A d u n i y a ta complt by huguma - Chapter 4
A d u n i y a ta complt by huguma Chapter 4: A d u n i y a ta complt by huguma Chapter 4. Dukkansu suka waiwayo suna dubanshi,kafin daga bisani wani dan…
4,450 words
Dukkansu suka waiwayo suna dubanshi,kafin daga bisani wani dan tsamurmurin mutum dake sanye da milk riga da wando na shadda,da kuma babbar riga ta koriyar shadda gami da baqaf hula daya karkatata gefe ya qaraso gabansa yana dubansa. Bakinsa cike da gashin baki,kai kace daya daga cikin qabilun da suka shude ne shekaru aru aru.
"Yaro me kake cewa?" Ya fadi yana saba babbar rigar da a zahiri an tafka babbar asara wajen ware shaddar aka masa rigar da ita gaba daya,don kuwa yadin ya masa yawa,alamu ma suna nuna kamar rinjayarsa takeyi
"Gidanmu ne nace,me yasa kuke rushe mana gida?" Ya sake jefa tambayar ga mutumin yana tsareshi da ido da zummar jin ba'asin maganar.
Qaramar dariya yadan saki yana sosa gashin bakinsa da alama qaiqayi yake masa.
"Yaro man kaza......kai!bakasan tsohuwarka ko ince uwarka ta karbi rabin kudin gidan daga hannun matata ba sanda zata bar garin?". Fuska da idanu gaba daya me babban suna ya yamutse yana duban mutumin cike da zallar mamakin da kwanyarsa ta gaza dauka.
" Ko da yake ma.ba fahimta ai zakayi ba,wannan zancan na babanka ne inda yana raye,ba abinda zaka gne yaro" Yana kaiwa nan sai ya juya yana dubañ mgainan
"Kuyi ku raba ku zagaye mana haqqinmu" Da hanzari yasha gaban mutumin jin kalaman da yake sake maimaitawa
"Kada su sake taba mana gida,don nan vidan ba gudan mamata bane da zata saidashi,gidan mahaidinmu ne daya ginashi da guminsa,ta nemeta ta biyata kudinta amma mu ba ruwanmu" Tsaiwa yayi yana qanqance idanu hadi da duban me babban suna
"Kai wannan yaron da alama zakayi tsaurin idanu,da alama dai abinda ake fadi a kanka gaskiya ne......to ai ko kai yanzu ba zakace ga inda uwar data haifeka take ba,tunda ta bazama yawon duniya ta watsar daku.....". Kalmar ta sokeshi qwarai kamar kowanne lokaci. Duk a iya adadin fadar da akeyi bai taba yunqurin kare musu jifan da ake musu da kalmar ba,amma a yau din sai yaji koda sau daya yana da sha'awar huce musu wannan takaicin shi da saddiq.......yana da marmarin maida martani koda sau daya ne tak......amma baya sha'awar bata kariya ko wanketa daga muggan kalaman mutane a kanta,don bashi da abun cewa a kanta,kwata kwata dukkan wata soyayya qauna ko tausayi na fil'azal a tsakaninsu yanxun baya jin akwai burbushinsa,abinda ya sani kawai ya kare kansa ya kare saddiq dinsa
"Ba abunda ya shafemu da inda taje ko inda take.......kaman yadda ba ruwanmu da karbar kudinku da tayi don nan gidan mallakin mahaifinmu ne mallakinmu......abinda muka sani kawai shine mu din halastattun 'ya'yane da aurar ya samar......"
Daya daga cikin ma'aikatan wanda kuma gidan su yake ta qarshen layinsu wanda ke tsaye gaban tsani ne ya bushe da dariya
"Dame kwado yafi gaya ku da shegun?,dame kuka fisu?" Yana kaiwa nan ya dauki qatuwar gudumar da suke dukan saman ginin da ita ya soma taka matattakalar tsanin yana hayewa da zummar ci gaba da aikinsa na ragargazar ginin da mahaifinsu ya kwashe lokaci yana zuba kudadensa wajen qawata musu shi. Ya sadaukar da kudi da qarfinsa wajen samar dashi,ya sanya burinsa akai na ganin sun rayu a cikinsa cikin aminci da kwanciyar hankali.
