME KIKE JIRA?_*
*WANNAN DIN GUARANTEE NE FA*
*TASTED AND TRUSTED 100% PERCENT*
*KI SIYA KI GODEMIN HAJIYA*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER*
*_DUNIYAR TURARE ME BADA ASALIN QAMSHI ME KAMA JIKI DA MUHALLI,NUTSATSEN QAMSHI ME SANYAYA ZUCIYA DA DADEWA A WAJE_*
*_IDAN KINA DA MATSALA KINA NEMAN TURARE ME KAMA WAJE,KINASON SAKEWA OGA SABON QAMSHIN DAKI DA PARLOR,KE KANKI KINASO KI SHIGA WAJE A DINGA TAMBAYAR WACE TA ISO NE?_*
*MAZA MAZA JEKI KI GWADA WANNAN_*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER 08032119803*
*_zaki dariya za kuma ki godemin_*
*_gani ya kori ji_*
*hakanan sai an gwada akan san na qwarai* _________________
*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*
_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA* *09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪
89825722 Nousaiba lawali maradi 1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰 *D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 08 __________________________
*_CIKIN DUBU DABAN TAKE_*
*_TABBAS AKWAI TURARE AKWAI MUNA TURARE_*
*_NA GWADA NA GANI_*
*_YA SUBHANALLAHI_*
*_QAMSHI NA TASHIN KAN ME GIDA_*
*_QAMSHIN DAKE DAGAWA KISHIYA HANKALI_*
*_NATACCEN QAMSHI DAKE KAMA GURI DARAM_*
*_WANNE GANGANCI NE YA SAKAKI TSAIWA SANYA?_*
*_ME KIKE JIRA?_*
*WANNAN DIN GUARANTEE NE FA*
*TASTED AND TRUSTED 100% PERCENT*
*KI SIYA KI GODEMIN HAJIYA*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER*
*_DUNIYAR TURARE ME BADA ASALIN QAMSHI ME KAMA JIKI DA MUHALLI,NUTSATSEN QAMSHI ME SANYAYA ZUCIYA DA DADEWA A WAJE_*
*_IDAN KINA DA MATSALA KINA NEMAN TURARE ME KAMA WAJE,KINASON SAKEWA OGA SABON QAMSHIN DAKI DA PARLOR,KE KANKI KINASO KI SHIGA WAJE A DINGA TAMBAYAR WACE TA ISO NE?_*
*MAZA MAZA JEKI KI GWADA WANNAN_*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER 08032119803*
*_zaki dariya za kuma ki godemin_*
*_gani ya kori ji_*
*hakanan sai an gwada akan san na qwarai* ___________________________
"Hamma" Ya tsinkayi muryar saddiq tana kiransa,sai ya waiwaya ya zubawa qanin nasa ido
"Wai sai yaushe maama zata dawo?,yaushe za'a daina yi mana gori?" Tambayar ta tsinka zuciyarsa sosai ta kuma sake yi masa tabo. Ya zuba masa idanu sosai,kamar bazai ce komai ba sai ya motsa labbansa
"Duk tsanani duk wahala.....kada ka sake zancanta sadiq,ta tafi kenam,ba kuma zata sake waiwayomu ba.....ni zan tsaya dakai a kowanne yanayi da.mataki na rayuwa,bazan bari kasha wahala ba in sha Allahu,bazan bari ka zubda hawaye irin wanda na zubar ba.....kayimin alqawari ba zaka sake zancan maama ba?" Ya qarashe maganar yana ritsashi da idanu.
Kai ya jinjina a sanyaye yana maida jikina ga bango ya jingina,wani abu sosai yaron yakeji da baisan yadda zai fasalta shi ba
"Ka cire uniform din" Ya bashi umarni ya sanya kai yana nufar qofa bayan muryar mama ta karade ilahirin gidan ta cimmasa har dakin nasu
"Yaaya zan tayaka wankin" Sadiq ya fada a gaggauce
"Aah banaso,kayi zamanka" Ya amsa masa yana qarasa ficewa.
Tun daga wannan rana ta sauya lokutan zuwansu makaranta zuwa lokuta na bauta da wahalar ayyukan gidan da basu ratayu a wuyansu ba. Duk wani aiki ta kallafa masa,har takai ta bawa ainihin masu gudanar da aikin hutu tace saita nemesu,hutu ba tare da an yanke musu albashi ba.