Kwata kwata kasa jurewa yaji yayi da mummunar kalmar da yaji ya jefesu da ita. Sanda ya daga gudumar zai doka......daidai lokacin ba tare daya ankara ba ya sanya hannu ya fusgoshi sai gashi qasa warwas!. Abinda ya sanya dukka jama'ar dake tsaitsaye a gefe tun dazun basuyi magana ba yunqurowa,masu salati sunayi masu yunqurin tayar da babba magini sunayi.
Wani irin mamakin sauyar rayuwa da mutanen dake rayuwa a cikinta ya kamashi. Da idanu yake binsu
*_TURQASHI_*
*_BIGI SAI BIGI_*
*_BABBAN GORO SAI MAGOGIN QARFE_*
*_TASTED AND TRUSTED_*
*_TASTED AND TRUSTED_*
*_TASTED AND TRUSTED_*
*_Kina da burin samun ingantaccen TURAREN WUTA me TSANANIN KAMA GURI?_*
*_TURAREN WUTAR DA ZAKI SANYAWA DAKI AMMA HATTA DA LABULAYE KAYAN SAWAN DAKE SAQALE A DAKIN SU KAMA DA QAMSHI?_*
*_TURAREN WUTAR DA KUJERUNKI ZASU KAMA QAMSHI DARAM?_*
*_KI BANKADA LABULAYENKI KIJI SASSANYAN QAMSHI?_*
*QAMSHI IYA QAMSHI 24HR*
*HUMRA ME TSAYAWA A ZUCIYAR ME GIDA*
*NASAN ZAKI TAMBAYI KANKI A INA ZAN SAMU WANNAN?*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER*
*_tayi muku tanadin abubuwa da yawa irinsu_*
Khumra Turaren wuta Kulaccam Lablab Oil perfumes Original musk tahara Multipurpose spray
*karki kuskura kada kiyi ganganci ayi babu ke,kai tsaye tuntubeta ta wannan number*
08032119803
Ko ki lalubeta ta nan👇🏾👇🏾👇🏾
*Instagram handle_incense by kabo daughter*
*Facebook_kabo daughter*
*Twitter_kabo daughter* *D U N I Y A TA*
*_H U G U M A_*
PAGE 11 _____________________________
*_CIKIN DUBU DABAN TAKE_*
*_TABBAS AKWAI TURARE AKWAI MUNA TURARE_*
*_NA GWADA NA GANI_*
*_YA SUBHANALLAHI_*
*_QAMSHI NA TASHIN KAN ME GIDA_*
*_QAMSHIN DAKE DAGAWA KISHIYA HANKALI_*
*_NATACCEN QAMSHI DAKE KAMA GURI DARAM_*
*_WANNE GANGANCI NE YA SAKAKI TSAIWA SANYA?_*
*_ME KIKE JIRA?_*
*WANNAN DIN GUARANTEE NE FA*
*TASTED AND TRUSTED 100% PERCENT*
*KI SIYA KI GODEMIN HAJIYA*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER*
*_DUNIYAR TURARE ME BADA ASALIN QAMSHI ME KAMA JIKI DA MUHALLI,NUTSATSEN QAMSHI ME SANYAYA ZUCIYA DA DADEWA A WAJE_*
*_IDAN KINA DA MATSALA KINA NEMAN TURARE ME KAMA WAJE,KINASON SAKEWA OGA SABON QAMSHIN DAKI DA PARLOR,KE KANKI KINASO KI SHIGA WAJE A DINGA TAMBAYAR WACE TA ISO NE?_*
*MAZA MAZA JEKI KI GWADA WANNAN_*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER 08032119803*
*_zaki dariya za kuma ki godemin_*
*_gani ya kori ji_*
*hakanan sai an gwada akan san na qwarai* ___________________________
Daga sanda ya jawoshi ya maidoshi qasa......daga sannan yaga iya yawan adadin mutanen dame wajen wanda sam baiyi zaton sunkai haka ba,bai dauka suna da yawa haka ba.....amma duk da wannan yawan nasu babu wanda yayi yunqurin yin wani anu guda daya sanoda ceton rayuwarsu da cetin ginin gidan dashi kadai suma!mallaka a rayuwarsu wanda zasu nuna suce ya fito daga jini da gumin mahaifinsu?. Me yasa al'umma ta sauya?,ya dinga duban fuskokin masu luguiguita zancan da kambama abinda ya aikata din,dukkansu suna tsaye sanda ake himmar rugurguza mafaka guda daya tasu da tayi saurs,ba wanda ya tallafa,ba wanda ya dakatar. Kusan dukkansu fuskokinsu bayyanannu ne a idanunsa,fuskokin daya saba gani sunzo neman taimako wajen mahaifinsu,wanda bai taba gazawa ba da taimaka musu da abinda Allah ya hore masa,amma yau tsantsar butulci irin na dan adam sune suka juye suna masu tsaiwa suna kallon wasy na shirin zaluntarsu.
A sanda yayi nisa da wannan tunanin a lokacin babba yayi amfani da wannan dama yakai masa duka,dukan da yazo masa a bazata banda jin hucin wucewarsa da yayi da hucin hannun Faruqee daya tare masa dukan. Yaja baya yana maida hankalinsa jikinsa,sai ya taka dutse ya kuma yi taga taga ya fadi da baya,wannan ya sanya babba ya sake yunquro masa da nufin turmesheshi cikin baraguzan ginin gidan da suka fara saukewa,sai Faruqee shima ya taso ya rufa masa baya da zummar baiwa me babban suna din dauki.
Cikin zafin nama fushi da kuma taurin kai gami da kafiya da taurin zuciya Shima ya yunqura ya miqe yana jiran qarasowar babba. Idanunsa a lullube suke da bacin rai,baya hangen nisan tazarar shekaru da kuma girman jiki dake tsakaninsa dashi.
"Kai.....kai......dakata.....meye hakan?" Muryar nan me cike da kamala tausayi da dattako ta ratso gurin. Kowa ya tsaya ya waiwaya yana duban saukowarsa daga motar zuwa takowarsa cikin fusassun duwatsun gurin. Alhaji hamza kibiya ne idanunsa na kai kawo tsakanin Faruqee me babban suna da kuma ginin gidan nasu.
Mutum ne me cikar kamala da dattako,wanda ya riqe mutuncinsa da kyau. Yana daya daga cikin dattijan unguwa dake bada Umarni ko shawara abi,musamman da yake yana da abun hannunsa wato kudi abokan tafiya.
Kunya tadan kama manyan dake wajen da basu hana ba sai tsaiwa kallo da sukayi,wanda sun tabbatar idanuwansa sun gansu gaba daya.
Bai tsaya sauraren barka da zuwan da suke masa ba,sai qoqarin qarasawa gabansu kawai da yakeyi bayan yace da saddiq da musaddiq su tsaya daga baya,wanda dukansu suka tsorata tun farkon rigimar,to amma basu dame kawo musu dauki bare suyi hanzarin garzayawa su kirashi ko zai cecesu.
Ta gefan babba dake tsaye yana kade jikinsa cikin jin nauyi yana kuma huci qasa qasa ya wuce,ya qarasa inda me babban suna ke zaune warwas ya miqa masa hannu ya tasheshi tsaye.
Yana tsaye a gabansa ya bashi handkerchief yana karkade jikinsa. Idanun alhaji hamza a tsaye sosai jikin uniform din nasa da suka fara alamta masa wani abu.
"Me yake faruwa a nan ne?" Ya watsa tambayar ga tsamurmurin mutumin daya lura kusan shine baquwar fuska a wajen.
Baiyi qasa a gwiwa ba ya kwararowa alhaji hamza bayani kaman yadda ya yiwa me babban suna,bayanin da maimaicinsu yake sanyashi jin kamar ya rufe idanunsa ya budesu ya ganshi ba'a wajen ba,kamar ya rufe idanu ya kuma budesu ya tsinci kansa haihuwar wata uwar daban ba maama ba......kaman ya tsugunna qasa ta hadiyeshi ya huta.