Dukka yawa da azabar aikin aikin banza ne a garesa idan aka kwatantashi da maganganu masu dafi da take jifansu dashi. Duk kalmarta guda daya me tsananin guba ce tana kuma same zuba masa dafi da guba me daci ne cikin zuciyarsa. Rashin ko inkula dinta a kansu da dukka dabi'unta basi fiya bashi mamaki ba,saboda ya riga da ya yiwa mata kudin goro gaba daya,tunda ya fara ganin sample daga kan mahaifiyar data tsugunna ta kawoshi duniya kuma. MATA BASU DA IMANI,BASU DA KIRKI,BASU DA TAUSAYI,BUQATAR KANSU CE A GABA DATA KOWA.
Wannan shine rubutaccen abu daya zauna radam cikin kwanyarsa da zuciyarsa,wanda baya jin akwai lokacin da zaizo wanda wannan zai wanke daga cikin kundinsa.
Duk yadda Faruqee ke cikin tsananin fushi da daukar alwashin sai ya gayawa abba idan ya dawo,in yaso ta kamashi ta gutstsira namansa ta kacalcala amma me babban suna ya danneshi ya kuma haneshi
"Maama ma data haifemu ta gujemu,ta gaza tausaya mana?,ta kasa haquri damu?,ina ga mama......mu din ba dolenta bane Faruqee,iya abinci da take sawa ana bamu da gurin kwana ma kawai tayi qoqari"
"Abincin nata ne?,ko gurin kwanan nata ne?,sannan shi kansa abincin waye yake qoshi?,bayan store din gidan nan cike yake da kayan abinci?" Qaramin murmushi ya saki. Duk da qarancin shekarunsa amma kwanyarsa tana aiki yadda ya kamata. Dukka wannan bai cika masa ciwo bafa,abinda maama tayi ya danne dukka wadannan ciwo da zafi da kuma tsaiwa a zuciya. Abu daya ne yakejin yana dab da kasa jureshi,hanashi zuwa makaranta......yana qaunarta yana qaunarta yana qaunarta har baisan iya adadi ba. Abu na biyu indai saddiq dinsa yana lafiya to komai me sauqi ne.
A haka suka debi wata guda cur babu abinda ya sauya. Yadda kowacce safiya da ubangiji zai bullo da ranarsa haka zata fidda wani sabuwar muguntar don quntatawa cuzgunawa a garesu. Duk fushi zafin zuciya da rashin daukar raini irin nashi bai taba daga kai ya kalleta bare ya tanka mata ba,yana duba cewa ta girme masa,gaba take dashi,a qalla ta ninka shekarunsa sau biyu. Duka duka shekarunsa sha shida basu kai adadin shekarun da zai tsaya yana jayayya da babba ba.
A hakane ALHAJI HAMZA KIBIYA ya waiwayo gida cikin iyalansa.
Yaran suna ranshi matuqa,babu kuma ranar duniya da zata bullo ta bace bai tambayeta su ba idan suna waya,amsar kuma daya ce suna lafiya lau. Koda ya buqaci magana dasu tana gabatar masa ne da wani uzurin a kansu.
Wanda ya rigaka kwana zai rigaka tashi. Sanda ya sanar da dawowarsa kaf ta hadasu ta musu mummunar jankunne data tsoratasu ainun. Saidai ko kadan shi bai tsorata ba,don ba komai yake bashi tsoron ba,bare a yanzun da zuciyarsa ke qarasa bushewa da qeqashewa akan komai na rayuwa.
Yadda aka saba haka ta sakar musu,sukaci gaba da zuwa makaranta abba yana kaisu da kanshi kamar yadda yakeyi idan har yana gari.
Ya tsumu sosai,zuciyarsa kuma ta cika da takaici da bacin rai me yawan gaske sanda ya isa class dinsu yaga yadda aka tsere masa a karatu. Kusan ranar duka ya qarar da ita wajen bibiyar dame dame akayi da baya nan?,ya karbi note books na classmate dinsa da dama ya taho dasu gida .