Sai daya kammala bayaninsa gaba daya sannan alhaji hamza ya gyada kai
"Nine a matsayin wakilin yaran nan,kuma bana nan,yanzu haka shigowata garin kenan,inaso a dakatar da aikin nan,ka kuma sameni gobe mu zauna muyi magana akan batun da kazo dashi,ina da buqatar qwaqwarar shaida da hujja ka taho da ita,idan ya tabbata da gaskiyarka,zaku fadi iya kudin data karba zan biya na fansarwa yaran gidan da suka gada,idan kuma aka rasa daya daga ciki kasan qarshen case din basai na qarasa ba" Abba yayi magana yana janye hannun me babban suna sunayin gaba. Ko daya bai amsa maganar mutanen ba,wanda ba abinda ransa keyi game dasu sai baci da soyuwa. Rayuwa ta lalace,DUNIYA ta zama wani abu na daban?,babu me kawar da barna?,babu me rungumar dan wani?,kowa nasa ya sani.
A baya suka bishi yana riqe da hannun me babban suna ba tare da yace komai ba.
Motarsa ya qaraso da ita bakin gate din gidan nasa sannan ya kulleta,ya soma takawa zuwa ciki yana kiran Faruqee. Cak ya tsaya daga gate din gidan shida saddiq suna kallon abba Faruqee da musaddiq suna wucewa zuwa ciki.
"Me babban suna" Abba ya ambata sanda ya sanya qafarsa ta farko cikin gidan
"Abba baya shigowa gidan mu yanzu" Musaddiq ya fadiwa babban qasa qasa yana tsoron kada mama dake can ciki ta jiyoshi. A mamakance ya kalli musaddiq sannan ya waiwaya ya kalli me babban suna dake tsaye daga baya kansa a qasa.
Yana jin nauyin abba qwarai,yana kuma jin nauyin saba umarninsa,amma bayajin qafafunsa zasu sake taka wannan gidan har abada kamar yadda yaci alwashi.
"Faruqee meye haka?" Abba ya tambayi farouq cikin rashin fahimtar abinda ke faruwa
"Abba ya koma gidan su,mama ta koreshi". Wani abu yaji ya sauka tsakiyar kansa har kaman qafafunsa suna neman yin rawa.
" Ya salam ya Allah" Ya fada a fili,tun yaushe ta aikatawa.marayun Allah haka?,ashe shi yasa hankalinsa yayi qololuwar tashi sanda ake taba ginin gidan nasu tunda yana kallonsa a mafaka guda daya duk duniya data rage musu?,ashe shi yasa yaji ya kasa samun nutsuwa kwata kwata a kwanakin?.
"Muhammadu" Abba yakirayeshi kai tsaye da cikakken sunansa da ba kasafai yake kiransa dashi ba.
Kansa ya daga,suka hada idanu da abban da idanunsa da suka jajur
"Zoka wuce muje ciki" Ya sake bashi umarni nakai tsaye.
Umarninsa dai dai yake da umarnin mahaifinsa da yayi silar kawoshi duniya,tabbas idan zaiyi musu da gardama wa mahaifinsa to la shakka zai yi wannan wa abban. Amma fa tabbas inda ya san abban zai ankara d wuri akan baya biye dashi,allai da yayi nisa da gurin tunda wuri,tun gabanin yayi masa umarnin shiga gidan irin haka.
A gaba ya jeresu yana biye da bayansu har zuwa sanda suka isa ainihin falon gidan. Daidai sanda take fitowa daga kitchen hannun ta dauke da jug data tanadarwa abban lemo,haka kuma tasha ado da lace bakinta ya cika taf da lipstick ja shar dashi.
Har cikin zuciyarta takejin bala'i da masifa suna tsarga mata. Yau kam dukkan juriyarta da karar da take masa ta qare muddin dai yace dawowa yayi da yaran nan masu zubin mayu. Iya zamanta da yaranshi ma ya isheta jarrabawar rayuwa bare ya qaro mata yaran da batasan matsayinsu a gidan ba,suba agololi ba,su kuma ba yaran masu gida ba.
A gaggauce ta isa dining ta ajjiye jug din idanunta bisa fuskarsu
"Ku kuma daga ina?,daga dawowarsa shine kuka biyoshi saboda tsabar maita?" Ta furta tana zazzare idanu hannuwanta riqe da qugunta.
"Ya isa da Allah asama'u" Abba ya fada da hanzari yana daga mata hannu,don wasu maganganun bai dace ace an yisu gaban yaran ba,koda saddiq da musaddiq basu da shekaru sosai,ai Faruqee da me babban suna zuwa yanzun sun fara kammala hankalinsu tunda sun shiga shekara ta goma sha biyar.
"Ku wuce dakinku ku canza uniform"
"Ba inda zasu a gidannan dai wallahi,basu da daki kuma basu da matsugunni tunda dai bakai ka haifesu ba.....danginsu ma sai watsar dasu wai ballantana kai abba?" Ta fada tana sake matsowa hanyar da zasu wuce zuwa dakin
"Abba babu kayansu ko daya a gidan nan fa.....baka dade da tafiya ba ta koresu,tunda.ka tafi suma suka koma kwana a gidansu" Faruqee ya fada gaba gadi,yana jin cewa shima yau yakai bango,komai ta fanjama fanjam.
"To baqin munafuki,na koresu din,kuma wallahi wallahi koni ko su a gidan nan" Maganar faruqee ta dagawa abba hankali. A cikin gidan da bashi da maraba da kango suke kwana?,gidan dake cike da memories na iyayensu da suka gushe?,ta yaya suke iya bacci su biyu rakkin wanda har zuwa yanzu ba wanda yakai shekara sha bakwai ma bare sha takwas a tsakaninsu?.
"Abba abinci ma aiki me babban suna yakeyi a tasha kullum yana kawo musi gari ko dan wanke" Musaddiq ya fada a dan tsorace yana satar kallom fuskar mama bayan ya riqe hannun mahaifinsa da kyau yana boyewa a jikinsa.
Sosai maganar ta dakeshi,zaka fahimci hakan ta yadda kalolin idanunshi suka sauya duk kuwa da tarin haqurinsa. Farat daya yaji asama'u ta fita a kanshi gaba daya. Duk matar da zata iya yiwa maraya haka tabbas ya sani nashi yaran ba zasu tsira ba wadanda suke da uwa da uba,Allah ne kawai mafi sanin haqiqanin abinda su kansu su musaddiq din suke kwankwada daga hannunta idan baya nan.
Bai taba barin garin ya tafi gurin neman kudinsa hankalinsa a kwance ba tun daga ranar daya saki mariya. Tun daga ranar daya rabu da mariya bai sake samun nutsuwa cikin gidansa ko aminci akan 'ya'yansa ba.
"Asama'u?,bakya tsoron fushin Allah kike cutar da marayin Allah?"
"Ni babu abinda Allah zaiyimin,don su din ba dole na bane,wadanda ma suka zame musu dole sun yakicesu sun zubda bare ni da aka tsinceni da haqorana talatin da uku.....don haka wallahi bazanyi riqonsu ba,yaranka dai ba yadda na iya dasu saboda ubansu nake aure"
*_TAFIYA DA GWANI ME DADI_*
*ZAFAFA BIYAR*❤🔥🥰 *zafafa biyar*❤🔥🥰 *ZAFAFA BIYAR*❤🔥🥰
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA*
_FITATTUN GWARAZAN MARUBUTAN LITATTAFAN NAN NE MASU DAUKE DA SALON LABARAI IRIN DABAN DABAN BISA TSARIN TAFIYA DAYA SUKA SAKE YUNQUROWA☺️😇_
_WADANDA SUKA SABA GABATAR MUKU DA QUNSHIN ZAFAFAN LITATTAFAI DA LABARAI MASU TAFIYA DA HANKALI DA TUNANI_
*_IRINSU_*
BURI DAYA INAYA AMEENATU DALAAL BAQON MUNAFUKI KAIMIN HALACCI TSUTSAR NAMA WUTSIYAR RAQUMI BAQAR INUWA SIRADIN RAYUWAR BILKISU TABARMAR QASHI KUFAN WUTA
*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*
*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*
*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*
*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*
*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*
*ZAFAFA BIYAR*
*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*
*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*
_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA* *09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪
89825722 Nousaiba lawali maradi 1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰 *D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
*Arewabooks:Huguma*
https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997 ___________________________
PAGE 12
"Qarya kike,wallahi tallahi yarana dinma ba riqonsu kikeyi ba,koda basu taba gaya min ba amma na tabbatar ba irin riqon uwa da 'ya'yanta kike musu ba.....irin riqon da mukayi alqawarin zakiyi musu" Qaramar shewa tadan saki tana tafa hannuwanta hadi da qare masa kallo tsaf ido cikin ido
"Dama waye yace maka uwar wani zata iya riqon dan wani tamkar nata?,au ashe bakaji abinda bahaushe ya fadi ba kenan,riqon uwar wani da dan wani ai sai Allah" Mamakinta ne ya qarasa kasheshi,ransa yakai qololuwar bacin da har ya mance da yara ma a wajen
"Haka kika ce?,to bari kiji na gaya miki......muddin ba zaki riqe wadannan marayun ba saidai kisan inda dare yayi miki" Idanu ta fidda tana kallonsa cikin maqurar mamaki,wato ya fifita matsayin yaran a kanta kenan?,ta yaya zata ma zauna ta karbi wannan fifikon?,ya za'ayi ma tayi sake har yaga warginta haka?,a gaban yaran ya kafa mata irin wanna sharadin?,ai duk yadda taso ga son zama dashi ba zata karba irin wannan mulkin qarfa qarfan ba.