Da yake abba yana nan akwai isashen lokaci 'yanci da kuma hutu,babu tarin aikace aikacen nan marasa dalili marasa kuma tushe ballantana makama,sai ya zauna ya qarar da dukka wuninsa a daki wajen ganin ya daidaita karatunsa dana 'yan uwansa.
Bashi da matsala da saddiq,don ajinsu daya da musaddiq,kuma duk sanda suka dawo gida Faruqee yana hadasu su sake maimaicin karatu tare ta yadda zai zamana ba'a wuce saddiq din ba.
Yana da wata irin baiwar basira ta gasken gasken,sharp brain dake da saurin koyo da kuma riqe abu tun yana dan mitsitsinsa ballantana a yanzun da yake shirin fara shiga shingen samartaka,danyan jini yana zagayawa da gudu a jikinsa. Wannan ya taimaka cikin sati gudan da abba ya musu hutu ya gama kammala komai,ya kuma tarar dasu tamkar dama dashi ake karatun. Sai a sannan ya samu sukuni ya soma dawowa daidai. Saidai kuma a satinne qarshen satin,a yammacin juma'a abban ya tattara ya koma lagos,abu guda daya dake alamta musu zasu koma RAYUWAR GIDAN JIYA kenan cikin gidan.
*********
*_MONDAY_*
Tushen aiki,bai sare ba ya shirya tsaf kamar yadda su Faruqee ke shiryawar,yana shirin Faruqee na rantse rantse da cewar ba abinda zai hanasu fita a makaranta yau din. Ya lallaba kitchen ya hada musu tea kaman yadda ya saba ya dawo ya bawa kowa,saidai ya tsallake me babban suna don yasan bazai sha ba,don kuwa tun daga wancan ranar data zagi abban bai sake ci ko shan wani abu da Faruqee zai dauko musu ba,ya tsani zagin iyaye matuqa,mutum ne kuma me fushi da gudun zuciya,wannan ya sanya yake takatsantsan,akan komai bai fiya zura jikinsa ba.
Fitowa sukayi kamar wancan karon,saidai a yauma sun sameta hakimce a falon. Idonsa yadan lumshe yana addua daga qasan zuciyarsa. Ya tabbatar wannan zaman ta yishi ne saboda su,son a lokutan da abba yake gari kwata kwata nasa ganin qyallinta sai kusan shada zuwa sha biyu na rana.
"Eh......wato akuyar daure an samu sake,to kuzo nan" Faruqee ne na farko daya fara cakewa guri daya,amma ya kama hannunsa ya jashi suka qarasa wajen.
"Me zakuyimin ku?,tunda kuna da uba ya daure muku gindi?,ku tashi kuban waje,ku kuma ku koma ta inda kuka fito a cire uniform azo a kama aiki ko?" Cikin tsananin bacin rai Faruqee ya miqe yana nufar hanyar fita yana kuma qananun maganganu qasa qasa
"Zagina kekeyi farouqu?,ka kuskura ka zageni ubanka zanci wallahi la'ada waje" Ta furta da hargagi tana nunashi da yatsa sanda suke kusa da ficewa daga falon. Abinda ya sanya me babban suna miqewa yana jin nauyi da kuma zafin zaginnan. Ko meye zatayi me ya gamo da iyayensu?,me su sukayi mata idan su din masu laifi ne a gareta?.
"Don Allah mama ki barmu muje muma,idan mun dawo zamuyi miki duk aikin da kikeso"
"Kai.....wasa nakeyi dakai?,zaka tashi ka bani waje ko sai na zagi uwarka mara daraja da ubanka dake qarqashin qasa?" Kamar saukar mashi haka kalamanta suka soki zuciyarsa,har sai daya kasa jurewa ya waiwayo yana dubanta.
"Don Allah mama ko meye,ko meye mukayi miki ki mana hukunci ba tare da zagin iyaye ba......"
"Ubanka da uwarka,shegen yaro me tsaurin ido,kaci ubanka" Ta fada har tana zullo tare da watsa masa daquwa. Ta jima da tsanar dama wannan kamewar tasa,ta jima da tsanar yadda yake da dauke kai da rashin hayaniya akan komai da zatayi masa,duk yadda takai ga tama masa wajen bashi baqin kashi da baqar wahala don ya magantu dukka ya shanye sai a yau din.