Hannayenta ta sake hadawa ta tafa ta kuma riqe qugunta da kyau tana dubansa
"Wallahi kaji na rantse bazan riqe su ba,har nakanma na gaji ai bamuyi abinda zanzo nayi kenan cikin gidan nan ba"
"Tunda kuwa kikace haka saidai ki qara gaba" Gabanta yadan fadi,amma batajin zata bari ya gano lagonta
"Hakan shi yafi sauqi,amma bazanje nayita zama da dakon aurenka ba,ka gayan meye matsayin tafiyar tawa idan na yita?" Ta kuma tambaya tana watsa hannuwa
"Na sakeki saki biyu"
"Innalillahi wa 'inna ilaihi raji'un" Me baban suna ya furta yana saka hannuwansa dukka biyu ya toshe kunnuwansa,sannan ya koma ya sulale yana zama tsakanin kujerun falon.
"Tafi nono fari,sai me?,dadin abun ai ba kai kadai bane namiji" Ta qarasa fada tana ture kujerun dining din ta sauka a gaggauce zuwa dakinta gabanta yana wani irin bugawa da sauri da sauri.
Daga su har abban ba wanda ya iya cewa komai,falon ya dauki shuru kawai sai motsinta daga can uwar daki tana hada kaya gami da sakin maganganu wanda basa iya jin ainihin me take fadi.
Mintuna goma kacal ta fito janye da akwatunta da qaramin mayafi yafe a kafadarta. Daga inda yake ya daga rinannun idanunsa yana kallonta. Abba ya saketa ne saboda su,me yasa abban zai saketa saboda dalilinsu?. Fitowarta sai tayi masa kama da fitowar mahaifiyarsu sanda take shirin barin gidan mahaifinsu.
Me yasa ake tafiya ne ana barinsu?,farinjini ne basu dashi ko kuwa?,ko wani maqalalle kuma boyayyen abune dasu?,me yasa iyaye mata basa tausayinsu saidai maza?.
Baisan yaushe ya yanke wannan hukuncin ba,shidai ya tsinci kansa a gaban mama ne,cikin matuqar tashin hankali da karyar da muryar yake fadin
"Don Allah mama kiyi haquri,kada ki tafi saboda mu......"
"Na rantse da Allah zan zabga maka mari idan baka bani hanya ba,munafukan banza da wofi wadanda babu alkhairi sam a jikinsu sai masifa da balai nau'i nau'i,ai daya sakenin sai ku ya aureku,gaku nan gashi,kara da kiyashi daukan mara sani" Sai ta wuce abinta ta barshi da zafafan maganganun daya gaza mancewa dasu.
"Dawo ka zaun me babban suna,waye yace maka ka bata haquri?,waye yace maka zan iya zama da ita bayan bata sonku?,ba zata iya zama daku ba?,ba zata iya haquri daku ba?......in sha Allah na muku alqawarin dawowa da mamanku nan da sati guda kacal" Maganar data Haifar da wani irin farinciki mara misali a zuciyar faruqee musaddiq harma da sadeeq din da baima mamansu musaddiq din farin sani ba. Yayin da me babban suna yake binsu kawai da idanuwa,don kunnuwansa da zuciyarsa harma da qwaqwalwarsa sunyi nisa qwarai da abinda ke wakana a falon.
Jarin maganganun mutane masu tsananin dafi daya soma girma da jinsu yaketa aunawa. Kullum kwanan duniya wayewar gari zuwa faduwar rana sai yaci karo da wata mummunar kalma da zata zamewa zuciyarsa tabo wadda ta shafesu da mutuncinsu,duk kuma MAAMA itace sila,dama uwa tana iya zama silar bacin suna da rayuwar 'ya'yanta?. Tambayar da amsarta ta kasa samuwa a gareshi kenan,musamman lokacin da MARIYA mahaifiya ga faruqee da musaddiq ta dawo ainihin dakin aurenta da zummar riqe yaranta harma da marayun Allah MUHAMMAD DA ABUBAKAR SADDIQ
***************
Faffadan tsakar gida ne ma'abocin yalwa da kuma tarin dakuna da zasu nuna maka yawan adadin mazauna gidan dake cikinsa.
Tun daga qofar gida,zauruka guda biyu masu girma har zuwa farfajiyar gidan da wani filin tsakar gida da gidan ya mallaka zakasan cewa asalin ginin gidan anyi gine na masu wadata a wani qarni can baya daya shude.
Duk kuwa canzawar siffar ginin zuwa zubin ginin daya dauki shekaru,amma yanayin yadda akayi zuba ginin da kyakkyawan tubali hakan ya hanashi muguwar lalacewa ko muzanta daga suffar kyau zuwa ta tsufa.
Dakuna guda hudu manya manya gidan ya mallaka lailaye da siminti da tsakar gidan ya wadatu dashi da fulasta wadda ke nuna yau ta jima da samuwa a jikin ginin gidan. Kafin idanunka yakai ga duqurqusar matakalar bene dake qarshen qofar daki na hudu a jerin dakunan gidan. Rijiya ce da aka dan dagata kuma aka rufeta da murfi na langa langa. Idan ka sake kai dubanka kuma can zuwa sashen hannun hagu na gidan,bayan ka wuce bishiyar mangwaro data samu muhalli na dindin da Tsakiyar gidan,kai tsaye kana iya hangen qofar da tafi kama data makewaye,da kuma qofar babban kitchen na gidan daya hada kowa da kowa.
Akwai gurabe daga jikin bangon gidan da zai sanyaka ka fahimci a baya akwai wasu shuke shuke da sukayi zamani daga bangwayen gidan,saidai yanzun babu ko wanne tsiro idan ka cire bishiyar dake a Tsakiyar wadda gushewarta ita din ba abu bane me sauqi.
A tsaftace gidan yake ba laifi,wanda kusan gado ne da kuma asali da tsafta daya samo cikin gidan koda kuwa bayan gushewar me gidan da rasuwar mace daya cikin matan aure uku da ma gidan ya mallaka a lokacin rayuwarsa.
Safiya ce sosai,kusan qarfe bakwai da rabi na safe agogo ya nuna a daidai lokacin. Kowacce qofa ta gidan a sakaye take,sai wata qofa guda daya qyaure ta ya banbanta da sauran qyamaren gidan kafataninsu.
Ba zaka gama fahimtar yadda banbancin yake bai tsaya daga qyauren kawai ba.....aah,har sai ka samu nasarar kutsa kanka cikin ainihin falon dake hade da uwar daki kaman kowanne daki na gidan.
Kyawawan labulaye ne da aka yiwa dakin qawanya dasu ruwan toka wadanda sukayi daidai da sofas guda biyu dukkansu 3sitter da aka gewaye falon dasu hakanan suka dace da lallausan daddumar da aka shimfida a tsakaninsu qirar qasar turkiya.
Akwai lausasan pillow guda hudu manya dake zube a qasa dukkaninsu kala daya da labule zuwa kujerun. Daga bangon dakin ta fuskar hagu kuwa,bango ne da yasha wallpaper me kyau aka kuma yiwa TV plasma me matsakaicin girma da reciever dinta mazauni na daban. Gaba kadan dasu 'yar madaidaiciyar AC ce ta tsaye wadda ke amfani da hasken rana da aka yiwa kafatanin dakin wayarin dinsa. Wannan ya sanya koda babu wuta ko ina cikin gidan,koda babu wuta ko ina a unguwar wannan dakin baya rabo da ita. Akwai freezer madaidaiciya itama data dace da tsarin dakin,sai manyan frames masu daukan hankali biyu masu sunayen Allah da ayoyin tsari,biyu kuma masu dauke da zanen nature me kyau. Sassanyan qamshin turaren icce dake zama a daki ya kama labulaye da kujeru da kyau falon yake fiddawa ya zarce kuma har uwar dakin,wanda ya cakuda da qamshin turaren daya zamewa mazauniyar dakin lazim amfani dasu.