Cikin qasa da minti guda launukan idanunsa suka sauya,baice qala ba amma kunnuwansa suna suna iya jin zafafan muggan kalaman da take jifanshi dasu. Ya tako a nutse ya iso gaban saddiq dake durqushe a gabanta ya sanya hannu ya damqi hannunsa ya tasheshi tsaye,abun sai ya masa kamanceceniya da sanda saddiq din ke tsananin roqon mahaifiyarsu akan kada ta tafi ta barsu.
Bai waiwayeta ba,bai kuma dakata ba ya durfafi qofar fita daga falon kanshi tsaye,ba tsoro ba shakka ba kuma shayi
"Ina zakaje,bance ba zakuje makaranta ba?" Ta furta da qaqqarfan sauti. Bai dakata ba bai kuma waiwayo ba ko ya nuna yasan tanayi har ya fice daga falon. A yau ta rushe dukkan wani ragowar kara da dagin qafa da yakeyi mata. Baya wasa da kalmar UBA sam a rayuwarsa,IYAYEN MA guda biyu,abba da Abbey.
https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997
________________________
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA* *09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪
89825722 Nousaiba lawali maradi 1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰 *D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
*Arewabooks:Huguma*
https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997
PAGE 09
Ko Faruqee baisan da zuwansa makarantar ba sakamakon banbancin abinda kowannensu yake karanta,har sai sanda aka fito break.
Har a sannan ranshi a jagule yake,bacin rai kowanne second yana sake motsa zuciyarsa. Faruqee ya sameshi daga bayan makarantar zaune qasan bishiya saman rairayin dake wajen,hannunsa riqe da busashen siririn reshen bishiyar yana tona qasa dashi,ya kafe qasar da idanu kamar me nazarin samar da wani abun amfani daga gareta. Ta gefansa ya zauna,yayi masa tambayar duniya akan ya akayi ya taho makarantar amma ya gaza cewa komai. Na Faruqee ba,tunda ya shiga class din baiyi manana da kowa ba,don bayajin koda ya bude bakinsa akwai wasu kalmomi da zasu iya fita daga cikinsa. Dole Faruqee ya haqura ya kuma tayashi zaman shurun,don dukkansu dama babu me 'yanci ko damar yin break,to inama kudin?,dukka dana transport din da komai ta hada ta kalmashe.
Sai a hanyar komawa yaji komai daga bakin saddiq. Qwafa yaja yana girgiza kai
"Duk yadda kake tunanin matar nan ta wuce nan,duk kuwa yadda zan fasalta maka,ta samu sassauci ne daga garemu shi yasa take abinda taga dama,ace mutum ya shiga shekara ta sha biyar,kana girma amma baka da 'yanci?" Shikam baima iya cewa komai ba har zuwa sanda qafafunsu suka maidasu gida.
Sai da suka gilma ta gaban gidansu kafin su cimma gidan RIQOnsu a yanzu,idanunsa zube bisa fuskar gidan dake garqame da kwado. Take yaji wata matsananciyar kewar gidan da kewar Abbie da jadda suka saukar masa. Duk da suna rayuwa ne cikin matsakaicin matsayi na rayuwa,amma rayuwarsu rayuwa ce me 'yanci da kuma dadi. Duk da suna rayuwa da maama cikin wani baqon hali da murdaddiyar dabi'a.......hakan yafi musu sauqi a kan rayuwarsu ta yanzun cikin gidan RUQO.
Ya janye idanunsa sanda ya dubu daidai wajen da mahaifinsa ya dogaro da qyar ya biyo bayan maaman yana cike da fatan zata dakata daga aiwatar da qudurinta nayin nesa da rayuwarsu,wani zafin akan na dazu ya sake yunqurowa ya mamaye zuciyarsa.
Daga saman balcony din da zata sadaka da ainihin falon suka sameta a zaune ta hakimce. Faruqee ne a gaba,musaddiq yana biye dashi,sai me babban suna da ko qaunar hada idanu da ita bayayi. Zuciyarsa yadda take a zafafen nan tana ayyana masa abubuwa masu dama a kanta.
"Idan ka kuskura ka qaraso na saina sanya an maka dukan tsiya......baka isa ka shigamin gida ba tunda kai din tantiri ne mara kunya.....nan gaba kadan shaye shaye zaka farayi da daba,kaga kenan ka samu hanyar da zaka hallakani a banza" Ta fada tana miqewa tsaye.
Dukka su hudun sukayi carko carko suna dubanta da jin kuma wani sabon bala'in daya tunkarosu kuma bayan na dazu da safe.
"Kai har ka isa na fadi magana ka sabamin bare ka maidamin?,don an zagi uwarka da ubanka,su su waye da ba za'a zagesu ba?,wato gaka kai me zuciya ko,to an zagesu din na kuma zagi banza da wofi".
Da qarfi ya damqi hannun saddiq ya kuma soma ja da baya yana janye jikinsa daga wajen
" Yauwa gwara daka fahimta,don wallahi kabar gidan nan kenan,tun yanzu kana tsayarmin ina ga nan gaba idan ka gama zama balagagge?".
Da sassarfa Faruqee da har ya isa bakin qofar falon ya soma saukowa yana takowa zuwa garesa ganin suna nufar gate din fita daga gidan yana qwala masa kira da niyyar tsaidashi
"Aisai ka bishi kaima don ubanku,na fiku iskanci qananun balagaggu" Ta furta tana komawa saman kujerar ta zauna
"Bar nan gurin" Ta kwatsawa musaddiq daya mace a wajen saboda tsoro da mamaki tsawa,baiyi wata wata ba ya juya shima yabi bayan 'yan uwansa.
Bai iya tsaidashi ba har sai da suka isa qofar gidansu dake garqame. Sai sukayi carko carko suna kallon kallon shi dashi. A yadda ya hangi kwantaccen fushi da bacin rai akan fuskar me babban suna sai ya rasa da wadanne kalmomi zai iya shawo kan me babban suna?,wacce kalma ce zatayi masa aiki?.
"Kayi haquri kazo mu koma,tunda gidan abba ne ba nata ba bata isa ta hanaka zama ba,yau ko kasheni zatayi saidai ta kasheni" Wani irin kallo ya yiwa Faruqee,ga mamakinsa murmushi ya gani ya subuce masa.
Da wani irin zafi ya waiwaya ya dauko dutsen dake yashe gefan malalen simintin dake gaban gidan nasu,har tsoro ya kama Faruqee yaja da gefe,sai yaga ya doshi qofar gidan,ya kama kwadon dake jiki ya fara bugeshi baji ba gani.
Tsakiyar azahar ne,wannan ya sanya ba yawaitar jama'a a layin bare a samu me dakatar dashi. A yanayin da yakejin zuciyarsa da kansa a ciki,bayajin akwai ma wanda ya isa ya dakatar dashi din sai MUTUM DAYA TAK A DUNIYA.....ALHAJI HAMZA KIBIYA.
Zare kwadon yayi ya watsar gefe,kansa tsaye kuma ya soma cusa kai cikin gidan ba tare daya damu da yana datti ko qurar data lullube qofar ba.
Wannan shine mafarin komowarsa gidansu......tushensa......asalinsa da yaji yafi masa kwanciyar hankali sau dubu akwan kwanansa cikin babban bedroom din gidan alhj hamza dake dauke da wuta 24/7 da kayan alatu na rayuwa.
Tun a asalin halittarsa shi jajirtacce ne tsayayye da bai yarda da faduwa ba......sanda komai ya dinga faruwa kuma daki daki,sai zuciyarsa ta qara qeqashewa ta kuma tsaya kyam......ya karantawa kansa da kansa cewar shine uwa kuma uban kansa da dan uwansa sadiq.......shine gatan kawunansu,ya fidda kowa daga cikin zuciya rayuwarsa dama hasashensa. Wannan ya sanya tun rana ta farko da suka dawo gidan bai kuma karbar koda ruwa daga gidan alhj hamza ba. Duk da yadda ran Faruqee ke baci da yadda yake wofantar da komai da ya kawo musu din kuwa koda ruwan sha ne. Da kansa ya tsaya,sadiq na debo ruwa shi kuma yana wanke komai da yayi saura na gidan wanda zasu iya amfani dashi. Cikin kwanaki uku kacal ya fara Qwadago.