Labulen bedroom din aka daga,sannan kuma a hankali ta bayyana hannunta riqe da hijabin yarinyar dake tsaye cikin uniform.
Matashiya ce wadda duka duka a qiyasce shekarunta ba zasu haura ashirin da biyu ke takowa a kasalance.
*_TURQASHI_*
*_BIGI SAI BIGI_*
*_BABBAN GORO SAI MAGOGIN QARFE_*
*_TASTED AND TRUSTED_*
*_TASTED AND TRUSTED_*
*_TASTED AND TRUSTED_*
*_Kina da burin samun ingantaccen TURAREN WUTA me TSANANIN KAMA GURI?_*
*_TURAREN WUTAR DA ZAKI SANYAWA DAKI AMMA HATTA DA LABULAYE KAYAN SAWAN DAKE SAQALE A DAKIN SU KAMA DA QAMSHI?_*
*_TURAREN WUTAR DA KUJERUNKI ZASU KAMA QAMSHI DARAM?_*
*_KI BANKADA LABULAYENKI KIJI SASSANYAN QAMSHI?_*
*QAMSHI IYA QAMSHI 24HR*
*HUMRA ME TSAYAWA A ZUCIYAR ME GIDA*
*NASAN ZAKI TAMBAYI KANKI A INA ZAN SAMU WANNAN?*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER*
*_tayi muku tanadin abubuwa da yawa irinsu_*
Khumra Turaren wuta Kulaccam Lablab Oil perfumes Original musk tahara Multipurpose spray
*karki kuskura kada kiyi ganganci ayi babu ke,kai tsaye tuntubeta ta wannan number*
08032119803
Ko ki lalubeta ta nan👇🏾👇🏾👇🏾
*Instagram handle_incense by kabo daughter*
*Facebook_kabo daughter*
*Twitter_kabo daughter* __________________________
*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*
*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*
*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*
*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*
*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*
*ZAFAFA BIYAR*
*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*
*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*
_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA* *09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪
89825722 Nousaiba lawali maradi 1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰 *D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 13 ___________________________ *_CIKIN DUBU DABAN TAKE_*
*_TABBAS AKWAI TURARE AKWAI MUNA TURARE_*
*_NA GWADA NA GANI_*
*_YA SUBHANALLAHI_*
*_QAMSHI NA TASHIN KAN ME GIDA_*
*_QAMSHIN DAKE DAGAWA KISHIYA HANKALI_*
*_NATACCEN QAMSHI DAKE KAMA GURI DARAM_*
*_WANNE GANGANCI NE YA SAKAKI TSAIWA SANYA?_*
*_ME KIKE JIRA?_*
*WANNAN DIN GUARANTEE NE FA*
*TASTED AND TRUSTED 100% PERCENT*
*KI SIYA KI GODEMIN HAJIYA*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER*
*_DUNIYAR TURARE ME BADA ASALIN QAMSHI ME KAMA JIKI DA MUHALLI,NUTSATSEN QAMSHI ME SANYAYA ZUCIYA DA DADEWA A WAJE_*
*_IDAN KINA DA MATSALA KINA NEMAN TURARE ME KAMA WAJE,KINASON SAKEWA OGA SABON QAMSHIN DAKI DA PARLOR,KE KANKI KINASO KI SHIGA WAJE A DINGA TAMBAYAR WACE TA ISO NE?_*
*MAZA MAZA JEKI KI GWADA WANNAN_*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER 08032119803*
*_zaki dariya za kuma ki godemin_*
*_gani ya kori ji_*
*hakanan sai an gwada akan san na qwarai* ________________________
Sanye take cikin lallausar doguwar rigar bacci me kauri me gajeran hannu off white wanda ta tsaya daidai idon sawunta.