Duk wani aiki da zai samar masa kudi......komai wuyarsa kuwa muddin halas ne yana karba yayishi hannu bibbiyu. Da wannan din ya dogara.....da dan abinda yake samu din ya dauke musu abinci dama abin sha......idan faraga ta samu harda kudin transport na makaranta koda na zuwa kadai ne banda na dawowa.
Sauyawar yanayi da kuma tsarin rayuwarsa ya sake canxashi gaba daya. Yana tsananin son karatu kowanne iri ne,na addini dana boko gaba daya
*_TURQASHI_*
*_BIGI SAI BIGI_*
*_BABBAN GORO SAI MAGOGIN QARFE_*
*_TASTED AND TRUSTED_*
*_TASTED AND TRUSTED_*
*_TASTED AND TRUSTED_*
*_Kina da burin samun ingantaccen TURAREN WUTA me TSANANIN KAMA GURI?_*
*_TURAREN WUTAR DA ZAKI SANYAWA DAKI AMMA HATTA DA LABULAYE KAYAN SAWAN DAKE SAQALE A DAKIN SU KAMA DA QAMSHI?_*
*_TURAREN WUTAR DA KUJERUNKI ZASU KAMA QAMSHI DARAM?_*
*_KI BANKADA LABULAYENKI KIJI SASSANYAN QAMSHI?_*
*QAMSHI IYA QAMSHI 24HR*
*HUMRA ME TSAYAWA A ZUCIYAR ME GIDA*
*NASAN ZAKI TAMBAYI KANKI A INA ZAN SAMU WANNAN?*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER*
*_tayi muku tanadin abubuwa da yawa irinsu_*
Khumra Turaren wuta Kulaccam Lablab Oil perfumes Original musk tahara Multipurpose spray
*karki kuskura kada kiyi ganganci ayi babu ke,kai tsaye tuntubeta ta wannan number*
08032119803
Ko ki lalubeta ta nan👇🏾👇🏾👇🏾
*Instagram handle_incense by kabo daughter*
*Facebook_kabo daughter*
*Twitter_kabo daughter* ________________________________
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA* *09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪
89825722 Nousaiba lawali maradi 1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰 *D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
*Arewabooks* https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997
PAGE 10
Baya wasa da islamiyya,amma wahala da nauyin kansa dana saddiq ya sanya ya sallamawa zuwa islamiyya. Duk da haka bai sare ba,ya lalubi makarantar magariba ta manya ya soma zuwa don karantar litattafan addini,duk kuwa da nisan zangon tafiya dake a tsakaninsu.
Su kansu ba 'yantattun 'ya'ya bane cikin gidan mahaifinsu......amma duk da wannan ya gaza barin me babban suna yakuma qyaleshi kamar yadda ya fuskanci yana da muradin hakan. Duk da basu da 'yanci ko fada aji a gidan......amma hakan baya hanashi dauko abinci daga cikin nasa kwanon data qayyade musu cikin gidan ya kawo don suyi tarayya suci tare,amma koda wasa me babban sunan bai taba dangwala yatsarshi a ciki ba.
Abun yana ma Faruqee zafi da ciwo matuqa,har daga qarshe hakan ya sanya suka samu sabani
"Don mama tayi maka laifi ai ba abincinta bane,abincin abba ne wanda har yanzu a nasa zaton kuna cikin gidansa ne cikin aminci bisa kulawarta,iyakarta da abincin nan tazo ta diba itama taci,don ko dafawa ba ita ke dafawa,larai ce......kuma ita ke qaramin yawan abincin a boye ba tare da saninta ba,to indai bawai nima gaba da fushi kakeyi dani ba banga abinda zai hanaka ci ba.....idanma kai ba zakaci ba....kada ka sake hana saddiqu yaci,kai ka zauna haka can ta matse maka". Busashen murmushi ya saki yana jin yadda cikinsa ke qugin yunwa,don yau ba wani abun kirki ya samo a aikin ba,wannan ya sanya basu wani qoshi ba wunin ranar sur.....ga kuma tafiya makaranta a gabansu gobe juma'a.
Yadda Faruqee yayi fushi ya kuma dauki zafi da abun ya sanya yake barin saddiq din suna hadaka dashi. Shikam yasan bazai taba iya sanya abincin cikin bakinsa ba. A duk sanda yayi yuqurin hakan sai maganganunta su dawo musu kar kar cikin qwaqwalwa
"Tunda uwarka ta zube ku ta tafi ta barku,banga uban da zai iya zama daku ba......uwarku ma ta barku ballanta wani?" Aduk lokacin da zai tuna da irin wannan maganar a take yakanji komai ya fita a kansa ne,tsananin baqinciki ya mamaye walwalarsa,wata irin wuta me zafi na taso daga qasan zuciyarsa da ruhinsa dangane da imaninsa. Ta wani fuskar da mama da sauran 'yan unguwa dake jifansu da muggan kalamai sai yaji sam baya jin zafinsu ko kadan,da uwa da uba da kuma dangi ake ado,su kuma basu da ko guda daya!. Ya tabbata lallai su din cikakkun marasa gata da galihu ne,kuma kowanne suna aka kirayesu dashi sun cancanta.
Yayi imani inda har jadda tana raye.....koda sunfi kowa talauci da matsin rayuwa......to babu shakka zasu zamo na sahun gaba gaba wajen zama yaran da sukafi kowa samun gata na kulawa da soyayyar kaka. Saidai Allah baya barin wani don wani yaji dadi,ya tabbatar haka ubangiji ya tsara musu tasu DUNIYAr,haka kuma yaso ganinsu a cikinta.
A wannna tafiyar abba yayi nisan kiwon da ya jima baiyi irinsa ba. Yana rayuwa bisa yaqinin lallai gidansa da marayun Allahn daya dauka riqo suna lafiya,tunda duk sanda zaya kirata hakan take gaya masa,sannan lokaci bayan lokaci tana hadashi da musaddiq,shima kuma
"Lafiya qalau muke abba" Shine amsar da yake bashi bisa jagorancin mummunan gargadi da idanuwa da maman take aike masa duk sanda suke wayar. Faruqee ne bata taba yarda ta bawa wayar ba,sai a wani yammaci da abban yace ya jiyo muryarsa ta hadasu.
"Lafiya amma ba qalau ba amma.....muna buqatar ka dawo a kusa abba" Bata iya barinsa ba ta fusge wayar daga hannunsa cikin hanzari ganin yana niyyar sauka daga layi.
Maganar ta tsayewa abban a rai,ta kuma sanyashi yaji dukkan hankalinsa yana tarkatowa yana yowa gida. Duk kuwa da akwai sauran abu daya tsara zaiyi a can din,amman sai yaji komai ya fita a kansa tahowarsa gida ce abu na farko da yake kwana yana tashi dashi.
*******Kusan dukkansu jan qafafunsu sukeyi,zafin rana yunwa ga gajiya dake tattare dasu. Akwai nisan tazara me dan dama tsakaninsu da makarantar wanda suke shanyeta a qasa daga tafiya zuwa dawowa. Babu ranar hutu a garesu idan ba asabar ko lahadi ba. Ga me babban suna kuwa,baya gane asabar ko lahadin cikin rayuwarsa da DUNIYARSA. Rayuwar tasa gaba daya a birkice take,bashi da wata dogon hutu daya wuce makaranta zuwa neman kudin abinci.
Yayi wani irin duhu,dukkan hasken fatar nan da suka gado babu shi,ya rame daga ainihin halittarsa zuwa wata halitta ta daban.
Tun daga nesa ya soma hangen wani abu da yayi matuqar girgiza hankali da kuma tunaninsa,ya sanya dukkan wani tunani nashi ya fara sauka daga kan layi,ya kuma daina gane me Faruqee daketa faman bashi labari yake fadi.
Wata qurace take tashi daga wani sashe na gidansu gami da qarar zubewar bulalluka. Gefe guda akwai tsaiwar tsirarun mutane da kuma yara wadanda basa raina abun kallo,hakanan basa bari abun kallon ya wucesu kamar qanqantarsa.
Zame hannunsa yayi daga jikin na Faruqee,a gaggauce da kuma hanzari ya soma tattaki har zuwa inda aikin ke gudana.
"Gidanmu ne fa.....me yayi ake rusheshi?" Ya furta bayan ya tabbata ya tsaya gaban mutanen dake gabatar da aikin futu futu cikin qasa da qura.